Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

BAKAR TA'ADA BOOK 1 Complete Hausa Novel

*BAKAR TA'ADA BOOK 1 Complete Hausa Novel* *NA* *Surayya Dahiru Gwaram* *(Mrs M.I. Nashe)* *Marubuciyar Halin yau da Sabo da kaza*. •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *Rok'on addu'arku*! *A irin wannan ranar ta 09 ga wata 09 shekarar 2000. Ubangiji ya karbi ran mahaifiyata. Dan haka ina baran addu'arku dan nema mata raham da gafarar Allah daga bakunanku masu albarka dan Allah*. *Haka nan ina mika sak'on ta'aziya ta ga dukkan musulmai bisa babban rashin da muka yi na bijimin malaminmu kuma uba*. *Sheikh Abubakar Giro Argugun* *Allah ya jikan magabatanmu gabad'aya kwata.* *JAN KUNNE* *KADA A TA'BA MINI LABARIN NAN, KO KARANTA SHI A KOWACCE IRIN KAFA TA SADARWA BA TARE DA IZININA A RUBUCE BA*. *IDAN KUMA AKA YI KARAMBANIN TABAWA, ZA'A FUSKANCI TUHUMA DAGA LAUYANA BAR MUSTAPHA ISA GWARAM*. *GARGADI*. *WANNAN LABARIN KIRKIRARREN LABARI NE* *BA SHI DA ALAKA DA KO WANNE MAHALUKI*. *IDAN KIN CI KARO DA RAYUWAR DA TA YI KAMANCECENIYA DA TA KI, KO WANINKI, TO ARASHI NE*. *DOMIN MANUFAR MARUBUCI ISAR DA SAKO DA HANNUNKA MAI SANDA A CIKIN ZAMANTAKEWARMU*. *LITTAFAN SURAYYA BASA NUFIN HABAICI KO SHAGUBE GA RAYUWAR WANI KO WATA.* *NA GODE*. *GODIYA GA* *SADIK ABUBAKAR* *NA GODE MADALLAH*. *GAISUWAR GIRMA GA IYAYENA KUMA MARUBUTA* *HAJ SALIHA ABUBAKAR ABDULLAHI ZARIA*. *HAJ HAFSAT C SODANGI*. *HAJ MARYAM KABIR MASHI*. *HAJ HABIBA ABUBAKAR IMAM*. *YABO GA* *K'AWATA JAMILA JANAFTY* *IDAN DA WANDA NA GAMSU DA TULIN SOYAYYARTA GA RUBUTUNA DA CIGABANSA TO KE CE* *DUK WATA KALMA TA YI KA'DAN TA FAYYACE GIRMAN SHA'ANINKI A WAJENA* *INA FATAN UBANGIJI YA SHIGA AL'AMARIN KI, YA BAKI MIJI NA GARI*. *GAISUWAR SADA ZUMUNCI GA MARUBUTA* *Sumayayyah Takori* *Binta Umar Abbale* *Fadilah lamido*. *Hassana D'anlarbawa* *Zainab MAZAWAJE* *Lubna Sufyan* *Nazifa Nashe* *Ayusha Muhd* *Nana Diso*. *Kulsum Baffah*. *Safiyya Um Abdul* *Umm Asghar*. *Aisha Dansabo* *Aisha jos* *Zee Kumurya* *Da dukkan y'an kungiyarmu ta lafazi*. *FATAN ALHERI GA IYAYEN D'AKINA*. *HAJ HALIMA D'ALHA SHEHU* *HAJ RABI SANI* *HAJIYA HALIMATUS SA'ADIYA* *HAJIYA HADIZA FARI*. *HAJIYA ZAINAB ABDULWAHAB* *ALLAH YA HA'DA Y'AY'ENKU DA MUTANAN DA ZASU MUSU KARAMCI FIYE DA YADDA KUKE MINI, INA MATU'KAR GODE MUKU*. *TUKUICIN LABARIN SUKUTUM GA* *AISHA MUHD LAME* *ALLAH KA SO AISHA, KA FARANTA MATA, KA BIYA MATA BU'KATUN TA NA DUNIYA, KA BATA BABBAN RABO A LAHIRA*. *IDAN AKWAI WANDA JINI BAI HA'DAMU BA, NA KE DAKACEN INA MA JINI YA RATSA TSAKANINMU TO AISHA LAME CE MAI KAYAN Y'AN GAYU TA ORIFLAME* *SURAYYA DEE TA GODE, TA YABA MIKI, UBANGIJI YA TAYA NI GODE MIKI*. *Doka mi lamba ta 68 ta nuna cewa satar fasaha Babban laifine da yake dai-dai da satar Dukiya* *BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*. *1&2*. *SHIMFI'DA*. Sunana Asiya Sani Toro. Amma mafi yawa da Yabi ake kira na a dalilin mahaifiyata ta yi aikin Hajj da ni a cikinta. Mama ce kawai bata kira na da hakan sai Asiya saboda tana adawa da Yabi tunda ana nufin nima Hajiya ce. Gidanmu babban gida ne a garin na Toro domin ko yaro k'arami ka tambayi gidan Marina zai nuna maka. A dalilin asalin kakanmu da ya zo daga Kano ya fara kafa wannan sana'ar a garin. Fiye da shekaru saba'in kenan, amma har yau ba'a juya wa sana'ar baya ba, duk da dai an zamanantar da ita, ba kuma cikin gidan ake yin ta ba saboda warinta. Gidanmu babban gida ne k'warai da gaske. Idan na ce babban gida ina nufin mai d'auke da ahali daban daban masu yawa. Ko a k'ofar mahaifinmu Alh Sani (Baban Marina) da shi ne babba mata uku ne. Hajiya Habiba ita ce uwargidan mahaifinmu, mace mai k'ifadi da kutunguila. Duk wani rikicin da yake k'ofarmu, dama cikin gidan tana da sa hannu, ta tsani ta ga ko wanne irin cigaban d'an wata sai nata yaran kawai. Sannan komai cikin dabara da girma ta ke yinsa, ba kowa ne ya fahimci irin makircin da take k'ullawa ba. Sai mu da mu ke rayuwa da ita kullu yaumin. Ta kanka ne komai, ta yadda komai ta shimfi'da akan haka za'a tafi, sai dai ranar da ta samu bacin rana Baba ya bijire mata. Ya'yanta biyar. Yaya Musa, Yaya Hadiza, Yaya Salamatu, Yaya Indo sai autarta da ta haifa bayan ta shafe shekaru masu yawa Nazira, wacce ita ce sa'a ta ta girme ni da wata uku. Sai Mahaifiyata Hajiya Àsma'u wacce muke kira da Goggo. Ba dan tana mahaifiyata ba, amma mace ce mai sanyin hali da matsanancin ha'kuri. Idan na ce ha'kuri, ina nufin ha'kuri gangariya, irin ha'kurin nan da mai yinsa kan saka a alummar da suke kewaye da shi su halaka saboda hakkinsa da za suyi