AKWAI LOKACI COMPLETE HAUSA NOVEL
[30/04, 5:37 PM] UMMU AFAN :
Bissimillahir Rahmanir Rahim
Ya Allah kamar yadda nafara wannan novel lafiya kasa nagama lafiya
Wannan novel hakkin ummu afan ne mallakarta ne kuma banyarda wata ta juyashi zuwa nata book dinba
Dedicated this page to
GORGEOUS WRITERS FORUM
GORGEOUS WRITERS FORUM
G.W.F
HOME OF GORGEOUS, INTELLIGENT AND EXPERT WRITERS,
WE ARE THE BEST AMONG THE REST
AKWAI LOKACI COMPLETE HAUSA NOVEL
PAGE 1 to 5
Alhaji abubakar dankoli shahararan Dan kasuwa ne Wanda yashahara gida da wajen kasan nan
Allahji abubakar d'an asalin garin Kaduna ne dake zaune a anguwar tudun wada
Ficeccene a duniya duk inda kuke tunani sunan shi yaje
Alhaji abubakar shikadai ne agurin mahaifiyarshi kuma amma agurin mahaifinsa su goma sha hudune
Mahaifiyarshi amina itace amarya agurin mahaifinsa kuma ita kadai Allah yaba d'a namiji wannan dalili yasa kishiyoyinta suke mugun matsa mata
Bama iya kishiyoyi ba harda 'yan uwan alhaji abubakar duk ba mai sonta kasancewar Allah yawa Dan uwansu arziki
Kofaduwa yayi yamutu suna da kaso mai tsoka acikin dukiyar tunda bashida da namiji
Sai kuma gashi kwatsam ya auro matarshi ta hudu kuma karamar yarinya tahaihu da namiji
Shikuma alhaji shuaib dankoli yayi murnar samun magaji da yayi
Ranar suna yaci sunan Abubakar
Tunda aka haifi abubakar mahaifiyarsa batada ishashan lafiya
Uwargidanta hajiya suwaiba da maibinta suka je gurin wani hatsabibin boka shine yabasu magani sukasa mata a abinci ranar sunan abubakar
Haka tayi ta fama da ciwo
Abubakar na da shekara daya aduniya Allah yayi wa mahaifiyarsa amina rasuwa
Rikonshi yakoma hanun uwargida hajiya suwaiba
Hajiya suwaiba yaranta biyar mata
Babbar yarta rukaiya sai kannata hudu
Rukayya tadau komai na bakin halin mahaifiyarta
Dan haka kawai itama tadauki tsanar duniyar nan ta daura akan abubakar
Gashi duk yadda zasuyi abubakar yabar duniya sunyi amma Allah yace basu isaba
Cikin tsanani da kunci abubakar ya rayu agidan mahaifinsa
'Yan uwan Alhaji shuaib ma sunfi nuna mishi tsana karara
Bayan shekaru 30 abubakar anzama saurayi kuma mai jini ajika
Mai Neman nakamshi duk da yawan dukiyar mahaifinsa hakan baisa ya nade hannu ba
Yayi karatu sosai inda yakai matsayin babban a karatunsa
Bayanwata biyar da kammala karatun professor abubakar ne
Mahaifinsa ya mishi maganar aure yace ba yanzu ba sai yasamu matar da ta dace dashi
Hajiya suwaiba uwargidan allahji shuaib tasameshi da zancen Yakama ta ya matsawa abubakar akan yayi aure Dan duk abokanshi yanzu suna da matayensu
Alhaji shuaib yace mata tunda yace abashi lokaci abashi mana suwaiba
Ran hajiya suwaiba yabaci tace wallahi alhaji kana bata yaron nan dayawa yanzu auren ne sai yagada ma zaiyi
Tashi yayi yabata guri Dan baicika San surutuba
Hajiya suwaiba taje tasamu kishiyarta maibinta tafada mata yadda sukayi da allahji akan abubakar
Hajiya larai tace aikema dai wasa kika tsaya
Mai zai hana muje musami baffa kisan shima mafa ba kaunar yaron nan abubakar yake
Sai muji shawarar dazai yanke
Hajiya suwaiba ta amince da shawarar hajiya larai
Sukayi gidan baffa sunci sa akuwa suka sameshi agida
Nan yazauna bayan sungaisa sukace fada mishi abinda ketafedasu
Yace aikin banza shi shaaibun ne yake daure masa gindin Dan na lura da hakan
amma badamuwa zanyi maganinsu
Zan hada shida hafsat kunga kenan kawar dashi aduniya bazai mana wuya ba
Cikin jindadi sukace hakan ma yayi baffa Dan wallahi muddin yaron nan yana gidan nan fa bawani morar dukiyar Dan uwanku zakuyi
Dan komai nashi abubakar yakesawa akai yanzu kamai na kadarorin alhaji abubakar ne jagoransu
Baffa yace nima abin yana damuna
Komai yazo karshe ita wannan yarin hafsa zata gama mana dashi
Nan dai su hajiya suwaiba murna yakamasu
Sukayi sallama sukatafi gida
Bayan kwana biyu baffa yasamu kaninshi alhaji shuaib da maganar hada yaransu auren zumunci
Alhaji shuaib yace abashi lokaci yayi magana da abubakar tukun
Baffa yace lalle ma shuaibu Ashe maganar da mutane suke fada akanka dagaske ne nawan wai yaronka yafi karfinka
Alhaji shuaib yace yaya kenan
Wannan kuma wani maganane na mutane Wanda idan mutum yanajin irin wannan jita jitar bazaiyi abinkashi ba
Baffa yace kwarai kuwa shuaibu dole kanunamin ban isa da kai ba balle danka
Duk abunda kefaruwa akunnen abubakar
Yashiga cikin falon yadurkusa harkasa yace wa babanshi abbu na amince
a aura min wace baffan yakeso abbu dalilina bazanso kasaba wa 'yan uwan kaba Allah yasa haka shine mafi alkari
Alhaji shuaib yace Allah yamaka all albarka abubakar Allah yarabaka da sharrin duniya da na lahira Allah kuma yakareka daga sharrin mutum da aljan
Abubakar yace ameen abbu
Baffa yace kagani ba Dan naka ma yafika hangen nesa idan bamu hadasu zumunci tun yanzu sai bayan ranmu zasuyi
Alhaji shuaib yace tunda ya amince ai shikenan
acikin yaran nawa
Wacece za ahadsun
Baffa ya wage baki yace hafsatu mana
Alhaji shuaib yace Allah yasanya alkari
Sukace amin
Baffa yace saika shirya kaje kufahimci juna ko abubakar
Abubakar yace insha Allah baffa zanyi kokari naga nasamu lokaci naje
Baffa yace yauwa hakan ma yayi kyau
Yace nizanwuce
Abbu yace tun yanzu yaya
Baffa yace tunda nayi abinda yakawoni zama ai banawa bane
Abbu yace hakane kagaida gida yace gida zaiji
Bayan tafiyar baffa abbu yakalli abubakar yace nidai hankali na baikwanta da wannan auren ba abubakar
Abubakar yayi murmushi yace karka damu abbu kasa albarka kawai aciki
Hajiya suwaiba da kishiyarta hajiya larai sunji dadin wannan Abu koba komai idan abubakar yamutu suna da kaso maitsoka cikin dukiyar alhaji shuaib
Hafsa yarinyace ga baffa kuma itace babbar yarshi
Hafsat kyakkyawace ajin farko Dan danginsu sungaji kyau ne Dan shima Abubakar ba bayaba gurin kyau
Hafsat tana da zafi Dan ita bata son raini ko kannata ba kasafai tafiye sake musu fuska ba Dan karsu rainata
Ko a school ba mai taka ta barshi sai dai kuma tana da wani hali Wanda ko agidansu ba asanta nadashi wato tausayi da son 'yan uwanta
Kwatata bata nunawa dan tasan halin iyayen nata
Lokacin da zancen hadasu aure da Abubakar yazo kunnen ta hafsat tayi murna sosai
amma sai ta bar abinda acinkinta
Ba Wanda ya fahimceta
******
Bayan auren abubakar da hafsat tun abubakar baya kulata irin kyautatawar da take mishi yasa yafara sakin jikinsa da ita
Soyayya sosai suke inda kasan auren soyayya sukayi
Bayan shekara daya da aurensu
Ranar asabar hafsat tana zaune kusa da abubakar tasa mishi ido kawai tana kallonshi yace yadai madam
Tace wallahi dama sonake kabarni naje gida na wuni yau kaga nafi wata banjeba
Abubakar yace shikenan bukatar tace shikenan
Da kanshi yashirya hafsa ma ta shirya suka shiga mota yajasu sai gidansu su hafsat
Suna zuwa yasauketa yabata kudi masu yawa yace tashiga shi sai yazo daukarta zaishiga
Tace Allah yadawo da kai lafiya
Yace ameen matar kirki tayi murmushi tashiga gidansu
Kannanta na murna ga adda hafsat ga adda hafsat tayi murna ita ma da ganinsu
Taci sa akuwa YAU suna da babbar bakuwa wato rukayya babbar yarinyar hajiya suwaiba
Wato yayar abubakar kenan
Nan akagaisa Rukayya tace anya hafsat kina amfani da maganin da akebaki kizubawa abubakar a abinci
Maman hafsat dinta ce nima dai abin yadameni wallahi ace duk wata sai munkashe makudan kudi akan sa munkarbo maganin
amma sai muji sajinkanya kuwa kina yin yadda akesaki kuwa
Hafsat ta zumburo baki tace inayi mana kawai dai shifa yana da addua sosai ajinkinshi Dan infada muku gaskiya ma baicika bacci ba saboda makiyansa
Rukayya tace a lalle wato mune ma makiyansa ko
Ashe bakida kunya hafsat
Hafsat tace kai nifa barin fito muku a mutum ina son mijina
Kuma koda banasonshi bazan taba kashe mutum ba balle ma Dan uwana kuma mijina
Salati sukasa tare da tafa hanu suna salati cikin tsananin kaduwa da maganar hafsat dasukayi
Hafsat batayi aune aune ba taji saukar bugu kota inta
Bakowa bane yake dukanta illa mahaifinta baffa yace ai wanna yarinya da haihuwarki gwamma barinki
Ashe bakya son cigaban mu kinje soyayya ya rufe miki ido ko
Maman ta tace to wallahi ko kiyi abinda mukace ko na tsine miki
Cikin tsananin tashin hankali hafsat tace mama babu biyayya ga aikata sabo
Barin taba aikata abinda kukeso ba sai dai kuhada dani da shi kukashe gaba daya
Nan ma baffa da maman ta suka rufu mata da duka dakyar rukayya takarbeta
aikuwa tana samun anbarta tadauki Jakarta da gudu tabar gidan takal manta a hanu
Tayi bakin titi ta tari keke nafef
Sai gidanta tana shiga tayi dakinta tayi kuka mai isarta kafin
Ta bakanta hakuri takudiri aniyar koza a kasheta bazata barisuyi galaba akan abubakar ba
Takira abubakar tafada mishi ya wuco gida kawai tadawo
Yana zuwa yasameta ba kaman yadda suka rabu ba
Yace meyasameki madam tace bani da lafiya ne shiyasa ma baffa yace na dawo gida
Yace ashsha maza tashi muje asibiti
Tace a a basainaje asibiti ma jikinda sauki yace shidai baiyarda ba
Bata son mishi gardama sosai
Cikin ikon Allah kuwa kitoci sukayi mata tambayoyi
Tayi ta bada na karya
Daga karshe dai suka mata pregnancy test aikuwa aka sameta da ciki na sati hudu
Itakam ma bata sani ba Dan bata laulayi komai
Cikin farinciki abubakar yayi wa Allah godiya
Bayan sundawo gida ne abubakar yatafi hargidansu yafada wa abbu mahaifinsa cewan hafsat na da ciki
Abbu ma yayi murna sosai daga karshe yayi fatan alkairi
Labarin cikin hafsat yabaza ko ina duk dangi asan da cikin dake jikin hafsat
Hajiya suwaiba da kishiyar ce cikin tashin hankali suke tattaunawa
Hajiya suwaiba tace amma larai kinsan baffa ya mugun raina mana wayo
Hajiya larai tace nima nayi tunanin haka kinga gashi yarinyar zata haihu idan ta haihu musamman akasamu namji fa shikenan kashin mu ya bushe
Shikuwa baffa jika za ahaifar mai kinga koba komai za anfana tanan
Nan dai suma suka hau kulla kullansu
Bayan wata tara hafsat tahaifi danta kyakkyawa namiji fari Sol dashi kaman atsaga jini yafito
Yaro sonkowa kin Wanda yarasa
Ranar suna yaro yaci sunan ABDUL HAKEEM
ana kiransa da HAKEEM
Hakeem yataso cikin soyayyar iyayensa ga wayo ga farinjini
Tako inta Hakeem ya hadu
Mujezuwa taku ummu afan ce
Sai mun hadu a next page
Comments & share
[30/04, 5:40 PM] UMMU AFAN :
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN
DEDICATED THIS PAGE TO UMMY KHALEEL
GORGEOUS WRITERS FORUM
G.W.F
HOME OF GORGEOUS ,INTELLIGETAND EXPERT WRITERS
WE ARE THE BEST AMONG THE REST
AKWAI LOKACI
PAGE 6 to 10
Please masu karatu karku rikice shuaib shine baban alhaji abubakar
******
BAYAN SHEKARA ASHIRIN
Hakeem yaro Dan kwalisa Wanda yagaji kyau tako ta ina kama daga kan uwa uba dangi da dai sauransu
Duk wani kulla kulla yafaru acikin shekaru ashirin nan
amma Allah bai ba wa makiyan alhaji abubakar nasaran cin galaba akanshi
Tare da gudumawar uwargida ran gida hajiya hafsat
Kwatata taki bada hanyar da za a cutar mata da miji ko danta
Dan yanzu mahaifinta wato baffa ya saduda tunda yaga samu tunda an Haifa mishi jika namiji
Hajiya suwaiba tare da hajiya larai sune basu yarda ba su sai sunga bayan alhaji abubakar da iyalanshi
Yayar alhaji abubakar wato hajiya rukayya itama fa tana nan akan bakanta
Naganin kanin nata yabar duniya da iyalansa
amma hakan ya gagara .
Hajiya hafsat zaune makeken falonta tana duba wani littafin ahalarine
Sai taji sallamar dan nata Hakeem
Tadaga kai ta kalleshi tace Dan albarka yace na am abin alfaharina ki tashi lafiya ,
Hajiya hafsat tace lafiya qalau Dan albarka daman kainake jira kamin dauri akan inda nake jiya
Hakeem yayi murmushi yace da fatan dai d'alibartawa zata kawo hadda
Idan bata kawo hadda ba yau ba dori
Mummyn shi tayi murmushi tace tunda kaga yau baka kirani ba kaima nakejira aikasan nawuce gun
Hakeem yayi murmushi yace a a fa mummy bagirin girin ba tayi mai fa
Mummy tace mai sosai makuwa
Yace muje zuwa inajinki d'alibata
Nan mummy hafsat tafara karatun da ya Dora mata najiya tiryan tirya.
Tana gamawa yace allahuakbar yaufa gaskiya daliba tayi kokari
Nan yaci gaba da Dora mata
Duk abinda suke daddynshi abubakar yana kallonsu cike da sha awa
Dan Allah ya daura mishi son iyalanshi da
Akullum ya kallesu yana godewa wa Allah daya bashi family kaman Wanda yake dashi a yanzu
Yana alfahari da hafsat
Saukowa yayi falon tare da sallama Hakeem yaje ya Rungume dad din nasa
Dan kullum haka suke gaisuwa kaman wasu larabawa
Baban yace Allah yamaka albarka Hakeem
Mummy tace ameen daddyn Hakeem
Nikam ina da tambaya daddyn Hakeem yace inajinki mummyn Hakeem inajinki yi tambayarki
Tace kullum saika tasawa Hakeem albarka Dan wani lokacin sainaji jikina yana sanyi saikace mai bankwana
Alhaji abubakar tayi murmushi manya yace hafsat kenan a duk lokacin da kalli Hakeem inajinsane harcikin raina kullum son d'ana karuwa yake acikin zuciya
Sai nakeganin ba Kalmar da dace dashi sai aduk lokacin da na kalleshi nasamishi albarka
Daddy yace tukun nama badai kishi kike bako
Mummy hafsat tayi murmushi tace kishim ma ai sainayi daddyn Hakeem kafin na haifi Hakeem duk ni kama irin wannan abubawar amma tunda aka haifeshi karage
Komai naka Hakeem
Hakeem yayi dariya yace wato ma d'aliba kishi kike dani ko zamuzo karatu zan fanshe ai
Daddyn Hakeem yayi dariya yace gaskiya kam yakamata kadau mataki
Mummy hafsat tace inkuwa hakane Nima saina dau maki
Nima Baku abinci d'an kadan
Kasan danka da ci kaman gara
Gashi bayacin abincin kowa sai na mummyn shi
Haka dai sukayi ta hira cikin nishadi
Hakeem tun yana shekara shabiyar yagama secondary school
Kuma ashekarar mahaifi sa yakaishi Saudi Arabian karatu ,
Duk shekara Hakeem yake da wowa gida Hutu.
Wannan shekarar ma yadawo ne har yanasa ran komawa nan da sati daya
Islamic law ne acan saudiya
Karatu yake sosai bakama kafar yaro wancen da wowar dayayi ne yayi service dinshi a
Kano
Kafin yakoma Dan hado degree dinsa nabiyu wato masters
Yanzu yake da shekara ashirin aduniya cas
Hajiya rukayya yayar alhaji abubakar suna zauna da mahaifiyarta
Tazo gida tace nikam hajiya maizai hana muhada su Hakeem da laila aure
Kinga dai laila kam kanwar lasa bace zata iya komai akasata
Hajiya suwaiba tace amma kinsan baza a wa Hakeem aure yanzu bako
Duka duka fa shekararsa ashirin
Kuma kakansa ya yarda ko babanshi ya yarda kinsanshifa da taurin rai
Dakyar ya yarda aka aura wa abubakar hafsat
amma Kinga yadda tazama bata jin maganar kowa
Hajiya rukayya tadubi uwartata tace hajiya tunda kekika rike abubakar ,
Ki aika akira miki shi kinsan shi da biyayya har kuka kisamishi akan lalle kina son a hada auren laila da Hakeem inyatashi komawa karatu yatafi da matarshi ,
Kinga idan kika gama kama kafar abubakar na Abba ba maiwuya bane saboda Abba yana son abubakar Kuma yana jin maganar shi ,
Hajiya suwaiba tace naji dadin wannan shawarar taki rukayya
Allah yamiki albarka 'ya mai kishin uwarta ,
Nan hajiya rukayya tace wa uwarta zata wuce gida dan taje tasamu laila tafara gaya mata abinda suke shirin yi .
Alhaji abubakar yana office dinsa na kasuwancinsa dan tunda yayi karatun shima har zama professor Sai yazabi da yayi kasuwanci
Kuma alhamdullila komai yasamu asanshi gida da wajen kasan nan
Yana zaune bayan sun gama meeting yaga kiran matar baban nashi wato hajiya suwaiba
Ta shaida mishi tana son ganinshi
Cikin girmamawa yace insha Allah yanzu zaizo
Wacece Laila
Laila 'ya ce agurin hajiya rukayya yayar alhaji abubakar
Laila ta taso cikin gata ga tabara bairin wacce batayinsa
Laila duk wani halin rashin mutumci takwashe tsaf na uwarta da kakanta hajiya suwaiba
Shekara daya ne a tsakaninsu da Hakeem amma saboda son zuciya irin nasu hajiya suwaiba da 'yarta suke kokarin hadasu aure.
Lokacin da hajiya rukayya tasamu 'yartata da zancen auren Hakeem bakaramin murna tayi saboda Hakeem tun bai kai koina ba billionaire ne
Dan komai na mahaifinsa nasane kowa yashaida hakan so ake kawai
Yagama makaranta adanqa mushi komai a hanunshi shiyasa takesonshi
Dan kudin shi Kuma laila tana ganin akan kudi zata iya komai ciki kuwa harda kissa
Dan haka taba uwarta rukayya goyan baya Dari bisa Dari
Hajiya rukayya tasan dama bazata samu matsala da 'yartata ba sanin halinta datayi"
****
Hajiya suwaiba ta zauna da alhaji abubakar tace tana son taroki wani alfarma agunshi Allah yasa zai iya mata alhaji abubakar yayi murmushi yace haba hajiya kema uwatace Ba alfarma a tsakanin mu Sai umarni ,
Umarni kawai Zaki bani na aiwatar
Cike da jin dadi hajiya suwaiba tawage baki tace Allah yamaka albarka abubakar
Yace ameen hajiya
Tace daman 'yar uwarkace tace maizai hana kuhada yaranku aure wato Hakeem da laila kaga za adada karfafa zumunci atsakanin mu ko yajagani
Cikin tsananin mamaki Alhaji abubakar ya kalli hajiya jin abinda tace
Yace hajiya aure fa kikace duka duka Hakeem din gudawa nawa yake yanzu fa yake ashirin hajiya gwamma ita lailar ta kai amma shifa namiji ne hajiya ai dasauranshi
Hajiya suwaiba tace inbanda abunka baka so muga 'ya'yan jikokinmune ai gwamma tun kan kasa ya rufe mana ido muga munbar baya ana zumunci a tsakani
Tace amma daman shawarane ba umarni dan nasan ban isa nabaka umarni ba tunda bani na haifeka ba saita fasheda kuka
Cikin tashin hankali Alhaji abubakar yace kiyi hakuri kidaina kuka na amince da bukatarki
Allah yasa haka ne mafi alkairi agaremu baki daya
Tace Allah yamaka albarka abubakar wallahi yadda kake min biyayya ko 'ya'yan Dana Haifa basa min haka
Allah yajikan Amina mahaifiyarka ya haskaka kabarinta
Abubakar yace ameen
Nizan wuce hajiya tace to yaushe zaka samu baban naka da maganar yace badamuwa gobe zandawo
Ya wuce cike da jin tausayin dan nashi a wannan shekarun zai hada damuwar mata akansa ""
Bayan yakoma gida ya huta
Ya ce hajiya ina Hakeem tace aitunda kuka dawo daga isha banganshiba baishigo ba alhaji yace OK namanta
Yana ganawa da wasu committee na gidan marayu
Nisuka zo gani nace yaji abinda suke bukata Sai yafada min
Mummy hafsat tace Allah sarki gaskiya daddyn Hakeem kana kokari Allah yakara budi
Kafin daddy yace wani Abu Hakeem yayi sallama yashigo bayan ya zauna yafada mishi yadda sukayi da committee din marayun
Sai dadddy yace dama inason zamuyi wata magana mudiga uku
Duk suka bada Hankalinsu ga abinda daddy zaice
Nan yafede musu biri har wutsiya
aikuwa Hakeem cikin tashin Hankali yace aure kuma daddy at this age of mine
No impossible Daddy
Mummy hafsat tace kwantar da Hankalinka babu Wanda ya isa maka aure a wannan shekarun
Wallahi basu isaba su samu a damuwa ba
Indai ni hafsat inaraye inkuna nasamu goyon bayan mahaifinka
Ta nuna daddyn da han nunta """
Muje zuwa fans'
Naji dadin comments dinku a first page dina ina alfahari da Ku masoya akwai lokaci
Please your comments is needed naji comments dinku
[30/04, 5:42 PM] UMMU AFAN :
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN
I DEDICATE THIS PAGE TO AKWAI LOKACI FANS'
MUCH LOVE TO YOUR COMMENTS
GORGEOUS WRITERS FORUM
G.W.F
HOME OF GORGEOUS, INTELLIGENT AND EXPERTS WRITERS WE ARE THE BEST AMONG REST.
AKWAI LOKACI
PAGE 11 to 15
Alhaji abubakar yanisa yace abin duk baikaiga haka ba hafsat
Nasanki da biyayya da jin magana ina son kubani goyon bayan akan wannan abun da hajiya takeso
Zata ga kaman dan ba ita ta haifeni bane yasa na kibin umarninta
Hajiya hafsat tace amma alhaji HAKEEM guda nawa yake da za ace wai za amishi aure yanzu
Gaskiya dai nasan wannan auren
Bana Allah da annabi bane auren manufa ne kawai dan sucinmma wani burinsu na daban
Alhaji abubakar yace ina son kidinga kyakkyawar zato akan mutum kuma kisa wa abin albarka a matsayinki na uwa
Kuma ai Hakeem namiji ne ko awani lokaci zai iya kara aure a lokacin dayake bukatar hakan
Wannan kawai kutai maka kubani goyan baya nasamu ladar zumunci
Hajiya hafsat tace amma dai kasan yaya rukayya ba sonka take bako
Tayi hakane dan kawai tasamu hanya ta cucemu
Daddy yace a musu kyakkyawar zato
Shidai Hakeem tunda yasaukar da kansa kasa baisake dagowa ba
Dan yadda yakejin zuciyarsa kaman zata bugs
Hajiya hafsat tace kuma ma arasa yarinyar da za ahadashi da ita Sai wannan Mara kunyar yarinyar da ita kanta yaya rukayyar ma bata barta ba
Alhaji abubakar yace shina mijine ai zai gayrata
Yadda yakeso ta zama
Hakeem dai yace Sai dasafenku
Daddyn yace harzaka bacci son
Hakeem yace a daddy
Ya kalli mummynshi yace mummy Sai da safe
Tace Allah yatashemu dan albarka
Daddy yace bakace min komai ba zakatafi bacci
Hakeem yace duk abinda kayi dai dai ne kawai daddy bazaka taba umartata akan Abu nakasa yima ba koda kuwa ni banasonshi
Ya wuce yatafi zuwa dakinsa
Alhaji abubakar yace masha Allah
Allah yayi gaskiya kabi iyayenka kaima za a bika
Kinga abinda nayi wa mahaifina nima nawa d'an yadawomun dashi ,
Hajiya hafsat tace hakane daddyn Hakeem gaskiya Allah yabamu d'a nagari fatanmu kawai shine
Allah yarabashi da sharrin makiya .
amma wallahi wannan aure na Hakeem bai kwanta minba kokadan
Haka dai sukayi ta tattaunawa tsakaninsu .
HAKEEM bayan yakoma dakinshi yashiga duniyar tunani yace tabas gaskiyar mummyn shine auren manufa zasuyi ,
Dan yadade da gane 'yan uwan mahaifinsa basa kaunarshi koka dan ,
Inba haka zasuce wai za a hadashi aure da yarinyar da bata da mutunci batada tarbiya ,
Nifa idan asona nane sai nan da shekara goma sha nayi aure ,
Dan sai tsaya na zaba matar da ta dace da rayuwata ,
amma idan tasake tashiga rayuwa ta a yanzu zan nuna mata waye ABBULHAKEEM
zata San koni waye duk wani shige da ficen dangin mahafin nasa yasani sarai
Dan haka yadauki aniyar yiwa mahaifinsa biyayya
Sai zai nuna musu shidin namijine wato dangin mahaifinsa kenan
Haka dai Hakeem yayi ta sake da warwara
Washagari da safe bayan Hakeem yagama break fast ne yadauki phone dinshi yakira Ahmad
Abokinsa yace kana inane ahamad yace ganin agida
Hakeem yace OK ganin nan shigowa gidan """"'
Ahmad abokin Hakeem kud da kud dan tare sukayu primary da secondary school
Kuma tare sukatafi makaranta a Saudi Arabian tare suke dawowa Hutu ,
Hakeem da Ahmad basa boye wa juna sirrinsu kokadan
Komai nasu tare sukeyi dalilin hakan yasa iyayensu sanin juna har ake zumunci sosai ""
HAKEEM yayi parking a harabar gidansu Ahmad
Kai tsaye ya wuce part din Ahmad yana shiga yafada kan kujerar falon Ahmad din
Ahmad yace ya man yanaga duk kayi wani iri meyake faruwa ne
Hakeem yaja dogon numfashi yace kaidai bari man wallahi so ake a hada min zafi agida
Ahmad yace zafi kuma kaman yaya
Ahmad yakwashe komai yafada wa Ahmad
Ahmad yayi dariya sosai yace to ai kai Allah ya kashe yabaka tunkana very young dinka zaka angonce ni wallahi banga abinda damuwa Ba
Tunda Ahmad yafara magana Hakeem yake kallonshi dan yabashi haushi sosai
Yace wato dariya ma nabaka ko
Ahmad yace dariya kabani mana kaida za ama auren gata
Ahmad yace amma fa ina tausayawa yarinyar saboda by the time din kake cikin samartakarka by then itakuma bayadda takaraji fa dan tazama baba
Hakeem yace kai man har ka mata lissafi kasan ko yar ten years za abani
Ahmad yace ai nasan baza a tabaka yarinyar da bata wuce goma Ba
Kaga kuwa may be 16 to 17 years haka
Kagakuwa ai kafin nan da wani lokaci tazama mama
Hakeem yace duk ma baka zogunba
Todai yarinyar shekara daya nabata a duniya
Ahmad yace cab wallahi hartabani tausayayi dan nasan bayadda za ayi kazauna da ita kadai a lokacin da samartaka yazo maka
Hakeem yace kaji dan rainin hankali yanzun wanene idan ba saurayin Ba
Ahmad yayi dariya yace sau dai baka kai rayi dinba
Hakeem yadauki trowing pillow ya jefeshi dashi
Yace kaiko nazo nafada maka damuwa ta memakon kakwantar min da hankali sai kuma bige da da yimin shiririta ko
Ahmad yace to naji abikona yanzu dai kasan muhimmancin bin umarnin iyayeko dan haka kawai kabi maganar daddy insha Allah komai zaizo dasauki
Ya da amaryar zamuwuce ne Hakeem ya yatsina fuska yace Allah yasauwake natafi da ita akanme
Ahmad yace ya hakuri maida wukar
Yanzu dai katashi mushiga cikin gida kugaisa dasu mummy
Sai muwuce sallar azahar ko dan naga time yayi .
Alhaji abubakar yasamu mahaifinsa alhaji shuaib akan maganar dasukayi da hajiya suwaiba
aikuwa alhaji shuaib yace baisan San zance Ba
Yace waini abubakar sai yaushe za abarka kayi abun kankane
Kai an baka mata batareda son rankaba ka karba sakamokon biyayyar da kayi Allah yasa kadace da mata tagari
Sai kuma yanzu andawo kan danka
Wanda shi ko auren ma bai isaba ance za abashi mata
Hajiya suwaiba tafito daga dakinta tana cewa haba alhaji ai nagani yaran nan fa duk jikokinkane daga ita lailar har Abdulhakeem din
Idan akayi wannan aure sai munfi kowa farinciki
Kaga ai tuwona maina kenan
Alhaji shuaib yace yanzu Nagano kekika kitsa komai suwaiba
Hajiya suwaiba tace a nice alhaji ganinayi da abubakar da rukayya ai duk 'ya'yanane
To ina laifi dan nace suhada yaransu aure tunda sauran numfashin mu muga hakan
Alhaji shuaib zaiyi magana abubakar yace dan Allah Abba maganar yawuce kawai ka amince kawai da bukatarta
Alhaji shuaib yanisa yace yanzu Abdulhakeem din ya amince
Abubakar yace namishi magana tunjiya kuma ya amince
Alhaji shuaib yace banyardaba katuromin shi idan bayason auren ba maiyi mashi dole ..