ta d'auka. Yaranta takwas cif. Yaya Salisu, Yaya Rabi'u, Yaya Ummi, Yaya Adnan, Yaya Ali, sai ni Yabi, duk dai bani nake bin Yaya Ali ba, akwai wani ya rasu ne, sai Anas da kuma autarmu Ikilima. Wannan yawan yara da mahaifiyata ta tara a d'akinta, kuma maza, ya sanya Mama ta tisa ta a gaba da masifa da tuggu, kusan kowa a gidan ya tsani mahaifiyarmu, ba kowa ne yake mua'amala da ita ba. Duk gidan bakinsu daya ne a kanta. Duk kuma Mama ce ta b'ata ta, take adawa da duk wanda zata ga ya mu'amalan ce ta Shi yasa hatta mu yaranta bamu da wani kwarjini har a wajen Dada kakarmu da ita ma tana cikin gidan bangarenta daban. Sai Hajiya Sahura muna k'iranta da Innah. Yaranta biyar Na farkon ma mun dan girme masa ka'dan Ubaid, Ubaida sai Abida, Hajara, Ismail da autarmu gaba'daya Saliha. Duk yadda Mama ta so wajen raba zumunta a tsakaninmu bai yi tasiri a tsanina da Nazira ba. Duk yadda bata kula ni, bata sakar mini fuska hakan bai hana ni yin dabdala a dakinta ba a dalilin Nazira. Bare ita kuma da dakin Goggonmu take kwana.. Sau dubu gara Inna akan Mama. Domin dai ba yadda za'a yi Inna ta ha'da wa Goggo sharri, ko ta tsokane ta da gangan, amma bata wani girmama ta a dalilin Mama ta dabarbarce ta, ta hana ta yin mu'amala da Goggo ta hanyar fa'da mata Goggo ce da gida, duk yaranta maza ne, idan Alhaji ya mutu duk su din y'an kallo ne. Da na fara mallakar hankalina sai nake tambayar kaina wai mene ne mahaifinmu ya mallaka da har ake fatan ya mutu? A da kam ya yi arziki k'warai da gaske, domin duk girman Gidanmu shi ya zaga ye ya gine shi, sannan mafi yawa na cikin zuri'arsu shine ya biya musu suka sauke farali. Amma tun shekarar da aka haife ni ya ha'du da y'an damfara suka yi masa sanadin karayar arziki, har yanzu da muke da shekaru goma sha biyar bai farfad'o ba. Yan'uwansa kuma kowa ya zuba masa ido ya zama abin tausayi. Amma a hakan Mama take fa'din Goggonmu ce zata ja komai. Wannan kenan. Sai k'ofar Alh Badamasi(Baban Tsakiya). Matansa biyu da yara sha biyu. Na uwargidan Hajiya guda bakwai . Babban d'anta Yaya Jabir, Zakiya, Jamila, Hauwa, Firdausi, Aisha sai k'aramarsu , Basira. Nan Firdausi ce warinmu. Sai amaryar Momi tana da yara biyar, Nasiru, Naziru, Sararu, Rumanatu da Kubrah. Anan ma Saratu ce sa'armu. Sai kofar k'arshe ta Alh Iliya (Baban kasuwa). Matarsa daya da yaransu shida. Amina, Aminu, Maijidda, Kaltume Abba andda Aliya. Maijidda ce sa'armu Sai wajen kakarmu Hajiya Binta! wadda Yaya Umminmu sunanta ta ci. Kowa Dada yake ce mata, wata irin tsohuwa mai wahalar sha'anin gaske. Tana daga zaune rikicin da take yi ba dan ka'dan bane, haka nan bata damu da ha'din kai a tsakanin ahalin gidan ba. Domin bayan su Babanmu akwai yan'uwansu mata biyu. Bangaren Dada ma hawa biyu ne, domin akwai wata k'ofar a can ciki bayan ka wuce k'ofarta ta farko, sannan ana iya fita waje ma ta wannan wajen Sai dai kofar a rufe take. Amma ba kowa ciki sai kayan ajiye ajiye da dangin kayan noma da tarkace. Babar Bulkachuwa(Hauwa) ita ta biyo Baban Tsakiya, tana aure a Bulkachuwa, mijinta Alh Yusufu babban d'an kasuwa ne a kasuwar kayan miya ta Muda lawal a Bauchi. Ita ce amarya amma sai a kanta ya samu haihuwa ta tsaya masa, uwargidan wabi take yi, ma'ana idan ta haihu sai su koma. Tijjani ne babba sai Aliyu, sai Nasir. Sai bayan haihuwar Nasir ne uwargidan ta haifi Maryam da kuma Hafsa. Daga nan sai Babah ta sake haifar Ihisan. Kenan yaranta hudu na uwargidan kuma biyu. Tijjani ya taso cikin wani irin gata a wajen mahaifinsa a dalilin tsawon lokacin da ya shafe babu haihuwa. Sai dai kash gatan ya zame masa d'an zani domin gaba'daya sai ya kangare, tun yana karaminsa ya ko yi fitina iri iri, shine kame kaji da awakin jama'a yana siyar wa, gaba'daya ya ki kar'bar tarbiyar da ake ba shi a sanadin duk abokansa lalattu ne. Duk yadda Baba ta Bulkachuwa da mahaifinsa suke son fige masa wannan dabi'ar abin ya ci tura. Akan dole suka raba shi da garin, suka dawo da shi wajen Mahaifinmu da Baban Tsakiya, tunda su din zafi ne da su ainun. A lokacin bai fi shekaru sha biyar ba. Sa'an Yaya Salisu ne, amma shiriritarsa ta mayar da shi cikin kannensa su Anwar, duk dai su din ma sun raina shi, sun ware shi ba wanda yake son a ganshi da Bulkachuwa saboda munanan TA'ADODIN sa. Yayin da mu muke k'ananu sosai Sai Baba Maryo ita ce autar Dada. A nan Toro take aure, yaranta biyar amma biyun farko na wajen Dada da ta haifa da mijinta na farko. Anwar da Nasiba. Yaya Jabir, Yaya Rabi'u, Yaya Abba da Yaya Anwar duk sa'annin juna ne tare suka taso, fikon junansu mafi girma watanni biyar ne. Kazalika muma y'anmatan tare muka taso. Duk da babu ha'din kai ko ka'dan a tsakanin iyayenmu mata, hakanan ni da Nazira an fi mayar da mu banza da wofi a dalilin mahaifinmu ba shi da shi, ga shi dai shine babba amma ya zama fanko, ya zama wofi dai dai da shawara ba a yi da shi. Duk yadda ba wani shakuwa a tsakaninmu irin na zumunci, in dai fita ne, to tare ake tafiya zuwa makarantar boko ko Islamiya. Haka za'a ganmu zaratan y'anmatan reras da mu. Kusan ba'a ta'ba yin y'anmata da muke sa'anni da yawa a gidanmu irin akan mu ba. Domin mun doshi bakwai Ni Yabi, Nazira, Basira, Firdausi, Maijidda, saratu, Nasiba. Dukkanmu kowa turbarakallah babu makusa, tunda asalin Kakarmu Dada Bafulatanar Lame ce asalin fulanin Mali. To kusan dukkanmu mun samu tsayi da gashinta. Duk da ni din bani da tsayi, yar shafal ce, matsakaicin kyau ne da ni amma fara ce sol, sannan kuguna a dan bude yake ka'dan, sai dai kirjina kam ko na kai shekarun budurci sosai baza su yi wani girma ba. Kowanne irin sutura na saka sai ta yi mini kyau. Duk da kayan nawa mafi yawansu masu sau'kin farashi ne a dalilin mahaifinmu baya samun sukunin yi mana sutura. Abinci ma da wahalar gaske muke cinsa, duk da ga yan'uwansa nan suna cin duk abin da suke so. Amma ba'a yi mana kara ni da Nazira idan zasu yiwa y'ay'ensu sutura su ha'da da mu. Ko da yake Nazira ta fini sutura a dalilin Mama tana sanya yayyenmu na d'aki suna yi mata. Yaya Salamatu tana d'an yin kara tana bada kuncen har da ni, da yake babu laifi mijinta yana da rufin asiri, amma Mama bata bari a bani, sai dai da Yayar ta fahimci hakan sai take bani a b'oye tana fa'din ba sai na fa'da ba. Ni kuma bana iya yin shiru sai na nuna wa mahaifiyarrmu, ita kuma sai tasan yadda ta yi ta yi mata godiya tana kuma jan hankalina na kula da ita. Sosai nake ganin kirkin Yaya Salamatu duk da dai sai ta zab'e mafi kyau ta bawa Nazira ni kuma ta bani saffa saffa, amma dai ta k'ok'arta a yadda mutanan yau suka dauki y'an uban ci. Yayata da muke d'aki d'aya ita ma tana cikin matsanancin babu, domin duk talaucin gidanmu a hakan Goggo take tara mata k'anzo dan ta ci ita da yaranta. Wani irin bahagon miji take aure, bai san hakkin komai ba sai hakkin auratayya tunda kusan duk shekara biyu suke haihuwa ita da uwargidanta tamkar masu gasa. Dan ma yanzu uwargidan ta daina yi. Hatsin da za'a yi tuwon dare kawai zai bayar, dai-dai da cefanen miya mace ce zata yi, da safe a yi dumame a ci yadda ya samu, ba dan an koshi ko dan da'di ba. Da rana kuwa ko wacce ita zata ciyar da kanta da y'ay'anta. Ba maganar sabulun wanki bare a je ga na wanka. Yaya Ummi kyakkawar mace amma wahalar da miji ya sakar mata da muguntar kishiya ta saka duk ta fita a hayyacinta. Domin ita ce mai k'ananun yara, ita d'ayar al'amura sun fara saisaita mata, tunda manyan ya'yanta sun kawo k'arfi, amma komai zasu kawo a boye ne, ita kawai zata amfana. Duk cikin yaran gidanmu tafi kowa shan wahala a gidan aure. Shi yasa take a ware, sai idan Yaya Rabi'u ya d'an figi wani abu ya kai mata a dalilin suma suna fama da rik'ewa Babanmu gidanmu. Rayuwar ta yi mana tsananin gaske, mahaifiyarmu ha'kuri take yi kan ha'kuri. Kuma wani abin mamaki da Mijin Yaya Ummi mai tarin dukiya ne amma fa baya iya ci, sai dai ya yi ta lissafin kadarorin da ya tara. Manyan yaransa sai fatan ya kauce su ci abin da bai bari sun ci ba suke. Gaba'daya tausayin Yaya Ummi nake ji, abubuwa sun yi mata yawa, ga tashin hankalin gidanta, ga azabar yan'ubancin da su Yaya Indo suke yi mata. Sun wareta, Yaya Salamatu ce mai sassauci kawai. Duk sadda ka je gidanta haka zaka ganta tamkar mahaukaciya. Wankau take yi, kamar me? yini take tana wanki. A hakan take samu ta wanke kayanta da na yaranta, ta kuma samu ku'din da zasu ci abinci da rana. Duk da dai bashi yafi yawa, sai ta yi wanki sau nawa ba a biya ba. Na kan yi mamakin yadda mutanen yau suka shagala da fa'din Annabi (S.A.W.) na cewa "Mafi adalcin mutum shine Wanda yake biyan hakkin Wanda ya yi masa aikin wahala kafin guminsa ya bushe. Amma a wannan zamanin sai mutum mai wadata ya bawa miskini aikin wahala amma biyansa hakkin wai sai ya zama bashi, abin kaicon ma idan an yi masa aikar a bayar da ku'din nan, sai ya zama laifi. Mace ma'aikaciya sai ta bari ku'din mai wanki, ko markade, ko kuma mai dakan hannu ya taru a kanta. Ba tare da yarjejeniyar sai k'arshen wata zata biya ba. Anya kuwa muna son ganin dai-dai jama'a? Wannan wahalar data taru ta yi mana k'awanya ya sanya na mayar kitsona na ku'di. Domin tun daga alhamis idan na fara k'itso har lahadi, amma ba wanda zai cire ko da sisi ya bani