Bayan kwana biyu Hakeem yayi shiri tsaf ya wuce gidan kaman nasa alhaji shuaib
Yana shiga falon gidan yasamu kakan nasa yana zaune yana kallon sunna TV
Sai yace a a tsoho mairan karfe an kura wa TV ido kaman kanagani da gaske
Alhaji shuaib yace aikuwa dai idona yafinaka naka karfi dan tar nakeganin ka
Hakeem yayi dariya yace fadi gaskiya dai kakus
Alhaji shuaib yace yanzu dai Ba wannan
Maganar da kuka yi da mahaifin ka nakeson naji ka amince ne ko baka aminceba idan baka amintaba Ba zanbada goyon baya amaka doleba amma idan ka amince shikenan Allah yasa albarka
Hakeem yayi shiru dan dai kawai yariga yayi wa mahaifinsa alkawarin amincewa ne
Nan yace na amince kakus
Alhaji shuaib yace Allah yasaka albarka
Sannan kuma ina maka albishir da cewan duk lokacin da zuciyarka yabaka kanason auren zabinka kana da dama yin hakan
Dan wannan aure ne kawai na hadi nasu na daban
Harcikin ran Hakeem yaji dadin maganar tsohon yayi wata dariya Allah yakara maka Nisan kwana kakus dina na kaina kaga irin wacce zanzabo a matsayin mata
Kakan yace Ameen dan albarka Allah yasa muna raye muga wannan rana
Hajiya suwaiba tashiigo taji duk abinda suke fada
Cike da isa tace wa alhaji shuaib aidai kabari ayi wannan din kafin afara zancen wata
Hakeem ganin shigowar hajiya suwaiba yasa yadaure fuska yakoma Hakeem dinsa
Danshi Sam jinin bai hadu da matar kakan nashi Ba
Ganin haka yasa yace sai anjima kakus zan dawo muyi hira na musamman
Batareda yakalli inda hajiya suwaiba take ba
Yace ina wuni hajiya
Baijira amsawarta Ba yayi hanyar waje
Tabishi da harara tace inan daku ai
Zamu hadu a karo na biyu ne
Laila da mahaifiyarta sunan suna ta murnar samun nasara
Dan ansa sati nan sati daya saboda komawar Hakeem school
Mummyn Hakeem kam batayi wani gayya Ba dan ita wannan auren ba aure bane agurinta
Duk lokacin da yakawo matar da zai aura alokacin ne zata yi nata bikin
Zata nunawa dunniya sai a lokacin dan yayi aure
Next page
Your comments is needed fan's
Much love to your comments
[30/04, 5:46 PM] UMMU AFAN : BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN
I DEDICATE THIS PAGE TO MY LOVELY MOM
MUCH LOVE TO YOU MOM
NO ONE LIKE YOU IN THIS WORLD❤❤❤
GORGEOUS WRITERS FORUM
G.W.F
HOME OF GORGEOUS, INTELLIGENT AND EXPERTS WRITERS WE ARE THE BEST AMONG THE REST
AKWAI LOKACI
PAGE 16 to 20
Hajiya suwaiba da hajiya rukayya kadai suke kidansu kuma suke rawar su
Abin yana basu haushi ganin Ba Wanda yake shiri akan bikin
Sai dai dayake suna ganin dazarar anyi auren shikenan
Zuriar alhaji abubakar sundawo hanunsu dan sai yadda suka juyasu
amarya laila ta gayya ci kawayenta sosai dan halartar bikinta
Maman amarya hajiya rukayya ce tazaunar da ita tace wai ke yau saura kwana biyu biki amma baki tambayi shi Hakeem din kudin dazakiyi hidima dasu Ba
Laila tace hmm mama kenan to ina managanshi ballantana har na tambayeshi kudi
Hajiya rukayya tace lalle ma yaron nan ya raina wa mutane hankali amma zai shigo hanunmu ne ai
Yanzu abinda nakeso dake kitashi kidauki kawarki daya tarakaki zuwa gidan su Hakeem din
Kikarbo kudin dazakiyi Hidima dasu
Laila tace wannan ma shawara ne mamana yanzu kuwa zan tafi
Haka laila tadauki biky daya daga cikin kawarta taraka zuwa gidan su Hakeem
Laila shiga tayi cikin wasu Riga da wondo parkistan Wanda siririn gyalenta tayafashi akan gashin dokinta dayazubo mata har gadon bayanta
Ga farce da akasa musu duk ita da kawar tata kana ganinsu kasan dai Ba tarbiyya
Laila tana parking cikin gidan su Hakeem tashiga direct zuwa falon gidan
Tana shiga ta tarar da hajiya hafsat mom din Hakeem zaune kan two sitter tana kallon tasharta na MBC 4
Mummy hafsat kawai ganin mutane tayi tsakiyar falo batare da sunyi sallama ba
Tadaga kai takallesu suka hada ido da laila
Laila cikin rashin gaskiya tace mummy ina wuni wallahi banganki bane nazo gurin Abdul Hakeem ne
Mummy hafsat tamusu wani kallon takaici tace Ku wasu irin marasa tarbiyar yarane dazaku shigo gida Ba sallama ko haka aka koya muku agidajenku
Cikin in ina laila tace sorry mom please ina Hakeem yake muna sauri lokaci na kurewa
Cikin tsanin mamaki mummy hafsat take kallonsu laila da suke tsaye kikam kaman andasasu suna karkada jiki
Mummy hafsat tace nikuke wa rashin kunya laila ankuwa fada miki halina
To kikoma kitambayi uwarki wacece ni idan ita ta turoki kimin rashin ni ina dai dai da lokacinku
Kuma kije kifada wa uwarki dan tana yar mijina hakan bazai bata dama hakan bazai bata damar saku kuzo harcikin gida kuna min dibar albarka Ba
Ita tasan wacece ni niba kanwar lasa bace
aikuwa daga Laila har biky kawarta sun tsorata da yanayin mummy hafsat
Mummy hafsat tace kubace min daga gida yanzun nan insake ganin kafarki agidan nan kiga abinda zaifaru
Da gudu suka fice agidan kuwa harsuna tun tube
Suna zuwa parking space
Zasu shiga mota sai ga motar abdulhakeem aikuwa Laila washe baki tayi tace biky Gashi nan fa biky tace waw wannan
Zazzafar motar shice
Laila tace kadan ma kika gani indai Hakeem ne kinga zomuje musameshi karyashiga
Hakeem kuwa shida Ahmad ne
Ahmad yace wa Hakeem ya kaman kunyi baki Hakeem yace maikagani
Ahmad yanuna mashi su wurinsu laila
Hakeem yakai idonshi gurin
aikuwa yana ganin sun nufosu yadaure fuska
Ahmad yace kai harda bakin ma zaka nunawa halinka ko
Hakeem dai baice komai
Laila suka karaso gurin su Hakeem din
Sai Ahmad yadan durkusa yace anty ina wuni
Cikin tashin hankali Laila tace wace ce antyn taka
Ahmad yakalleta cikin rashin mahimta danshi yadauka yayar Hakeem ce dangin su
Danshi baitaba sanin laila Ba tunda Hakeem bazuwa yakeba
Abin yaba wa Hakeem dariya amma yaci fuska sosai dan kar laila taga hakorinsa da sunan dariya
Yarufe motarshi ya kalli Ahmad yace mujeko
Laila ta tari gabanshi tace haba Abdul kasanfa gurinka nazo ko
Hakeem yakalleta ya watsamata wani mummunar kallo yace gurina kikazo namiki me
Abin yaba Laila haushi dan ya tsinkata agaban babbar kawarta
Ta daure tace naga har yanzu baka zo gida munyi maganaba kuma baka kuma tambayeni abinda nake bukata na game da harkar bikinba shine mama tace nazo nakarbi kudin dazan yi hidima dasu
Sai a lokacin Hakeem yayi wani killer smile yace lalle kuwa bazakiyiba
Kikoma gurin wacce ta hada abin sai tabaki
Nikam kwandala ta bazaiyi ciwo akanki Ba
Nan ya wuce ta Ahmad yabi bayansa suka shiga cikin gida
aikuwa da gudu Laila tafada mota
Dan tunda take Ba a taba wulakantata irin wannan Ba
Kawarta biky tayi ta rarrashinta kasa driving tayi biky ce tayi
Hakeem da Ahmad suna shiga falon mummy
Suka ganta zaune kan kujera
Hakeem yasaki murmushi yace mummy na yadai naga kaman antaba minke
Ahmad yanemi guri yazauna yace mummy an wuni lafiya
Cikin fara a mummy hafsat tace lafiya qalau Ahmad ya su hajiyartaka
Ahmad yace lafiya qalau tace zata zo anjima
Mummy hafsat tace aikuwa kaman tasan inason ganinta Allah yakawo ta lafiya
Hakeem yace mummy shine wato kinga Ahmad ina miki magana kina wani basarwa ko
Mummy tayi murmushi tace ai matarka ce taba tamin rai shiyasa
Hakeem yadaure fuska yace daliba zakifara ko
Mummy tayi murmushi takalli Ahmad tace Ahmad katayini da abokinka dan Allah matarshi tazo ta bata min rai dan Allah basai na huce akanshi Ba
Ahmad yayi dariya yace kinyi dai dai mummy
Tace a to kaima kafada dai
Hakeem ya harari Ahmad ya kalli mummy yace daliba bazaki daina kiran wannan Mara kunyar yarinyar da mata ta bako
Mummy hafsat tace toya zamuyi komunki ko munso sai anyi
Nan tabasu labarin yadda sukayi da su Laila dasuka shigo
Hakeem yatashi ya suri key din motarshi yayi hanyar fita
Mummy hafsat tace dagata dan albarka ina zaka yace mummy kibarni naje naci ubanta har tana da gost da zata zo gidan nan tasaki magana haka
Mummy hafsat tace kalesu nima din ai sunsan wacece ni zata je tafada wa uwarta
Zasu sake sabon shiri mu basusan shirinmu yafi nasu dan muda Allah muka dogara
Hakeem yace wai mummy maiyasa daddy yakasa gane mutanen basa kaunarshi Ba sonshi suke ba fa
Mummy hafsat tace nima abun yana damuna wallahi hakurin mahaifinka yayi yawa wallahi
amma bakomai duk mai hakuri wataran yana tareda riba
Mummy tace kutashi kushiga kuci abinci
Suka tashi zuwa part din HAKEEM
Suna shiga dariyar dayake cin Ahmad yafito dashi
Yayi sosai Hakeem yace wai kai kuma wakake wa dariya
Ahmad yace wallhi matarka da nacewa anty
Hakeem yace karkasake cewa matana kace kawai matar kaddara
Ahmad yace narki gaskiya man na tausaya ma wannan yarinyar wallahi kokadan wallahi bakuyi marching ba kokadan
Da zanbata shawara data nemi mijinta a wani wajen tabarka
Hakeem yayi dariya yace akai man shine wannan dariya haka amma nima naso nayi dariyar Dan bakaramin dariya abin yabani ba
Kawai dai banson rainine yasa na make kawai
Ahmad yace oh baruwana fa randa zaka angonce ina ina Dan haka nayishiru Allah yabada zaman lafiya
Tsaki Hakeem yayi yace katashi muje muci lunch idan kuma baka gama surutun ba to
Nan dai sukayi hira amma Rabin hirar tsokanane Ahmad yakewa Hakeem
***
Bayan komawar su Laila gida tana kuka tana bawa mamanta labarin abinda mummyn Hakeem da Hakeem din suka mata
Ran hajiya rukayya yabaci
Tadauki waya takira uwarta hajiya suwaiba ta fada mata komai abinda Laila tafada mata
Nan itama hajiya suwaiba ranta yabaci tace bakomai ai sunkusa shigowa hanunmu
Tayi hidimarta da kudinta kawai zata fanshe ai
Hajiya ruakayy tace amma hajiya kinsan wallahi bakudi a hanu na sosai
Hajiya suwaiba tace kwantar da hankalinkki
Kituro min ita jikallen sai nabata wasu kudi
Nan hajiya rukayya tayi godiya ga mahaifiyarta kafin takashe wayar takalli 'yartata dake kukan wulakancin da akamata
Tace kidaina kuka kitashi kitafi gidan hajiyata zata baki kudi konawane sai kufara hidimarku na kawaye
Nan Laila ta washe baki tace kai Allah yabarmin kakallena yanzu ita zata bani kudin
Hajiya rukayya tace kwarai kuwa aiba abida bazatayi miki ba kece fa jikarta tafarko
Nan dai Laila suka tashi suka tafi karbo kudin """"
Ranar daurin aure dasafe hajiya suwaiba takira alhaji abubakar tace mishi yau daurin aure amma haryanzu basuga kayan lefe ba
Alhaji abubakar yace ai mun sha afa ne hajiya kaman nawane za a hada lefen dashi
anzo inda takeso tace million biyu sun isa
Alhaji abubakar yayi signing a cheque yabata tace yauwa Allah yayi albarka
Alhaji abubakar yace Ameen hajiya
Nan yatashi yashige wajen mahaiginsa alhaji shuaib
Yanashiga yasameshi yagama shirin daurin auren ne ma
Yace a a abubakar kaine tafe kohar kafito gurin daurin auren ne
Alhaji abubakar yayi murmurshi yace
ai hajiya ce takirani akan maganar kayan lefen Daba akawo ba
Alhaji shuaib yayi dariya yace wargi ma guri yakesamu
Tamin magana nace tawa angon magana shine taki kai dayake sunga kana da hakuri shine suka bita kanka ko
Alhaji abubakar murmushi kawai yayi baice komai ba
Alhaji shuaib yace yadda yaron nan yake yana burgeni suna mugun shakkarsa
Dan ina mata maganar ta tambayi Abdul Hakeem dakanta bakaga yadda ta yiba
Alhaji abubakar yace ai yaron nan nima yana bani mamaki wlh gashi karamin yaro amma koyanzu nasake mishi komai zai riqe sosai
Alhaji shuaib yace ai Allah ne yama sakayyar biyayyarka gareni da wannan d'anaka ABDULHAKEEM
Zakayi alfahari da haihuwar Abdul Hakeem saboda kaima nayi alfahari da haihuwarka Allah yajikan mahaifiyarka amina
Alhaji abubakar yace ameen Abba
Nan sukayita hirarsu har lokacin daurin aure yayi suka fita zuwa gurin daurin auren
Hajiya suwaiba ta kira yarta hajiya rukayya tafada mata yadda sukayi da alhaji abubakar
Wani irin ihu hajiya rukayya tayi tacikin waya tace million biyu fa kika ce hajiya
Hajiya suwaiba tace to meza afasa
Hajiya rukayya tace aikin ki nakyau hajiya ta
Kinga munfara bambara tun yanzu ko
Hajiya suwaiba ta ce kidai bari yarinya dai Allah yakashe yabata
****
Bayan andaura auren Abdul Hakeem da Laila usman
Daddyn Hakeem ya dawo gida bayan yazauna
Mummy hafsat takawo mishi abinshi yaci sannan yabata labarin yadda sukayi akan kudin lefe
Mummy hafsat tayi murmushi tace a lalle sun wankeka
Yanzu zasuga kaman shirinsu yafara aiki kenan
Murmushi Daddyn Hakeem yayi yace Hafsat mata agurin abubakar maman Abdul Hakeem
Rigimar ki yana bandariya kefa baki yarda dawannan auren bako
Mummy hafsat tayi murmushi tace ai Dana baiyi aureba
Dan banmasan anyiba wallahi kawai dai za aiya kiran aurn da kaddara
Daddyn Hakeem yayi murmushi yace zanso kimishi fatan dacewa kamar yadda nadace dake
Dan ko zabin kaina nayi ba lalle nayi dacen danayi akankiba hafsat
Next page
Your comments is needed fan's
[30/04, 5:48 PM] UMMU AFAN : BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN
DEDICATED THIS PAGE TO LOVELY SON AFAN
❤❤❤❤❤❤❤
GORGEOUS WRITERS FORUM
G.W.F
HOME OF GORGEOUS INTELLIGENT AND EXPERTS WRITERS WE ARE THE AMONG THE REST
A KAWAI LOKACI
PAGE 21 to 25
Ankai amarya Dan kararen part dinta dake gidan su Hakeem .
Mummy hafsat kam a ranar ma gidansu taje wa wuni
Saboda batason damuwa """"'
HAKEEM suna zaune shida Ahmad
Ahmad yace kai kasan karfe nawa yanzu katashi muje narakaka dakin amarya fa .
Cikin halin ko inkula Hakeem yace lalle kuwa su amarya manya bari ma kagani
Ya kashe phone din shi ya gyara kwanciyarsa akan bed din Ahmad .
Ahmad yace banganeba mekake nufi badai anan zaka kwana ba
Hakeem yayi banza dashi yayi baccinsa Ahmad yace OK halin ya motsa ko
ai wannan amarya taja wa kanta data waye. Hakeem da bata kanta wahala ba wajen auranka ba
Nan shima yakwanta abinshi Dan yasan duk yadda zaikai ga magiya Hakeem bazai tashi ba .
Amarya Laila tana ta zuba ido taga ango yashigo shiru kakeji malam yaci shirwa kawayenta ma sun gaji suntafine
Idonta biyu har wajen karfe uku ba ango
Tadauki waya takira Maman ta Maman tace yadai laila naga kiranki yanzu
Kingane dai yadda akace kiyi anfani da maganin ko karfa kiyi wani abin da zaisa yaki kusantarki kinsan maganin na yau ne kawai
Duk hanyar da zakibi yakusance ki
Kiyi shi karmuyi asara makudan kudaden da muka narkar wajen karboshi
Laila tace yanzu dai dakin tsaya na fada miki abinda zanfada miki
Hajiya rukayya tace inajinki meyafaru
Laila tace haryanzu fa bai shigo gidan ba ma
Cikin tashin hankali hajiya rukayya tace munshiga uku
Yanzu soyake muyi asarar makudan kudaden nan
Ki kirashi a waya mana
Laila tace ina naga numbarsa
Hajiya rukayya tace shikenan munyi asarar kudinmu
Dan malam yace maganin kwana daya yakeyi idan yakusanceki zai zaima rakumi da akala bazaiji maganar kowa ba sai abinda kikace mishi
Kuma zai tsani iyayensa
To gashi Hakan su bai comma ruwaba
Har kuka sai da hajiya rukayya tayi Dan maganin nan naira million daya haka suka caske wa malam
Gashi yanzu wannan Dan ban zan yaron yaja musu asara
Daga laila har uwarta basuyi bacci ba
*********
Washagari da misalin karfe goma Hakeem yafito daga wanka daga bathroom din Ahmad
Yashirya cikin wasu kananun kaya sun balain mishi kyau ya fesa turare
Kafin nan yakalli Ahmad da yariga yashirya Dan yariga Hakeem tashi tunda suka dawo daga sallar asuba shi Hakeem sai yanzu yatashi
Hakeem ya kalleshi yace yace muje mukarya zanje naga dalibata fa
Ahmad yace to ango muje dining din ko
Suka wuce zuwa dining area na Ahmad
Sukayi break fast
Kafin suka dauki hanyar zuwa gidan su Hakeem
Suna hanya kafin sukai gidan su Hakeem sai daddyn Ahmad yakirashi akan yazo zai aikeshi
Ahmad yace man sauke ni kawai nakoma gida idan na dawo daga aikan dad zan shigo mugaisa da amarya
Hakeem bai kalleshi yajuya da motar yamaida Ahmad gida kafin shikuma yakoma gida yanazuwa yayi parking a gurin parking dinsu """"
Laila tana jin shigowar mota tabude labulen window din ta
ai kuwa taga shine
Harfitowarsa tagani
Yamata kyau kuwa Dan Hakeem mai kyau ne bakarya
Da badan son kudin dayamusu yawaba ai Hakeem miji ne na nuna wa sa a
Hakeem ya kulle motarsa yayi part din mummy
Yanashiga yaga bata falo ya haura bedroom dinta
aikuwa tana can tana ninkin kayan ta tana jerawa a sif
Yashigo yace assalamualaikum mummy na
Cikin murmushi mummy tace Dan mummy yakake
Dafatan dai katashi lafiya ko
Hakeem yace lafiya qalau daliba kawo kiga ni koma kawai kizauna muyi hira
Mummy hafsat ta nemi gefen bed din ta tazauna
Tsaf Hakeem yagyara wa mummy kayan ta yasake gyara mata bedroom din kafin yace mummy kinci abinci kuwa
Mummy tayi dariya tace kaima dai tsokanata kake yaushe zankai har wannan time ban ci abinciba "'''
Hakeem yayi dariya yace acici
nasan ai dama agurinki na dauko ci
Mummy tayi dariya tace a a nikarka min sharri
Mummy tace ba wannan ba ma
Dama inason magana dakai
Hakeem yadawo da hankalinsa kanta
Tace Dan albarka jiya ba agida ka kwanaba hakane
Hakeem yace hakane mummy a gidansu Ahmad na kwana
Mummy tace ai baka kyauta ba
Tunda anriga andaura dole zamu rungumi kaddara
Yanzu dai Laila tariga zama matarka
Dan haka ina umartarka da karka wulankanta aure
Aure ba abin wasabane duk kuma wani sharrinsu zai koma kansune da izinin Allah bazasu taba tasiri akanmu ba
Hakeem yace ai mummy ki kwatar da Hankalinki adduoi na tsarin jiki ba Wanda bamayi agidan nan dai
Dan haka ba abinda zasu iya mana
Mummy tace Allah yasa Dan albarka acigaba da kula da addua Dan ina tsoron sharrin mutane """"""
Bayan sun gama magana yace Mum zanje wajen Daddy a office Dan kinsan jibi mukeson dagawa fa Hutu yakare zamuje mutattauna
Mummy tace kadage dai sai katafi ajibinko
To da amaryar zakatafi Hakeem yace Allah yasauwake tayi zamanta ba inda zantafi da ita
Mummy tace bazan maka doleba amma ka tabbatar komai kabari a kafin tafi
Hakeem yace insha Allah mummy
Yace barinje gurin daddyn
Mummy hafsat tace a a kafara shiga kaduba yar mutane tukun ko
Koba komai fa yar uwarkace
Yace to mummy sai na dawo
Tana jin dadin inda Dan nata baya mata musu
Hakeem yashiga part din shi
Direct bedroom din shi yawuce
Yaje yadauko wani file kafin yasake fitowa
Laila kuwa basan shigowarshi ba fitanshi tagani
aikuwa kafin yakarasa fita tasha gabanshi
Yace lafiya kuwa zaki sha gabana haka
Laila cikin yanga tace Haba Abdul ya kake min wasu Abu kaman ba mijina kuma Dan uwana ba Dan Allah kadawo muzauna kona minti biyar ne .
Hakeem ya watsa mata wani kallo Wanda dakanta tabashi hanya yawuce abinshi zuwa office din dad dinsa
Hankalin Laila yatashi tace anya kuwa wannan
Mutum """
********
Da daddare bayan daddy da Hakeem sundawo sunci abinci can wajen karfe goma
Mummy tace Dan albarka tashi katafi kabar Laila ita kadai
Badan yasoba yamusu sai safe ya wuce part dinsa ,
Yana shiga falon Laila ta na kashe wayarta dasukaga gama da gawarta
Ko kallo bata isheshiba ya wuce abinsa zuwa bedroom dinsa
Yanashiga wanka yafada
Yana fitowa sukayi ido hudu da Laila cikin wasu arnar kayan bacci wato sleeping dress kenan
Kallo daya yamata yakau da kanshi
Danshi idan ya raina kasuwa ko sauto baya mata
Ya goge jikinsa yashafa mayukansa masu kamshi kafin yasaka night Wear din shi
Ya kwanta tare da kashe wutar dakin """""
ai kuwa Laila tafashe da kuka
Tun abin na bashi haushi har yagaji yace dalla malama kitashi kifita min adaki
Cikin kuka tace Haba Abdul yanzu wannan shine zumuncin da iyayenmu suka hada muyi kenan
Hakeem yayi wani uban tsaki kafin yajuya ya kwanta abinshi
Can tace ai idan kai baka bukatata ni ina bukatarka
Bai kamata kahanani hakkina da Allah yarataya a wuyarka ba """"'
Tabbas yasan hakane kuma mummynshi ma ta mashi tuni akan haka
Koba komai gwamma yafita a hakkinta
Yajuya yace mata damuwarki kenan yasa aka miki aure ko
Kafin tayi magana ya bajadda ita akan bed din
Yacire sleeping dress din nata yayi wurgi da shi bako romance
Sai dai adduar da akeyi lokacin da miji zai sadu da iyalinsa
ai kuwa dai Laila tafada musu
Tagane shayi ruwane
Yanagama abin da zaiyi ya tureta ya kwanta abinshi
Ita kuwa Laila tana cikin farin ciki Dan ita yadda taji din ne kuma bazata iya hakuriba """""
Kullum zata kawo kan nata indai zai biya mata bukatarta kafin ta shekashi lahira taci dukiya
Nan itama ta kwanta bacci ya dauketa cike da farincikin kasancewarsu da Hakeem a Daren nan .
Washagari Hakeem kota kanta baiyiba yana gama shirinsa cikin wata yadi mai tsadar gaske iri daya ma sukayi da Ahmad
Yadin ash colour ne sai yasa bakin takalmi da hula Wanda akekira da senator
Duk Wanda yakalli Hakeem sai yasake kallonsa Dan ya hadu iya haduwa
Yana fitowa Laila ta tareshi tace abdul ga break fast dinka fa mai aiki tagama ,
Wani matsiyacin kallo yamata yace kinga nayi miki kama da mai cin abincin masu aiki """
Ban guri nawuce ni
Tabishi da kallo tace aikuwa sai dai idan bazaka ci abinci agidan nan ba Dan ko kwai ban iya soyawa tayi dadi batare da ya kone ba """
Hakeem suna break fast daddy yace mishi
Shi Ahmad din yashirya kuwa Dan naga kaman kai ka matsa kutafi
Hakeem yayi dariya yace bahaka bane dad kasan fa I want to be come professor like you kaga yakamata indage ko dad
Daddyn Hakeem yace hakane but please son take care of your self sosai kaji ko banda harka da mutanen banza """
Mummy tayi murmushi tace kai daddyn Hakeem duk komawarshi school saikayi mishi wannan nasihar yanzu fa babban mutum ne tunda ya ajiye iyali
Daddy yayi murmushi yace wai haka son
Shidai Hakeem baice komaiba
Daddy yace nifa wallhi ina mantawa yarinyar nan tana cikin gidan nan
Ya bara kace tazo akarya da itaba .
Hakeem yace daddy ai tana da mai aikinta har tagama komai sunci abincinsu
Daddy yace duk da hakadai ai itama yar gida ce
Mummy tace kasan alamarin yara sai a hankali
Kawai kabarsu nan dai mummy ta canja magana
Tace jirgin safe zakubi ko
Abdul Hakeem yace da asuba makuwa mummy tace aikuwa kaman nasani nagama hada ma komai
Mummy Allah yasa kinmin wanna cake din naki medadi
Tace ai duk abinda kasan ina maka ba abin da na rage
Cikin jin dadi Hakeem yace that's my mom Allah yabar minku iyayena
Daddy da mummy sukace ameen Allah yamaka albarka
Yauma da daddare sai da Laila takai kanta gurin Hakeem
Tun karfe uku yatashi yagama shirinsa tsaf bai Dade da gamawa ba Ahmad ya kira yace man kataho tafa nigani a air port ma
Hakeem yace OK gani nan
Yadauki cheque ya rubuta dubu Dari biyar yasama Laila akan bed
Da kuma short note
Yafita daddy da mummy shi kawai suke jira suka rakashi
Next page
Your comment is needed fan's
[30/04, 5:49 PM] UMMU AFAN :
BISSIMILLAHI RAHMANIR RAHIM
HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN
DEDICATE THIS PAGE TO MY ONE AND ONLY HUSBAND
ABU AFAN (DOCTOR SULEIMAN)❤
GORGEOUS WRITERS FORUM
G.W.F
HOME OF GORGEOUS INTELLIGENT AND EXPAERT WRITER'S WE ARE THE BEST AMONG THE REST
AKWAI LOKACI
PAGE 26 to 30
Laila ta tayi taga ba Hakeem
Sai ta tashi tashiga tayi wanka tana fitowa idonta yakai kan takardar da ya ajiye mata
Tadauka ta duba taga cheque ne na kudi """""
Nan da tawashe baki tace kai tun yanzu bata gama rufe baki ba taga wani guntun takarda .
Tadauka taduba
Cewa yayi Nina wuce ga kudi nan
Idan kina bukatar wani Abu zaki iya samun mummy
Laila na gama karantawa ta wurgi da takardar tace kutuman uba Ashe tafiya yayi yabarni anan ,
Nida nake ta burin tafiya Saudi
Ashe ma badani zaitafiba """
Tadauki wayarta takira hajiya rukayya
Tanadawa Laila tafashe da kuka
Hajiya rukayya tace Lafiya kike kuka Laila cikin kukan Laila tace mama kinsan
Abdul Hakeem yakoma Saudi yau """
Maman tace yakoma fa kika ce
Lalle ma yaron nan wato badake zai wuce ba kenan """"
Laila tace ai niban Masan yatafi ba rubuta min yayi
amma yabarmin dubu dari biyar yace kuma idan ina bukatar wani Abu na sami mummynshi ,
Hajiya rukayya tace aikuwa sun ja wa Kansu
Nan da jibi kice kina bukatar kudi
Kinga sai musamu mufara shiri kafin yadawo ,
Laila tace to mama wallahi amma naji haushin rashin tafiya dani din nan dayayi ,
Hajiya rukayya tace kwantar da hankalinki zai dawo ne ai zai shigo hanunmu daga shi har iyayensa .
Yanzu zanzo gidan naki nakarbi kudin na ajiye su a wajena
ai gwamma ma da yatafi abinsa kinga matara kafin yashigo hanu mu kawar dashi banza"'''''
******
Bayan kwana biyu Laila taje gidansu daga nan itada mahaifiyarta suka wuce gidan hajiya suwaiba wato kakan Laila kenan ,
Suna isa hajiya suwaiba takira hajiya larai kishiyar suka shige can dakin hajiya suwaiba
Laila ta kwantar da kanta akan cinyar kakarta
Nan hajiya rukayya tafada musu komai abin da Hakeem ya ma Laila
Hajiya suwaiba tashafa kan rukayya tace hakuri kinji jikalle zai shigo hanun mu ne kinji ko ,
Dazaran yashigo hanun mu sai yadda kikayi dashi kinji ko
Cikin jin dadi Laila tace Allah yasa haka kakalle na
Dakuwa kinga gata Dan sai na canja maki gida kekadai basai da wannan tsohon ba
Hajiya rukayya tace a lalle ma uban nawa ko
Hajiya larai tace Dana dashi aka ware
Hajiya suwaiba tace a dinta ji anwarekun
Nan dai suka ta kulla tsiya
Sai can wajen karfe goma na dare kafin Laila ta tashi tayi hanyar gida
Dan dama ita tasaba da driving din dare ,
tana shiga maigadi yabude mata gate din yana gaisheta ko ta amsa mai .
Tana parking sai daddyn Hakeem yafito yace Laila daga ina a wannan Daren haka
Laila tace daddy daga gidansu alhaji nake a can na wuni .