a cikin matan gidanmu da duk kusan sati nake yi musu kitson su da y'ay'ansu. Kuma na sani hakan baya hana su karbin ku'din kitson a wajen mazajensu, ko iyayensu. Bisa shawarar Nazira na daina yiwa kowa kitso sai ta biya. Iya y'an k'ofarmu kawai nake yiwa kitso kyauta. Mama kuwa bata yarda ta ba ni kanta dama. Amma ina yiwa Inna da Gwaggonmu. Da kuma yan'uwana na k'ofarmu. Ai wannan bijirewar da na yi akan sai an bani ku'din kitso ya sake jefa tsana a tsakaninmu, domin duk inda Mama ta zauna sai ta ce "Uwarta ce ta kitsa mata, me za'a yi da irin wannan haihuwar a ce ba zaka bari aci arzikinka ba?" Iyayenmu maza da suka san suna biya basu dauki al'amarin a wani abu ba. Domin suna k'yashin a ce mu d'in muna da mamorar da zamu yi musu alfarma. Domin fa'di suke yi "Idan ku'di ne ku bata kudinta daidai da yadda na waje zasu biya ta, ko kuma daidai da wanda idan kun je wajen bare zaku bayar. Ita ce bata gaji arziki ba". Yayin da muka k'udire a ranmu ni da Nazira ba wanda zai sa na yiwa yaransa ko matarsa kitso akan dole domin suma basu taimake mu ba, dai-dai da ku'din islamiya da bai taka kara ya karya ba, basu ta'ba ha'da mu da y'ay'ansu sun biya ba. An sha koro mu da sauran k'annenmu, akan ku'din islamiya. Yayin da sauran yaransu basu da wannan matsalar. Idan zamu yi wata a zaune, Mahaifinmu ko iyayenmu mata basu samu sukunin biya ba, ba wanda zai dube mu. Dada kuma ba zata ce wane biya wa yaran nan ba. Ita kanta ta manta irin da'din da Babanmu ya jiyar da ita. A yanzu kam ta mayar da shi da dukkan ahalinsa tamkar wasu barori a cikin ahalinta. Tarin Baban kasuwa ya fi maganar Babanmu sau dubu. Tunda shine yafi kowa rufin asiri, sai Baban tsakiya. A batun soyayya kuwa kowa shaida ne Dada bata ha'da lamarin Yaya Anwar, da Tijjani da kuma Nasiba da kowa. Sun fi kowa lasisi a gidan, gasu dai ba y'an gidan ba ne tunda iyayensu mata ta haifa. Amma sun fimu gata da gadara a gidan. Yanzun nan Dada zata hau ihu matu'kar aka ta'ba guda a cikinsu. Sai yaran Baban kasuwa, sai na Baban tsakiya. Hakan dai hawa hawa abin yake. Canjin da nake samu a kitso ba k'aramin taimakona yake yi ba. Haka Gwaggo tana yin kokon safe, muna samu mu sha a ciki, har watarana a aikawa Yaya Ummi. Asusu na siya nake tura dan wani abu, domin ina matu'kar jin haushin yadda mu da gwaggonmu muke koma baya a gidan. Yaranta maza an d'ora musu nauyi mai yawa. Yaya Salisu ne kawai ya yi aure, shima ba wai wadatar ne da shi ba, aikin gini yake yi duk da ya yi karatu amma aiki ya yi wuyar samuwa tunda babu hanya. Su Yaya Rabi'u kuwa koami na gidan sune, Mama fa'di take ai sune maza, sune zasu taimaki ubansu, ga karatunsu su suke daukar nauyin kansu. Dan haka Gwaggonmu bata samun komai, amma idan an nutsu za'a fahimci kowa a kofarmu yana cin arzikin yaranta. Duk yan dakinmu ni ce mai tsiwa, ban dauko sanyin halin uwarmu ba. A tsaye nake kan kafafuna cak, haka zuciyata bata daukar raini. Sai dai kuma bani da kullaci, ina da saurin afuwa. A duk sadda na kalli Gwaggonmu da Yaya Ummi sai na tsinci kaina da yiwa kaina da Iklima addu'a samun miji na gari mai wadata, ko muma ma shiga sahun masu mutunci. Tun kafin hakan kuma sai Ubangiji ya hore mini iya yarfa kitso. Duk wata matashiya yar kwalisa a yankin nan ni ce mai yi mata kitso. A hankali sai na fara gwada lalle. Nan da nan sai Ubangiji ya sake haska mini. Layi ake yi mini na kunshi da kitso duk satin duniya. Muka fara dan warware wa, domin muna samun yan kuda'den yin bu'katar yau da kullum. Hatta Yaya Ummi ta d'an samu sau'kin matsatsacin da take ciki. Domin duk sati sai na cire mata wani abu. Da ku'din asusuna ya yi auki na fasa na siya mana kayan kwalliya masu sau'kin ku'di ni da Ikilima da Nazira, har ma da Ubaidan Innah. Sai kuma na sake siyan wani na k'udire niyyar dinki zan yi mana idan kudi ya taru. Tsawon dauki lokaci ina zubi, kafin na samu na yi mana y'an suturu ni da Iki. Ai Mama tana ankara da y'ar nutsuwar da muka fara samun kanmu a ciki, sai ta tayar da ballin sai na bar kitso, domin gashi yana yawa a gidan, ba dama ta zubo abinci, zata yi ta ganin gashi. Ko ina gashi ne, ta gaji da wannan k'azantar. A wannan karon Babanmu ya yi jarumtar cewar ba zai hana ni yin sana'a ba, tunda shi da kansa ya sani ba k'aramin rufa masa asiri sana'ar take yi ba. Kusan kullum sai na ba shi naira dari hud'u. Maganar maganina kuwa idan ba ni da lafiya, na dauke wa kowa. Dan haka sai muka fara saje wa da su Maijida. Tunda muma yanzu muna samun yan suturu babu laifi, duk da bai kai nasu daraja ba. Idan akwai abin da ya yiwa Mama tarnaki rashin kintsuwar Yaya Musa ne. Gashi dai shi ne babba, amma gaba'daya ya lalace, ya zama d'an iska, hakan kuma yak'i ya zame mata izna, a kullum cikin aibata yaran da ba nata ba take. Ta kuma gasgata hannu aka sawa d'anta, da kuma bakin mahassada. Ta kasa fahimtar rayuwa har yanzu. Tsabar kyashinta ta hana ya'yanta mata su tallafawa Babanmu da d'an abin da zasu iya . Kullum fa'di take ai hidima ta y'ay'a maza ce. Dan haka komai yaranta mata zasu kawo gidan to nata ne, sai ko idan dafaffe ne sai ta samma wadanda take so, wadanda bata so kuwa ko ta yi babu. Sai nake mamakin idan tana habaicin ku'din kitson da nake kar'ba, wai Gwaggo ta kasa bari a mori haihuwarta, ko ita wa ta bari ya mori tata haihuwar? Ko Babanmu da ya yi mata hidimar yaran ba dai tasa su kawo masa wani abu na tallafin gida ba tunda yana da k'ananun yara. Idan ma sun yi hankalin kawo wa to fa ita ce a hakku a kan kayan, ta dinga gadara kenan duk ba wasu kaya masu yawa ba ne, tunda dai ba wai ku'din ne da su ba, rufin asiri ne kawai. Sai nake mamakin wai mene ne manufarta ne? Da na kasa gane wa sai na ha'kura, amma hakan ya ja hankalina har nake sha'awar yin bincike da nazari akan gidan yawa mai dauke da mabanbanta iyalai. *GIDANMU ne kawai kwamacala ta dabaibaye shi?* *A GIDANMU ne kawai ake yin kasafi irin na kashin dankali ma'ana na sama ya danne na kasa?* *A GIDANMU ne kawai ake mayar da babba k'arami saboda ba shi da wadata ko kuwa?* *A GIDANMU ne kawai ake ta'ba yan ubanci ko kuwa?* *Ba k'aramin caji kwakwalwata take yi ba dan neman sahihohin amsoshi wadannan tambayoyin*. *Ayi bitar da nutsuwa domin wannan karon gidan yawa zamu kutsa sosai* VIP 1K. REGULAR 500. 2384876855 SURAYYA IBRAHIM ZENITH BANK. *ASSALAMU ALAIKUM* *Masoyan rubutun Surayya Dee na gaishe ku, na kuma yaba muku* *Dafatan zaku yi hakuri, ku bi labarin sannu a hankali, har ku fahimci sakon da nake nufin isar wa.* *Ba zan ce muku komai ba. Abu d'aya nake da tabbaci ba zaku yi nadamar bibiyarsa ba.* *Kawai fatana kada ku kosa da yanayin rubutuna.* *Allah ya taimakemu, Allah ya zaunar mu lafiya da y'anuwanmu da abokan zamanmu*. *Allah ya bamu lafiya, ya bamu hakuri da k'addarar da muke fuskanta a rayuwar nan*.   *Surayya Dee* ✍️. *BAK'AR TA'ADA* *NA* *SURAYYA DAHIRU GWARAM* *MARUBUCIYAR HALIN YAU DA SABO DA KAZA* •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *GODIYA* *INA MATUKAR GODIYA BISA ADDU'AR DA KUKA YI WA MAMA*! *ALLAH YA KARBA, YA BADA LADA*. *HAKA NAN INA NEMAN UZZIRINKU BISA RASHIN AMSAWA. DOMIN NA KARBI SAKON MUTANE SAMA DA DARI BIYAR, TUN INA AMSAWA HAR AL'AMARIN YA GAGARI KUNDILA*. *DUK WACCE BAN AMSA BA, INA AMFANI DA WANNAN SHAFIN WAJEN GODIYA TARE DA YABAWA A GAREKU GABADAYA* *ALLAH YA JIK'AN DUKKAN MAGABATANMU*. *KUNSAN DAI YADDA AISHA LAME MAKEUP ARTIST DIN GUDUYO, TA KWARE WAJEN SANIN HAKIKANIN MAN DA ZAI DACE DA KOWACCE FATA, WALA DRY KO OILY*. *BABBAN ABIN BIRGE WA DA KAYANTA FARASHI MAI SAUKI NE DA YA ZARTA NA SAURA SALAMA* *HANZARTA KI TUNTUBE TA DAN KI GA JERIN KAYAYYAKIN ORIFLAME KALA DABAN DABAN* *SANNAN TANA DA HADADDEN GANYEN SHAYIN DA AKA YI SHI DA GANYAYYAKI MASU SAISAITA JINI DA KITSE A JIKIN DAN ADAM.* *LAME TEA YAFI SHAYI MAE MADARA*. *IDAN KUWA KIKA CI LAME POPCORN INA TABBATAR MIKI KIN YI ADABO DA SAKE CIN WANI GUGGURU MATUKAR BA LAME POPCORN BA NE*. *07036662633*. *3&4* K'aramar hukumar Toro tana cikin k'ananun hukumomin jahar Bauchi. Duk wani mai nazari yasan yadda Ubangiji ya wadata Toro da girman k'asa. Ita ce k'aramar hukuma mafi girma a dukkan fa'din tarayyar Nigeria dama Africa ta yamma gaba'daya. Garin Toro an kasa shi zuwa Gundumomi uku. Gundumar Toro, gundumar Jama'a da gundumar Lame. Sannan akwai kabilu daban daban bayan Hausawa da Fulani. A karkashin jahar Bauchi ta ke amma tafi makwbataka da jihar Filato. Shi yasa garin kewaye yake da ni'imomin kayan itatuwa da rashin zafin rana sosai. Ba dan ina y'ar garin ba, Ubangiji ya dabaibaye garin Toro da tarin faloli Alhamdulillah. Dare ne amma ba ainun ba, mafi yawa mun ha'du a kofar Kakarmu Dada ana ta hira da tatsuniya. Kannenmu kuma sai wasan d'an dunmi suke yi. Dukkanmu y'anmata mu bakwai da muke kai d'aya muna zaune akan tabarma, idan aka dauke shalele Nasiba da take kishingi'de a jikin Dada. Sannu a hankali Dada take taunar goron bakinta tana mulmulawa. Kyakkawar dattijuwa mai kyakkawan jiki. Asalin Bafulatanar Lame ce, kowa kuma yasan asalin mutanan wannan garin fulanin Mali ne da kiwo ya saka suka tsallako Nigeria suka yi sansani a yankin na Lame. Wani ikon Allah mafi yawa na ahalinta sun samu kyawun halittar fulanin Lame. Haka muke