Daddy yagane wani alhaji take nufi wato alhajinsa,
Yace kin tabbata tace a daddy kakira ma katambaya
Yace a a shikenan karkisake kai dare a waje haka kinji ko tace naji Daddy
Yace maza wuce dakin kin dare yayi
Namishi saida safe
Tana shiga falonta tayi wurgi da gyalenta tace nifa bana son sa ido haka kawai mutum yafita amma ana gadinsa
*****
Bayan wata biyu Laila ce kwace cikin lallausar kujerun falon Hakeem tana kallo
Sai tafara jin tashin zuciya
Ta tashi tayi hanyar bathroom tafara amai sosai take amai kaman zata fitar da kayan cikin ta
Kanwarta suby wacce taci sunan hajiya suwaiba ce tazo
Tana ta sallama amma shiru
Dan tunda Hakeem ya tafi suby tadawo gidan gurin yarta ,
Itama dai duk halin nasu dayane da yaruwarta
Taje siyo wa Laila balangune a bakin titi
Taduba bedroom din Laila bata ganta ba tace anty Laila da karfi
Can ta duba bathroom din falon Hakeem aikuwa nan taganta tayi sharaf ,
aikuwa suby ta rude ganin yar uwar tata a kasa jiki ba karfi tadauki waya takira uwarsu hajiya rukayya tafada mata tace gatanan zuwa
Can dai taga karfa Laila ta mutu Dan haka sai ta
Tashi tayi hanyar part din mom din Hakeem
Mummy hafsat tana kitchen Dan daura abincin rana sai taga suby kaman anjifota
Tace lafiya kuwa suwaiba zakishigo ba sallama
Suwaiba tace kiyi hakuri mummy anty laila ce balafiya ,
Mummy hafsat tace meyasameta tace wallahi bansaniba nima naje aika kafin nadawo nasameta a haka
Mummyn Hakeem tace wace muje naganta
Wannan shine farkon shigowar mummy hafsat part din Dan nata
Kusan atare suka iso da Maman su Lalai hajiya rukayya
Mummy hafsat tace a a yaya ashekema kinzo
Hajiya rukayya tace a gani nan ai
Mummy hafsat tace bara na dauko mota akaita asibiti ko
Hajiya rukayya tace duk yadda kikayi
Mummy hafsat tace afito da ita mutafi ko
Hajiya rukayya ta kalli mummy hafsat wato ita bazata kamata afita da ita ba sai dai tabasu command
Hajiya rukayya da suby suka kama Laila zuwa mota
Mummy hafsat ita taja motar zuwa hospital
Bayan gwaje gwajen da aka wa Laila likita yagano tana da cikin wata biyu
aikuwa hajiya rukayya da suby dama ita kanta Lailar murna suka hauyi sosai ko kunyar mummy hafsat basaji
Itadai mummy hafsat tunda doctor yace Laila cikine da ita
Bata ce komai ba tausayi kawai danta yabata hada zuria da irin hajiya suwaiba
Nan dai tana ta tunanin zuci
Hajiya rukayya tace hafsat bakice komai ba zamuyi jika mummy hafsat tayi murmushi kawai tace Allah yaraba lafiya
Yanzu dai bari na sami doctor nabiya komai sai muzo muwuce gida
Hajiya rukayya tace ai inaganin zan wuce da ita gida kawai idan tasamu lafiya sai ta koma dakinta
Mummy hafsat tace badamuwa hakan ma yayi zama Ku iya bari saita haihu sata dawo
Hajiya rukayya maganar mummy hafsat yamata zafi sosai wato subasa ma bukatar zaman Lailar agidan kenan
Hajiya rukayya tace tokuma idan mijinta yadawo fa
Mummy hafsat tayi dariya tace ai daga har ta haihu son bazai sami damar zuwa ba
Hajiya rukayya tace duk karatun ne zaisa yaki dawowa gida
ai yanzu idan kika kirashi kikafada mishi zai iya samin lokaci yazo yaga matarahi kafin yakoma ko
Mummy hafsat tace sai dai nabaku numbar nashi ita lailar saita kira tafada mishi
Cike da jin haushi hajiya rukayya tace ai ashikenan takira tafada mishi da kanta
Mummy hafsat tace dayafi dai bara na biya kudin nazo mutafi ko
Hajiya rukayya tace a a kibarshi kawai driver na zaizo yanzu yamaida mu gida
Mummy hafsat tace to Allah yabata lafiya ni na wuce
Laila tayi saurin cewa mummy baki bani numbar abdulhakeem dinba
Mummy tace OK kawa wayar taki na samiki
Laila Tamika wa mummy hafsat wayar
Nan tasamata numbar HAKEEM
Laila tace thanks mom
Mummy Hakeem tawuce abinta
aikuwa tana fita hajiya rukayya tace zanyi maganinkine
Muza ayi wa wulakanci duk abin mutaum dai
Ciki dai sai an haife shi tsaf
Ta kalli Laila tace kekuma harda wani godiya Dan anbaki numbar mijinki
Suby tayi dariya tace kai mama kaman Bakisan halin anty Laila ba
Tasan metakeyi fa
Laila tayi dariya tace Haba mama anfada miki Dan Allah nayi godiyar caf
Nan dai sukayi gidan hajiya suwaiba suka shaida mata abin farin
aikuwa harda gud'a hajiya suwaiba tayi Dan murna tace kaman muzuba ruwa a kasa musha Dan dadi
Hajiya rukayya tace kinga yanzu saimuyi addua ta haifi namiji Dan mukasa mutsare gidan
aikuwa hajiya suwaiba tace ai namijin ne ma zata Haifa kuzuba ido kugani
ai tunada wuri zamuje gurin malamin nan yabamu taimako
Haka dai sukulla wannan su kulla wancan
*****
Mummy hafsat bayan daddy ya dawo gida ta shaida mishi abin dake faruwa
Daddyn Hakeem yace kai amma naji dadi Allah yaraba lafiya
Kice son dina yagirma fa
Harda da d'a
Mummy dai bata ce komai ba
Yace ai sai a tura musu kudin dazai ishesu kula da ita abin da kecikinta
Mummy hafsat tayi murmushi tace hakane
Nan daddy yakira yayarshi wato hajiya rukayya maman laila
Tana ganin kiran daddyn Hakeem tasan sunwarke Dan tasan zai jikasu da kudi
Nan da nan tadaga wayar daddyn Hakeem yafara gaisheta kafin yace yaji abin farinciki Allah yaraba lafiya
Sannan kuma inason kuturo da account number dazanturo muku da abinda zatayi anfani dashi
aikuwa farinciki Yakama hajiya rukayya tace yanzu kuwa zanturo
angode fa Allah yakara arziki
Tunda yake bai taba jinta tamishi godiya ba sai yau yace bakomai
Mudai fatanmu dai Allah yarabasu lafiya
Ameen hajiya rukayya tace takashe wayar nan da nan taba wa suby wayar tace ta tura wa daddyn Hakeem account number din Laila
aikuwa suby bata Dade da turawaba sukaji alert din dubu Dari takwas cas
aikuwa murna awajen su kaman me
Hajiya rukayya tace wanna ma ai kadanne ne
Dan nasan nan da wani lokaci zai kara mana
Nan dai Laila ta dauki wayarta takira Hakeem sai da yayi ta ringing kafin yadauki
Tare da sallama cikin kwarewa da harshen larabci Dan bazaka kadauka bahaushebane
Can yace dawa nake magana please
Cikin sauri Laila tace Laila ce
Hakeem yace inajinki ya akayi
Nan tafada mishi what's kina da ciki
Laila tace a mummynka cema takaini asibiti
Hakeem yaja numfashi yace Allah yasauke ki lafiya daga haka baikara cewa komai ba yakashe wayarsa
Laila tabi wayar da kallo ta kalli mahaifiyarta tace mama kodai shima baya farinciki da cikin ne
Suby tace kai bahaka bane kinsan halin ya Abdul yanzu hakama murna ne yasa yakashe wayar
Hajiya rukayya tace komai dai menene shine dai uban d'a
Da su so da karsu so duk uwa ubansu daya can ta matse musu
*****
Hakeem bayan ya kashe wayar ya kalli Ahmad dake fire musu doya
Dan basa cin abincin waje
Yace man kasan meye kuwa
Ahmad yace saika fada
Hakeem yace wai Laila cikine da ita har na wata biyu
Cike da farinciki Ahmad ya ajiye wukar yadaga hanu sama
Yace Allah mungode maka
Wai mune zamu baba
Hakeem ya watsa mishi harara
Yace dadina da kai Ahmad yarinta wallahi
Ahmad yace nayarda yarinta nedan gaskiya kam yanzu fa ka girmeni tunda gashi kana shirin ajiye baby
Hakeem yace please man muyi maganar arziki mana
Nifa harga Allah banso samun da daga jikin lailaba
amma tunda Allah yabani Allah ya albarkaci abinda za a Haifa
Ahmad yace adduar kenan kawai
Allah yashige mana gaba
Nan Hakeem yace ameen
*******
Bayan wata bakwai
Abubuwa da dama sunfaru
Su hajiya dai an tatsi Daddy Dan abin kadan zasuce a turo kudi
**
Yau laraba Laila ta tashi da nakuda
Sukayi da ita hospital
Nan da nan aka shiga da ita labour room
Mummy hafsat itama ana fada mata tazo asibitin daddy ne yasauketa kafin yawuce office bayan kaman awa hudu da shigarta
Ta haifo yarinyarta maikama da ita sak
Aka gyarasu itada babyn kafin akazo sanardasu mummy
ana ce ta haihu sukayi cikin dakin dasauri banda mummy hafsat
Tace wa likitar me akasamu likita taçe mace
Mummy Hafsat tace Allah yaraya
Takira daddy tafada mishi
Yace gashinan zuwa
Su hajiya kuwa ganin Allah baicika musu burinsuba yasa sukacika tam kaman zasu fashe
amma ganin yadda daddy yake farinciki da samunjika yasa suka kwantar da hankalinsu kadan
Nan daddy yakira Hakeem yafada mishi Hakeem yace Allah yaraya Daddy yace Ameen Ameen
Yakamata kasamu lokaci kazo kaga yarinyar da ita Lailar ko
Hakeem yace ai daddy bayanzu Dan karatu yafara zafi sosai sai dai mumsami time zanshigo
Daddy yace Allah yamuku albarka inashi Ahmad din
Hakeem yace yashiga wanka
Nan sukayi sallama da daddy
Ranar suna yarinya taci sunan maman daddy wato amina
Mahaifiyar daddyn Hakeem kenan marigayiya
Alhaji shuaib yasaka sunan da kanshi ba ma daddynba
Haka Laila tacigaba da rainon yarta Amina
*********"********
Tofa
Yanzu akafara kubiyo ummu afan
Your comment is needed fans
[30/04, 5:51 PM] UMMU AFAN :
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN
DEDICATE THIS PAGE TO MY ONE AND ONLY HUSBAND ABU AFAN (DOCTOR SULAIMAN)❤
GORGEOUS WRITERS FORUM
G.W.F
HOME OF GORGEOUS INTELLIGENT AND EXPERT WE ARE THE BEST AMONG THE REST
AkWAI LOKACI
PAGE 31 to 35
Laila kwance take tana danna wayarta
Yayinda hajiya rukayya takeba wa Amina cerelack
Hajiya rukayya tace kinga wasa wasa fa watan meenat shadaya amma amma haryanzu mahaifinta baizoba
Suby tace wai Ku meye kuka damu sai yadawo ne bakusan idan yadawo Baku basamun abinda kuke samu yanzu ba """""
Laila tace nimadai haka nagani
Nifa wallahi tunda acikamin jaka da abinda nakeso yashekara goma ma baizoba ba abinda yadameni
Hajiya rukayya tace duk kurinta ne yake damunku inba yarinta ba ai wallahi idan yashigo hanu zamufi yadda muke yanzu
Dan sai abinda tace zaibata komai ta tambaya zaiyi jiki na bari
amma hakan bazaiyu ba sai
Yaci abinci da maganin har na wajen wata daya inji malam
To ta yaya hakan zaifaru idan bata jawo shi jikinta ba
Laila tace kuma fa hakane mama yanzu manene shawararki mama
Hajiya rukayya tace yauwa anzo gun danakeson azo
Kinga yanzu abinda zakiyi ke Laila kisamu Daddyn Hakeem kice kizakibi mijinki can saudin
Nasan shi da hangen nesa bazaiso shiga hakkin waniba
Idan kikaje can duk wani Abu na biyayyya ki kirkiro kiringa mishi inda zamusamu yasaki jiki dake sosai inda har zaki bashi abinci kuma yaci
Laila tace to mama yanzu dai zanshirya na tafi gidan mummy hafsat
Zanfada wa daddy komai
Hajiya rukayya tace yauwa yar gari tashi maza kishirya kiyi kama hanya
Suby tace anty Laila zanrakaki
Lailatace shirya muje
Hajiya rukayya tace kuje kawai kubar min yarinyar
Laila tace dama bazamu jeda itaba
****
Laila sukayi sallama a falon mummyn hafsat tana zaune tace a a
Laila kune atafe
Laila tace a mummy Allah yasa daddy na nan
Munzo gurinshi ne
Mummy hafsat idan da sabo tasaba da zuwa Neman daddy agunsu Laila
Mummy tace yanan yanzu zaishigo ya fita sallah ne
Nan su Laila suka zauna zaman jiran daddy
aikuwa daddy shigowa suka gaisa
Yace Lafiya kuwa Laila kokuna bukatar wani abunne
Laila tafada mashi damuwarta nason bin mijinta
Daddy yace wannan ba wani abinda damuwa bane
Kishirya kawai kije kiyi passport agama komai kafin jibi sai kitafi
Laila tace To daddy Allah yakara girma yace Ameen
Ina amaryar tawa
Suby tace tana wajen hajiya
Yace to ace angonta na gaisheta
Nan suka wa mummy sallama suka fita
Daddy ya kalli mummy yace Lafiya kuwa mummyn Hakeem
Mummy tace wallahi alhaji mutanen kotata ban yarda dasuba
Mezaisa tabishi har can yabari mana ai komai daran dadewa zadawo
yanzu haka uwartace ta kitsa mata komai
Daddy yayi murmushi yace insha Allah ba abinda zaisamu Hakeem
Kokin manta Dan naki
Ma abocin riko da addini ne
Dakuma yawaita adduoin tsarin jiki
Mummy tayi murmushi tace hakane daddyn Hakeem
Gaskiya Hakeem kam akwai addua
Sai dai muce Allah yadada tsare mana shi
Daddy yace Ameen
Washagari daddy yagama wa Laila komai nashirin tafiya
Wanda jibi jirginsu zaitashi
Zuwa Saudi
Hajiya rukayya da hajiya suwaiba ne suka sata gaba kan yadda zata yi anfani da magun gunan dasuka karbo daga gurin malam
Komai Laila ta haddace Dan hartafara hango kanta cikin daula
Washagari jirginsu Laila yadaga zuwa Saudi
Inda tabar meenat 'yarta agurin mahaifiyarta hajiya rukayya
Daddy yadauki waya yakira Abdul Hakeem cikin ladabi Abdul yagaida mahaifin nasa
Daddy yace kashirya kaje airport kadauki matarka
Tana hanya
Cikin mamaki Abdul Hakeem yace Laila kuma daddy
Meyasa zata biyoni har nan
Gaskiya takoma gida kawai Daddy
Daddy yace Haba Dan albarka aure fa ba abin wasa bane
Na kusan shekara bakanan
Ta nemi data zo tagan ka ai baza a hanata bako
Hakeem yace amma daddy
Daddy yace karkace komai ka je airport kadauketa kawai kaji ko
Yace naji daddy Allah yakara Lafiya daddy yace Ameen
Allah yamuku albarka Hakeem yace ameen daddy
Suna gama waya da daddy yace ya Allah
Ahmad yace Lafiya kuwa Man naganka haka
Hakeem yasauke ajiyar zuciya yafada wa Ahmad komai
Ahmad yayi murmushi yace kace nakoma dayan part tunda amarya zata zo
Hakeem dai baice komai ba
Yazauna akan kujera
Karfe hudu dai dai yaje yadauko Laila
Tana ta rawar kai shikuwa Hakeem tunda tagaisheshi ya amsa bakaracewa komai
Wannan shine mafarin zaman Laila a saudiya
Dan bata koma ba
*******
Bayan shekara goma shabiyar
PROFESSOR ABDUL HAKEEM ABUBAKAR
Dan shekara talatindashida aduniya
Cikakken saurayine Wanda ya amsa sunan
THE YOUNG PROFESSOR
ko ina haka akeranshi gida da wajen kasan nan
Yayi suna sosai aduniya saboda kudi da kuma ilimin da Allah yabashi
Har yanzu yanazama a sauddiya ne a inda yake koyarwa a jamiar Saudi Arabian
Dashi da babban abokinshi professor Ahmad
Wanda a yanzu suke shirye shirye komawa kasarsu Nigeria
Laila anzama manyan mata koda wasa bazaka kaga Hakeem kace shine mijinta ba
Ba alamun dacewa a tsakaninsu
HAKEEM bashida rowa koka kadan kudi masu sunan kudi yana cika
Laila dasu
Dan yanzu taza business wuman sosai suke kasuwanci da kanwarta Suby
Idan ta saro kaya a Saudi sai ta tura wa Suby Nigeria
Su duk aganin su Hakeem magani ne yake aiki akansa
Wanda abin bahaka bane dai niyya kawai yayi yake mata abinda yake mata
Amina kuwa agurin hajiya rukayya take sun shaku sosai Dan yarinya dai tayi mugun gado
Shiyasa basa shiri da kakarta mummyn Hakeem Dan tana mata wa azin tabi a hankali kartayi mugun gado
Yanzu haka ma basa Kaduna suna can kano nan hajiya rukayya takoma Dan mijinta yayi ritaya sai ya koma garinshi kano
Shiyasa hajiya rukayya tadauki jikarta meenat suka koma can
Yanzu meenat ta Dade a kano
Tana zuwa Hutu Saudi gurin iyayenta
Wannan kenan
KANO
Malam sualaiman yana zaune a wata unguwar talakwa ne dake nan kano
Yana da mata daya da rana biyu
Yaya shamsu shine babba zaikai shekara 36 aduniya
alokacin da umma ta haifi yaya shamsu sai da yashekara ashirin cas
Kafin tasamu cikin asmaullahil husna
Wato asmau kenan
Inda akecemata husnah
Husnah ta taso cikin gata da tattalin uwa Dana uba da kuma Dan uwa rabinjiki wato yaya shamsu
Tunda aka haifi husnah shamsu ne me dawainiya da ita kasancewar yadade baisamu kani ko kanwa ba
A yanzu haka husna tasamu scholarship a wani makarantar masu kudi a inda take s s two a halin yanzu
Husna tana da hankali da nutsuwa ga kuma uwa uba kyau da needed
da Allah ya horemata
Husna yar kimanin shekara shabiyar aduniya
Sun hadu da Amina Abdul Hakeem abubakar
A school lokacin da husna ta samu scholarship tashigo itama Amina alokacin tashigo makarantar
Amina taso husna Dan Abu guda biyu ne na farko iliminta farinjininta da kuma kyau
Dakyar husnah ta amince wa Amina suka zama kawaye sosai duk inda kaji ance husnah to za ace amina
Muje zuwa anfra fa
Fan's kubiyo ummu AFAN
Kawai
Your comments is needed
[30/04, 5:53 PM] UMMU AFAN : BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN
GORGEOUS WRITERS FORUM
G.WF.
HOME OF GORGEOUS INTELLIGENT AND EXPERT WRITERS WE ARE THE BEST AMONG THE REST
DEDICATED THIS PAGE TO MY ENTIRE FAMILIES
AKWAI LOKACI
PAGE 36 to 40
HUSNA nata saurine saboda tayi latti yau Monday yau ne za a Nada zabin prefect a school dinsu
Ummu tace husnah naga kina ta sauri yau Lafiya kuwa
Husnah tayi murmushi har dimple dinta suka lotsa tace wallahi ummu yau za a nad'a sabbin prefect a school ne shiyasa mukeson muje muga wadda za a ba
Yaya shamsu yace kokuma kije a nad'a kuba
Husnah tace aini bandani yaya Dan an min
Interview ma naki bada amsa a hall din
Duk Dan kar abani damuwar nan
Yaya shamsu yace ai duk yadda kikayi sunsani tunda sunsan dalibarsu
Kokinyi shiru sunsan bawai baki sani bane
Tunda dama sunsan bakyaso
Bakince min saki dole akayi kiyi interview din ba
Husnah tace wallahi wani malaminmu ne copper yace lalle sai nayi interview
Kuma duk abinda suka tambayeni Nace I don't no
Komai I don't no kawai
Yaya shamsu yayi dariya yace kedai jekidawo kiban labarin wadda akazaba
Husnah tace to shikenan yaya
Tajuya ta kalli ummanta tace ummu sai na dawo
Ummu tace Allah yadawo dake Lafiya tace ameen umma na
Har takai bakin kofa yaya shamsu yace husnah kiyi hakuri kinji bakudi ajikina yanzu nakeson zuwa nayi buga buga naga abinda za a samo acigidan
amma namiki alkawari idan nafita nasamu wani abin zana biyo har school dinku
Inbaki Abu mai dadi
Husnah tayi murmushi tace karka damu yaya na wallahi bani da damuwar komai Dan bancika son cin komai a school ba ma
ai kana kokari yayana Allah yakawo maka aiki maitsoka nasan zamu huta sosai
Yace ameen yar kanwata jeki karkiyi latti
Tafita abinta tana murmushi
Umma ta sauke ajiyar zuciya tace wa yaya shamsu
Kasan wani Abu kuwa shamsu deen yaya shamsu yace a a umma saikin fada
Tace wato akullum na kalleku kaida kanwar ka ina wa Allah godiya daya mallakamin 'ya'ya nagari
Dan ba abinda zance wa Allah sai godiya kawai
amma duk inda ake neman 'ya'ya nagari nasamu
Abba dayake shirin fitowa daga dakinsa yace munsamu dai zakice zainaba
Tunda Allah yasa shamsu yakawo kwari fa shiyake dawainiyya damu agidan
Shine komai na kanwarsa shine namu aiba abinda zamuce sai muce shima Allah yabashi mai mishi
Umma tace Ameen malam
Malam sulaima yace babban damuwata shine inga kasamu aiki kayi aure Dan shine cikar mutuncin mutum
Umma tace hakane ai baki yayi tunda yana da wacce yakeso khadija yarinyar kirki taki kowa saishi take jira
Ko a yanzu aka tura za ayi komai tunda iyayen ma sun komai
Malam sule yaja numfashi yace hakane kam to Allah yabamu yadda zamuyi
Ya kalli shamsu da tunda suka fara zancen auranshi yashiga duniyar tunani
Dan yana matukar son budurwarshi khadijat wacce akekira da kubra kitama tana son yaya shamsu sosai Dan
Shekarar ta daya kenan dagama secondary school
Manema sunzo Neman aurenta taki ita sai shamsu
Haka iyayen suka hakura suke zaman jiran shamsu yakawo sadaki a daura aure
Malam sule yakalli shamsu yace karka damu akwai Allah
Shamsu yace barinje Abba sai na dawo ya ma umma ma sallama ya wuce zuwa Neman abinda zasuci
YAYA SHAMSU daga secondary bai kara gaba ba saboda rashin kudi daya musu katutu shida mahaifansa
Dan haka kawai ya hakura yake Dan buga bugansa dahaka kuma har Allah yasa aka haifi kanwarsa husna saiya yaci burin Husna zatayi karatu tunda shi Allah baisa zaiyi mezurfiba
Sai kuma gashi Allah yafara cikawa shamsu burinsa inda husnah taci scholarship
**
Husnah tana isa school tasamu anfara assembly
Ta tsaya daga bayan 'yan mate dinsu suna sauraron jawabi daga bakin principal dinsu
Can sai vice principal yace yace zamufara kiran new prefect dinmu daya bayan daya
Principal tace a fara da head girl ko
Sai copper bash yace am sorry ma
Gwamma afara da sauran kafin head girl
Zaifi Jan ra ayin su
Principal tace OK afara kira kawai
Nan akafara kiransu ana samusu hula da kuma belt
Dansu prefect din hula suke sawa green gabadayansu na head girl ce kawai ya banbanta Dan nata read cap take sawa
Can taji ance social prefect AMINA HAKEEM ABUBBAKAR
Nan aka dau tafi raf raf raf ana murna
Can sai vice principal yayi gyaran murya yace yanzu zamu Kira me gayya me aiki wato our head girl
Nan aka kira sunan ASMAU SULAIMAN SHAMSU
cikin gigicewa Husnah tadago kanta aikuwa tana dogowa sukayi ido hudu da Copper bashir
Ya kashe mata ido daya
Cikin tashin hankali Husnah ta daga kafa dakyar tana zuwa ta hau kan stage
Principal ta rungume Husnah tare da
Da samata hulan head girl dinta read cap
Ta daura mata belt dinta read shima
aikuwa daga students har malaman dake wajen aka dautafi Dan sunburge kowa ga read cap din yawa Husnah kyau sosai kaman Dan ita akayi hulan
Nan dai aka rantsar dasu Husnah a matsayin new prefect
***
Copper Bash ya tsare Husnah alokacin dazata wuce gida itada meenat
Copper bash yace asmau
Ya naga kina ta shan kamshi ne Yau
Meenat tafashe da dariya
Tace uncle ai Husnah fa batasan za abata prefect ba ballantana Head girl
Copper bash yayi murmushi yace ai kuwa ta yaudari kanta
To inba a bata ba waza aba wa
Meenat tace aifa dai kam
Husnah dai tana jin su batace komaiba
Nan driver din meenat yazo daukarta
Husnah kuma dama da kafa take zuwa take komawa
Meenat tace Dan Allah Husnah kizo musaukeki a gidan kinga sai naga gidanku ko
Husnah tayi murmushi dimple dinta suka lotsa
Copper bash ya tsaya kawai yana kallon Husnah komai nata cikin aji takeyinsa da nutsuwa shiyasa takeda farinjini a school din
Husnah tace wallahi meenat idan ya shamsu ya ganni a mota zai min fada sosai .
Meenat tace kedai kawai bakyason kibimu sai kiyi tayiwa yaya shamsu sharri
Copper bash yace kinga kuyi sauri kutafi gida kar anemeku kuntsaya surutu
Meenat tace to shikenan sai mun hadu goben idan munzo ko
Husnah tace to meenat Allah yakaimu kigaida gidan
Nan sukayi sallama
Copper bash yace wa Husnah muje nakaiki gida da kaina
Tunda kinki kawarki takaiki
Husnah tace Dan Allah uncle kayi hakuri wallahi yayana yaganni da kai zaimin fada
Copper bash yace mezaisa yamiki fada baki kai a rakakin bane ko yaya
Husnah tayi shiru tace kayi hakuri Dan Allah
Yace wato har yanzu Husnah kinkasa yarda da sonda nake miki ko
Kibani dama nasan gidanku da iyayenki wallahi dagaske nake auranki zanyi Asmau
Husnah tace Dan Allah malam kayi hakuri kar yaya yasan da wannan maganar
Dan ya hanani kula koda kawace ballantana
Maganar soyayya tun yanzu
Da kyar yabani dama kawance da Àmina Hakeem ma
Copper bash yace OK na fahinceki
Ba wai nidinne bakyaso ba umarnin yayanki kikebi ko
Husnah ta rufe ido tana murmushi tayi hanyar fita daga gate din school din
Copper bash yayi murmushi tunda ya gano yafara shiga zuciyar Husnah
Zaisan hanyar da zaibi Dan yasan iyayenta da yayanta shamsu
Bashir Dan wani hamshakin maikudi ne sosai acikin garin kano
Bautar kasa wato NYSC yakaishi school dinsu Husnah
Tunda yadora idonshi kan Husna yaji yakamu da son ta
amma takibashi daman hakan
Next page
[05/05, 11:05 AM] UMMU AFAN :
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN
FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION
F.C.T.W.A
HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITERS OF THE NATION
DEDICATE THIS PAGE TO UMMY KINA KOKARI WAJEN GANIN NOVELS DINA SUNA KARBUWA A KOWANI GROUP ALLAH YABAR KAUNA
AKWAI LOKACI
PAGE 41 to 45
ABDUL HAKEEM THE YOUNG PROFESSOR
kwannansu biyu da dawowa daga saudiya dashi da madam laila
HAKEEM yana shirin zuwa sashen iyayensa ne don yagaishesu
Yafito daga wanka ne yashirya cikin wani farisol din jallabiya ya faffesa turarruka masu kamshi Dan akwaishi da son kamshi sosai
Har yagama shiransa zaifita Laila bata tashiba
Ya kalleta kawai ya girgiza kai yayi gaba abinsa zuwa part din su mummynshi
Yanashiga yasamesu akan dining da mummy da daddy
Daddy yace Dan halal kaki anbato yanzu nace baka shigo break fast ba mummyn ka tace ai tasan kana hanya
HAKEEM yayi murmushi cike da kaunar iyayensa
Yace ai mummy tafadi gaskiya Dan bazan taba karyawa a wani waje ba matukar muna tare da mummy
Mummy tace yauwa son fada mishi dai
Nan mummy tayi serving din HAKEEM abinci yafara ci
Bayan sungama break fast ne mummy zata kwashe kwanukan Hakeem yace haba daliba yazakimin haka kuma
Kezaki kwashe kayan zuwa kitchen nikuma meye anfani na
Mummy hafsat tace nabari tashi ka kawashe
Daddy dai dariya yake musu yakoma kujerar falo yazauna
Hakeem bayan yagama kwashe kwanukan zuwa kitchen saiya dawo falo Dan hira da iyayen nasa
Daddy yace wai acikin makarantu biyu dasuke bukatarka wanne kazaba kayi lecturing din agun
HAKEEM yayi murmushi yace ai daddy daga ni har Ahmad munzabi muje BUK kano
Daddy yace Allah yasa haka shine alkairi
Mummy hafsat tace amin
Daddy yace kace kuna tare da amaryata kenan
Mummy hafsat tayi murmushi tace MEENAT ko rigima
Yakama ta ma suturota tazo tagaida iyayenta ai
Daddy yace karkice komai tunda basuyi hakan ba shi saiyaje yaganta
Kafin Hakeem yayi magana wayar daddy yadau kara
Daddy yadaga sai sukaga daddy yace subuhanallla a wani asubiti
Mummy da Hakeem suka maida kallonsu kan daddy
Bayan daddy yakashe wayar ne suka tambayeshi abinda kefaruwa
Yace Abba na aka kai hospital
HAkeem yace subuhanalla muje kawai daddy
Mummy hafsat tace nima bazaku barniba muje tare
Suka he asibitin Hakeem ne me driving dinsu
Suna isa suka sami alhaji shuaib bayadda yakara ji
Dan yanajin jiki sosai
Alhaji shuaib yarike hanun Dan nashi wato daddy
Yace Allah yamaka albarka abubakar da kai da zuriarka
Ba abin da zance dakai sai Allah yàmaka sakayya da gidan aljanna duk inda akeneman yaro nagari ka kai abubakar
Ya kamo hanun Hakeem yace jikallena ga mahaifinka nan nabar maka amanarshi duniya da lahira
Kabishi kamar yadda yabini
Ya kalli mummy hafsat yace kema Hafsatu Allah shizai biyaki akan yadda kika nuna kaunarki ga abubakar
Duk yadda aka kai cutar dashi kinki bada damar hakan
Allah yamiki albarka
Tunda alhaji shuaib yafara magana suke kuka musamman daddyn Hakeem
Da mummy
ABDUL HAKEEM ne kawai ya daure amma shima idonshi yayi ja sosai
Can dai likitoci sukace sufita zasu samishi
Oxygen Dan numfashinsa yafara kasa
Alhaji abubakar ne kawai akabari a dakin
Can wajen La asar 'yan kano suka iso asibitin
Kuma harda meenat
Hajiya rukayya itama a rikice tazo jincewa jikin mahaifin nasu ya tashi
amma anhanata shiga taganshi
Hakan kuma ya bata mata rai sosai
Amina kuwa tana ganin daddynta Hakeem tare da mummynshi takarasa wajensu cike da murnar ganin uban nata
Bayan tagaida Hakeem ne take tambayarsa dad ina mummyna yace tana gida yanzu zata zo itama
Amina ta kalli mummy hafsat tace wato ma bazaki kimin magana ba ko
Mummy hafsat tace kaga jaira kinga babanki bakima San ina wajenba zaki ce ban miki maganaba
Sannu uwata mummy hafsat takarasa maganar tana tsokanarta
Amina tace ai wallahi duk abin kidai saina auri mijinki sai naga yadda zakiyi
Mummy hafsat tayi murmushi tace kishigo mana kigani da tabarya zan koraki ai nan mummy Hafsat tana jikinta ajiki sukata Dan hirarsu amma cikin jimamin rashin lafiyar alhaji shuaib
Ahmad yakaraso hospital din shima cikin jimami
Hakeem na ganin Ahmad yace Man ka karaso kenan
Ahmad yace ai kana kirana nace wa mummy zanzo hospital namata bayani
Itama zasu zo tanason gama abincine sai ta taho dashi
Hakeem yace Allah yakawota Lafiya
Ahmad yace barinje na gaida su mummy suka karasa harwajensu mummy
Yagaishesu yamusu ya maijiki
Amina tace daddy Ahmad ina wuni yace Lafiya qalau daughter ya mummyn ki
Tace banganta ba mu yanzu mukazo daga kano
Kafin Ahmad yayi magana daddyn Hakeem yafito daga dakin yana goge hawaye
Hakeem da Ahmad suka karasa dasauri Hakeem yace daddy yajikin alhajin
Daddy abubakar yace Hakeem Allah ya yi wa mahaifina rusuwa
Alhaji yatafi yabarni Hakeem
Yanzu bani dakowa dama bansan mahaifiyata ba shikadaine min aduniya
Shima yatafi
Duk matan dake gun sukasa kuka
******
Bayan arbain din alhaji shuaib
ABDUL HAKEEM da aminin sa suka fara lecturing B U K
Dan karakaran gidaje makaranta tabasu a matsayinsu na professional akan aikin su
Yanzu Haka suna shirye shiryen auran Ahmad kuma a kano zaitare da matarsa
Itakuma Laila tayi tayi yabarta tadawo kano yaki
Sai dai yazo masu Hutu yakoma
Yanzu haka bikin Ahmad saura sati biyu cas a daura auren Ahmad
*****
Yaya shamsu zaune akan kujera yar tsugune umma kuma na hada zobo Dan duku gidan suna azumin Monday da alhamis
Itakuma Husnah tana kan hada musu abincin buda baki a kitchen
Kanin kubra budurwar yaya shamsu ne yayi sallma yashigo ya tire
Ya gaisheda umma kafin ya ajiye abincin yace yaya shamsu gashi anty kubra
Kafin shamsu yayi magana umma
Tadauko naira hamsin tace zoka karba ko kace mata angode Allah yasaka da alkairi
Yaron yaki karbar kudin umma yaya shamsu yace haba kanina karba mana ai ba roka kayiba
Yakarba yayi godiya zaifita kenan
Husnah ta tace sani kace wa anty kubra gobe zanzo kitso
Sani kanin kubra yace to zanfada mata
Umma tace kajita kaman wani kitson takeso
Yanzu zatace maka zata kitso taje tadawo da kalba
Husnah tayi murmushi tace umma wallahi banason kitso nafison dai amin kalban kawai
Tagama kwashe komai ta ajiye musu akan taburma
Jelouf din taliya ta musu Wanda ya shamsu yakawo dazu yace a dafa yasan tana son taliya sosai
Umma tace wallahi yarinyar nan kubra akwai kokari
Bata gajiya da aiko maka da abinci duk Monday da alhamis
Husnah tace gaskiya kam wallahi anty kubra Nada kirki
Yaya shamsu Allah yabaka kudi wannan sallar dai kasamu kamata kayan sallah
Umma tace amin gaskiya kam ta cancan hakan
Shamsu yaja numfashi yace kuma wallahi umma kubra bata jin dadin gidansu
Indai ba abbanta yana gidaba
Kishiyar mamanta tana matsa mata sosai
Yanzu fa wai akwai Wanda yamata magana yanson kubra shine tadage sai kubra ta amince da auran wani baniba
Dan taki amincewa shine take bata wahala
Kuma abbanta yace bazai mata auren doleba
Sai Wanda takeso zaibata
Shine tayi bakin jini agidan
Umma tace Allah sarki marainiyar Allah
Allah yabaka abinda zaka auro yarinyar nan karabata da gidan nan
Shamsu yace amin umma
Husnah ma tace amin
Yaya shamsu yace barinje sallar magriba indawo muyi buda baki
Shamsu yana fita Husnah tace wallahi ummu yaya shamsu yana bani tausayi
Dan wallahi shima yana son kubra sosai
Umma tace bakomai AKWA LOKACI
watarana sai labari Husnah tace Allah yanuna mana lokacin amin ummu tace
Suma tashi sukayi Dan gabatar da sallah
**
Bayan kwana biyu wani abokin shamsu yabashi
Shawarar mezaihana yakai takardunsa Neman aiki B U K koda masinja aka bashi zai rage zafi ai
Shamsu yace gaskiya naji dadin shawarar nan daka bani kabiru
Allah yabar zumunci
Kabiru yace bakomai ai zaman taren kenan
Kaga ni a secondary school nake masinja amma alhamdulilla ina samu
Ya shamsu yace hakane yanzu zanyi wanka nakai kuwa
Bayan ya shamsu yashirya zuwa kai application dinsa
Saiya wa umma sallama Yakama hanya
Bayan yakai akace za anemeshi idan yasamu idan kuma baisamuba zaiji shiru
Yabasu number dinsa
Yatafi gida yana ta aduar samun nasara
Idan Allah yasa yasamu aikin nan zaiyi kokarin raba kubra da gidansu tazo suyita maneji yasan kubra zatayi hakuri da abinda zaibata umma kuma bata da matsala zasu zauna Lafiya
*****
Professor Abdul Hakeem zaune a office dinsa yana duba wasu takardu sai wata mata tashigo tagisheshi
Tace wai itace sabuwar sakatariyarsa
Abdul Hakeem yace OK zaki iya tafiya sai na nemeki
Tafita
Tana fita Hakeem yakira management din makarantar
Suna ganin wayar office dinsa
Aka je dasauri Dan yanakirane
Manager nashiga yagaishe da professor Hakeem
Hakeem yace ina buka tar a canza min secretary ma ana bayason mace
Namiji yakeso akawo mishi
Manager yace angama sir
Hakeem yabashi izinin tafiya
Sukaje suka zauna meeting
Nan akayi shawarar daukar SHAMSUNDEEN SULAIMAN a matsayin secretary na THE YOUNG PROFESSOR ABDUL HAKEEM
Yaya shamsu yana kofar gidansu kubra yaje zance
Sai yaga kira da bakuwar number
Yayi picking call din
aikuwa kubra taga yana ta fara a yana godiya
Bayan ya kashe wayar ne
Ya kalli kubra yace kiyimana murna munsami aiki kinga kenan burinmu yakusa cikako
Cikin tsananin farinciki kubra tace alhamdulillahi
Gobe zafara azumina kenan
Da mamaki shamsu ya kalli kubra yace azumin mekuma zakiyi
Kubra tayi murmushi tace aina wa Allah alkawarin cewa duk randa kasamu aiki sainayi azumi uku cas
Shamsu yace aikuwa bazakiyi kekadaiba tare zamuyi
Nan dai yamata sallama ya wuce gida Dan yasanar wa umma
**
Umma tayi farinciki sosai haka ma mahaifinsa
Husnah kuwa tsalle taringa yi tana murnar ankusa kawo musu anty kubra gidansu
Mahaifinsa yace gobe zaka fara zuwa kenan
Yaya shamsu yace a daga gobe sukace wai karfe takwas zandinga zuwa
Sainaje ma zasubani dokokinsu
Nan iyayen sukayi ta albarka
Washagari yaya shamsu yashirya zuwa wajen aiki
Bayan yayi sallama da su umma
Ya wuce gidansu kubra itama tamishi adawo Lafiya
Yana isa aka gama komai aka turashi office din PROFESSOR HAKEEM
yana zuwa yayi nocking akace yashiga
Professor Hakeem yanakan kujerar shi yana fama da wasu takardu
Shamsu yashiga yagaisheshi professor Hakeem ya amsa batare da kalleshiba
Yace ta akayi malam
Shamsu yace daman nine sabon secretary din da aka turo office dinka
Professor Hakeem yace OK dafatan zamuyi da gaskiya malam
Shamsu insha Allah sir
Sai alokacin professor Hakeem yadago kai ya kalli ya shamsu
Yace ko zan iya sanin sunan malamin
Yaya shamsu yayi murmushi yace Shamsuddeen
Hakeem yace malam shamsu Allah yatayaka riko za iya tafiya
Shamsu yayi godiya yace nagode sir
Ya wuce abinshi professor Hakeem yacigaba da aikinsa
Can wajen shabiyu da rabi professor Ahmad yashigo office din Hakeem yace ya man muje muyi lunch kasanfa bana jure yunwa
Hakeem yayi murmushi yace wai damma ka kusa shiga daga ciki
Aisha Nada aiki wallahi sai dai ta ringa samaka wani flask
Ahmad yayi dariya yace ai dani dakai duk jirgi daya yakwàso mu
Nan dai Hakeem ya tattara suka fito tare Hakeem yakalli shamsu dake kan kurarshi yace
Abokina zamufita ga key din office din take care
Shamsu OK adawo Lafiya
Suna zaune a gurin cin abinci Ahmad yace waini wannan Dan gayun ne sakatarenka
Hakeem yace kaima kaji mamaki ko
Da naso namishi tambayoyi sai naga rashin dacewar hakan gwamma nagama fahimtarshi kafin
Naji tarihinsa
Ahmad yace hakan ma yayi
amma mutum very responsible person kaman wannan ace yana sakatare
Shamsu yashiga office din maigidan nashi yaga kudi a kasa
Ya dauka ya ajeye mishi a saman tebur
Bayan su Hakeem sundawo yashiga office din sa
Sai ya kalli inda ya zubar da kudi yaga babusu
Dan dama da gangan yayi hakan Dan ya gwada shamsu ne kawai
Yazauna akan kujerarshi aikuwa idonshi yakai kan kudinshi da shamsu ya ajiye mashi su
Professor Hakeem yayi murmushi akaro na farko
Yaya shamsu yashiga ranshi
Karfe hudu dai dai Hakeem yatashi a office dayafito yaga kujerar da shamsu yake yaga yana waya ne amma yanaganin fitowar Hakeem yawa kubra sallama
Hakeem yayi murmushi yace hala kaida uwargida kuke wayar kuma ka kashe
Yaya shamsu baice komai ba sai murmushi kawai
Hakeem yace natashi kaima zaka iya tafiya
Shamsu yace aisunce wai sai time din tashi yayi zantashi
Hakeem yace no zan musu magana kaje kawai abinka
Hakeem har yayi gaba ya dawo yace sunbaka kudi kuwa
Ya shamsu yace wani kudi kuma nida nafara aiki yau sir yakarasa yana murmushi
Hakeem yayi murmushi yace yakamata subaka kudin daukar aiki
amma zanbaka aro idan anbaka sai ka dawo mundasu ko
Ya shamsu yayi dariya kabarshi kawai sir kar azo basu baniba
Hakeem yayi murmushi yace idan basu baka na barma
Kuma banason musu yashiga tsakaninmu malam shamsu ka karba kawai karmuyi haka dakai
Shamsu yakarba yace nagode yallabai
Yace karka damu
Sai gobe kayi kokari ka koma gida
Shamsu yasake baki kawai yana kallon Hakeem
Yaduba damin kudin da Hakeem yabashi
Nan dai yayi wa Allah godiya cike da farinciki shamsu ya kulle kofar office din su
Yayi gida
Yana zuwa Husnah ta tareshi da murna oyoyo yaya na sannu da dawowa
Shamsu yayi dariya yace yauwa yar kanwata ina umma
Ummu ta fito daga daki tana daura dankwali tace a a dawuri haka
Yaya shamsu yace wallahi Allah ne ya hadani da shugaba nagari yace karfe hudu ma ina iya tafiya
Umma ta ce alhamdulilla ai haka akeso
Yaya shamsu yace umma ina Abba tace yanzu zaishigo sunje gaisuwar Mara Lafiya shida malam tanko
Kafin tarufe baki ma sai ga Abba yayi sallama yace a a Dan albarka har andawo
Nan suka zauna kan ta Burma yafito da kudin ya ajiye gaban mahaifinsa
Nan yamusu bayanin komai
Abba yayi gyaran murya yace to yanzu idan akazo ba a baka kudin daukan aikin bafa
Ya shamsu yace nima haka nagani dai
Na nuna yabar kudinsa kawai yace aishi yabani
Umma tace to kaidai duk inda kake ka tabbatar karike gaskiya kazauna da kowa zuciyarka daya
Ya shamsu yace insha Allah
Zankiyaye
Nan dai Abba da umma sukace baza a taba kudinba harsai
anbaka angani koba hakaba yaya shamsu yace hakan ma yayi gaskiya
Husnah tace Abba kawai da yaya shamsu yayi anfani da kudin gurin kai sadakin anty kubra
Koba a bashi tunda yana aiki saiya biyashi a hankali
Abba yayi murmushi yace uwatakenan ke yarinyace har yanzu bakisan duniyaba
Indai aure ne ai zaiyi insha Allah
Suka ce Allah yasa
Bayan kwana biyu ranar alhamis ya shamsu yaje wurin aiki aka kirashi akabashi kudin daukar aiki naira dubu goma shabiyar
Da yadaqo gida yace wa ma haifinsa ambashi yanuna musu
Abba yace alhamdulilla kaga gobe saika mayar mashi da kudinsa
Allah yayi albarka ya shamsu yace ameen Abba
Abba yace yakabar kudin kuma anan
Ya shamsu yace Abba kayi abinda yadace kawai
Abba yace wa umma tadebi kudin ta ajiye agunta
Washagari ya shamsu yasami professor Hakeem a office yamishi bayani yamayar mashi da kudinsa
Hakeem shi har ya manta ma yaba wa ya shamsu kudi
Ba karamin burgeshi ya shamsu yayi ba
Yace
Gashi kasiya wa yara sweet
Ya shamsu yayi dariya yace ai banida aure
Hakeem yakalleshi yace
Malam shamsu idan bazaka damu zanso jin labarinka
Next page
Your comments is needed
Fan's
[05/05, 11:08 AM] UMMU AFAN :
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN
FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION
F.C.T.W.A
HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITERS OF THE NATION
DEDICATE THIS PAGE TO UMMU HANIF
AKWAI LOKACI
PAGE 46 to 50
PROFESSOR HAKEEM yace ina sauraronka malam shamsu
Ya shamsu yayi murmushi nan yabashi kadan daga cikin tarin rayauwarsu
Hakeem yace kace kai din dai har yanzu dai gaurone murkusheshen gaurone
Ya shamsu yayi murmushi yace a nakusa fita a layin gaurayen tunda nasamu abinyi
Hakeem yace hakane
Ya kalli kudin da ya shamsu ya ajiye mashi akan tebur
Yadauko wani rafar ya hada mashi dasu yace
Kadauki wannan kudin kaje kamuku cefane
Sannan kuma ka Isar min da gaisuwata wajen Abba da umma
Da kuma yar kanwarmu
Ya shamsu yace amma ai kudin sunyu yawa yallabai
Hakeem yayi murmushi yace karkadamu
Malam shamsu kana da sha awar cigaba da karatu ne
Shamsu yayi murmushi yace
Zanyi kokari bayan aure na ga nasamu ko degree na samu insha Allah
Hakeem yace Allah ya nuna mana ya shamsu yace nagode Allah yasaka da alkairi
Hakeem yace godiyan yana yawa kuma.banason godiya malam shamsu
Ya shamsu yayi murmushi yace ai ka canci hakan ne yallabai
Nan dai suka Dan taba hira har lokacin tashin Hakeem yayi suka tafi shida Ahmad
Ya shamsu kuwa yana fita yaje kasuwa yamusu cefane sosai har kaji da lemuka masu sanyi
Yana isa kofar gidansu mai adai daita sahu ya tsaya yabiyashi yafito da ka yansa
Yashiga cikin gidan da sallaman shi
alokacin Husnah tana alolar La asar
Tana ganinshi ta karasa wanke kafarta ta zo takarbeshi tana mishi sannu da zuwa
Yace alolar mekikeyi tace LA asar ya shamsu yace haba Husnah yazaki bari lokacin sallah ya wuce kina da lafiyanki
Kafin tayi magana umma daga kitchen tace ai yau Husnah bataji dadiba ne
Tun da tadawo daga makaranta take kwance kanta naciwo
Ya shamsu yace ashsha barin je nasiyo miki magani
Yanzu zandawo
Husnah ta rike rigar ya shamsu tace wallahi naji sauki yaya
Dama abin da ya haddasa min ciwon kan ma
Wani taro akayi a school dinmu kuma nice presenter
Hayaniya ce yasani ciwon kan amma Dana dawo gida umma tabani magani nasha na kwanta yadaina
Ya shamsu yace kinta tabbata
Husnah tadaga kai alamun ta tabbatar
Abba ne yayi sallama yashigo
Da Leda a hannunsa Husnah ta ajiye Wanda ya shamsu yakawo akan taburma tayi saurin karbar na Abba alkamace Abba ya auno Dan Abba akwai son tuwon alkama dashida ya shamsu
Bayan sun zauna ne ya shamsu yace Husnah dauko kayan can kiraba mana
Husnah ta tashi ta dauko
Plate guda uku da tasawa Abba kajin da kuma Irish potato wato dankalin turawa
Ta ajiye mashi maltina Dan tasan zaifi sonshi
Kafin tasawa umma itama maltina tamata
Sai ta hada musu itada ya shamsu ta dauki lacasera
Ta dauka wa ya shamsu fanta dantasan abinda kowa yakeso
Umma ta ce yau fa shagwaban yatashi Abba yace a din tayi baruwanki ai sunfi kusa yakarasa maganar yana dariya
Husnah tace yauwa Abba fada mata dai
Ya shamsu yayi murmushi Dan yanason yadda suke rayuwarsu cikin son juna acikin gidansu
Suna gamawa Husnah ta tashi tadauko Dan karamin kula tasaka naman da komai yadda sukasha sai wannan lemu sunkai uku
Tasaka a Leda tace ya shamsu wannan na anty kubra ne idan kaje kace mata inji sweet kanwarta
Umma tace kai wannan soyayya da Husnah takewa kubra
Inba auren nan akayi ba hankalin Husnah bazai kwanta ba ba
Abba yace ai soyayyar Dan uwantane yashafi khadijan
Husnah tace gaskiya Abba kana da ganewa wallahi yadda anty kubra takeson ya shamsu yasa na ke ganin girmanta
Shidai shamsu inbanda murmushi ba abinda yakeyi
Nan yawa mahaifinsa da ummansa bayanin yadda sukayi da maigidansa
Abba yace Allah yasa hakan shine mafi alkairi
Kaga girman alkawariko
To haka akeson mutum aduk inda yake ya rike gaskiya
Ya shamsu yace hanekam
Nan yabawa mahaifin nasa kudin gabadaya yace ya ajiye agunsa
Ya tashi yashiga wanka Wanda Husnah ce takai mai yana fitowa yayi alwala zuwa sallar magriba
Bayan ya dawo daga isha ne yadauki kayan da Husnah tabashi yakaiwa kubra
Ya fesa turarensa mai Dan arha duk da talaucin su ya shamsu baya rabuwa da turare danshi mutum ne mai tsafta sosai Dan gado sukayi a wajen iyayensu
Saikuma Husnah tace matsa kaban guri akan tsafta kokadan Husnah bata son datti
Yana isa gidansu kubra ta fito da hijabinta dogo
Duk yadda takai taboye abinda aka mata agida kubra takasa sai da yagane
Yace Lafiya naga fuskarki haka kubra
Kubra tayi yake tace bakomai wallahi abune yafada min a idona amma nacire
Kafin ya shamsu yayi magana wata kanwarta wadda suke uba daya tazo tace wai kizo inji mama kicigaba mata da abinda tasaki
Kubra tace kice inzuwa yarinyar tajuya takoma zuwa cikin gidan
Tausayin kubra Yakama shamsu sosai yace kiyi hakuri kinji watarana sai labari nasan duk akaina kikaganin wulakanci Dan kin ki bada hadin kai
amma namiki alkaqarin komai yazo karshe insha Allah
Yace karbi wannan inji kanwarki tace nakawo miki
Kubra tace Allah sarki Husnah Dan Allah kace mata nagode sosai
Yaciro dubu uku a aljihunsa yace karbi wannan kirike a hanunki
Kubra ta kalleshi ta kalli kudin tace haba sahibina ya daga samun aiki zaka fara barna da kudi kawai kabarshi
Yace ai duk abinda zansamu kina da kaso aciki kikarba kawai kubra idan baki karba ba zaki bata min rai
Cikin sanyin jiki kubra ta karbi kudin
Tace nagode Allah yakara budi yace amin
Maza koma gida kikarasa abinda aka saki karkiyi laifi ko
Tace to sai anjima ko kuma saigobe ba inji ya shamsu
Washa gari dasafe ya shamsu yagama shirin zuwa aiki bayan sun karya
Yafito yace wa Husnah muje ko
Husnah tace to yaya suka wa umma sallama
Suna futa kuwa suka yi sa ar keke napep yaya shamsu yatare musu sukashiga
Suna tafiya suna hira yace inga jakanki tabashi bata kawo komai a ranta ba
Ya shamsu kuwa yafaketa yasaka mata 1000 a ciki dubu daya kenan
Suna zuwa dai dai gate din su Husnah ya shamsu yace wa driver tsaya ta sauka nikuma kayi dani BUK Husnah tasauka tana daga wa ya shamsu hanu
Yayi dai dai dannowar motar copper bash
Yaji lokacin datace ya shamsu kanan ya shamsu ne acikin keke napep din nan
Inkuwa shine zanbisa namishi bayanin komai
aikuwa copper bash yayi ta bin yaya shamsu abaya har yasauka a gate din BUK
Bayan ya shamsu yabiya kudin yayi gaba abinsa
Copper bash yayi parking yafito
Yabi bayan ya shamsu
Har yaje yayi signing yazo kafin yaje can kujerashi kofar
PROFESSOR HAKEEM yazauna
Copper bash yamishi sallama ya shamsu ya amsa yace kozan iya taimakonka
Copper bash yace a daman taimakon nazo nema
amma a gurinka ya shamsu
Yadda copper bash yakirashi ya shamsu yasan duk yadda akayi yasanshi ne
Ya shamsu yanuna mishi kujera
Nan copperbash yafada wa yaya shamsu irin son da yake wa kanwar shi
amma taki bashi dama hakan
Ya shamsu yace bazata ta taba amince maka har sai nabata izini
Umarni nabata nima kuma bazan taba amincewaba har sai nayi bincike akanka kafin nan kuma na tabbatar tana sonka na uku kuma zakamin alkawarin barin ta tayi karatu bayan kinyi aure amma wannan zaizone bayan nayi bincike nagar tarka
Copper bash yace wallahi ya shamsu indai akan asali ne bana shakku aje ayi bincike fata na kawai idan kabincika bani da matsala ka amince min nakawo sadakina gidanku shikadai ne zaisa hankalina yakwanta
Ya shamsu yayi murmushi yace karka damu Allah yashige mana gaba
Nan yawa ya shamsu sallama yatafi
*******
HUSNAH zaune kan kujerar class dinsu teacher din dazata shiga musu ta haihu shiyasa suka samu Free time
Meenat tace gaskiya Husnah baki da kirki yanzu kakan dad dina da mummy na ya mutu amma kikasa Neman gidan mu kije kiwa kakata ta aziyya
Husnah tace afuwan aminyi insha Allah ranar asabar zanzo gidanku nawa kakanmu ta aziyya
Meenat tace kai amma danaji wallahi har na matsu asabar tayi
Hajiya ta taganki labarinki kawai takeji agurina
Husnah tace aikuwa zanzo nagaisheta
Tace amin Allah yasa daddy ma yazo sai kigaisheshi
Kinsan tun yadawo kano aiki duk Saturday yake zuwa yaganni
Husnah tace to Allah yakaimu ranar
Suna haka wata junior tashigo tace anty husnah wai kizo inji uncle bash
Husnah tace OK kice ganinan zuwa
Meenat ta kebe baki tace wai meke tsakaninku da copper bash ne
Husnah tace sirrine amma zakiji nan gaba tashi muje kirakani kawai
Meenat ta tashi jiki a sanyaye tabi Husnah zuwa office din uncle bash
Suna shiga suka gaishe da bash ya amsa idonsa akan Husnah
Takaici Yakama meenat
Dan ita ba namijin datakeso irin copper bash
Tayi shishigin amma bata samu karbuwa ba
Ya kalleta yace zaki iya jiranta a kofa magana zamuyi
Meenat cike da bakin ciki ta fito
Copper bash ya kalli Husnah yace munhadu da ya shamsu
Cikin sauri husnah ta dago kanta da sauri tace meyace maka shikenan nasan yaya zaiyi fishi dani
Copper bash yace karkidamu ba abinda zai miki shima naga alama yana da fahimta
Nan yafada mata yadda sukayi da ya shamsu
Cike da jin dadi Husnah ta tashi tayi hangar waje
Yana kiranta amma taki juyowa saboda kunya
Tana shiga sukacikaro da meenat
Kuka shabe shabe a fuskar meenat
Husnah cikin tashin hankali tace lafiya kuwa meenat cikin rashin sanin mezatace tafara in inna
Tace wallahi bansan menayi wa copper bash ba ya tsani yaganni aguri sai yakoreni
Husnah tace kiyi hakuri zanmishi magana kuma I sha Allah zaiyi dai dai
Meenat ta share hawayenta tace Husnah na tambayeki meketsakaninku da shi baki fada min ba
Husnah tayi murmushi tabata labarin komai
Meenat tace yanzu kinaso kice min kun Dade kuna soyayya da shi
Husnah tayi murmushi tace a
Amma ni banbashi daman zuwa gidan mu ba
Shine yanzu yake cemin ya wa yayana magana
Meenat tarike kai alamun jiri nason yarda ita
Husnah ta taimaka mata tazauna tace Amina Hakeem anya lafiyarki kalau kuwa
Gaskiya kitashi mu dispensary
Abaki magani
Meenat tace gida ma zantafi tai maka min da phone dina acikin bag
Husnah tabude jakar meenat taga wasu hadaddun wayoyi masu tsadar gaske kuda biyu aciki
Ta kwaso duka tace gasu meenat ta karbi daya takira driver din ta
Taba wa Husnah wayar ta mayar mata dashi jaka
******
Bayan kwana hudu ankai sadakin yaya shamsu gidansu kubra
Sannan kuma Abba yasai block da yashi ma aikata sukafara aikin gyaran inda ya shamsu zai zauna acikin gidan ne amma ciki da fall da bayan gida acikinshi
Har Dan karamin kitchen dinta basai ta fito tsakar gida ba
Komai nasu aciki yake
Umma da Husnah sukaje kasuwa suka nemo akwatunansu masu kyau guda uku
Aciki akafara zuba kayan lefe
Wanda yanzu kusan duk asabar sai sunfita kasuwa
Dai dai gwargwado dai aka hada lefen ya shamsu
Aka kai gidansu kubra
Nan da sati biyu za adaura auren
Dubu ashirin ya shamsu yaba wa kubra tayi hidiman biki dashi
*****
Hakeem zaune kan kujerar yana hada wani muhimman file
Sai Ahmad yashigo yace wai baka gama ba har yanzu kasan time kuwa
Hakeem yace nagani ai nan da Kaduna dai insha Allah komai dare
Ahmad yace Allah yasa nidai kai nake jira kawai nagama shirina
Hakeem yayi dariya yace bantaba ganin ango merawankai irinka ba Ahmad
Ahmad yayi dariya yace ai gwamma ni kai inkatashi karawa ai bansan dokin dazakayi ba
Hakeem yayi murmushi dayake kara fito da zallan kyanshi
Yace tabbas kuwa lokaci yakusa zuwa inji ajikina nakusa samun choice dina sai dai bansan a inabane
Ahmad yace kai amma fa akwai rigima Dan madam Laila zatayi rikici bakadanba
Hakeem yayi murmushi yace zatawa kanta danzan iya komai akan matata da zan aura Dan itace zabina
Kaga kuwa ta taka a sannu
Ahmad yace wallahi man I like your style gaskiya zanso Gina gidana kaman yadda kake handling naka
Hakeem yayi murmushi yace banbaka shawarar hakanba
Dan na tabbatar Aisha ba halinsu daya da Laila ba
Kagakuwa ba za amusu hukunci iri dayaba ko
Ahamad yace gaskiya Dan hankalin Aishat nagani yasa har nayi shaawar aurenta
Ya shamsu yashigo ya musu sallama suka amsa suka mika mishi hanu suka gaisa
Ya shamsu yace wa Hakeem gani yallabai
Hakeem yace dama zanfada maka ne zamu tafi Kaduna
Sai nan da sati daya zamu dawo
Hakeem yadauko invitation card na auren Ahmad
Yabawa ya shamsu yace muna gayya tarka daurin aure
Ya shamsu yayi murmushi yace masha Allah
Allah yabasu zaman Lafiya
Sai dai ranar yazo dai dai danawa auren
Hakeem yakalleshi yace har ansa rana baka fada minba malam shamsu
Dama bakayi niyyar gayya tarmu bakenan kokana ganin inka fada ma bazamu bane
Ya shamsu yayi murmushi kawai yace aikuna kokari ma da aiki
Kuma har ga Allah bani tunanin inna Baku invitation zakuzoba
Saboda matsayinmu badayaba
Hakeem da Ahmad suka kalli juna
Ahmad yace haba malam shamsu karkace haka saikasa muga kaman mu ba mutane bane
Ya shamsu yace to afuwan
Nayi kuskure
Hakeem yace to yanzu dai bazamu samu zuwaba amma muna maka fatan alkairi
Tace ban account number din ka inbada nawa gudumawar asiyawa amarya kaji
Ya shamsu yace wannan yana daga cikin dalilin dayasa naji fada muku zamanin yanzu kowa yana fama da kanshi
Dan Allah kabarshi karka damu kanka
Hakeem yace karka damu ni nayi niyya kuma kasan bakyau maida hanun kyauta baya
Ya shamsu yace hakane yakaranto wa Hakeem number account din
Shima Ahmad yanaji kuma ya kwashe number.