y'an gidanmu son kowa k'in wanda ya rasa. Wani irin kallo take mana na kurillah. Ta kasa ha'kuri ta ce "Na fa'da muku dukkanku ku zauna cikin shirin ko ta kwana. Domin kuwa ba zaku fi haka gandare wa a gabanmu ba. Dukkanku abubuwa sun cika muku k'irji. Ko wacce a cikin ku wanki take yi a gabanmu, ina kallon zamani ni Binta! Muna cikin alhini. Allah yasa intingifarin da muke nacin yi mun samu rabauta ana karban sallarmu". Dariya ta kama mafi yawanmu. Ni da nake da kaud'i na ce "Dada Ashe ba'a karban sallarku ne?" Ta rausayar da kai gwanin tausayi ta ce "Ai matu'kar kana da yarinyar da ka yi saken da ta fa'di a gabanka, to kuwa babu makawa sallarka bata isa gaban zati, daga bakin k'ofa ake dakatar da ita!" Nasiba ta ce "Allah ya kawo mafita. Yanzu biya mana karatun na yau". Nan da nan ta furzar da goron bakinta dan girmama karatun da zata d'ora mana. Ta tsume ta ce "Mu karanto na jiya". Muka ha'da baki wurin rera karatu cikin sigar wake muka ce "Idan attishawa ta sauko mana, idan wani bawa a kusa da mu ya ce mana "Rai ya hadu da Gafarar Allah!" Sai mai attishawa ya ce "Ya-hadi kumalle. Idan kuwa zamu ci adda'ami. Zamu fara da ambaton Allah. Idan koshi ya zo mana sai mu ce "Sawaba ta sauka akan me nemo wa da mai dafa wa". Dada ta murmusa tabbacin ta gamsu mun ri'ke karatun nata da kyau. Ta ce "Madallah!". Cikin alfaharin muna da fikirar fahimtar karatun da take yi mana. Ta muskuta ta ce "yau karatun yiwa kai rigakafi daga shaidanu da makarai zan dora muku". Muka ha'da baki wajen fa'din "Mun gode Dadarmu, Allah ya kara miki nasibi. Annabi yasan da ke". Ta numfasa ta ce "Ameen, a kuma tsananta yi mini rokon dacewa da shiga cikin masoyan SHEHU". Na kasa jure wa na ce "Ashe Dada ba zaki bar zancen Shehu ba? Kowa ya bar Allah da ma'aiki ai ya bar hanyar tsira." Nan da Nan ta fusata ta ce "kaico da Yabi! Yabi ba zaki tsira ba, waya yake inkari da jikan Manzo? Tabbas sai gafalalle". Na ci je na sake ce wa, Annabi dai aka ce mu ri'ke ba waninsa ba Dada, iyalan gidansa suna da girma da hakkin mu so su mu kare mutuncinsu. Amma ba'a ce a kai su wani bigire da zai iya zama halaka ba. Da kansa ya ce "Zan bar muku kura'ani da sunnata wato (Hadisansa) idan kuka bisu kun tsira. Amma ku kun shure komai, kun dauko shehu kuna neman mayar da shi abin bauta?". Ai kuwa ta sake harzuka ta ce "Wahalar rayuwa akan ki Yabi! Mai gadon taurin rai da kafiya, kaicon ki, kaicon ki! Da yi mini izgilanci Asiya". Jikina ya sabe da rawa a dalilin ba irin jan kunnena da Gwaggo bata yi mini ba, akan kada na sake na janyo abin da Dada zata dinga yi mini mugun fata. Ga shi ban ji ba, na yi sanadin da take fatan na dauwama cikin wahalar rayuwa. Kafin na ce komai sai ga Tijjani wanda mafi yawa an fi k'iransa da sunan garinsu Bulkachuwa. Wani irin zabgegen saurayi. Dogon gaske har d'an rankwafa wa ya yi ka'dan. Fari ne tas, irin fulanin Bulkachuwa, a murde yake, shi ba siriri ba, kuma ko ka'dan baya cikin masu kiba. Ga dogon hanci da ya k'awata doguwar fuskarsa. Baya ga hakan manyan idanuwansa ka'dai sun isa abin burge wa. Ban ta'ba ganin namiji mai jajayen lebe ba sai Tijjani kyakkawan gaske. Wani irin mutum mai saurin fishi, da k'arfin zuciya. Amma mai saurin saukowa da mantuwa. Illarsa d'aya manemin mata ne, a yadda a ke fa'da. Na shaida kuma duk wata budurwa ballagaza a Toro to kuwa budurwarsa ce ko kuma suna d'asa wa, shiyasa kowa yake jan kunnen y'arsa a kansa, barin ma ni, kullum ne sai Gwaggo ta ce kada na sake na bashi fuskar da zamu dinga doguwar magana. Gaba'daya dabi'unsa na tantiran yan-iska ne, sannan k'azami ne, baya damuwa da yin wanki sai kayansa sun k'are. A hakan kuma shashan y'anmata suke sonsa, ko da yake baya yarda ya fita da dattin sosai, yana wanke wa ya jira su bushe, guga ce sai ya samu ku'di, sai ya bayar da kayan ma a wanko a gogo masa, amma da wahalar gaske ya yi guga da kansa. Duk yadda Dada take kulafacinsa, matu'kar ya shigo muna nan sai sun haura da shi, domin yafi kowa takalarmu da magana, yana yi yana lumshe ido ta yadda zai sure zuciyoyinmu. A hakan ya yi nasarar yin wuf da zuciyar Nasiba. Idan Dada ta ga yana sakin maganganu ko lumshe ido a gabanmu ta dinga bagarar da shi, ko ta tsiri aiken sa, ko kuma ta ce mu je ta sallame mu, duk yadda take sonsa to bata son doguwar magana a tsakaninmu, kazalika kuma bata son a k'i gaishe shi. Burgar da yake yiwa mata ya sanya har yanzu bai bar dauke dauke ba, komai ya gani zai dauka ya siyar ya kashe wa budurwa ku'di. Amma iya kayan Dada yake dauka. A duk sadda take yi masa fa'da kuma zai waske ya ce bashi ba ne, ko kuma