Hakeem yace zakaji alert Allah yabada zaman Lafiya
Ya shamsu yace ameen nagode
Sukayi sallama har wajen mota
*****
Da daddare suna zaune tsakar gida ya shamsu yace Abba da ina son ba wa manemin auran Husnah dama yaturo iyayensa
Kaga tana gama makaranta sai aiyi aurenko
Baban yace ai nalura yaron nan bashir kaman da gaske yakeyi
Umma ta ce sau biyu yana kawo mahaifiyarsa muna gaisawa
Shamsu yace alhamdulillahi gaskiya konina yaba da bashir
Kara shigowar sako yaji a wayarsa yaduba yaga alert ne na dubu Dari biyardaga professor Ahmad
Kafin yayi magana wani alert din yasake fadowa daga boss dinshi a office
Wato professor Hakeem
Shima dai dubu Dari biyar dinne yaturo
Sun hada mishi 1 million NIRA cas su biyu suka bashi
Nan shamsu yakalli mahifinsa yafada musu
Abba yace kai amma wannan uban gida naka Allah yasaka mishi da alkairi
Umma tace ameen wallahi ko a mafarki bamutaba tunanin samun dubu Dari nan kusaba
Ballantana har million daya Allah yasaka musu da alkairi
Kai kuma saika kazauna dasu da zuciya daya
Nan dai ya shamsu yakira Hakeem a waya yace ga Abba na zai muku godiya
Hakeem yace haba shamsu yanzu saboda kyautar da baitaka kara ya karya ba zaka wahalar da Abba wajen gode mana
To gaskiya indai Dan inbari Abba yagode min ne zankashe wayata
Insha Allah idan nadawo zanzo nagaisheshi da ka ina amma banda godiya tsakanin malam shamsu
Ka gaida umma da kanwarmu
Sai da safe
Dif
Hakeem yakashe wayarsa
Dama wayar ya shamsu a handsfree take duk su Abba sunji komai
Abba yace gaskiya duk inda akeneman shugaba nagari wannan yaro ya kai
Allah yarabashi da sharrin duniya Lafiya
Ameen Ameen gaskiya dai bantabajin mekudi hakaba da Jan talakawa ajikinsa kamar wannan uban gidan naka
Nan dai suka ta tatattaunawa akan yadda za ayi da kudin
Abba da umma dai suka barmai zabi
Ya shamsu yace shikenan Allah yakaimu gobe aga yadda za ayi
Itakuwa Husnah Allah Allah take safiya tayi taje school taba wa aminiyarta labari
Za a ba copper bash daman turowa gidansu
Washagari Husnah da meenat suna zaune a inda suka saba zama
Husnah tabata labarin za a ba copper bash daman turowa gidansu
aikuwa gaban Meenat yatsinke ras
Wani tashin hankali ya ziyarceta
Tarasa meyake mata dadi
aikuwa har aka tashi daga school meenat batadawo dai dai ba
Tana kallo copper bash ya budewa Husnah gaban motarshi zai kaita gida
Dan tunda aka sanshi yaroki alfarmar zai dinga dawo da Husnah gida idan antashi
Da kyar aka yarda mashi Dan saida yahada da mom dinshi
Husnah tana daga wa meenat hanu Ina AMIN ABDUL HAKEEM kam batasan tanayiba
Ta Lula dunitar tunani
**
MEENAT tana zuwa gida tafada cinyar hajiya rukayya kakanta
Tafashe da kuka maitsanani
Hankalin hajiya rukayya yatashi Dan ta dauki soyayyar duniya ta daura akan 'yar jikan nata bakaramin so takewa Amina ba
Nan dai dakyar tasamu meenat tayi magana
Tace hajiya nashiga uku nakusan mutuwa
Wallahi idan ban auri copper bash hajiya zaku iya rasani dan mutuwa zanyi
Nan hajiya rukayya tace kwantar da hankalinki kimin bayanin komai
Nan meenat ta kwashe komai tafada mata
Ba abinda yafi burge Hajiya rukayya a labarin sai jin cewan
Bash Dan hamshakin mai kudine a kano
Tace kwantar da hankalinki kaman yazama naki ma anfama
Aure shida Husnah kuma yazama tarihi
Zanje Kaduna aiko
Zan baki mamaki bash da bakinshi zaice yanasonki
Next page
Your comments is needed fans
Kamar yadda nayi typing metsayi haka nakeson
Comments dinki da tsayi
Wallahi comments mai tsayi yana burgeni
Sosai
Ina yinku masoya AKWAI LOKACI
[05/05, 11:08 AM] UMMU AFAN :
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN
FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION
F.C.T.W.A
HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITERS OF THE NATION
DEDICATE THIS PAGE TO adda khadija and shamsu ina yinki over sister
Dik ina ganin comment din ki akan novel di na
Wato AKWAI LOKACI
Daya bayan daya zakuji sunanku masoya AKWAI LOKACI FANS GROUP keep comments kawai
AKWAI LOKACI
PAGE 51 to 60
Ya shamsu ya yagyara wa iyayensa gida dai dai gwargwado
Har anyi fenti sabo gida sai kamshin sabon fenti yakeyi da sabon siminti
Ya zuba wa umma sabbin kujeru dai dai karfinshi
Sannan shima ya zuba a dakinsu shida kubra
Yasai TV guda biyu dayasa wa iyayensa daya kuma yasa a sashinsa
Sannan kuma yama umman shi dinkuna kala biyar na fitan biki sai yama abbanshi ma kala biyar shima masu kyau shadda da kuma yadi
Umma har da hijab uku da ta kallamansu
Uku
Sai Husnah kuma yamata kusan kala bakwai dai dai karfinsa
Ya hada mata da mayafai guda biyar da takalman ta hudu
Sai kayan kwalliya da dai sauransu
Yafi kashe wa Husnah kudi acewanshi ita tafi bukatar hakan
Yama kubra ma kayan fitan biki yace kartayi amfani Dana lefenta
Sannan kuma yasa wa abbanshi kaya a shago Dan dama Abba yana shawa ar sana ar awu na hatsi
*****
Yauce ranar daurin auren shamsu da amaryarsa khadija
Komai yatafi yadda akeso
ankai amarya dakinta dake cikin gidan su shamsu
****
an daura auren Ahmad da amaryarsa Aisha
Suna shirin zuwa dinner ne Wanda PROFESSOR HAKEEM ya hada wa babban abokinsa
Hakeem da Ahmad sunyi shiga iri daya wani hadadden suit suka saka ango yasaka baki nacikin ja
Sai Hakeem kuma yasaka brown colour na cikin sa fari
Duk Wanda ya kalli PROF HAKEEM sai yasake kallonshi
'Yam mata sai rawankai suke musam man kawayen amarya
Laila ma taci ado cikin wani tsadadden less Wanda tayi order daga malesia
Tayi kyau kan nan yasha gashin doki
Fuska kuma yaci bleaching kana ganinta dai kasan anci duniya
Ango yashiga mota zuwa gurin dinner
Hakeem yabude mishi bayan mota Laila kuma ta babbar kawar amarya kuma ta bude wa amarya dayan gefen tashiga
Hakeem ne zaija motar ahmad yace Man please kamin wata alfarma mana
Hakeem yace ina sauraronka malam ango
Ahmad yace kasan idan muisa wajen babbar kawar Aisha ce zata bude mata kofa tunda kai kadaine a gaban motar ta shiga muje kawai
Hakeem yayi shiru alamun ya amince kenan
Shine rahma kawar amarya tashige gaban mota tana gaida Hakeem ya amsa a dakile kaman bayaso
Suna isa kuwa bayan Hakeem yayi parking aikuwa har 'yan gulma sunje sun sanar da Laila cewan ga Mijinta ya dauko budurwa a gaban mota
ai kuwa tafito kaman wata mahaukaciya dai dai lokacin da rahma kawar amarya take fitowa daga motar Hakeem
aikuwa rahma batayi tsammani ba sai taji mari kau sannan kuma akasa kafa aka kwasheta
aikuwa yazo da tsautsayi rahma tabuga kai sosai take kuwa ta suma
aikuwa cikin tsannanin bacinrai Hakeem yadauki hanu ya zabga wa Laila mari yasake kwasheta da mari
Nan fa mutane aka taru ganin wannan Abu da Laila ta aikata
Nan da nan 'yan uwan rahma dama suma suna gun sukace basu yarda bayan ansa mata ruwa ta farka
Hakeem yace kinayin abin kika dama ina kyaleki idan zanyi aure kin isa kiha nanine
To barin fada miki daga yau kikasake min dabban ci irin haka wallahi zanyi maganin ki ban wawaiya kawai
Wasu da basusan suwayeba
Wata 'yar dattijuwa ta matso tace haba 'yar nan Kinsan fa yaran yanzu ba a hanasu auren abinda sukeso koda kuwa iyayensu ne
Ballantana keda gani dai baki haifeshi saidai kizama yarshi aisai hakuri
Tajuya kan Hakeem tace haba d'ana da hankalinka zaka mari yayarka a cikin mutane akan mace
Wasu abin dariya yabasu wasu kunya wasu kuma haushi
Musammam meenat cikin gatsali tafito daga cikin taron
Tacewa matar nan dalla malama kirufemana baki
Wayafada miki kanintane dazakisa mutane agaba da surutu to banana ne itakuma mamana ne Dan haka kikama gabanki bamason muna furci
Wato cikin tsananin bacin rai Hakeem yadanko Amina yayi mota da ita ya wurga ta ta tashi motar sai gida
aikuwa Laila tace shikenan zaikashe min 'yartawa Dan zata kwacewa uwarta 'yanci
Tana ihu tana kokarin shiga mota sai saiga motan police nan sunzo tafiya da ita 'yan uwan rahma kawar amaryace suka dauko 'yansanda aikuwa suka tafi da Laila
Hankalin Ahmad yatashi yace wa Aisha amarya tayi hakuri bari yakira akawo mishi mota subi bayan Hakeem Dan komai zaiya faruwa
Hakeem na isa gidansu yayi sashen sa Meenat ya dauki belt dukanta yasoma
Kuka sosai meenat take tana bashi hakuri
Wayyo Allah daddy kayi hakuri wallahi bazan sakeba yace Ashe baki da mutunci kikalli kaman wannan matar kimata rashin kunya ko
Abinda uwarki da kakanki suka koya miki ko
To ba agidana ba Dan ubanki
Mummy hafsat ce yashigo da kyar ta karbi meenat agurin uban
Hakeem ya kalli mummy yace mummy Dan Allah bana son yarinyar nan ta koma gurinsu
Kwatata sunbata wa yarinya tarbiyya
Mummy hafsat tace wai meyafarune nan Hakeem yafada wa mummy hafsat komai harda dabbancin da uwarta tayi a wajen dinner
Mummy hafsat tayi salati tace yanzu wadan nan mutane bazasu canja haliba gashi harsuna Neman bata mana jika
Kaman daga sama kuwa suka ance sannu masu tarbiyya
Dana nasan ba Wanda yake haddasa fituna saike hafsat
To wallahi anzo gurin da banzan bariba dan me zaudauki hanu yata dukan matarshi acikin bainar jama a
Mummyn Hakeem tace aini abinda Hakeem yayi amin dai dai duk abinda Laila takeyi tasamu daurin gidinkine yaya rukayya
Hajiya rukayya tace wato kekikabashi daman yadauki karuwa a mota ko
Mummyn Hakeem tace ya isa haka yaya rukayya wallahi zanyadda da komai amma banda mummunan kazafi akan Abdul Hakeem
To wai ma da kuke wannan haukan wayace muku Hakeem bazai kara aure ba
ai Karin aure akan Hakeem wajibine Dan wallahi koshi baiyi niyya ba nizansashi aure dolene
aikuwa hajiya rukayya tafashe da kuka tace yanzu hafsat nizaki cewa mahaukata ina matsayin yar mijinki kidubi tsaban idona kice muna hauka
Mummy hafsat tace duk abinda yafaru kokuka janyo
Kuma wannan yarinya da kuka sangarta bazata koma wajenkuba
Zanriketa har Allah yasa tagane gaskiya tadawo hanya bakaman Ku da kuka bata ba
Hajiya rukayya tace wannan kuma baki isaba hafsat kinyi kadan kirabani da jikata
Mummy hafsat tace zancen kikeso
Tana amina fuuuuuu suka bar falon
Hakeem kuwa barin falon yayi zuwa dakinsa
Sukabar hajiya rukayya kaman tafashe dan bakin ciki
Wayar hajiya rukayya tayi kara taduba taga Suby ce kanwar Laila tace kekuma ya akayi
Suby cikin tashin hankali tace mama gamunan a police station ankulle anty Laila
Hajiya rukayya tace wani station din kuke
Nan tafada mata tafita zuwa police station din
Hakeem yana shiga bedroom dinshi wanka yashiga
Kafin yafito yadan kwanta yana tunanin bakin hali irin na Laila da 'yan uwanta
**
alhaji abubakar yana office din shi azaune saboda yayi baki daga India
Sai yaji kiran yayarshi hajiya rukayya
Yadauka tare da sallama
Hajiya rukayya tafashe da kuka tace duk inda kake kazo gida ba Lafiya
Matarka da 'danka zasukashemin 'yata da jikata
alhaji abuabakar yace subahanalla ganin zuwa yaya kidaina kukan Dan Allah
Ya kashe wayar yadau hanyar gida
Yana zuwa yasamu yayansa hajiya rukayya a kofar gidanshi
Yafito amota da sauri yace mekefaruwa ne haka
Nan dai ta kwashe karya da gaskiya tafada mashi yace yanzu kishiga mota muji police station din ayi belinta
Inyaso sai mudawo gida a yi magana
Hajiya rukayya tashiga mota suka nufi can police station din
Suna isa tun kamin ayi parking suka ga Ahmad da Laila
Ahmad yaga motar daddyn Hakeem sai yakaraso gurin motar yagai da daddy
Daddy yace sunbaka belin kenan
Ahmad yace a amma dakyar suka bayar sai da nasa hanun zata je har gida tabawa yarinyar data sumar hakuri
Daddy yace Allah yarufa asiri kaima kayi kokari Ahmad Allah yabaku masu yimuku
Ahmad yace ameen daddy barin karasa gidan
Daddy yace wa Laila tashiga bayan motar sutafi tabude bayan tashiga
Ta madubi hajiya rukayya tace Dan Allah kalli yadda suka mayar min yarinya saikace wacce bata da gata
Alhaji abubakar dai baice komai har suka isa gida
Duk yatarasu a falo Hakeem na zaune daddy yace banji daddyn abinda yafaruba naji komai
amma ina insan kai Hakeem wace mata kadauko agaban mota nan Hakeem yawa mahaifinsa bayanin
Hajiya rukayya tace karya kakeyi kana nufin Laila Karya zata maka
Mummyn Hakeem tace to ita Lailar uwarshice dabazata mishi karya ba
Daddyn Hakeem ya ce ban baki iznin maganaba hafsatu kiyi shiru
Mummy hafsat tayi kwafa
Nan dai daddy yayi musu nasiha meshiga jiki
Hajiya rukayya tace sai maganar yarinya sunce wai bazan koma da Amina ba
Daddy ya kalli Hakeem yace yazakayi haka bayan kuma yarinya dasu tasaba
Hakeem yace daddy idan har yarinyar nan zata koma to ta gaggauta fito da miji tana gama secondary school kawai aiyi aure
Dan wannan da irin tarbiyyar dasuka bata nan gaba zata iya fin karfin mutane
Mummy hafsat tace wannan shawarar taka tayi dai dai
Dan bazanso jikata ta acikin wannan rayuwar da ba asan nagaba ba
Hajiya rukayya tace kaga abubakar kashiga tskanina da matarka
Daddy Hakeem yace wa mummy hafsat Dan Allah karkisake cewa komai sai na baki dama
Nan alhaji abubakar yace zata koma amma gaskiya nima anan naba da goyan bayan tafitar da miji kafin nan da tagama secondary school
Hajiya rukayya tace wannan ba abin muwabane
Abamu nan wani lokaci saurayinta zaizo dakanshi yagaisheku aitana dashi
Alhaji abubakar yace to alhamdullila Dan Allah komai ya wuce
Ke Laila ba wa mijinki hakuri
aikuwa hajiya rukayya tace ya za ace tabashi hakuri bayan shiyakamata yabata hakuri daya dauki hanu ya tsinka mata mari acikin mutane
Ganin abinda hajiya rukayya takeyi yasa Hakeem barin falon yayi sashinsa
Yana fita suka hadu da Ahmad
Hakeem yace ango
Ahmad yace komaidai yakoma dai dai ko Hakeem yace barin shiga nashirya nazo muwuce
Muje musallami friends dinmu na nesa
Ahmad yace karka damu nagama komai
Hakeem yace yanzu har ka rakasu airport Ahmad yace kwarai
Hakeem yace amayar fa Ahmad yayi murmushi yace ai andade da tafiya da amarya
Dan dazu nakirata harsun huta ma
Yan uwanta ma sun kamo hanyar dawowa
Hakeem yace to ai sai musamu mushirya muwuce muma ko karnayi laifi dayawa agurin Madam Aisha
Ahmad yayi murmushi yace a haba aitasan komai
Idan taga bamuzo ba tasan abinda yatsare mu
Hakeem yace yau zaka shiga dakin amaryar ka
Barima kagani Hakeem yashige sashinsa
Yafada bathroom yayi wanka
Yana gama shiri cikin shadda marun colour ya balain masa kyau kamar danshi akayi shaddar
Yana fesa turare Laila tashigo
Tace daddyn meenat naga kaman tafiya zakayi baka sallamemuba
Hakeem ya watsa mata wani kallo
Yace mekuke bukata tace kayan abinci da na amfanin gida yace kizauna kirubuta duk abinda bukata zansa driver yakawo muku
Daga yau nabar baki daman da kikesamu harkike ganin kaman kinfi karfina sai yadda kikayi dani ko
cikin tashin Hankali Laila tace Dan Allah karkamin wannan horon kasan nasaba sayan abinda nake bukata da kaina
Hakeem yayi murmushi mugunta yace nawa nakebaki dama
Laila tace dubu Dari uku duk wata
Hakeem yace hakane ko ta ce a hakane
Yace kedawa nabari agidan nan tace nikadai
Yace good yanzu duk wata zanturo miki dubu hamsin
Kekadai dai nasan zasu isheki
Yana gama fadan haka yayi waje da brief case dinshi
Haukane Kane kawai Laila batayi ba
Amma hankalinsa yatashi sosai nan tadauki gyalanta tayi gurin mahaifiyarta hajiya rukayya
****
Bayan wata shida professor Hakeem zaune kan kujerar office din shi
Yadauki wayarshi yakira yaya shamsu
Ya shamsu yashigo yace Barka dai yallabai sannu da aiki Hakeem yayi murmushi yace yauwa malam shamsu
Yace ga wannan ya shamsu yakarba yace ina zankai yallabai
Hakeem yayi murmushi yace nakane malam shamsu zaka kaiya dubawa kagani
Ya shamsu yabude Aikuwa ya shamsu ya dago ido yakalli PROF Hakeem
Yace admission fa nake gani yallabai
Hakeem yace yes nasan kana da burin karatu a rayuwarka
Iyakacin zamana da kai na lura kai mutum ne mai son karatu
So yanzu ga dama nan malam shamsu zaka iya farawa nagama komai har registration da komai sai dai ka kai credentials dinka asa maka a file
Kuma daga Level two zakafara nariga nayi komai
A department of business administration
Ya shamsu baisan lokacin da tashiba yace yallabai gaskiya ba abinda zance da sai dai Allah yabaka abinda kake nema duniya da lahira
Allah ya jikan mahaifanka ya ramaka zuria
Hakeem yace ameen malam shamsu na gode kwarai da adduarka a gareni
Sai dai ni har yanzu baka taba tambayata wani Abu da yashafi rayuwata ba malam shamsu koba bukatar sanin daga ina nafito ne
Ya shamsu yayi murmushi yace zanso sanin tarihinka dakuma tarihin nagartarka a rayuwar alumma
Nan professor Hakeem yayi murmushi
Yabashi labarin rayuwarshi kaf bai boye mai komai ba
Ya shamsu yaja numfashi yace yanzu tun kana 20years kayi aure kenan
Hakeem yace kwaraikuwa ina da 17 year old girl yanzu haka
Da mamaki ya shamsu ya kalleshi yace masha Allah
Gaskiya kai kam duk abinda ake nema a rayuwa Allah yabaka
Hakeem yace zakasan daughter nawa ma ai duk sati tana zuwa ranar alhamis
Ya shamsu ko wacce kake cewa amina
Hakeem yace yes ita nake nufi
Ya shamsu yayi shiru yace am sorry sir wallahi duk azatona madam dinkace
Hakeem yayi murmushi yace 'yata ne nacikina
Ya shamsu yace masha Allah wallahi gaskiya labarinka ya burgeni
Bude kofar office akayi Prof Ahmad ne yashigo yace
Kace kuna tare da malam shamsu ne Hakeem yace ai tundazu muke hira anan
Ahmad yabawa ya shamsu hanu sukayi gaisa
Ahmad yace wa Hakeem madam fa tagama abincin rana yakamata muje muyi lunch
Hakeem yace gaskiya dai nima yaka mata nasan abinyi
Kaga madam Aisha sai tadinga hutawa ko
Ahmad yace Aisha ce zagaji wai caf yanzu kasan Allah da zankoma inje cin abinci nikadai sai tambayi ina kake baka biyoni ba
Duk randa kake azumi haka nake fama da ita
Hakeem yace Allah sarki madam tana tausaya wa marayan Allah
Ahmad yayi murmushi yace maraya a kano ba
Ahmad ya kalli ya shamsu yace malam shamsu gaskiya yau Na kamaka sai munje kaci abincin amarya
Hakeem yace aifa dai kam tunda shi yana mana rowan abincin amaryarsa da kuma ladan da zamu samu wajen gaida su umma da Abba
Ya shamsu yayi murmushi yace bahaka bane banyi tunanin inna gayyaceku zakujeba shiyasa
Hakeem yayi murmushi yace saboda gamu aljanu bama cikin jinsin mutane ko
Ahmad yayi dariya yace zamu baka mamaki sai dai kaganmu agidanka
Ya shamsu yace ina zuba ido ,nan dai kyar ya shamsu ya yarda suka je dashi cin lunch
Suna kan dining din Ahmad suna cin abinci itakuma Aisha tana kan two sitter
Tace wa Ahmad honey yaushe zaka kaini yawo kasan fa bansan kowaba a kano kuma inason inga gari
Ahmad yace zan hadaki da kawance da madam din malam shamsu kinga saikije mata itama tazo miki
amma sai malam shamsu ya amince
Ya shamsu yayi dariya yace ina zata iya erea mu ai sai mu
Hakeem yace kaidai kawai malam shamsu kace bazaka bar madam dinka suyi zumunciba
Ya shamsu yayi murmushi yace shikenan Allah yashige mana gaba
Sukace amin
Dazasu tafi ne Aisha tace wa ya shamsu Dan Allah agaisar mata da kawarta kafin suhadu
Ya shamsu yace zataji insha Allah
****
Bayan wata biyu da fara zuwa makarantar shi
Ankawo sadakin Husnah
Harda kayan lefe akwati gomashabiyu cas
Sadaki kuma naira dubu Dari biyu
Yanzu haka ana jiran suyi waec da neco ne kawai asha biki
Shakuwa ce maitsanani da kaunar juna tsakanin copper bash da Husnah
***
Meenat zaune kan carpet dinsu hajiya rukayya tadawo daga tafiyan datayine wajen boka Dan karbowa meenat maganin MALLAKA da zata mallake copper bash yazama nata
Hajiya rukayya tace a abinci zaki zuba mishi idan yaci zai kamu da soyayyarki Wanda ko uwarsa bazai mata Sannan kuma zaiji ya tsani Husnah aduniya
Cikin farincki amina tace kai Allah yabar minke kakus dina
Laila dake gefe tana kallonsu Dan itama jiya tazo
Laila tace hajiya Nifa ba abinda kika karbo min Akan daddyn meenat
Hajiya rukayya tace ai wannan yaro fa asiri bazai kamashi ba sai dai kawai musa a kawar mana dashi
Har lahira kinga masamu dukiya muyi yadda mukeso da shi
Meenat caf daddyn nawa za a kashe wallahi bazaiyi yiwuba
Haka kawai ita mummyn bata San yadda zata karbi kudi a ahanunshi ba sai ankasheshi
Hajiya rukayya tace to ai murasa yadda zamuyi da wannan uban naki ne jikalle
Meenat tace natabbata baza arasa wani hanyar ba kudaiyi tunanin
Husnah zaune a dakin amarya kubra tana asigment dinta
Kubra tace kedai Husnah kinji dadi wallahi wannan irin gashi aikoda shi zaki yaki mijinki balantana ga uwa uba kyau da diri duk
Allah yabaki Husnah tadago manyan idonta ta kalli kubra tayi murmushi
Tace anty kubra kenan sai kace ke
Kubra tayi murmushi tace zakicimin fuska ko ai idan dai kina guri muai saidai muyi shiru
Husnah tace banda zuga fa matar yaya
Husnah ta fashe da dariya ita kadai
Sai kubra tace meyabaki dariya
Husnah tace kawai danku nakeson gani keda yaya wannan irin kyau da kyau ai sai dai kuhaifo mana aljani Dan kyau fa
Kafin Husnah takarasa maganarta kubra ta dauki pilon kujerarta zata kwadawa Husnah
Husnah ta tashi ta gudu dai dai shigowar ya shamsu
Yace lafiya kekuma Husnah tace Lafiya qlw ya shamsu
anty kubra ce ta biyoni
Umma dake kan sallaya a faranda tace o keda kubra dai zanga ranar rabuwanku akwai drama
Ya shamsu yayi murmushi yace sai tabita ai
Umma tayi murmushi tace andawo Dan albarka ya makarantar
Ya shamsu yace alhamdulillah umma bara nayi wanka sai nazo muyi hira umma tace
To banana
Ya shamsu yashiga dakinsa yasami kubra zaune ta tashi tana mishi sannu da da wowa
Yayi murmushi Dan kullum son matanshi karuwa yakeyi saboda yadda take matukar mutunta 'yan uwanshi hakan nasa yana Dada jinta cikin ranshi
Murmushi yasakar mata yace kamu hanunta yace meya hadaki da kanwartaki
Kubra ta yi murmushi tace tsokanata tayi shiyasa tagudu
Wai karmu haifi aljanu Dan kyau fa
Ya shamsu yayi dariya yace ai haka tace
Shiyasa na tambayeta tamin shiru
Washagari da safe bayan anfito break sai copper bash yakira Husnah office din sa Dan ta serving din abinci Dan baya break shima sai goma
Shiyasa daga gida akekawo mishi
Ba kullum yake kiran Husnah ba Dan idan yakirata bata zuwa Dan kare mutuncin kanta
Ba kullum ana ganinta a office din shi ba
Suna zaune itada meenat wayarta yayi kara ta dauka tace aslammu ailaikum
Yace wa alaikumussalam my love
Husnah tayi murmushi tace inajinka ranka yadade
Yace alfarma nake nema kizo Dan Allah ki serving dina break fast
Husnah takalli meenat tace kice to Dan Allah
Husnah tace shikenan ganin nan zuwa
Husnah takashe wayar ta kalli meenat tace meyasa kikasa na amsa mishi
Meenat tace tace haba kekuwa Dan ya roki alfarmar yau dai ai sai kiyi mishi
Husnah tace bazaki gane bane
amma tashi muje kiraka ni dama abinda meenat kesonji
Suna isa office din copper bash
Yace wa amina taje cikin motarahi zataga basket din abinci ta dauko mishi
Aikuwa amina cike da farinciki ta wuce class dinsu ta dauko maganin ta da zata sawa bash
Sai da ta bude flask din ta zuzzuba dama soyayyan doya da kwai ne
Sai ruwan tea
Aikuwa ta zuba ta dauka takai mai
Husnah tayi serving dinshi
Yayi dai dai lokacin komarwar su class
Husnah tace zata wuce class yace ita bazataciba
Tace ai yau alhamis suna tana azumi
Yace yayi kyau kikula min da kanki kinji ko
Tayi murmushi dimple dinta suka lutsa yace I like your smile
Husnah tace thanks
Ta wuce zuwa class Wanda tuni meenat tarigata
Yagama break dinshi tsaf
Washagari jumma a
Dama bashir yasaba zuwa duk Jumma a
Husnah zaune tagama shirinta tsaf bashir kawai take jira
Kubra tace gaskiya dai tunda yasaba kiranki kuma yasaba zuwa yakamata kikarashi kiji kolafiya
Husnah ta yarda da shawarar anty kubra
Takira bashir yakai sau goma amma yaki dauka sai a kiran karshe
Yadauka yace dalla malama me na damuna haka
Kebari nafada miki karkisake kirana daga yau banza Mara mutunci
Na tsaneki Husnah bana son jin sunanki kifita a rayuwata
Sadakina da kayan aurena duk za azo karba kafin yafadi wata magana
Husnah ta yanke jiki ta fadi
Ya yi dai dai da shigowar kubra
Aikuwa kubra tayi ihu umma da abba da ya shamsu suka zo
Next page
Your comments is needed fans
Ina dadin comment din Ku fan's
Ina alfahari da Ku
[05/05, 11:08 AM] UMMU AFAN :
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN
FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION
F.C.T.W.A
HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITERS OF THE NATION
DEDICATE THIS PAGE TO MOM IMAN &HANIFA
MUCH LOVE TO YOUR COMMENTS SIS
KEEP IT UP
Ina alfahari daku masoya novel din AKWAI LOKACI
daya bayan daya zakuji sunanku ina bin comments dinku sosai
Allah yabar zumunci
AKWAI LOKACI
PAGE 61 to 65
HUSNAH kan cinyar umma ansamata ruwa ta farfado
Ya shamsu yace Husnah kiyi magana meya haddasa miki wannan suman
Husnah ba baki sai kuka
Abba yace ke kubra kukinsan abinda yafaru
Kubra tace gaskiya dai ba abinda yafaru sai takira bashir
Bansan meyace mata ba kuma nasan tabbas abinda yasameta yana da alaka da bashir
Kafin suyi wata magana wasu mata sukayi sallama suka shigo
Umma ta sannunku da zuwa suka yauwa
Umma ta ce sannunku da zuwa sukace yauwa Allah yasa nan ne gidan su Husnah ba bata mukayi ba
Ya shamsu ya kallesu yace nan
Suka shiga yiwa gidan kallon wulankanci suna kebe baki
Dayar tace ni wallahi dama banga gamin kifi da kaska ba da za ace wai bashir yarsa gidan dazai nemi matar aure sai gidan matsiyata
Wato kubran ya shamsu wani takaici ya debeta ta tashi
Ta cakumo wuyar wacce tayi maganar
Ta wanke ta da mari zata kara mata ne ya shamsu yariketa
Kubra tace Dan Allah ya shamsu kabari
Nakara mata
Inbanda cin mutunci kishigo har gidan mu kuce zakuci mana zarafi
To wallahi ubanku yayi kadan
Ita wacce aka Mara tace kika mareni to wallahi sai kinyi da nasanin marina
Kuma abinda yakawo muda ma munzo abamu kayan auren mu da sadakinmu
Mai auren yace bayayi mudama bason gidan matsyata irinku mukeba
Cikin tace kune kuwa babban matsiyata wadda basusan darajan nagaba dasuba
Abba yace wa kubra shiga daki
Kubra tabi maganar Abba tayi dakin
Abba yace wa ya shamsu fito musu da kayansu
Ya shamsu yafito da kayan daya bayan daya
Umma ta ce kuna iya kwashewa kufita mana daga gida ko
Ita wacce aka Mara tace aiko bakuce mufita zamu fita ehe
Ya shamsu yace ke idan kina rashin kunyarki ya tsaya iya kan dai dai ke banda iyayena
Kwarjinin ya shamsu ya musu suka kasa mishi rashin kunyar
Nan da nan suka fara jidan kayansu suna fita dashi
Ya shamsu yashiga daki yadauko musu sadakinsu yakai musu har gurin mota
Yace gashi sai Ku hada basai wani yasake zuwa mana gida
Suka karba shiru Dan sunkasa magana ma
Ya shamsu yashiga gida yaga yadda Husnah take kuka yace kiyi shiru kidaina kuka kinji yar kanwata
Allah zai miki canji da mafi alkairi
Umma tace gaskiya yaron nan yabani mamaki yanzu memuka mishi da zai mana wannan cin mutunci
Abba yace ai sai agode wa Allah ba akaiga aurenba
Da anyi auren ne ya wulakanta mana yarinya ai bazamu ji dadi ba
Ya shamsu yayi ajiyan zuciya yace shiyasa ba kuwani maikudi ake yarda da soyayyrashi akan talaka ba
Yayi amfani da talaucin mu ne yasa har ya iya yin abin da yayi
Amma bakomai watarana sai labari
Shiyasa ni kwatata yanzu bazan sake wa Husnah auren mai kudi Ba
Gwamma ta auri dai dai ita sayi arzikin tare zaifi ganin mutuncinta
Umma ta ce wallahi na goyi bayanka
Dari bisa Dari
Abba yace muna namune kuma Allah na nasa Allah yazaba mana abinda yafi alkairi
Sukace amin
Nan akayi ta rarrashin Husnah da kyar tasamu tayi shiru
***
Satin Husnah biyu bata je makarantaba school ba saboda rashin Lafiya datayi
amma yanzu jikin alhamdullila
Dan tana ma shirin zuwa school gobe insha Allah
Washagari Monday da safe Husnah tashirya cikin sabon uniform dinta Wanda ya shamsu yadinka mata
Tayi kyau sosai tasaka read cap dinta da belt dinta na head girl
Bayan ta fito tayi wa umma sallama umma tace Allah miki lbarka kinje Dan kicire komai aranki
Tace umma namiki alkawari cire damuwa daga raina
Tawuce bangaren ya shamsu
Ta Dan bubbuga kofar ya shamsu tace ya shamsu nagama mutafi yace OK daman kenake jira
Suka fito tare da kubra tana rataye da jakar mijinta
Ta kalli Husnah tace kai tawan wallahi kinyi kyau sosai
Husnah tayi murmushi tace anty kubra kenan ya Shamsu
Mutafi kasan anty idan tafara sai tasa muyi latti
Kubra tayi murmushi tace to Dan Allah kisayo
Wannan kunun ayar da kike kawo min
Husnah tace karki damu
Zantaho miki dashi
Kubra yauwa kanwata
Nan dai ya shamsu da Husnah suka fita yatare musu keke napep
Yabata dari biyar tace kai yaya shamsu yamin yawa ai
Ya shamsu yace ai nasan bakya azumi Dan haka kiyi amfani dashi kiyi break karkizauna da yunwa
Husnah tace wallahi umma ce ta hanani yin azumin wai saina warke
Ya shamsu yace ai gaskiyar tane
Gwamma yar kanwata tayi katuwa
Husnah tayi murmushi tace nagode yaya
Ta shige cikin school dinsu
Tana shiga an buga assembly nan ada sauran prefect din suka tayata
Shirya yara Assembly
Nan dai Husnah ta hau kan stage tafara control din data sabayi
Bayan angama assembly principal ta aika akira mata head girl dinta Husnah
Tace mata nakiraki ne nabaki hakuri akan kinyi rashin Lafiya har natsawon sati biyu school bataje tadubokiba
Husnah tayi murmushi tace mummy ai an wakilta prefect sunje sun dubani
Mummy principal tayi murmushi tace ai duk da haka yakamata a hada da malamai
amma dai muna Neman afuwa
Husnah tace wallahi mummy bakomai aikema bakya gari da kinje
Nan mummy principal tace bata wani envelope tace ga wannan kikai gida
Husnah tace to mummy
Nan principal tabata daman ta koma class
Husnah nazuwa class taga meenat sai alokacin take zuwa
Husnah tayi murmushi tace ai wallahi aminyi bakida kirki
Banda Lafiya kokije kidubani ko
Amina ta kalleta sama da kasa tace Allah yabaki Lafiya
Abin yaba wa Husnah mamaki
Har zatayi magana sai Ku ma tafasa
Dagana kuma malamin su na
Math's yashigo
Ana cikin musu teaching wata daliba tayi excuse sir copper bash yana kiran anty amina Hakeem
Sir yace amina Hakeem
Meenat tace yes sir
Yace oya tashi kije
Kafin amina ta fita sai da tajiyo taga ko Husnah tana kallonta
Itakuwa Husnah batasan tanayi ba
Dan ita kosunan bashir bata son ji tatsaneshi sosai
Har aka fita break amina batadawo ba
******
Yauce su Husnah suke graduating a school dinsu
Aka kawata hall dinzasu yi taron aciki
Principal bata ba da damar graduating students Susa kayan gidaba wato personal wear's kenan
Shiyasa duk inda kaga SS 3 zaka gansu sunsha guga sunsha kyau
Dan ba hana suyi make up ba
Duk prefect kowacce da hulanta akanta sunjeru a kujera na musamman sai kuma sauran graduated students dinsuma suna nan akujera ta musamaman
Husnah ma duk 'yan gidansu sunzo mata Abba ne kawai baisamu zuwaba amma ya shamsu da anty kubra da umma duk sunzo
Amina Hakeem dakyar tasamu daddynta Hakeem yace zaizo
Ahmad da amaryarsa sai Hakeem sukazo sai mamanta da kuma hajiya rukayya duk sunzo
Hakeem tunda yazauna yake ta fama da wayarsa
Dagowar da Ahmad zaiyi yaga ai anzauna kusadashi
aikuwa dai ya shamsu ne da anty kubra umma kuma tanacan bangaren dattijai mata
Ahmad yace kaga ikon Allah malam shamsu kai ne anan kokuma wa
Ya shamsu yajuyo jin ankira sunanshi
aikuwa yaga su Ahmad da Hakeem
Hakeem ma jin an ambaci sunan malam shamsu
Yasa yadago mai suka yi murmushi gadayansu
Nan ya shamsu yabasu hanu suka gaisa
Yace wasuka zowa Ahmad yace daughter dinmu ai nan take karatu
Kaifa yace nikuma kanwata ce anan
Kubra tace ina wuninku Hakeem da Ahmad suka amsa
Ahmad yakalli inda madam dinshi Aisha take yatashi yaje yarada mata magana akunne aikuwa Aisha ta task da sauri
Tana zuwa ta kama hanun kubra tace alhamdullilahi yau dai nima na hadu da kawata
Kubra ma dayame wayayyiyace tace nima naji dadin haduwata dake
Nan Aisha taja hanun kubra suka koma gurin su daban
Nan kuma ya shamsu da Hakeem da Ahmad suka can gaba wajen special guest
Nan akafara taron da addua
Can principal tafara jawabinta kamaryadda aka saba
Daga can kuma ta ce itada kanta zatakira best student of the year
Wanda duk shekara akeba principal dama tazaba da kanta ta kuma bata kyauta duk karshen shekara haka akeyi
Wani daga cikin teachers dinsu ya tashi yakarbi Mike din hanun principal da list din hanunta
Yafara kiran suna kaman haka
Best student of the year
Kowa ya kasa kunne
ASMAU SULEIMAN SHAMSU
aikuwa duk student aka dauki tafi raf raf raf
Dan daga malamai har student sunsan Husnah ta cancanta sosai
Cikin nutsuwa Husnah ta tashi ta isa gurin principal
Nan principal tace wazata kira ya tayata karba
Husnah tace wa principal ya shamsu za akiramin
ya shamsu suna zaune duk hankalinsu yakoma kan head girl
Shi ya shamsu baifada musu wacece kanwar tashiba
Sai jisukayi ankira ya shamsu yatashi cike da alfahari da 'yar kanwarshi bata bashi kunya kokadan
Ahmad da Hakeem suka hada ido
Ahmad kaddai itace kanwar tashi
Hakeem yayi murmushi yace ga zahiri amma fa yarinyar taburgeni matuka
Yayi maganar yana kallonsu Husnah
Cike da mamaki Ahmad yakalli abokin nashi
am I dreaming ?
Man what are you saying
Hakeem bai kalleshiba murmushi kawai yayi ya dauke idonshi daga gurin su Husnah ya mayar da kanshi kan wayarshi
Murmushi Ahmad yayi dai dai lokacin ya shamsu yadawo yazauna
Ahmad yace kanwarkace ya shamsu yayi murmushi yace yar karamar kanwata kenan
Yace masha Allah
Allah ya albarkaci rayuwarta
Ya shamsu da Hakeem suka ce ameen
Daga nan kuma sai akafara ba wa prefect satificate dinsu ya rage sauran na social prefect da Head girl
Aka kira social prefect AMINA HAKEEM ABUBAKAR
Nan akabata sertificate dinta da kuma gift dinta maman Laila ita tayata karba
Hakeem kallo daya yamusu yacigaba da abinda yakeyi
Can akakira me gayya mai aiki wato head girl
Husnah taje ta karba itada yaya shamsu principal Tamika kyautar aka musu hoto
Duk wani kyauta da akerabawa Husnah ita takarbi na farko abin yaburge kowa ana karshen
Husna ta tashi zata karba sai kawai tafashe da kuka Dan tasan koba komai yayanta zaiyi alfahari da ita
Principal ta rungumeta tana share mata hawayen
Tace asmau Allah ya albarkaci rayuwarki
Ya shamsu yaji dadin adduar principal
Yace Ameen hajiya mungode Allah yabar zumunci
Nan fa students sukayi tazuwa suna daukar hoto da Husnah suna mata fatan alkairi
Masu bata gift nabata kai gaskiya Husnah tayi farin jini sosai har malamai suna tururruwar hoto da ita
Meenat zaune abin duniya yadameta tana matukar jin bakin ciki abin da kefaruwa da Husnah
Laila tace wai ita wannan yarinyar fa saikace aljana komai ta handame ita kadai
Meenat tace kyaleta dama yunwa ne yakawota school din Dan dama 'yar matsiyata ce
Scholarship taci tashigo
Hajiya rukayya dole ai yanzu naji batu
Motar school ce ta kaiwa Husnah gift dinta har gidan
****
PROFESSOR HAKEEM yana zaune cikin falonshi kusan sati kenan da graduation dinsu Husnah amma kullum da ita yake kwana da itayake tashi aranshi
Kuma tunda yake a rayuwarshi bai taba saka 'ya mace a rayuwarahi ba
Kuma a yadda ya fuskanci zuciyarshi takamau son 'yar baby nan
Shida kanshi yake wa kanshi dariya
Ya duba agogo yaga sai yanzu 8:30 nadare tayi
Yaje ya hada Kofi
Yanasha kadan yana tunanin Husnah
Abinda baisaniba shine Ahmad yadade a bakin kofa yana kallon abokin nashi daya fada shauki
Ahmad yayi gyaran murya hade da sallama
Hakeem yajiyo suka hada ido da Ahmad
Ahmad yace abokina wai meyake faruwa ne
Kwana biyu naganka kaman akwai wani Abu
Hakeem yayi murmushi tareda kurbar copee yace shine kabar matarka kazo gulma ko
Ahmad shima dariyar tare da dauko lemu maisanyi a fridge
Yadawo yazauna
Ahmad yace inkarashida gulma kaikaso
amma dai ni bazan bar nan ba sai kafada min
Hakeem yatashi yakoma bayan kujera yace
Ahmad am in love
Ahmad yayi dariya yace daman nasani
Duk wannan boye boyen naka duk kallonka nakeyi
amma gaskiya idan har kasamu yarinyar nan kayi sa a wallahi
Hakeem yace wace yarinya kenan tunda nidai ban fada wacce nakeso da bakinaba
Ahmad yayi dariya yace karka rainawa wa kanka hankali mana
Kawanwar shamsu koba hakabane
Hakeem yayi murmushi yace amma ya akayi kagane hakan dawuri
Ahmad yace shekaru talatin muna tare fa dan uwa taya za ayi barangane matsalarka ba
Hakeem yayi murmushi yace hakane amma bazan fada ba sai na musu
Jarabawa daya kaga daga tabbatar gidan danaje Neman iri
Next page
Your comments is needed fans❤❤❤❤❤
Anfara wasa fa fans❤❤❤❤
Sainaji ku
[05/05, 11:08 AM] UMMU AFAN :
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
HAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN
FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION
F.C.T.W.A
HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITERS OF THE NATION
DEDICATE THIS PAGE TO sis JIDDER (BAEWAR ALLAH)
WANNAN PAGE IN NAKI
SABODA KAUNA DA KIKE NUNA WA WANNAN
NOVEL NAWA NA
AKWAI LOKACI
Allah yabar zumunci keep it up ❤❤
Masu comment ina sane da Ku kafin na kamla littafin nan duk sai kunji sunanku daya bayan daya so kucigaba da bin ummu afan takuce ❤
AKWAI LOKACI
PAGE 66 to 70
PROF HAKEEM zaune kan resting chair dinsa a bakin sweeming fool yana shan iska dan yanzu yafito daga cikin ruwan
Wayarshi ta daukara yana dubawa yaga dalibata wato mummynshi kenan dan sunan dayasa mata kenan
Bayan sungaisa Hakeem yace mummyna albishirinki mummy hafsat tace goro
Yace naga matar aure a kano fa
Cikin tsananin farin ciki mummy hafsat tace alhamdulilla naji dadin wannan albishir
Yaushe zakazo katura mahaifinka gidansu yarinyar
Hakeem yayi murmushi yace daliba kenan ai ban ma taba fada wa yarinyar ba nikadai nake kida kuma nake rawa na
Mummy tace shirme ni harkasani ina murna to idan bazaka iya fada mata nika nuna min gidansu yarin sai naje
Ayau saina zo kano wallahi akanka my son
Hakeem yayi murmushi yace nasani mummy na
Nasan zakifi kowa farinciki shiyasa nafada miki tunkafin na fada wa yarinyar
Sai mummy Kinsan masu soyayyar Allah kadan suke aduniyar nan
Kuma dadin da dawa ma yarinyar danagani din ba masu karfi bane
Kinga idan naje kaitsaye Kuma akayi rashin sa a saikiga sun soni don kudina badan Allah
Mummy taja numfashi tace hakane son sai dai zuciyata tana bani bazataba son abinda baidace dakaiba
Hakeem yayi murmushi yace Kinsan menakesonyi mummy tace a a son sai kafada
Yace zan jarabasu nagani zanje amatsayin talaka banida komai
Ingani zasu karbeni kokuwa
Mummy tace hakan ma tayi son dina
Kuma ina maka fatan alkairi
Insha Allah zasuci duk wani jarabawar da zakayi musu
Wasunan surukartawa Hakeem yayi murmushi mummy ta sosa mishi inda yake mai kaikayi
Yace ai harma tazama surukarki
Mummy tace aiba surukaba ma 'yata zama son
Hakeem yayi murmushi yace asmau amma anakiranta da HUSNA
kai masha Allah ashema babban suna ne da ita
Insha Allah asmau zata Mata agareka tun kafin naganta naji inasonta
Hakeem yace shiyasa nakeson Ku iyayena kuna matukar daraja abinda nakeso
Allah yabani matar da zata bauta muku da zuciya daya badan kudinku ba ko kudin danku
Mummy hafsat tace aikasamu son zantayaka da addua
****
Washagari Hakeem Bayan sungama komai ya shamsu yazo musu sallama zai wuce gida dan karfe hudu yake tashi a lectures
Ahmad yace wa ya shamsu yaufa kafanmu kafarka zamuje mugaida Abba da umma
Dan idan muka biye maka bazaka gayyace zuwa samun ladan nan ba
Ya shamsu yayi dariya yace shikenan idan kun shirya muna iya tafiya
Hakeem yace na dauka zaka kawo wani excuse ne ince ai ba umma kai kadaibane muma namune
Ahmad da ya shamsu sukayi dariya
a motar Hakeem akatafi ya shamsu agaba Ahmad yabaya
Ya shamsu yana nuna wa PROF HAKEEM hanya
******
HUSNAH ce zaune tsakar gida tagama aikin gidan kenan tas ko ina yadau kamshi
Ita kuma anty kubra tana kitchen tana hada abincin dare Wanda sudama kafin biyar sungama komai sun zuba a kula
Kuma aikin sukayi Husnah da kubra yau idan kece da aikin gida to dayar kuma saitayi abinci
Yau Husnah ce da aikin gida
Tagama komai da wuri tana wa anty kubra dariya tana kitchen dan yau ya shamsu yace ayi tuwon semovita miyar kubewa danya
Har kudin danyar kifi yabayar
Anty kubra tace zanrama ai Allah yasa ran girkinki Abba yace sakwara yakeso
Husnah tayi murmushi tace kai ai danagane kuskurena kuwa
Umma datake jinsu tace tun tuni kinjuye ruwa Yakama kishiga kiyi kisamu kifito kije min aika ko
Husnah tace to umma
Umma ta kalli kubra tace sannu kinji kubra Allah dai yamaku albarka yabaku masu yimuku kuma
Kubra acikin zuciyarta ta amsa da amin dan tana jin kunyar umma idan tace Allah yabasu masuyi musu
Husnah tafito daga wanka tayi dakinsu tashafa mai tadauko powder tashafa sai kwalli sai tasa lips glow alebenta
Tabude akwatin kayan ta tafara zaban wadda zata saka
aikuwa idon ta yakai kan wani material pink da kuma ratsin baki ajiki Wanda ya shamsu yamata a bikin shi
Tunda tasa a biki batasake sawaba
Sai tadauko shi tasaka dinki duguwa Riga ce
Daga sama ya dameta sosai dan Husnah fa akwai kayan aiki
Shiyasa umma bata cika barinta fita da gyaleba saidai hijabi dan Allah yamata kira
Husnah takalli kanta a madubi itakanta tasan tayi kyau sosai
Sai kuma tasan dakyar umma zata bari tasaka gyalen material din
Itakuma yau mayafi takeson yafawa
tace barin gwada dai tagyara gashinta tadaure da ribbon fari
Kafin tayafa gyalenta dan bata saka dankwaliba
Kota saka dankwalima abanza
Dan bayazama akanta sabonda tsantsin gashinta
Tadauko turarenta tafesa kafin tadauki Jakarta na suwaga pink da takalminshi duk pink tasaka
Kai masha Allah da wannan kyakkyawar hallita
Tafito tace umma nafito
Umma ta kalli 'yartata tace au da wannan gyalen zakifita
Husnah tace Allah sarki umma na gyalen kayan nefa
Kuma kinga kayan ai yana da fadi sosai
Kafin umma tayi magana anty kubra taleko tace umma dan Allah kibarta wallahi tayi kyau kuma kinga ai kayan yana da fadi
Umma ta ce wato bakinku daya ko to shikenan kije Allah yakiyaye hanya
Husnah tace to umma baki min bayaninba umma tace kinci gidanku yau kika saba karbomin zuman ne
Husnah tayi murmushi dimple dinta tsuka lotsa sosai
Tace to ummana afuwan nadauka bakaman na kullum bane
Tayi waje sukace mata adawo Lafiya
adai dai kofar gidansu ya shamsu yanuna wa Hakeem yayi parking
Suka fito atare Ahmad yace kashiga saikamana iso
Ya shamsu yace to shikenan yaya cikin gidan alokacin umma ce kadai a tsakar gida kubra ta fito mata da taburma
Dan anna suke hirar Daren su gadaya
Ya shamsu yayi sallama umma tace a a ubana har andawo yace a umma yagidan nan dai yagaida umma kafin yace umma daman su ogana na office ne sukazo gaisheku
Umma ta ce shine kabarsu a waje kuma sushigo ciki dan Allah haba waje
Ya shamsu yaje ya musu iso zuwa cikin gidan
Umma ta ce kashiga dasu daki Ahmad yace a umma mu kusa da ummanmu zamu zauna basai munshiga dakiba
Umma taji dadin har ranta tace to shikenan 'ya'yan ummu kuzauna nan suka kwashi gaisuwa agurin umma ta amsa cike da farin ciki
Nan kuma ta musu godiyar hidimar dasukeyi da su
Hakeem yace haba umma ai mu da shamsu Yanzu munzama 'yankuma bagodiya tsakaninmu ai yiwa Kaine
Umma ta ce hakane kam Allah yake mutum da mutum
Kodai Allah yasaka muku da aljanna
Umma ta ce wa shamsu ubana aisai kayi maza kaje nan shagon mati ka karbo musu lemu mai sanyi da ruwa
Hakeem yace haba dai umma mufa ba bakibane
Komai ummanmu tabamu cizamuyi
Ba umma ba harta ya shamsu yaji dadin wannan kara da Hakeem da Ahmed suke musu
Sallmar HUSNAH ce yasa Hakeem daga ido yakalli hanyar waje aikuwa suka hada ido cikin ido Husnah tayi saurin dauke idonta dan dama akasi aka samu ta kalleshi
HAKEEM yasamu Kansa cikin wani yanayi Wanda yakasa fassarashi ba Ashe ganin da yayi mata a school ma tafi haka
Husnah ta durkusa har kasa tagaishe da su Hakeem Ahmad ne karfin amsawa shikam ogan ba baki
Yakasa komai ne
Ba Wanda ya kula da canzawarshi sai Ahmad
Ahmad murmushi yayi shikadai
Kubra tafito tagaishesu
Ahmad yace ai kawarki basan zamuzo ba dakinganta
Kubra tace dan allah yakawo mata Aisha Dan zaman da sukayi a gurin graduate dinsu Husnah sun saba sosai
Ahmad yace ya mata alkawari ran sabar zai kawo Aisha tamata wuni daga nan tagaida umma
Umma ta ce Allah yakawo ta Lafiya umma na maraba da ita
Husnah da kubra suka kawo musu abinci a kula da biyu suka ajiye
Husnah tadauko plate guda biyu da serving spoon duk ta ajiye musu
Sai ta dauki jug ta kawo musu ruwa maisanyi na randar umma ta kawo musu da cups biyu
Umma ta ce maza hada musu zobo Husnah
Husnah tace to umma ai na dafa tunda dazu hadawa kawai zanyi saidai ba kankara
Ya shamsu yace hada barin karbo kankara
Ya shamsu yafita jimawa kadan sai ga shida kankara yakawo yaba wa husnah
Hadaddan zobo ta hada Wanda yasha kayam kamshi da cocumba
Tasa musu a jug shima takai musu kafin ta wuce dakin anty kubra umma tace bara nashiga kuci abincin Ku
Ya shamsu yace bissimillarku kuci abinci
Hakeem yayi murmushi yace aiko baka fada ba
Ahmad yayi murmushi dan yasan dalilinsa na fadar hakan
Hakeem yayi serving kanshi
Tuwo daya yasaka sai sai yasa miyar baiga ruwan wanke hanuba sai
Yace yaya shamsu ruwan wanke hanu dan bana cin tuwo da cokali
Ya shamsu yayi dariya yace amma yallabai kaso barkwanci ninekuma yayan
Hakeem yayi murmushi baice komai ba
Ya shamsu yakira Husnah takawo ruwan wanke hanun
Takawo ta ajiye gaban ya shamsu shikuma ya mikawa Hakeem gabansa
Hakeem sosai yaci tuwon dai Bayan ya cinye Leda daya sai ya kara Ahmad nema yarage kadan
Ya shamsu yace haba yallabai dan Allah kacinye wallahi umma zataji dadi
Hakeem yace rabudashi ya shamsu tsoron madam Aisha yakeyi kartatsareshi sai ya cinye abinta yakasa Bayan yacinye na gidan umma
Duk suka kwashe da dariya
Hakeem yatsiyayi zobon da Husnah ta hada musu yasha
Aikuwa yaji kunnenshi kaman zai yanke dan dadi
Kodan ya hadu da soyayyane oho
Kafin yayi magana Abba yashigo dattijon arziki
Duk suka mike tsaye sai da Abba yazauna suka zauna suka kwashi gaisuwa
Ya shamsu yagabatar dasu
Abba yace a manya baki ne damu agidan Ashe
Nan shima yashiga musu godiyar hidimansu akansu
Sun dan taba hira kafin Abba yashiga daki yabarsu nan da ya shamsu
Hakeem yace Gaskiya ya shamsu wannan zobon asamin awani Abu natafi dashi zansha zuwa dare
Ahmad yace narigaka azuci karigani a baki dan kasan duk inda nasha abinda yamin dadi sai narage wa madam
Hakeem yayi murmushi yace kai man kafadi gaskiya
Ya shamsu dai dariya yakira Husnah yace tasamo jugs guda biyu ta zubo zobo tace to
Hakeem tabita da kallo komai na yarinyar yamishi Dari bisa Dari
Tana da duk wasu qualities din dayake bukata ga mace
Husnah ta zuba takawo ta ajiye
Ta yigaba abinta
Sai da akakira magrib suka yi sallama da su umma da Abba da anty kubra
Husnah tana kan sallaya idan tayi magrib bata ta shi sai tayi isha
Hakeem yaso yasake ganin Husnah
Amma taki fitowa
Ahmad ya ajiye bandir din kudi 'yan dubu dubu yace a ba wa kanwarsu tasai kayan kwalliya
Ya shamsu yace dan Allah karmuyi haka kudauki kudinku
Ahmad yace ai nariga na ajiye kuma ma aibakai muka ba ba kanwarmu muka ma kyauta
Da kyar ya shamsu yabar kudin nan
Suna cikin mota Hakeem ya karya kwana zuwa baibi hanyar gida ba
Ahmad yace man yana zaka kaimu kuma Hakeem yayi murmushi yace sa ido kawai kayi kallo man
Ahmad yace OK baringa ikon Allah to
Hakeem yayi parking adai dai gurin wani malamin almajirai suka sauka
Malam na ganin HAKEEM yataso yazo sannu da Zuwa professor Hakeem yayi murmushi suka gaisa da malam Garba
Malam Garba yace mukarasa daga taburma nan suka karasa
Hakeem yace malam bawani Abu yakawoni ba illa Neman wata alfarma
Malam Garba yace alfarma kuma alhaji da kanka
Hakeem yace a malam
Aure nake nema malam
Amma kasan rayuwa ta baci yanzu sai aureka badan anasonkaba sai dai don abinda kakedashi
Malam yace hakane
Hakeem yaja dogon numfashi
Ya kalli Ahmed da ya kagu yaji dalilin abokin nashi nazuwa nan
Hakeem yace malam zanje Neman aure da sunan talaka talakan ma futuk Mara iyaye
Koda anzo Neman tarihina guringa za azo dan
Kai zanfada a matsayin malamin danayi karatu agurin shi
Kai kuma inason kanuna tun ina karami aka kawo maka ni
Wannan kadai nakeson kamin malam
Malam Garba yayi murmushi yace gaskiya alhaji kana da tunani mai kyau Allah ya tabbatar da alkairi
Hakeem da Ahmad suka ce amin malam
Nan suka wa malam sallama Hakeem yadauko bandir din kudi yaba malam yace gashi a rabawa yara sadaka
Ya ba malam wani kuma yace Gashi wannan nashine
Malam Garba yayi ta musu addua
Acikin mota Ahmad yace amma meyasa makayi wannan tunanin haka Hakeem
Ahmad yace kana nufin bazasu ganeka ba wai kome
Hakeem yayi murmushi yace duk zan shirya wa hakan
Ahmad yace Allah yasa amma dai yakamata duk wani abinda zakayi wallahi kayi sauri kafin wani yariga ka
Hakeem yayi murmushi yace inaji ajikina wannan yarinyar rabonace
Ahmad yace to tunda kana da tabbacin haka
Meye na gwada ta kuma
Hakeem yace inason nasan mena aura ne kuma rayuwata zanbata kaga kuwa ina bukatar bincike sosai
Ahmad yace sai prof komai naka daban ne wallahi gaskiya bazan boye maka ba I like your life style Bros
Keep it up
Hakeem yayi dariya yace baka jiya abokina
Ahmad yace ai bazangaji
Komai naka is so special
****
Bayan sati uku Hakeem yayi order na fuska daga India
Yau yakesaran za akawo mishi
Hakeem ya zaune wani abokin
Wayar shi tadau kara yana sai yaga number din Wanda yaba sautun siyo mishi fuska
Yadaga wayar yace badai har kun isoba
Doctor isah yace gani ma acikin school dinku
Hakeem yace what's a surprise
Ganin zuwa
Hakeem yafita yaje yashigo da doctor isah
Nan Bayan sungaisa doctor isah
Yafito mishi da sakonsa
Hakeem yakarba yace masha Allah kuma gaskiya kayi yadda nace
Doctor isha yace to ai kasan aikan manya irinku ba kasafai akacika muku shirme ba
Hakeem yace zakafara kaima ko
Doctor isha yayi murmushi yace ansamu ragi sosai yallbai dan Rabin yakai dubu Dari da hamsin
Hakeem yace OK zaka iya barinshi a wajenka yazama naka doctor
Doctor yace a yi haka yallabai
Hakeem yace karka damu ai kamin komai
***
Da daddare Hakeem ya fesa wanka yadauki jallabiyya yasaka yadauko fuskarsa yasaka kafin yadauki carbi yarike a hanu
Yadauko wayar Nokia da yasa akasayo mishi second hand wacce duk tasha dauri da roba
Ya kalli kanshi a madubi shida kanshi yaba kanshi dariya
Yadauki kudi yan hamsin da kuma 'yan goma yasaka a aljihunshi
Ya kulle gidanshi yafita zuwa gidan Ahmad yayi sallama
Maigadin yace sannu malam daga ina haka kuma gurin wakazo
Yace inason kamin sallama da maigidan ne
Bayan Ahmad yafito ne yaga mutum ustaz har da gemunshi
Yace assalmu alaikum
Hakeem ya amsa mishi cikin canjawar murya
Hakeem dai yakasa danne dariyar shi yacire fuskan
Ahmad wazaigani Hakeem ne
Cike da mamaki Ahmad yace amma ka shammaceni
A ina kasamu masks nasan dakyar akesamu a Nigeria
Hakeem yace daga India aka kawo min
Kaga kai ma danake tunanin zaka ganeni baka ganeniba
Bana tunanin shamsu da mutan gidansu zasu ganeni
Dan haka ni wuce daga yau zafara basu exam's din su
Hakeem ya mayar da fuskarshi yagyara da kyau yadda baza a ganeba
Yayi bakin titi yatari kekenapep zuwa anguwar su Husnah
Next page
Tofa fans za afara wasa fa
Your comments is needed
Ina alfahari da masoya novel na AKWAI LOKACI
[05/05, 11:08 AM] UMMU AFAN :
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Story & written
By
The special writer
UMMU AFAN
FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION
(F.C.T.W.A)
HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION
I DEDICATE THIS PAGE TO YOU sister surayya auwal ina matukar jin dadin comments din ki amma Dan Allah sister kikara yawan comments din ki ina alfahari da Ku da da comments din ku❤❤❤❤❤
AKWAI LOKACI
PAGE 86 to 90
HUSNAH zaune tana gyaran farcenta Umma tace auta nikam ya kukayi da Alhaji ne naga jiya yazo
Husnah ta bata fuska tace wallahi Umma guduwa nayi dakin anty kubra na buya Dan wallahi Umma nibana sonshi
Umma tayi salati tasanar da ubangiji
Tace aidaman zaran hijabin dakikayi kaman kinje
Bazuwa kikayi ba
To ma wai meyasa bakya sonshi meyamiki husnah karki zamo me saka alkairi da sharri mana
Tunda Allah baiyi aurenki da shi abdullahinba sai ki ba
Wannan dama kodan halinsa na kirki badan abin hanun shiba
Anty kubra tace wallahi Umma kullum sai namata wannan nasihar amma kamar anshuka dusa
Husnah tace wallahi ni kwatata bana jin zan iya son wani bayan ustaz ne
Kuma bana son na aureshi nakasa yimashi biyayya Umma na Dan Allah kufahimceni
Umma tace ai shi so ahankali yake shiga
Kyawawan halaiyar wannan yaro kadai zaisa kifara sonshi azuciyarki
Dan yana da duk wani nagarta atare dashi
Kafin Husnah ta yi magana ya shamsu yayi sallama yashigo yazauna
Yana gaida umma kubra ta tashi tace sannu dazuwa tayi hanyar fridge tadauko mishi ruwa maisanyi
Takawo mishi
Ya dauka yasha kafin yakalli umma yace mekuke ta tattaunawa ne ummana
Umma tayi murmushi tace wallahi wannan shasharce muke taba baki saikace wata uwarmu
Sai waina mu takeyi
Ya shamsu ya kalli Husnah yace wai meyake damun kine husnah
Ustaz yariga yatafi bazai dawoba
Wallahi husnah da ace zaidawo lokacin da akeshirin daurin auranki da Abdul Hakeem za afasa a daura dashi
Sai dai kash ba a mutuwa adawo
Sai dai ina miki albishir dacewan Allah yamiki sakayya da mafificin alkairi
Mun dade muna Neman hanyar da zamu sakawa wadan nan mutane
Sai gashi Allah yakawo tunda yasawa yallbai kaunar ki aransa
Maizai hana kitayamu maida alkairi da alkairi husnah
Abdul Hakeem yamana komai a rayuwa kuma duk abubawan da yayi mana na tabbatar Dan Allah yayisu
Kaman yadda kema zamu bashi dan Allah badan abin hanun shiba
Husnah tace shikenan yayana
Namaka alkwarin bazan baka kunya ba
Na amince da shi
Amma wallahi danku Dan wallahi yaya bana sonshi
Ya shamsu yayi murmushi yace Abu mafi mahim manci dai shine ki amince
Husnah ta turo bakin shagwabar tace wato bakadamu dani bako yaya na
Ya shamsu yayi dariya yace caf waya fada miki yar kanwata
Yace ai nafi jidake
Dan idan kikayi aure ma fa tare zamu tafi
Husnah tayi murmushi tace ai wallahi yaya da dagaske kake da naji dadi sosai
Amma nasan kana fada be kawai
Amma nifa kullum sai nazo gidan nan
Umma tace kwarai kuwa daga ke har yayan naki zan ga me hankali acikin Ku
Anty kubra tace gaskiya kam umma
Nima naga alama tana dariya
Ya shamsu yace dawa kikeyi yadauki pillow na gefensa ya wurga mata ta tashi
Tagudu yabita shima
Umma tayi murmushi Dan yadda Dan ta guda yake zaune lafiya da matarshi bata taba ganin wani abun ki agurin kubra
Husnah tace umma Dan Allah yau kimana danbun tsaki da kanki
Kinga yau nice da girki
Umma tayi murmushi tace naki wayon sai girkin 'yata azo zanyi
aikuwa husnah tayi murmushi duk kugama badaini ba wato sai ran girkin anty kubra zakiyi ko
Shikenan nasan mezanyi muku a gidan kuma dole kuci
Umma tayi dariya tace kinga kuwa kyayi aiki har dare kenan
Husnah tayi murmushi ta tashi tace Abba yakusan da wowa
Barin yi kitchen
Tana shiga kitchen din tafara tunanin abinda zata daura
Taduba store dinsu taga suna da doya
Tadauki guda biyu tafere shi tas ta wanke
Ta rarraba shi kanana
Tazuba tunkuya takawo gishiri tasa dai dai misali
Kafin tadebo albasa attaruhu da tattasai dakuma tomatoes amma kwaya hudu tasa tomatoes din bata bukatar tumatir dayawa
Nan ta wanke komai tas
Tafara greating dinsu a greater ba a blender ba
Dan bata bukatar suyi laushi
Nan tasoya su da mangyada saidataga tayi soyu sannan tadauko yankakkakun kayan namanta kanana dake cikin fridge tafashashshe
Tazuba tadauko gyararran kifinta Wanda tariga tacire kayar tas shima tazuba tacigaba da juyawa
Kafin tadauko maggi tazuba dai su curry da thyme da dai sauransu
Tahada tacigaba da soyawa haba ai nan da nan gida ya hau kamshin girkin husnah
Sai da ta tabbatar ya soyu kafin tarage gas din kadan
Tadebo kwai (eggs) guda biyar
Tafasa su a kwano daban tasaka magi guda daya takada
Kafin tadauko tana zubawa kadan kadan tana gaurawa har tagama tacigaba da juyawa
Gaskiya ko itada datayi miyar yakayatar da ita balantana Wanda saidai yagani kawai saici
Nan ta sauke tasama Abba a kulansa kafin tasa ma umma ma anata kulan
Ta ajiye a gefe
Tadauko nasu ya shamsu da anty kubra tasamusu dama tumsafe tayi kunun ayarta Wanda yasha madara tasaka a fridge yayi balin sanyi kuwa
Ta dauka nasu yaya shamsu tayi da shi part dinsu
Taje tana ta sallama taji shiru
Can saiga anty kubra tafito da gudu daga bedroom dinsu kanta ba Dan kwali ga gashinta duk an hargitsa
Ga rigarta zif din agaba yake kana ganin kasan akwai magana Dan anfara Jan zif din amma baikai kasaba
Kubra bata San ma da mutum a falonba ganin husnah kawai tayi tasake baki tana kallonta
Kubra ganin kallon yayi tace ke malama lafiya kuwa
Husnah tayi murmushi tace a a bakomai gani nayi kinfi to kamar wacce tayi dambe da zaki
Takarasa maganar tana dariya
Kubra tasan metake nufi
Itama tayi murmushi tace kema kwana nawane zakije fada da zakin
aikuwa husnah tabarai ta turo bakin tace zakifara ko anty kubra
Ta ajiye musu abincin tace gashi idan kungama soyayyar kwaci
aikuwa tana fadar haka tagudu
Kubra tayi murmushi kawai kafin ta koma ciki
Husnah wanka tafada tana fitowa tayi sallar La asar dinta kafin taje gaban dressing mirro dinta tafara shafa mai abinta tanagama shafa maidin tadauko body spray tafesa kafin dauko wani doguwar rigar English wear tasaka