sharri ta yi masa, haka kuma sai ya d'auke mata wuta, har sai ta nemo shi ta bashi ha'kuri. Bayan soyayyar da take yi masa, yana sake samun alfarma a wajenta saboda sunan SHEHU ne da shi. Kullum bakin ta akan ya nutsu ne, ya bar shiririta ya kawo matar aure, tunda ga Yaya Salisu nan da yake sa'an sa tuni ya yi aurensa har matar ta haihu, amma shi ko maganar aure baya yi saboda sharholiya da mutuwar zuciya. Duk da k'arancin shekaruna ina tambayar kaina ko waye zai iya d'aukar y'arsa ya bawa Bulkachuwa aurenta? Tabbas sai idan yarinyar ta kasance shasha ce irinsa. Na tabbatar mahaifiyar Nasiba ba zata ta'ba bari a bashi ita ba, domin kuwa kowa nasa yake so, bare idan maganar gaskiya za'a yi bai cancanci a bashi ba, domin bashi da sana'a, gashi manemin mata, shiyasa kowa yake masa kallon shasha. A duk sadda Dada take yi masa fa'dan shigar da yake yi ta gajerun wanduna yana yawo a gari babu kunya, ko tara suma ya gegareta daga gefe, ko kuma wani zubin ya sauya launinta bayan ya mayar da ita cibiri cibiri. "Akan kunnena na sha jin tana ce wa "Saboda bamu da mutunci a idonka shiyasa kake iya zuwa gabana a hakan ko kuma gaban kawunanka". Ba jin nauyi yake ce wa "Tunda nake yin sallah a hakan, ai kin ga bai zama aibu dan kun gan ni a hakan ba. Domin Ubangijina ma a hakan yake gani na, kin takura mini fa Tsohuwa" Nan da nan ta zabura ta ce "Imaninika ai a makogaro yake shi yasa kake hakan, amma da za'a jarrabe ka da son wata yarinyar ba zaka yarda ka je mata a hakan ba. Alfarmar Shehu sai ka samu wacce sonta zai hanaka yin wannan shakiyancin. Tunda ka ki daina wa saboda Allah da Ma'aikinsa." Dariyar iyashege yake yi ya ce "Ni da nake da y'anmata kamar jamfa a Jos suna bina dan na so su, shine har son wata zai canja ni? Lah! Ba dai Bulkachuwa ba". Da wani kuma a Cikinmu ko a cikin samarin gidan matu'kar ba Yaya Anwar ba ne zai saka musu baki, a take Dada zata nuna wa mutum shine bare a tsakaninsu. Tana kuma sake kambaba shi da kawar masa da kai saboda alfarmar mai sunansa ne, domin ko ta yi masa sababi, sai ta yi ta tuba tana kamun kafa da mai asalin sunan akan a saka mata jikanta cikin shirayayyu. Hatta shi kansa dariya take bashi akan yadda take tuba idan ta saki harshe a kansa. Amma wani ikon Allah jarumi ne na gaske. Idan na ce jarumi ina nufin zai tsaya ya fafata da kowa akan hakkinsa, matu'kar kuma ya sanya kansa zai yi abu, to duk tsananin wahalar abin sai ya ga abin da ya turewa buzu nad'i. Baya ga hakan kuma tausayi ne da shi, duk zafinsa inda zai ga kana kuka to zaka ga ya bar yi maka tijara. Sai dai kallon marowa ci nake yi masa na gaske, ni dai ban ta'ba ganin ya yi kyauta ba. Ko garinsu ya je ya dawo, duk abin da zai samo ba dai ya kawo gidanmu ba. Amma kullum a cikin karbe wa jama'a nasu yake, mussaman Dada da ko ta hana shi a k'arshe take kasa juriyar ganinsa cikin rashin sukuni, sai kawai ta bashi. Mazan gidan kuwa basa bashi duk irin yadda zai karyar da kai yana fa'din bashi da lafiya, tunda suka gane matu'kar ku'di ya shiga hannunsa y'anmata banza yake kashe wa, sai kowa ya kulle bakin aljihunsa dama kuma masu k'aramar niyya ne. Sai dai gara shi ma suna bashi, amma da a ce wani ne cikin y'an k'ofarmu baza su bayar ba, daman kuma bamu isa mu ce a bamu ba. Haziki ne na sosai, kwarai da gaske yake ja, amma lalacewar da ya yi ya sanya da k'yar ya iya kammala Diploma a kwalejin Tatari Ali data ke cikin Bauchi. Ya riga su Yaya Salisu samun gurbin karatu a jami'ar amma yak'i mayar da hankalinsa akan karatun har sai da aka kore shi. Hankalin mahaifinsa ya yi tashin gauron zabi, domin zaryar da ya dinga yi tsakanin Bulkachuwa zuwa Toro ba ka'dan ba ce. Haka ya sake samo masa yin diploma akan shaanin tsaro da tafiyar da gwamnati wanda da k'yar ya kammala dan ma shekaru biyu ne. A hakan kuma sakamakon ya yi kyau, domin ya wuce fallasa. Duk da hakan Babansu bai bar shi ba, sai da ya sake samo masa gurbin karatun digiri a jamiar jahar Bauchi ta garin Itas-gad'au. Inda zai karanci ilimin halayyar dan Adam. Wannan kam da taimkon Ubangiji ya kammala domin ba ya zuwa sai an kusa fara jarrabawa, sannan bai fasa al'amari da y'an mata ba. Shekaru biyu da rasuwar mahaifinsa kenan. A kuma wannan shekarar ya tafi bautar k'asa, da shekara ta dawo ya kammala. Yanzu zaman kashe wando kawai yake yi. Sai dai yana yar buga bugarsa domin kusan kullum sai ya je Bauchi. Haka ya dinga satar jiki yana siyar da kadarorin da ya mallaka. Abin kaico kuma ba komai ya yi da kudin ba sai sharholiya da burga a mata. Wani k'aton fili a Bauchi kawai ya tsira da shi, shima dan an zuba masa