Ta dauki gashinta daure da ribom baki kasancewar kayanta marun colour ne
Yana da bakin dankwali tadaura tayi daurin tauban
Tasaka jambaki shima marun colour gaskiya ba karya duk Wanda ya kalli husnah sai yaso yasake kallo
Kayan dama dayane daga cikin kayan da mummy hafsat takawo mata ne
Ta fito tasami Abba da umma sungama cin abincinsu
Abba yayi murmushi yace autar Abba gaskiya abincin yayi dadi wallahi
Waya koya miki ne autar ummanta
Umma tayi murmushi aini wani girkin ma fa kirkiran abinta takeyi kuma saikaga yayi dadi
Husnah tayi murmushi tace aini a school dinmu Abba food &nutrition naza ba akan agriculture
Abba yace kai amma auta ta kinyi dabara
Umma ce takatse musu zancen nasu
Tace anya kuwa kinci abinci Dan nasan halinki sarai idan ba aganki ba saiki kai har goma na dare bakici komai ba
Abba yace wai har yanzu rashin cin abincinta yanan
Umma tace sai abin da yakaru
Idan tagadama wataran dakanta zata dafa indomie
Ya shamsu ne yashigo falon yagaida iyayen nasa
Ganin fitowar ya shamsu yasa husnah zuwa gurin kubra
Wayar ya Shamsu yayi kara yana yaga yallabai kamar yadda ya saving wayar
Yadauka bayan sungaisa prof yakecewa gani acikin gidanku
Ya shamsu yace haba yallabai kaman wani bako kashigo mana
Hakeem yayi murmushi yace ai gurin matata nazo katurota Dan Allah yakashe wayar yana dariya
Ya shamsu yafada wasu Abba Hakeem ne yazo
Abba yace ya zai tsaya a waje kuma kaje kashiga da shi falonku tunda yau surkunta yakeji damu
Umma tayi murmushi tace ina ruwan Abdul Hakeem yaron kirki wallahi
Ya shamsu yaje suka shigo tare da Hakeem harkasa Prof yatsuguna yagaida su umma
Kafin ya shamsu yace mune daga ciki tana can ma
Suna sallama dai dai lokacin husnah take gwadawa kubra rawan ittiki
aikuwa Hakeem idonsa kyam akanta ya shamsu yace to dancer of the year
Anty kubra tayi dariya tace sannu dazuwa tana wa Hakeem cike da kulawa ya amsa tareda tambayarta gida
Nan ta tashi tayi falon su umma Husnah zata bita ya shamsu ke dawo nan baki iya gaisuwa bako
Cike da jinkuyar Prof tun ranar daya ganta half nacked bata kaunar su hada ido
Tadawo tazauna gefen ya shamsu kai a kasa
Ya shamsu yace to yallabai saika fito
professor Hakeem yace Weldon ya shamsu
Ya shamsu yayi murmushi yafita
Hakeem yamaida kallonshi kan husnah wacce take ta wasada da yatsunta daya sha Jan lalle
Batayi tsam Mani ba kawai taganshi agabanta
Zama yayi kasan shima yana fuskantarta
kasa dagowa tayi saboda kunyarshi gashi itadai bawani sonshi take ba
Yace tunda nibaza a gaisheniba nibarin gaisheda my wife
Dafatan kin wuni lafiya kasa amsawa tayi
Yace koki amsa gaisuwata konasa hanu na dago da fuskarki
aikuwa bashiri tadago tace cikin shagwabbiyar murya tace kayi hakuri karka tabani ina wuni
Professor Hakeem yayi matukar kaduwa jin wanann murya na husnah
Gawani masifaffan kyau tamishi
Kayan data sa ajikinta kaman Dan ita akayisu
Prof jiyayi kaman ya rungumeta a kirjinsa kozai zamu saukin sha'awar data taso mishi lokaci daya
Husnah ganin hanun Prof kawai tayi yadanki hanunta
Cikin tashin hankali husnah tabi hanunshi da kallo
Yace baby kinsan damuwata wallahi kece ina matukar son kasacewa dake amatsayin mata
amma haryanzu bansan matsayina ba agurinki
Husnah tace zanfada maka amman saika sake min hanu
Hakeem yayi murmushi yace shike nan inajinki
Husnah tafara magana tace na'amince zan aurekà amma bana jin zaka sàmi soyayyata Dan nariga nagama soyayya a rayuwatà Dan ni kwata kwatà soyayya bai karbeniba
Kar sàinafara sonka kaima narasàka
Takarasa maganar da kuka mecin rai
Hakeem jiyayi kukan har cikin ranshi yadauko hand kacif a aljihunsa fari Sol yasha kamshi yamika mata
aikuwa ganin hankacif din nan saiyada ta girgiza
Ta karba dasauri tace Dan Allah yaya a ina kasamu wannan hand kacif din
Hakeem yace nawane kokina sone cikin sauri tadaga kai tace Dan Allah kabarmin wallahi irin Wanda ya muallim yake amfani dashine
Koranar da zamu rabuma shine a hanunshi
Takarasa maganar hawaye mai tsanani Hakeem yace banason kukan nan kigoge fuska kimin magana Wanda yamutu ai yamutu
Husnah tayi murmushin data kumatunta lotsawa sosai
Tace aikuwa sai dai kayi hakuri Dan har abada bazan daina tunaninshi ba saboda yatafi da zuciyata gabadaya
Hakeem yaji matukar jintausayinta kaman yarungumeta ya rarrasheta
Husnah tacigaba da bashi labarin soyayyarta
Akan bashir da abinda yayi mata bayan tadauki zuciyarta tabashi lokaci kawai akejira ayi biki amma yafasa
Kuma yakoma suna soyayya da babbar kawarta
Sannan takarabashi labarin masoyin asali ya muallim
Hakeem yace nikuma na godewa Allah nakuma godewa saurayinki dayace yafasa
Dan da befasaba danayi asarar zukekiyar yarinya kamarki
Kinga kuwa nidan gatan Allah
Akaro nabiyu yasake kama hanun Husnah yace please baby kiyarda dani
Yakura mata ido tace naji amince amma kasake min hanu Dan Allah bakyau fa
Hakeem yace nasani baby shiyasa nakeson abanike a matsayin mata saboda banason nacigaba da sabawa Allah taba jikinki batareda aure ba
Because I can't control my self in front of baby
Husnah ta tabbatar dagaske yakeyi
Tayi murmushi bara maka ruwa da lemu
Yaji dadi har ranshi data nuna kulawar ta agareshi
Murmushi kawai yayi tare da 'daga mata gira ta tashi zata je sai kuma taga idonshi akanta
Ta juyo a shagwabe please yaya kajuya kadaina kallona inbasokake nafadiba
Maganar yaba Hakeem dariya yace jeki na rufe idon
Da gudu kuwa tafita yabi bayanta da kallo
Sai yatuna da ranar dayazo amatsayin ustaz
Zataje dauko masa kudi wai sai yarufe idonsa
Murmushi kawai yayi shikadai
Tare da zaro wayarsa daga aljihunsa
Sallama tayi da tire a hanunta dauke da abinci ta ajiye gabansa
Hakeem yaganta cikin wata jibgegen hijabi abin yaso bashi dariya ma
Kar dai ace tagane abinda yake kallo
Sai yayi murmushi kawai
Husnah tace ga abinci yaya
Hakeem yace nakoshi
Husnah takalleshi tace saboda me
Hakeem yace saikin fada dalilin ki nasaka min hijabi daga shiganki dauko min ruwa
Husnah tayi murmushi kawai
Tace sanyi nakeji tafada tareda boye kanta cikin hibinta
Hakeem yace baby
husnah tadago batareda ta amsa ba
Yace cire hijabin nan kizo ki serving dina
Husnah ta marairai ce kaman zatayi kuka tace Dan Allah kayi hakuri yaya wallahi kunyarka nakeji
Prof ya tsareta da maya tattun idonshi masu kwarjini
Yace OK kinfison acire miki da kauna ko
Husnah tayi saurin girgiza kai
Yace OK do as I said cikin sanyin jiki husnah tacire hijabin ta ajiye kan kujera tasauko kasa ta
Samishi abinci
Prof ya gyara zama yafara cin abincin tareda tsareta da ido
Duk kallonshi yasa ta takura
Yace batayi tsanmani ba taka spoon din a hanyar bakinta
Tadago ido takalleshi ya daga mata gira
Tace azumi nake yi
Yau Wednesday dama ana azumin nafila
Husnah tace wallahi Nina koshi cikina ma kaman zafashe
Yace tunda yayi niyar bata tabude baki kawai yasamata
Bata da zabi haka tabude Dan karamin bakinta yasaka mata
Yanayin yadda take cin abincin nata ma kawai abin kallone
Yatsaya kawai yana kallon ikon Allah
Yace bude bakin nagani
Tayi saurin cewa na am da karfi
Tace inazuwa umma nakirana ta tashi tagudu abinta
Hakeem murmushi yayi kawai yagama cin abincinsa yafita yashamsu yace har zaka gudu
Hakeem yace a nayi bakine
Shine zanje nagansu
Ya shamsu yarakashi har gurin mota
Prof yakira megadi yabashi manyan lodoji yashiga dasu gida
Ya shamsu yace yallabai Dan Allah karage kashe mata kudi haka sunyi yawa karka manta fa yarinyace Husnah har yanzu bata gama sanin kantaba
Prof yayi murmushi yace karkadamu itama ai hakkinace so konawa zankashe mata basuyi yawaba
Karka damu ya shamsu
Nagode da kulawarka
Yashige mota yayi gaba
Yabar ya shamsu da tunanin irin karamcin na PROFESSOR HAKEEM
****
Meenat sun wuce honey moon itada agonta bashir a inda zasu zaga kasashe sama da biyar
Shiyasa ma suke saran sai nan da 5 months zasu dawo Nigeria
Dadddyn Hakeem da shi dawasu amin tattun abokansa sukaje nemawa ABDUL HAKEEM ABUBAKAR SHUAIB
Auran ASMAU SULAIMAN SHAMSU
Sun bada sadakin husnah da zinare Wanda akalla zai kai million daya da rabi
Abba da ya shamsu suka suka kikarba
Daddyn Hakeem yanuna rashin jindadin shi
Sai su Abba suka karba tare da wa abin albarka
Nan daddyn Hakeem yace yana Neman alfarmar asaka auran nan da two Weeks
Next page
Your comments is needed Fan's
Ina alfahari daku masoyana ❤❤❤❤❤❤
[05/05, 11:08 AM] UMMU AFAN :
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Story & written
By
The special writer
UMMU AFAN
FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION
(F.C.T.W.A)
HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION
I DEDICATE THIS PAGE TO YOU SIS NERFEESERT A MUSA
INA MATUKAR JIN DADIN YADDA KIKE COMMENTS DINKI DAFATAN ZAKI CI GABA DA SUBURBUDO COMMENTS
KEEP IT UP
AKWAI LOKACI
PAGE 91 to 95
PROF zaune cikin falonshi na gidansu yanawa da Ahmad madam Laila tazo tazauna kusa da shi fuska a kode
Tace ina da magana fa baban meenat
Hakeem yakalleta da nutsuwa yace ina sauraronki maman meenat
Laila tadago kanta ta kalleshi Dan taga kaman yau akwai abin arziki
Sai tadauko ko kwalliyar da tayi ne ta burgeshi
aikuwa sai tasake wani shagwabe fuska wai ita zatayi shagwaba
Abin yaso ba Prof dariya amma sai ya make
Tace daman inason wasu kudine Dan Allah
Hakeem yayi murmushi tare da kurban copee dinshi
Yace kaman nawa kike bukata uwargida rangida idan bake bagida
aikuwa kanta yasake fashewa
Tayi dariya tace kuma daga ni bawata nice amarya nice uwargida
Saboda dariya Hakeem har kwarewa yayi
Ya ajiye coffee din yana murmushi Wanda yake karawa kyakkyawar fuskarshi kyau
Yace Allah ko tace sosai
Yace nawa kike bukata kenan
Tace million biyu Hakeem ya kalleta yace sun isheki
Laila tankalleshi da mamaki
Sai dai kuma tabasar tace a idan zansamu kari ma aizankarba
Yace OK yatashi yaje dakinsa yadauko cheque yarubuta naira million biyar
Yabata aikuwa madam laila data karba taga abinda keciki
Kusan suman zaune tayi agun
Sosai takasa control din kanta
A take ta dau waya takira hajiya rukayya tafada mata kudin da hakeem yabata
Tsaban batan basira irin nasu daga uwa har 'yar suka hau murna
Ta ma mance agaban Prof take da mamaki Hakeem yake kallonta
Kuma godiya haka ta tashi zata fita
Hakeem yace baki jiba zokizauna
Baki tambayeni kudin menene ba
Laila tace aina sani tunda Nina tambayeka kuma ka nunka min fin abinda na tambayeka
Hakeem yace OK wannan kudi kiyi amfani dasu ne naki
Dan nan da two weeks za a daura min aure
Kinga saiki sai abinda kike bukata ko
wani wawan ihu tafashe dashi
Tacire Dan kwali ta yar tace cikin tsananin tashin hankali tace wallahi Abdul baka isa ka cimin mutunci ba kayi kadan
Kuma wallahi banga 'yar iskar data isa nayi kishi da ita
Wani wawan kallo Hakeem wa watsa mata
Yadawo PROFESSOR ABDUL HAKEEM dinsa data sani yace karkisake kiran matata da 'yar iska if not zan baki mamaki
aikuwa Laila ta tafa hanu tace auwa harma tazama matar taka to wallahi Baku isaba
Kodayake kaima ba yinkanka bane duk abinda kakeyi saka akeyi
aikuwa tawuce fuuuuuuuuuuu tayi hanyar part din mummy hafsat
Hakeem daya kai cup din coffee baki ganin tafita ya ajiye coffee din
Yace tashin hankali badai matar nan gurin mummy na zata ba
aikuwa yatashi yazare belt din jikinsa yayi part din mummy hafsat
Mummy tana zaune tana waya da hajiyar Ahmad suna shirya yadda zasu tsara komai kafin bikin ganin Laila tashigo a fusace yasa mummy hafsat tace zankiraki hajiya
Laila ta tsaya agaban mummy hafsat tana girgiza jiki
Mummy hafsat tace ke lafiyar ki kuwa zakizo kitsaya kina girgiza
Laila tace burin ki yacika sai dai ina son kisani wallahi ba aisa akawo min wata 'yar iska gidaba
Nidaman nadade dasanin bakya kaunata kuma wallahi ba yadda kika iya dani
Mummy sake baki kawai tayi tana kallonta
Zata sake wata maganar taji belt ta kota ina ajikinta
Hakeem ne sosai yake sauke mata belt din nan ajiki
Mummy hafsat tashiga tsakani tace barta haka son
Yace mummy kibarni na babballata hartana da gost dazata sameki tana miki rashin kunya Who is she by the way
To bari kiji bazan dauki raini ba ballanta na ki ma mummy na wacce bani da kaman su aduniya
Kekinsan zamana dake ma ai darajarsu kike ci Dan ubanki
To kije nasakeki kuma yanzu zaki bar gidan nan nonsense '""
Ya kalli mummyn shi yace mummy Dan Allah kiyafemin wallahi nayi da nasanin hada zuria da hajiya rukayya
Bantaba tunanin zan ajiye matar da zata iya miki abinda Laila tamiki yanzu ba
Mummy tace kayya son kayi sauri da baka saketa ba
aiko wace mata da irin nata kishin idan mijinta yazo mata da zancen Karin aure
amma ni baka min komai ba hasali ma kanuna min kai d'ane Allah yamaka albarka
Tajuya ta kalli Laila dake kurma ihu tana kuka kaman ranta zai fita
Mummy tace kekuma tunda rayuwa da kika zaba wa kanki kenan aishikenan
Mummy ta wuce abinta Hakeem shima komawa sashinsa yayi nan da Laila ta dauko waya tafashe da kuka hajiya rukayya ta rude tace ke lafiya kike kuka waya mutu
Laila tafada mata abinda kefaruwa
aikuwa itama hajiya rukayyar kusan haukar tayi
Tace ba inda zakije ganin nan zuwa kadunan shidin banza share hawayanki
Kekadaice a gidan mijinki
Kwantar da hankalinki ganin ta howa
Alhaji abubakar daddyn Hakeem yana hanyar dawowa daga office
Hajiya rukayya takira wayarshi tana kuka
Daddyn Hakeem yayi tafada mishi abinda abinda kefaruwa
Daddyn Hakeem yace Abu baiyi kyau ba ammanshima yanzu zaikoma gidan
Tace itama gatanan a hanyar zuwa yace Allah yakawoki lafiya
Ya kashe wayar yacigaba da tukinsa
Hajiya rukayya nazuwa sai da tabi tacan gidansu ta taho da uwarta itama wato hajiya suwaiba sukazo tare
Laila na zaune tana jiran hajiya rukayya suby kanwarta tuntuni tazo suke zaman jimami tare
Karasowar kowa da kowa aka hadu a falon daddyn Hakeem
Tunda daga kan hajiya suwaiba mummy hafsat hajiya rukayya Laila suby da kuma uban gayya ABDUL HAKEEM suna zaune gaba dayansu
Daddyn Hakeem yafara gaida hajiya suwaiba tunda itace uwa agaresu bakidaya
Kafin yagaida yayarsa hajiya rukayya
Daga nan kuma yabukaci yasan abinda kefaruwa
Hajiya rukayya tafara magana cike da zafin zuciya
Tace bantaba tunanin abinda wannan yaro zaimana bakenan ya suna zamansu lafiya da matarsa
Za azuga shi yayi aure wannan ma ai Neman tashin hankali ne
Kuma abin batsaya nan ba sai su hadu shida uwarshi sun mata duka
Sannan kuma tabashi umarnin ya saketa saboda bakin hali da akasha a nono
Ran Hakeem tafarfasa yake saboda bakaken maganganun da akejifar uwarsa dasu
Hajiya suwaiba tayi salati tasanar da ubangiji tace yanzu duk wannan abubuwan dake faruwa shine ba asanar daniba
Ta kalli Hakeem tace yanzu kai Ashe har yanzu baka daukemu da mutunciba
Kokana ganin Dan bani na haifi ubanka ba
To bari kaji idan bani da iko da kai inadashi da ubanka kuma ai ubanka yana da iko dakai ko
To wannan aure bazakayi shiba
Kuma maganar saki babushi dole yarinya ta zauna gidan ka
Daddyn Hakeem da tun da hajiya suwaiba tafara magana baice komaiba
Yayi gyaran murya yace to hajiya naji duk hukuncin dakika yanke
Maganar Saki tabbas zai maida matarsa kobakomai saboda darajar 'yar da ke tsakaninsu
Maganar fasa aure kuma babushi
Ba fashi
Idan bazaki matanba alokacin dakika zo da bukatar hada su aure sai da Abba na Allah yajikan rai yafada cewan duk lokacin dayazo da bukatar kara aure bawanda ya isa ya hanashi
Sannan kuma koda SON bashida sha awar kara wallahi sai namishi da kaina
Saboda kugirbi abinda kuka shuka
Hajiya rukayya da Hajiya suwaiba suka kalli juna
Daddyn Hakeem yaciga dacewa
Narayu cikin maraici tunda natashi bansan dadin uwaba sai na uba ga kuma gallazar matar uba wato ke Hajiya suwaiba narayu a hanunki cikin kunci da gallazawa
Kuma.abinda bakisaniba shine kice silar mutuwar mahaifiyata amina bayan ta haifeni kukamata jifa da ciwo da haka har Allah yadau abinsa
Kinsan a ina naji kamaku nayi kuna zancen keda Hajiya larai kishiyar ki
Nayi kuka kaman raina zaifita
Dana ji wannan magana daga bakinki
Kunsani maraicin dole kuma kuka kasa rikeni tsakaninku da Allah
Ba irin abinda bakuyiba ganin namutu amma Allah yace saina rayu a duniya
Alokacin da Allah yabani haihuwar ABDUL HAKEEM nadade ina mishi adduar Allah yarabashi da sharrinku
Dan nasan yanzu hankalinku zai komo kan 'Dana
Kullum cikin mishi addua a ruwa nake inabashi yasha
Wanda nasan ko mahaifiyarshi batasan niyya na ba
Saikuma kwatsam kukazo da gudirin aurawa Hakeem Laila alokacin shekarunsa basu wuce ashirinba kuka dage sai anyi na amince ne saboda wani dalili
Dan koda din ma abbana bai aminceba inzaku iya tunawa
Saboda haka babu Wanda ya isa ya hanshi aure
Idan kunga 'yarku bazata zauna da kishiya you are free to live with her
Hajiya rukayya da jike sharkaf da zufa
Zatayi magana daddyn Hakeem yadaga mata hanu ba abinda zakice yaya rukayya
Hajiya suwaiba ta sauka har kasa tace Dan Allah abubakar kayafe min wallahi duk sharrin shaidan ne hakan bazai kara faruwaba
Daddyn Hakeem yace haba Hajiya ai duk da abinda kika min bazaisa nadaina ganin ki a matsayin uwaba
Dan haka kitashi daga tsuguna min
Hajiya suwaiba tace nagode Allah yamaka albarka kaida zuriarka
Hajiya rukayya ma tana kuka taba wa daddyn Hakeem hakuri daddy dayake shiba meruko bane ya yafemata
Hakeem ya kalli mahaifin nasa yaga daddy na goge kwalla
Bakomai yasa daddy kukaba sai rashin imani irin nasu
Idan ya tuna sune sillar rabashida mahaifiyarshi da ko kamannin ta baisaniba saiyaji wani kunci
Daddy kasa jurewa yayi yatashi yashige bedroom dinsa
Abdul Hakeem yabi bayansa mummy hafsat ma tashi tayi tabisu
Hajiya rukayya tabuga tsaki aikin banza wallahi wannan kukan danayi bazai tagi banzaba
Hajiya suwaiba tace towayafada miki dama tubar gaskiyace
ai kawai ganinayi asirinmu yatonu shiyasa na bullo musu tanan
Laila cikin kuka tace yanzu dai kuna gani Hakeem zaikawo wata dasunan mata
Suby kanwar Laila ta ce ai wallahi duk wacce tayi gigin shigowa gidan ki anty Laila wallahi taja wakanta balain duniya Dan wallahi sai mun nakasa rayuwarta
Hajiya rukayya tace ai zama bai kamamuba
Ke Hajiya bari musa driver yamaidake gida
Gobe zamuyi nijar saboda ke Laila yau kije kibashi hakuri
Kinuna kinyi ladamar abinda kika aikata har dai yasamu yabarki gobe mutafi
Laila tace shikenan hajiyarmu Allah yabar mana.ke kina kokari ganin farin cikinmu
Nan sukatashi kowa yakama gabansa
Laila ta koma part dinsu tazauna tana tunanin abubuwan da suka faru
Wanda sana diyarshi allura ta tono garma
****
Laila sundawo daga nijar yanzu tana zaune ne zaman jiran amarya Dan tafara aiwatar da niyarta
Hakeem kuwa sake tsarin gidannasu yabayar akeyi badare ba rana
aiki ake zabgawa
Zama yayi yaga gaskiya a yanzu yakamata dadinsa yadaina fita office
Shiyakamata yayi komai su su huta
Kuma bashida da sha'awar raba gida da mahaifansa
Yayi shawarar dawowa A B U Zaria sunfi kusa da nan
Zaisamu daman da dazaije ya kula da harkokin kasuwancin daddynsa
Ahmad ma yace shima kawai kadunan zaidawo yacigaba da rike company daddynsa
Shiya sama yasa ma aikata gyaran gidanshi na Kaduna
Sunyi parking gabadaya zuwa Kaduna Aisha matar Ahmad ta tare a sabon gidanta dake Kaduna
Hakeem ankam mala komai ainda aka fitar wa da kowa dinshi
Part din Hakeem yana tsakiyarsu
A babban folon PROF zai iya shiga part din kowacce falon nashi guda biyu akwai a sama Wanda idan ka haura sama falon PROF shima daga gefe kuma wasu maka makan bedroom dinshi guda biyune
Kai gaskiya dai naira tayi kuka a gidan Prof
Gabakidayansu yasakewa was furniture's har daiyayensa
Komai yazuba wa Husnah Wanda uba yake wa 'yarsa Prof ya dau nauyin komai
Bakin ciki kamar zai kashe Laila amma ba yadda ta iya dole tanuna bakomai saboda tasamu ta cimma burin ta akan amaryarsa
Mummy hafsat gobe zasu daga zuwa Dubai itada mummyn Ahmad
Hado kayan lefe
*******
Biki ya rage saura kwana hudu Hakeem ne cikin motarshi yana zaune agefen mai zaman banza
Yayinda Ahmad kuma yake driving zasu kano gidan su husnah
Ahmad yace kai prof gaskiya kacanja wallahi gaskiya Allah yawa husnah albarka data saita mana kai
Dafa magana wahala yakebaka
amman yanzu sai a zauna dakai asha hira musam man ma na husnah
Hakeem yayi murmushi yace kaikuma dadina dakai sa ido wallahi
Ahmad yace aidole ne asamaka ido yadda yarinya karama tacanja ka
Hakeem dai murmushi yayi yace bazaka kanebane abokina bakasan yadda nakejin babyn a raina bane ko
Ana kiran la asar suna shiga gidansu husnah ya shamsu yataresuda murna yace kaga manyan kannena
Ahmad yayi murmushi yace fada dakyau ya shamsu girma fa Allah yabaka
Hakeem yace kana mamakine yaya shamsu
Ya shamsu yayi dariya yace waneni da mamaki Dan na zama yayan manyan maza
Daga shiya shamsun dayayi maganar harsu Ahmad da Hakeem sai da sukadara
Ya shamsu yace bissimilla mushiga daga ciki
Hakeem yace mudai fara gabatar da sallah tukun
Nan suka wuce masallacin unguwar
Husnah zaune itada anty kubra
Anty kubra tace Dan Allah husnah kisanar da kawayenki
Maganar bikinki
Husnah ta yatsina fuska tace nifa bazanyi taroba ma
Nibana mason hayaniya wallahi
Kuma da kika damu bagakiba dake da anty Aisha kusai kuzama kawayena
Kubra tarike baki tace lalle husnah wuyanki ya isa yanka
Nice ma zan zama kawarki ko
Husnah tace to Baku kuka dage saina aureshi ba
Anty kubra tayi murmushi tace aini dadina da gobe saurin zuwa
Kaman yaune zakizo kinacemin anty kubra
Wallahi inason mijina
Husnah tayi murmushi tace humm anty kenan nifa nafada miki auren biyayya kawai zanyi amma ba wai danso ba
ai nagama soyayya
Anty kubra tace shikenan tunda haka kikace akwai ranar maida martani
Anty jumai wacce aka dauko tunda Sudan saboda gyaran amarya tunda akasa bikin washagari ummu tayi Sudan dama can ita mutuniyar cance
Anty jumai tadubi husnah tace tashi muje kishiga wankar tunda
Hadin yayi awa biyu da shafawa
Husnah tace anty wai Dan Allah yaushe za adaina min wannan shafe shafen nan da shaye shayen nan
Anty jumai tayi dariya tace sai randa kikabar gidan
Kuma kuji dakyau dawasu zaki taki tafi
aikuwa Husnah ta turo baki ta tashi taje ta shiga wanka
Tana kansaka kaya taji muryar su yayanta da PROF suna gaisawa da umma a falo
Tayi niyar kwalliya tafasa Dan mutumin nan yabata tsoro ranar
Riga da skirt tasaka nawani tsadaddan net tayi kyau bakadanba
Powda kawai tashafa sai man baki
Tana kan maida kayanta cikin durowa anty kubra tashigo tace amarya ango nakira yana falonmu husnah ta turo baki tace anty kinfara ko
Zanrama wallahi nasan abinda zanmiki kema
Kubra tace ya hakuri 'yar kanwata nadaina
Dan nasan ki sarai wallahi
Husnah tayi murmushi tace a to dole abani hakuri dai
Tadauki mayafin kayan tayafa
Kubra tace kai husnah kedai komai baki baiwane
Wallahi kinwani canja ne fa gabadaya
Kinciko tako ta ina
Jin abinda anty kubra tace yasa husnah tunani tabbas ko itakanta tasan komai nata yacanja
Kuma acikin sati biyun nan da akafara mata gyaran jiki ne
To gaskiya bazata tasa gyaleba
Ta ajiye gyalen tadauki jibgegen jijabinta
Anty kubra tace haba Dan Allah mijinkine fa yazo zakije masa da wannan katon hijabin
ai gwamma dai kidau ki mayafin dakikayi niyar sawa
Kinga zaisake shiga hanu kafin nan da kwana hudun nan
Husnah tace aikuwa kinja ma wallahi rayuwar hijabin zanyi agidansa
Ta wuce anty kubra tayi falon
Tashiga da sallama ya amsa mata tamkar wani balarabe
Kamshin sa yacika falon
Husnah tanemi kasa tazauna
PROF yakureta da kallo wani kyau yaga tamishi
Kaman yau yafara ganinta
Husnah tagaisheshi bai amsa ba jin bai amsa ba yasa tadago suka hada ido yakafeta da idonshi
Kasan yasauko yazauna yana fuskantarta yace haka ake tarbar miji baby
Tayi shiru batace komaiba yace babay magana nake fa
Husnah cikin shagwabarta Wanda ita bada niyya tayi shiba tace menama kuma
Yace nafarko nace kidaina samin hijabi idan zakizo gurina bakida mayafaine
Tace tokai meyasa bakason insa hijabin
Hakeem very good question
Nafarko inason hijabi amma a muhallin daya dace asaka kaman kiganni da wani ko abokaina da kuma sauransu
amma banda dagani saike kisaka
Bakisan nazo naganki Dan nasamu nutsuwabane ?
Husnah tayi shiru tana wasada da zobenta
Murmushi Prof yayi Yakama hanunta tana kokarin janye hanunta prof yacire zoben hanunta
Kafin yasaketa
aikuwa Husnah ta kalleshi a tsorace tace Dan Allah kayi hakuri kabani zobenan
Yace meyasa zan baki tace nima bani akayi
Yace wakenan tayi rau da ido kaman zatayi kuka
Tace masoyina ya muallim
Yace zan baki amman saikinbi maganana kicire wannan jijabin
Dan ba anan yakamata kisaba
Husnah tace Dan Allah yaya kayi hakuri kabarni da hijabina nariga nasaba
Hakeem yace OK yasaka zoben a aljihunsa
Yace nawa kike bukata game da events din ki
Husnah takalleshi tace nima bana bukatar komai
Ya kalleta da mamaki yace saboda me tace bakomai wallahi ni duk wani Abu dayashafi bidia bana kaunarsa
Dan Allah yaya daman inason na roki alfarmar events din dakukasa akatin nan wallahi banaso
Dan Allah kabarshi kawai
Hakeem yace duk abindakikace haka za ayi amma bashi ne
Duk randa kika haifamin baby zan baki mamaki duk abinda ba ayi a bikin nan ba saina yishi
Husnah tayi shiru can tace tokabani zoben yashare zancen
Yafito da kudi dubu Dari shida ya aje mata yace gasu nasan zaki bukaci kudi banason kitambayi ya shamsu ko Abba
Duk abinda kike bukata let me know OK
Ya cigaba da kallonta kawai kaman yasami TV
Husnah tace maganar zoben
Yace sakinyi abinda nace miki
Husnah tace nayarda amma saidai nakoma na dauko mayafina
Baice komaiba sai binta dayayi da kallo
Shigowar husnah Hakeem kusan suman zaune yayi Dan baitaba tunanin abinda idonshi zaiganiba kenan
Da sauri yace baby go and wear your hijab please
Husnah takoma da sauri
Tana shiga dakinta fashe da dariya
Dan bakaramin dariya yabata ba
Hakeem dafe kai yayi take hankalinsa ya tashi
Nan yafara tambayar kansa
Meyasa sai akan yarinyar nan yake jin feelings haka
Maiyasa komai nata is so special to me
Da kyar yaja kafarsa yafita zuwa gurinsu Ahmad da ya shamsu
Ahmad yace muwuce ko PROF yace
Hakeem yace muje muma su umma sallama
*******
Laila takira meenat tafada mata duk abinda kefaruwa
aikuwa meenat kaman tayi tsuntsuwa tazo Nigeria
Tace kiyi abinki mummy babu matar data isa kiyi kishi da ita wallahi
Idan mukazo koni ko 'yar iskar da tayi kasadar auran daddyna
Suna gama waya da Mummynta Laila
Tadubi Bashir tace kaji kuwa mekefaruwa agidanmu
Bash yace saikin fada
Takwashe komai tafada mishi
Tsaki bash yayi yatashi
Yabar gun
Next page
Your comments is needed fan's
Love u all
[05/05, 8:53 PM] UMMU AFAN :
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Story & written
By
The special writer
UMMU AFAN
FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION
(F.C.T.W.A)
HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION
I DEDICATE THIS PAGE TO YOU Hauwa'u idris ( maman daddy )
Allah yabar zumunci inajin dadin comment din ki Allah yabar kauna keep it up
AKWAI lokaci
PAGE 101to105
PROF yashigo direct dakin amaryar ya wuce sai yaji kofa gam
Kuma gashi bashida spire key
Duk guda hudun suna hade da juna
Ya koma dakinsa yayi wanka
Ya koma kan bed dinsa yadauki waya
Yasoma dialing din number husnah yayita ringing
Husnah bata daga wayar ba
Prof yayi mirmushi Wanda shikadai yasan abinda yasashi murmushi
Ya rufe ido Dan bacci amma bacci yace baisan zancenba
Yadauki wayarshi kawai yakira Ahmad
Saida yakira Ahmad sau biyu kafin ya dauka
Ahmad yace kai ango yadai kira da wannan lokacin
Hakeem yace kai dai bari wallahi man
Wallahi yarinyar nan ta kulle min kofa
aikafin yakai karshe Ahmed yafashe da dariya sosai yayi dariyarshi
Kafin yace amma wallahi husnah ta burgeni
Sosai
Hakeem yace Dan iska dariya zaka min ko
Ahmad yace aikaine abokina duk kabi ka tsorata masu yarinya aidole ta kulle kofarta
Dan batasan mezaifaruba idan akabarku Ku biyu
Hakeem yayi murmushi yace duk tagama buyanta badai ta shigo hanu ba
Zanbata mamaki zata shigo hanu ai
Ahmad yace wallahi dai kabi yarinyar mutane a hankali
Bafa babbar mace bace
Dan nasan kasaba da manyan mata
Yayi dariya yakashe wayar shi
Hakeem cikin murmushi yabi wayar da kallo
Yace zanrama ne
Kafin yakoma amma bacci fa yaki Sam
Daya rufe ido zaiga husnah alokacin da yake kissing dinta
Sai yayi murmushi ya rungume pillow kawai bacci yayi awun gaba dashi
Laila duk abinda kefaruwa tana lebe tana gani aikuwa ganin Hakeem ya burda kofa yaji akulle duk ta gani
Har wayan dasukayi da Ahmad taji aikuwa cikin farinciki ta koma part dinta ta sanar da su hajiyarta da kanwarta suby
Dan basu komaba ita suby auran nata ya mutu shiyasa zata zauna gurin Laila
aikuwa cikin farinciki hajiya rukayya tace aikin banza Ashe ma duk abinda suke yarinya bata so
Suby tace a a karku manta dama boka yace zai sa gaba a tsakaninsu
Watakila aikin ne boka ne yafara aikitakanta
Inbahakaba wazaiki yaya Hakeem a matsayin miji
Hajiyarsu tace tabbas maganarki hakatake
Kunga ganiba gwamma da muka sake mishi kudi gashi anfara aganin cigaba
Laila dai da farin ciki ta kwanta abinta zuciyarta fati kal
Karfe hudu dai dai na asuba Husnah tafarka cikin nannauyar baccin da ya dauketa
Tashi tayi tashiga bathroom alwala tayi kafin tayi nafilfilunta kamar yarda tasaba ana kiran sallar asuba tayi sallarta tayi adduointa da karatun alkur'ani
Kafin tacire kayan jikinta Dan jiya bata samu daman cire kayan ba saboda gajiya
Tashiga wanka kafin tafito
Spray kawai da shuwa tashafa sleeping dress tasaka duguwar riga abinta tafada gado abinta
Sosai taji dadin baccinta Hakeem bayan yadawo daga sallar asuba yasake tana dakin husnah shiru bata budeba
Direct dakinshi ya wuce dakinsa
Shima baccin yakoma
Karfe bakwai da rabi dai dai mai aikin mummy ta buga kofa
Suby kanwar Laila ita tabude kofar
Taga me aikin mummyn Hakeem ce
Tace sannu suby ta yatsina baki yadai ina zaki da basket din abinci haka
Tace hajiya ce ta aikeni nakawo ma amarya abin karyawa
Suby ta kebe baki tace to aikuma basu tashiba amma kawo saina na mika mata
Tabata abincin
Suby ta karba tashige dashi part dinsu gurin su Laila da hajiya rukayya
Laila cikin murna tace yauwa suby dauko maganin a side drawer kikawo
Aikuwa haka suka barbade komai da maganin nan
Farfesuf na kayan ciki sai kunun gyada da kosai
Kai kuma farfesun ganda Wanda yasha kayan hadi sosai
Haka suka bikomai suka badeshi tas
Hajiyq rukayya tace maza ke suby tashi kikaimata
Laila tace abarta ta kai Dan tanason ganin amaryar
Hajiya rukayya tace a a idan kika kai dakanki za azargi wani Abu
Zakiganta ai mudai burinmu kawai tabar gidan
Suby tace wallahi nimafa basanin amaryar nayi bama dan haushi
Husnah cikin bacci taji ana buga mata kofa ta tashi tayi hanyar falonta
Tayi kofa tabude sukayi ido hudu da suby
Suby sai tadauka kaman gezo idonta suke mata wannan irin zukekiyar yarinyar kuma daga ina
Husnah ta ce sannu suby tace ina antyntaki
Husnah ta yatsina fuska tace antyna kuma
Suby tace ina nufin amaya
Husnah tayi murmushi tace OK ai tashiga wanka
Tana ganin suby tasauke ajiyar zuciya
Husnah ta kibata hanya kuma
Suby tace ga shi inji hajiyar yaya Hakeem akawo mata
Husnah tace OK angode barin kaimata
Suby ta mika mata basket din husnah tarufe kofarta
Murmushi husnah tayi ta ajiye basket din ta ajiye kan dining kafin ta koma kan bed koma bacci
Sai karfe goma dai dai ta tashi
Ta gyara bedroom dinta da falonta ta badeshi da kamshi
Ko ina yadau kamshi kafin tashiga bathroom tayi wanka tafito ta shirya cikin wani tsadaddar super Holland dark blue sai adon pink ajikinsa
Yadda dinkin yazauna ajikinta shizaifi Baku sha'awa sosai das yamata dinkin ma kawai a in kallone
Matsalarta daya bata son dankwali ta tace gashinta takama da ribbon pink
Kafin ta murza daurin Dan kwalinta abin wuyanta ma pink ne
Gaskiya husnah tayi kyau matuka
Tadauki ta kalminta plate shoe tasaka
Har ta zauna zatafara break fast saikuma taga rashin dacewar hakan
Bata je tagaida mummy ba
Gyalenta tadauka maishegen kyau tayafa
Pink colour
Tafita tayi hanyar kofarta tasaka key ta kulle
Bayan ta fita
Dama dole saitabi ta main falonsu gabadaya tana fitowa kuwa taga mutan gidan gaba dayansu a falo
To itabasaninsu tayi ba
Ganin harda manya yasa husnah ta durkusa tana gaida su hajiya rukayya da kuma Laila
Laila ta watsa mata harara
Wai ita hakimar bata fitowa ne saike
Hajiya rukayya tace inazata fito ansamu duniya
An auri mekudi an asirceshi
Suby ta kalli husnah tace 'yar buzuwa kotafiya za ayi ne
Husnah ta kalleta tace inje ina ai munsamu gida nida antyna
Dan nadawo kenan gwamma muma muzauna muci arzikin Dan da alama bamu kadai bane 'yan cin arzikin
Husnah tana gama yada musu magana tayi waje abinta
Har suby zata bita hajiya rukayya tace a a kyaleta kar ajimu tun yanzu mana
Laila race lalle ma Dan talaka be iya samun wuriba
Wannan zakewa haka harda dauko 'yar riko
To wallahi wannan yarinyar kamar aljana bazata tazauna min agida wallahi
Kalli yadda take tafiya kamar wata 'yar sarki
Hajiya rukayya tace aibakisan halin talakabakenan idan yasami guri
Kuma ke Laila da kike cewa bazata zauna ba yayar tata ma ba zaman zatayi balle ita 'yar cin arziki
Nan dai suka muna funcinsu
Husnah tayi sallma a falon mumy shiru ba kowa
Ta nemi guri tazauna a tafkeken falon su mummy
Mummy ta sauko daga sama bata lura ba harzata shige kitchen
Husnah tayi saurin sauka kasa tace mummy ina kwana
Mummy hafsat tajuyo tayi tazali da surukar tata
Tace a a husnah ai ban lura bama meyasa kika zauna nan baki haura saman ba saikace bakuwa
Husnah tace bakomai mummy nan ma yayi
Mummy hafsat tace a a nan gidanku ne ko ina zakishiga
Kina da damar hakan kinjiko
Ya bakunta husnah tayi murmushi kawai batace komai ba
Mummy tace kinci abinci ko husnah tace yanzu zanje nayi
Kafin mummy tayi magana Abdul Hakeem yayi sallama yashigo wata tsadaddiyar shadda milk colour sai wata hadaddiyar hula da ya murza akansa Wanda yasake fito da kyakkawar fuskarshi mai kewaye da kwantacen saje dayakarawa fuskar tashi kyau
Gaskiya PROF Fa kyakkawar mutumne bankarya
Yashigo idonsa yakai kan Husnah dake zaune kan kafet
Wani farinciki yaji sosai
Ya kalli mummy
Yace mummy na antashi lafiya
Mummy tace lafiya kalau son maza kuwuce dining kawai kuyi break idan kungama kukirani zanje nayi salar walha
Hakeem yace angama dalibata
Mummynsa tayi murmushi tace a a tun yaushe daliba ta canja malami ai
Hakeem yace amma tunda yanzu nadawo gida
Sai kisake sayan form agurina Husna da mummy sukayi murmushi
Mummy tace kaga idan nabiye maka sai lokaci ya wuce banyi sallar ba
Ta kalli husnah tace 'yata tashi kije dining kinji kikarya abinki kinji
Ina zuwa yanzu
Mummy tayi sama tabarsu anan
Hakeem yakure wa husnah ido yace wana kama
Husnah ta saukar dakai kasa
Hakeem shima zamayayi shima tabayanta yakamota yasakalo Kansa tagefen wuyarta hanunshi yakai cikin rigarta ta yashafo cikinta
Yace bakice abinciba baby jicikinki fa kaman zai hade da baya
Itadai husnah wani iri takeji tabatan dayakeyi
Yace tashi muje nabaki abinci banason musu
Cikin shagwaba husnah tace ni anan zanci ba a dining ba
Prof yace angama baby dakanshi yatashi yakawo musu komai plate daya yazuba musu
Yace oya bude bakin bayan yadauko kofin kunun gyada tace dakaina zan sha kabari kawai
Yace bason musu fa
Badan tasoba tabude baki yabata
Nan yabata farfesun ma kosai da duk wani abin dake gun saida yashiga cikin husnah tace mishi ta koshi yaki
Yace daman ya shamsu yamishi bayanin bata cin abinci
Cikin shagwaba husnah tace wallahi inaci kuma nakoshi sai da yaga tana shirin dawo Dana cikin nata yabarta haka kafin shima yafara cin abincin
Bayan yagama ne yasa hanu zai dauke tiren abincin husnah targashi yace yadai yakureta da ido
Tace kabarshi kawai zankai
Bai hanataba husnah tadauka tayi hanyar datake tunanin nan ne kitchen din
Tana zuwa ta ajiye a sink din wanke wanke ta wanke tas duk wani abin da za a wanke saida ta wanke
Shikuma prof be biyo sa wuba saboda yana waya ne
Mummy tasauko daga sama tagashi shikadai ne a falon
Tace a a asmaun
Hakeem yayi sallama dawani abokinshi yace tashiga kitchen
Kai kwanuka
Mummy taleka kitchen dintaga ko ina tsaf an goge
Mummy tace kai haba husnah da kanki Aida kinbarima yanzu mai wankewar zatazo yau tayi ranar dawowa ma
Husnah tace bakomai mummy
Mummy tace maza jeki huta kafin nafito
Husnah tayi murmushi tace
a a mummy meza adaura Dan naga kaman abinci kikeson daurawa
Mummy tace a haba dai daga zuwa harkifara shiga kitchen a a jeki huta
Idan kunyi sati saikifara dafa abincinki
Husnah tace mummy kigafarceni amma banzan taba zama inga kina shiga kitchen
Yakamata kema kihuta Dan Allah
Tunda na taso agidan mu Nina ke abinci umma ta na hutar da ita saboda haka Dan Allah mummy kibari na ringa miki abinci kihuta kema kisan kinada yarinya a yanzu
Cike da mamakin kalaman husnah mummy tace lalle husnah kin haifu Allah ya wa iyayenki albarka dasuka miki tarbiya maikyau
Nagode da kika daukeni matsayin uwa
Allah yabaku zaman lafiya keda mijinki yazaunar daku lafiya kinjiko
Husnah kai akasa tayi shiru
Mummy tace na'amince zaki rinkawa mummy abinci amma fa mummy ma tayi alkawarin satayi sati kina cin abincin mummy kinjiko
Saboda haka kibar mummy tacika alkawarin ta
Husnah tayi murmushi kawai kafin tayi magana
Hakeem yayi gyaran murya mummy da husnah suka kalleshi
Mummy tace wato labe kake mana ko
Hakeem yayi murmushi yakaraso cikin kitchen din
Yakama hanun mummy yace haba mummy please kibar yarinki tasamu ladarki
Allah ne ya amsa adduarki yakawo mana husnah cikin rayuwar mu
Kinji mummyna
Mummy hafsat tayi murmushi tace shikenan tunda kunmin yawa Allah yayi albarka
amma bayanzu za adaura abinciba sai yamma idan anyi la'asar
Yanzu muje kawai muyi hirar mu
Mummy taja hanun husnah wacce tunda Hakeem yashigo takasa magana
Ranar dai a sashin mummy husnah ta wuni sai da ka kira isha tabar dakin mummy ganin Hakeem da daddy sunfita sallah
Mummy tace yau husnah Allah yatashemu ki huta gajiya ko
Ita mummy a tunaninta husnah zata je tashirya ne kafin mijinta yasameta
Husnah kuwa tashiga falon taga Laila da suby a zaune
Ta wuce abinta batareda ta kalli kowa ba
aikuwa suby tace ke zonan
Kojuyowa husnah batayi bare ma tasan da ita sukeyi
Ke 'yar talakwa bakiji menace bane husnah tayi banza dasu kafin suby ta karaso husnah tashige ta banko kofarta tasaka key
Direct wanka tafara kafin tayi sallah tayi karatun ta data saba
Suby tace anty anya kuwa ba wannan aljanar yarinyar bane kishiyarki kuwa
aikuwa jitayi Laila ta zabga mata mari
Suby tace mena miki anty Laila
Cikin tashin hankali Laila tace damme zaki min wannan mugun fatan
Taya za ayi yaje ya auro 'yar cikinsa
Bama hakaba idan yakasance wannan yarinyar ce ai yayi abinkuya
Nikuma nashiga uku taya zafara kishi da wannan yarinyar
Suby tace aiko dai koki kokiso itace
Dan agabanki tasa mukulli ta bude sashinta kuma dazu Dana kai mata abincin ma ita nagani kawai raina mana hankali take
Laila ta daura hanu akai tace nashiga uku ni Laila wannan ai inaganin ko meenat ma ai tagir meta
Lalle Hakeem yacuceni
Yanzu sakayya da zaimin kenan ya auro 'yar cikina inyi kishi da aita ina Sam bazaiyuba wallahi
Suby tace wallahi idan kika bari aljanar yarinyar tazauna agidan nan
Zikidawo jaka wallahi Dan abinda kike samu bazaki samu ba
Yarinya kaman ita tayi kanta Dan kyau tahada komai da d'anamiji yake bukata
Laila tace ya isa haka suby zakisa zuciyata tafashe kibarni naji da Abu daya Dan Allah
Hakeem yashigo falon da sallama Laila ta taso sannu da zuwa baban meenat
Hakeem yace yauwa yashige bedroom dinshi Dan karya taba kofar husnah yaji akulle agabasu su fahimci wani Abu
Laila tabishi har yafito Daga wanka yana yashirya ya kwanta
Laila taga bashida niyar kulata yasata ce baban meenat har yanzu fa bansan kanwartawaba
Sai kanwarta muke ta gani tana shige da fice
Hakeem yayi murmushi Dan ta tabo inda yake mishi kaikayi
Yace kanwa kuma ai bata da kanwa itadai wacce kikagani din itace amaryata
aikuwa Laila ta tashi tace amma wallahi kaji kunya Hakeem yanzu da girman ka da darajarka zaka auro 'yar cikinka wannan ma ai zubda mutuncin Kaine da zubar wa 'yarka da mutunci
Prof baki kawai yasake kallon ta
Yayi murmushi yace kinyi sake maman meenat da kika auri mijin asmau saboda yanzu nasan nima namijine kuma na auri dai dai Dani kije aduba miki nidake bamu taba dacewa ba kuma bazamu daceba
Meenat da Allah yabani na karba kuma inason 'yata
Idan tazo ruwantane taso matata ruwantane takita
amma zanfada miki wannan Kalmar mummy da daddyne kawai bazan iya rabuwa dasu ba saboda husnah
Amma bayansu zan sabama kowa akan matata so get out of my room
Cikin tashin hankali Laila tafito Daga bedroom din Hakeem
Kuka sosai taci suby nabata hankuri
****
Bayan sati uku Hakeem ya Dade da komawa aikinsa gashi aikin yamishi yawa ga kullum tunanin husnah ne da sha'warta acikin ranshi
Ba inda yake samun ganinta sai a part din umma Dan Anna take wuninta
Tana fita sallar isha zata gudu
Hakeem zaune kan kujerar office dinsa Ahmad kuma yana cike wani file's
Ahmad yace yauwa kagani ko yana nuna wa Hakeem abinda yacike
amma hankalinsa baya taredashi
Ahmad yace wai meke faruwane Prof
Hakeem yayi murmushi wallahi baby ce take bani ciwonkai
Taki bari na rabeta Sam wallahi
Bana ganinta idan ba a gurin mummy ba
Ahmad yace zanbaka shawara idankabi yau din nan kadaina damuwa
Hakeem yabada hankalinsa sosai
Ahmad yace bakace agurin mummy take wuniba prof yace a
Ahmad yace sallar ishar dazakaje yau kabari kawai kamuku jam'i
Kana shiga kacewa mummya da daddy da ciwon kai kadawo
Idan kaga zata tashi saikace jirani mutafi tare agaban mummy nasan bazatayi musu ba
Hakeem yace kuma wallahi sai dai kuma yau laila ce da kwana
Ahmad yace saikayi hakuri yau da gobe ai duk dayane yayi dariya
Hakeem yace a a baduk dayabane wallahi kai bakasan halin danake cikibane shiyasa
Ahmad yace kai haba mai mata biyu fa amma kana fadin haka ai saika kabani tsoro nakasa kara tabiyu
Hakeem ya harareshi
Husnah falonta suna waya da ummanta da ya shamsu da anty kubra
Bayan sunagama wayarne ta dauko mayafinta zata koma banngaren mummy
Sai taji Laila tana waya amma bata San dawa take ba
Laila tace dadin abinma fa yarinyar baso shi take kullum a dakinta take kwana
amma wannan aikin bokane yace bazai taba bari harya kusanceta ba
Yanzu fa kusan sati uku kenan amma suna wasan buya bata ma bari yaganta
Shikuma na mamajo kina gani shi kisan yana cikin damuwa
Can ta matse mishi kinga haka malam zaicire mishi sonta aranshi kwatata
Dan nima yace karnabari ya kusanceni har sai yarinyar tabar gidan
Kinga kuwa ai yana cikin matsala dannima bana zuwa bedroom dinsa harsai ranar da wannan aljanar yarinyar tabar gidan
Nan dai sukayi sallama da kawartata
Ta kalli suby tace insha Allah saura kiris yarinyar nan tabar gidan nan
Daga nan kuma sai mufara shirin yadda zamuyi mukasheshi idanba haka ba wallahi wata zaisake hangowa
Suby tace wallahi da dai yafikam
Dan wallahi nima inason naga munfara fantamawa fa anty
Laila tace kidai yishirunki kawai saura kiris
Husnah toshe baki tayi sai kuma wani jiri data ji yana dibanta dakyar tasamu takai kanta kan kujerarta
Tace innalillahi qainnairraihirraju'un nashiga uku meya musu suke son kasheshi
Gaskiya bazantabari kuyi nasara da yardar Allah
Kuma mijina zaisamu abinda yakeso insha Allah
Allah yakaimu gobe nashiga ukuna ni husnah wani irin zunubi na daukarwa kaina
Tabbas yaya Hakeem bai can canci wannan sakaiyar daga garaniba kayafemin Dan Allah duk da banasonka nayi alkawarin faranta maka kamar yadda kake faranta mana nida iyayena
Duk wannan maganar da husnah take yi tanayinsane itakadai
Hmmmmmmmm
Next page
Your comment is needed fan's. Love u all
Duk wacce bantaba bata page ba
Tayi comments mezafi next page natane
[05/05, 8:53 PM] UMMU AFAN :
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Story & written
By
The special writer
UMMU AFAN
FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION
(F.C.T.W.A)
HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION
I DEDICATE THIS PAGE TO YOU BINTA ADAM (MAMAN IMAM) COMMENTS DINKI YANA SANI SANI CEWA NIMA WATACE SO PLS KEEP IT UP
INA ALFAHARI DAKE ❤
AKWAI LOKACI
PAGE 96 to 100
YAU take asabar daurin auren prof da husna
Wanda za adaura karfe uku na rana saboda bakin da zasuzo daga kasashen waje saudiya da sauransu
Duk Wanda baisamu yakaraso tun juma'a ba saboda wani uzirin
Shine aka daga daurin auren
Kuma a yaune ake kai za akai lefe gidansu husna anasu aladarkenan
Mummy hafsat ce zaune cikin kawayenta matan mayan mutane
Da kuma 'yan uwa da abokan arziki
Kowa taganta yasan tana cikin farin ciki Mara misaltuwa
Ana ta kallon lefen Hakeem Wanda za akaima husnah anata yabawa
Mummyn Ahmad tace kafin atafi kai lefen yakamata akira uwargida tazo taga kaya ko
Mummy hafsat tace to akirasu mana
Dai dai lokacin Aisha matar Ahmad tashigo da daukar wayarta data saka caji Dan tunda aka fara hidam bikin nan agidan mummy take kwana
Mummy hafsat tace yauwa 'yar albarka mazaje kicewa su Laila suzo zuga kaya
Aisha tace to mummy tayi part din Hakeem tashiga part din Laila
anan ta tarar da suby kanwar Laila da hajiya rukayya da hajiya suwaiba da ita Lailar kanta
Sai kuma kawayenta
Aisha ta gaishesu bawanda ya kalleta suby kanwar Laila ce tace dalla malama meyakawoki nan
Aisha tace to bani nakar zomom ba nima rataya akabani
Hajiya rukayya zatayi magana Laila tace yishiru kawai hajiya bake yakamata kimayar mataba
Suby tace kema anty bake yakamata kibata amsa ba nice dai dai da zamaninta
Aisha dadina da jaki duk yadda akayi da shi saiyaci kara
To nima bazuwan kaina nayiba mummy ce tace kuje kukaga kaya Dan za a wuce da shi
Tajuya tayi waje abinta
aikuwa Laila ta mulmulo zagi tabita da shi
Hajiya rukayya ta yi saurin rufe bakin Laila tace ai banso kukayi sainsa ba
Kunga idan muka ki zuwa ganin kayan zasuyi tunanin har yanzu akwai Abu akasa
Kunga kuwa ida suka gano mu ai akwai matsala
Dan haka ke Laila kidaure mutashi muje kinuna bakomai azuciyarki
Suby tace kuma fa hakane hajiya gaskiya kin iya taku mai kyau
Hajiya rukayya tayi murmushi tace kutsaya sanya yara
Nan sukayi part din mummy aikuwa ganin irin mutanen da suke cikin makeken falon daddy suncika shi dam
Duk wani dakuna na gidan suna cike da 'yanwan da kawaye dakuma makota
Wani katon bakiciki ya lullubesu su hajiya rukayya
amma Sai suka make
Hajiyar Ahmad tace sannu Ku da shigowa hajiya rukayya tayi taken dole
Idon Laila yakai kan wasu maka makan tsadaddun akwatuna tagani tsakiyar falon akalla zasu kai goma sha takwas
Nan Mummy hafsat tace kumatso kuga kayan mana nan suka shiga kallon aljan nar duniya duk akayan bakaramin zani
Karami aciki shine 25 thousand
Banda sarkoki masu tsadar gaske ga takalma da jakankuna suma awani jibgegen katon jaka aka narko su
Jakar kanshi abin kallone
Mummy Ahmad tashiga musu bayani kayan tace wannan shabiyun dakuka gani gefe shine Wanda ango yayi wannan kuma Wanda hajiya tayi ne
Hajiya rukayya da Laila suka hada ido
Tsaban bakin ciki sunkasa magana ma Dan haushi duk yadda sukayi kar agane su sunkasa
Mummy hafsat murmushi kawai takeyi tace wa hajiyar Ahmad Yakama ta kukai kayan nan lokaci karyawuce
Hajiyar Ahmad da wasu daga cikin kan nan mummy hafsat saiwata kawar mummy
Suka tafi kano kai kaya kuma suzasu dauko amarya
Laila kuka take sosai bayan sunkoma sashin su
Hajiya rukayya tace lalle hafsat tacika Mara mutunci kuma zan nuna mata nice gaba da ita aduniyar ma
Zata kwashi kashinta a hunu
Suby cikin bakin ciki tace ai ba ita kadai bace munafukar
Kinga dukiyar da ya kashe a lefen
Hajiya rukayya tace nashi shabiyu na hajiyar itama ta wa maryar shida
Kuma wallahi duk kayan ba na nan kasar
Suby tace wai wannan amaryar ma 'yar gidan uban waye ita da har suke rawar jiki akanta
Hajiya rukayya tace talakawa ne futuk Dan a yadda nasa aka min bincikema gidan dasuke ciki shiya saya musu
Laila ta ce nashiga uku hajiya yaushe rabon Hakeem yabaki ko naira Dari ne
amma shine har da siyawa sirakanshi gida
gaskiya saina kashe yarinyar nan
Hajiya rukayya tace kedai kidaure kawai musamu bukatar mu ta biya
Tana cin abincin nan fa shikenan
Taya zata ci abinci saikin nuna mata bakomai azuciyarki
Laila tace kodan burina yacika ma zanyi kokarin ganin komai ba komai bane
Suby tace wai fa harda mother's nigh mummyn Hakeem tahada
Hajiya rukayya tace munafuka ba kinsan dama tace Sai zaisake aure zatayi biki
*****
Umma da mutanenta suka hadu suna ta karbar bakin 'yan kawo lefe su hajiyar Ahmad kenan
Sosai sunji dadin karbar da aka yi musu daki guda aka ware musu ga kayan ciye ciye nan burjik Sai Wanda suka zaba
Husnah kuwa tana nan zaune kan gadonta cikin wata kwalliya ta musamman Wanda aka dauko mai make up
Husnah tayi kyau shar da ita
Cikin wata rantsatstsiyar less
Golden colour ga sarkarta mai tsada shima
Anty kubra ce zaune gefenta da Aisha matar Ahmad Dan itama tabiyo masu kawo kaya
Aisha tace gaskiya Laila zatayi hauka idan taga husnah ce kishiyarta
Kubra tace kaman yaya
Aisha tace to ai banbanci tsakaninsu a bayyane take
Wallahi kubra koni danake mace bana gajiya da kallon wannan tsadaddiyar amaryarmun
anty kubra tayi dariya tace gaskiya dai kam Husnah mace ce wallahi
Wani lokacin sainaji dama husnah bamai mata ta aura ba saboda gaskiya dayar zata iya cutuwa
Aisha tayi murmushi tace hakane kam Sai kuma Allah yasa itadin dai rabom ce
Husnah dai batace musu komaiba tana ta shashshekar kuka ne ma tunda dataga dai tabbas auran za amata
Wayar husnah tadau kara ta tsinke bata daga ba
Aisha tasa hanu tadauki kiran
Tayi sallama Hakeem yace wacece Aisha tayi dariya tace ango kasha kamshi wato ma harkagane ba ita tadau wayarba
To Aisha ce
Hakeem yayi murmushi madam dakanta kenan yace ina babyn
Aisha tace gaskiya baccima take saboda ciwon kai
Yace what meyasa bata fada minma
Ganin nan zuwa
Aisha tace haba dai cikin matan zaka shigo yace mata ko iyaye da 'yanuwa
Naki wasane Ku kulamin da ita kafin nazo
Aisha tace Dan Allah kabari a daura saikazo kaga mutane sun ragu
Hakeem yayi murmushi yace kanki akeji
Ya kashe wayarshi
PROF yakalli Ahmad dasuke cikin tarin abokansu larabawa da turawa dama dai 'yan kasar baki daya
Yace zanje inazuwa yanzu Ahmad yace zakafara ko
Gaskiya ba Inda zakaje Sai andaura auran nan my sallami kowa
Hakeem yace kafahimceni wallahi ko na zauana bazaku gane kainaba
Idanba naje nadubo babyna naba
Ahmad yace aidai idan kayi hakuri gidanka za akaita yau ko
Duk yadda Hakeem yakai ga son zuwa gurin babynsa Ahmad yahana
Haka ya hakura kawai amma zuciyar nawurin amaryarsa
3 : pm dai dai aka daura auran PROFESSOR ABDUL HAKEEM ABUBAKAR SHUAIB DA AMARYSA
ASMAU SULAIMAN SHAMSUDEEN
Wanda yasamu hallartar duban jama'a suka shaida daurin auran
Ana gama daurin aure ango yafara gaisawa da mutane Wanda suke mushi fatan alkairi
Sosai yake tajida jama'a kansa yayi zafi sosai
Su daddy ma sun wuce Kaduna shida abokansa da kuma daddyn Ahmad
Da kyar Hakeem yasaci idon Ahmad yayi gidansu
Husnah
Yana zuwa gidan yakira wayar Aisha matar Ahmad
Yace please Aisha yaza ayi naganta
Aisha tace barin zo saikashiga ta falon kubra
amma fa Sai dai kashiga ciki Dan bacci take
Hakeem yace OK ganin nan zuwa
Yafita yashiga har dakin husnah anty kubra ta mishi sannu dazuwa suka gaisa kafin tafita itama
Ya kalli gefen da husna ke kwance
Hakeem yace baby meyasa baki fada min kanki naciwo ba
Tayi shiru yace OK bazakiyi maganaba dama zoben ki na kawo miki
Yana fadar haka Husnah tamike tace ina yake Dan Allah
Tashin datayi dasauri Hakeem yazuba wa kyakkyawa fuskarta ido
Shifa gani yake kulum karawa yarinyar nan kyau akeyi
Sosai tamishi kyau
Yace kinaso tace a Dan kabani
Hakeem yaci fuska yace zoki karba
aikuwa husnah bata kawo comai a rantaba ta tashi taje gaban prof Dan dama ta kunce daurin da akayi mata gyalen ne kawai akan lallausar gashinkanta daya sha gyara Sai kamshi yake fitarwa
Gata ita kanta wani kanshi take fitarwa na musamman
Tana zuwa kusa da Hakeem tamika hanu yabata bakin lallen da aka zana mata da ja Wanda yasha stone mai kyalli
Hanun nata yabida kallo
Husnah batayi tsammaniba kawai tajita ajikin mutum ya rungumeta tsam ajikinshi kaman zaimaida ita ciki
Tabude baki zatayi magana ya hada bakinsu guri daya
Tayi ta kokarin ta kwace kanta kar ashigo asamesu haka amma takasa
Dan Prof namjin gaske ne
aikuwa bai kyaletaba Sai da yaji wayarsa tana kara yanasaketa
Husnah tadurkushe agurin datake
Hakeem Ahmad yagani yake kiransa
Yadaga yace wai ya akayi kuma Man
Ahmad yace wai Dan Allah ina kayi
Hakeem yayi wani murmushi kaman Ahmad nakallonshi
Yace ganinan ina tare da matata
Ahmad kai amma wallahi baka da kyau yanzu Sai da kaje zaka samusu yarinya agabako
Anya kuwa prof zakabari sukawo maka itakuwa
Hakeem yafashe da dariya yace gaskiya dai daza a mun adalci da anbani matana munwuce
Ahmad yace lalle angon karshen zamani
To Dan Allah yafito su shek zasu koma kuma suna son kuyi sallama
Hakeem yace OK gani nan zuwa amma fa kan katse min hanzari wallahi
Ahmad yayi dariya yace to sabonshiga
Suka kashe wayar gabadayansu
Husnah kuwa tunda ta durkushe agaban prof takasa tashi
Tayi tayi ta tashi Amman takasa saboda bakon alamarin da prof yazo mata da shi
Jikinta bari yake sosai Dan wani tsoron prof nema yakamata
Shima durkushewa yayi gabanta yakamo hanunta yazura mata zobenta
Kafin kuma yadago habanta suka hada ido Husnah tasaukar da nata kasa
Hakeem yace I love you baby
Kikula min da kanji kinji ko
Bata dai bashi amsa ba saboda kunyarsa datakeji
Ya manna mata kiss a goshi
Ya tashi zai bude kofar kenan husnah tayi cewa Dan tsaya Dan Allah batareda ta kalleshiba tayi maganar
Cikin mamaki Prof yajuyo yazuba mata ido ta tashi tadauko hankacif tabashi batare da tayi magana ba
Tanuna mishi madubinta
Bai ce komaiba yakarasa gaban dressing mirror dinta
aikuwa jambaki yagani duk lebensa da kumatunsa
Murmushi yayi Wanda yakara wa husnah tsoron shi
Ya goge kafin yajuyo yakamota yace meyasa bakya son nafita ahaka
Kowa yasan daga wurin matata nafito kobahaka bane
Kuma ma wannan dadewar danayi agunki kowa yasan hakan saiya faru
Husnah tadago fuskarta ta kalleshi kaman zatayi kuka
Tace yanzu harsu umma ma sun San hakan
Hakeem yayi murmushi yace duk Wanda ke cikin gidan nan Sai yayi zaton haka
Toke meye na damuwa mijinkine fa
Husnah tace nashiga ukuna Dan Allah kafita karsu shigo
Hakeem yace inzan kwana anan bamai shigowa kowa yasan ina ganawa da matata ne
Husnah kuka ya gangaro mata
Tace wayyo Allah na Hakeem yace matso kusa da ita shima zaman yayi bakin gadon hawayenta tas saida goge mata su da harshensa
Yace bana son nasake ganin kuka a wannan kyakkyawar fuskar
Ya tashi ya wuce yabarta da kunya
Dan idan duk ansan meya mata ai tashiga uku da wani idon zan kallesu ni husnah
Ganin fitan Prof yasa su anty kubra suka shigo dakin
Anty kubra ta kalli husnah data kasa hada ido dasu
Kubra tace har yafita kenan tanafada tana dariya
Husnah tasaukar da kai kaman munafuka
Aisha tace kai anty kubra wannan sa ido haka
Anty kubra tayi dariya kitashi yanzu za ashigo asake miki make up saboda yanzu za awuce dake
aikuwa husnah ido yayi rau rau jin za a wuce da ita
Anty jumai mai gyaran amarya tazo tadauki husnah suka wuce zuwa bedroom din umma anan za amata kwalliyar tafiya gidan angon
Aisha ta kalli kubraa tayi dariya tace wallahi na tausaya wa Husnah Dan daga ganin yadda Prof yake bare bare akanta basauki
Anty kubra tace ai wallahi naga alama
Sai dai muce Allah raba lafiya Dan nan da wata Tara suna zamu je Kaduna
Kuma gaskiya husnah tayi dacen miji Allah yacika wa yayanta burinshi
Kullum acikin addua yake Allah yabawa husnah mijin da zai kaunaceta tsakaninshi da Allah
Aisha tace aikuwa dai addu'arshi taci
Dan professor Hakeem badaga nan ba wallahi
Bayan angama gyara amarya tafito tayi shar daita
Anty jumai ta kamota zuwa falonsu anan umma takara mata fada sosai tareda mata gargadi takula da ibada addua
Umma saidatayi kukan rabuwa da 'yatata guda daya
Abinda yasake ba husnah kuka kenan ma
Sosai sukayi kuka da kyar aka rabasu
Ya shamsu shiya rakata har mota
Kafin yamata rada a kunne
Saiga husnah tana murmushi da haka su hajiyar Ahmad suka shiga mota tadaga zuwa Kaduna
ankai amarya bangaren mummy hafsat aka ajiyeta sai dare za amikata sashenta
Karfe takwas na dare akafara mother's night sosai Mummy hafsat tayi barin kudi Dan bakaramin kudi daddyn Hakeem da Hakeem dinkansa suka kashe mata ba
Anci ansha ansa albarka
Washagri kuma walima aka yi namaza daban na mata daban
Inda aka gayyato manyan malamai nakasa dama kasashen ketare
Karfe Tara na dare aka mika husnah sashin uwargida
Da kyar ta danne zuciyarta duk da bata ga fuskar amaryarba saboda tana cikin lullubi
Mummy hafsat dakanta taraka husnah zuwa part din ta darakiyarsu anty kubra da Aisha matar Ahmad
Sai datasa husnah tayi addua sannan kuma tashiga dakinta da kafar dama
Har bedroom dinta akaita mummy tazaunar da ita bakin gado
Kafin nan tace wasu anty kubra sutayata hira
Mummy tamusu Sai dasafe tafita zuwa part din ta
*****
MEENAT zaune abi duniya yadameta
Wai yau ake auran babana dawata 'yar iskar
Gashi kwatata bata gane kan bash
Abinda yakemata duk ya daina shi bazai yi hira da ita
Sai takama tarasa meke shirin faruwa da itane
Mummy bash takasa gane kan yaronta tunda aka yi auran
Dan ita dama ba ason ranta yafasa auran husnah ba
Kawarta ce tabata shawarar tsayawa da addua Allah ya karkato mata da kan danta lafiya
Sadaka gidan marayu gajiyayyu bainda bata kai sadaka
Ga azumi datake
Cikin ikon Allah kuwa addua tasoma karbuwa
Dan jiya wuni bashir yayi waya da 'yan uwansa
Meenat takalli bashir tace uncle yashe zamu zamu koma gidane tunda har gashi mun wuce lokacin damuka tsara
Bash yace Sai lokacin danaga dama zata sake magana ya daga mata yace ya isa bana son surutu shasha kawai wuce kibani guri
Da gudu meenat tayi bedroom tafara kuka tace nashiga ukuna kar dai bash yadaina sona
Abinda zai burgeku daya ne Ahmad da ya shamsu sune suka rako Hakeem dakin amarya
Ya shamsu yayi addua kafin kuma yamike tsam ya kalli kubra madam muwuce ko
Ta tashi Aisha ganin Ahmad yatashi suka fito atare Hakeem yarakosu har gate
Husnah tana ganin fitansu ta tashi tasawa kofarta key a kofarta
Tayi bedroom dinta ma tasa key
Next page
Your comments is needed Fan's
Much love to your comments
Post a Comment for "AKWAI LOKACI COMPLETE HAUSA NOVEL"