matakan tsaro ne. Yau da wata sana'a yake da ku'din ko kuma wani gini yake fa'da'da wa da an samu sau'kin bacin ran da ake ciki. Ya zauna kusa da Nazira da take kusa da karshen tabarmar. Murya ba amo ya ce "Madallah da Dada da y'anmatantanta". Duk suka hau rige rigen gaishe shi Amma ban da ni. Ya amsa hankalinsa na kaina. Ya kasa ha'kuri ya ce "Asiya Toro how far?". Na yi banza da shi. Domin dai na tsani yadda yake gatsa ainihin sunana, dan kuturun wula'kanci har sai ya ha'da da Toro. Kusan kowa Yaya Bulkachuwa yake ce masa, ni da bama shiri bana ce masa Yaya Bulkachuwa. Amma sai nake mutuntunta shi wajen kiransa da Yaya Tijjani amma bai yaba ba, bare ya gode. Yabin da zai ce ne yake ganin asara saboda an cika zuciyarsa da k'yashi. Shi yasa nima na janye yayan tuntuni nake gatsa Tijjani gatsal wanda na lura shi ko oho. Ina nan, ina kallon wadanda basa ce mini Yabi, duk ranar da Ubangiji ya sanya na je Saudi akan girma da hankalina ko tsarabar abin da ba'a so ba zan basu ba. Tijjani na cikin sahun farko. Yaya Ummi ce mutumiyarsa, baya zuwa gidan kowa amma yana zuwa gidanta, har idan da ku'di a tare da shi ya yi wa ya'yanta alheri. Sosai suke d'asawa, mutimiyarsa ce ta sosai. Dada ta fusata ta ce "Mugun nufi ya k'are miki Yabi! Ko wacce ta gaishe da dan-uwanku amma ban da ke, bai yi fishin wula'kanta shi da kika yi ba, ya sake bu'de baki ya yi miki magana amma kina ji sarai kin k'yale shi, saboda ke din kina gaji nunkufurci da ba'kin hali ko?" Raina ya baci domin a kullum kalaman Dada a kaina kenan, bansan me Goggo ta tsare mata da a kullum sai ta jingina mata munafurci da ba'kin hali ba, ko da yake na taba jin labarin cewar tun haihuwar Yaya Ummi da dangin Goggo suka zo suna daga garinsu na Kangire cikin k'aramar hukumar Birin Kudu suka fuskanci wulakanci daga wajen Mama. Shikenan duk haihuwar da take yi basu sake yin gayya sun zo ba. Sai dai a samu mutum biyu su zo su ganta washagari su juya sassafe. Wannan matakin da suka dauka shine ya zama laifin da yak'i wuce wa a wajen Dada da take ta musguna mata da gorin ba y'ar babbar haula ba ce, sannan yan'uwanta masu k'ullaci ne, duk kuma cikin matan gidan mahaifiyarmu ce kawai bata da kowa a garin Toro shi yasa ma wani abin ake yi mata da gan gan. Duk da ba jin dadin zaman take yi ba, ta jure dukkan kalubale dan kawai ta zauna da mu yaranta, amma bata tsira ba tunda Babanmu ma haka siddan sai ya dauke mata wuta na tsawon lokaci mai yawa. Mama kuwa bata fasa yi mata yankan baya a duk inda ta zauna ko ta samu damar yin hakan ba. Ko yaushe Gwaggo a cikin mutuntunta Dada take hatta wankin kayanta har yau bata daina yi mata ba, amma babu gwaninta bare yabawa. Nan da nan na tunzura na ce "Da yake shi kina jin tsoron kada ya keta ki shiyasa kike fa'din hakan. Amma ni kin bu'de baki kina niyyar tozarta ni. Tunda ban gaishe shi ba, ya yi mini magana ban amsa ba, ba sai ya rabu da ni ba? Bana son harka da shi ne, a duniya na tsani sunan da yake kirana da shi. Sannan idan zai mini magana sai ya lanjare murya, kuma kinsan dai ba sosai nake ji ba, bare na ji shi da kyau". K'wafa ta yi tare da cewa "Kowa ya yi na gari ai dan kansa Yabi". Basira ta ce "Yi ha'kuri Dada d'ora mana karatun kawai". Ta rausayar da kai gwanin tausayi ta ce "Kayya Basira zuciyata ta jagula ainun karatun nan sai gobe kuma". Firdausi ta ce "Yaya Bulkachuwa saka baki Dada ta d'ora mana karatun, bata ha'kuri mana". Ya kalle ta ya ce "Dadarmu share kawai, nima na ha'kura ai. Kinsan hankalin Asiyan Toro a k'auri yake". Na sake hauro wa na ce "Tijjani ka bari, ka ga dai bana shiga harkarka akan me zaka nemi takure ni ne? Gaskiya bana son haka". Dada ta sake yin k'wafa tare da cewa "Yabi kin janyo muku, domin na lura tashen balaga kike ji, zan kuwa yi maganinki." Kafin wani ya yi magana sai ga Ikilima k'anwata da a yanzu take shekaru tara. Ta shigo cikin nutsuwa ta kalle ni ta ce "Adda Yabi ki zo". Da azama na mike domin nasan Yaya Jabir ne. Saurayin da yake gigita zuciyata da ruhina. Ban ce komai ba, na mike ina cewa "Sai da safenku". Dada ta bimu da ido tana cewa "Jabiru ne ko kuwa wani ne?" Ban kula ba, ba kuma wacce ta tanka. Domin dai na fi su farin jinin mane ma duk kuwa da ba finsu kyau na yi ba, asalima wasu sun fini kyau, sun kuma fini cikar mace. A bakin kofar Shashenmu ya jingina. Matashin saurayi mai cike da nutsuwa da kamala. Wankan tarwada ne, siriri mai matsakaicin tsayi, mai sanyi a halayya da kuma dabi'a. Bashi da kwaramniya tun tashinmu, mai hakuri ne na gaske, da wahalar gaske ka ga fa'dan Yaya Jabir. Sosai muke shiri da shi, duk kuwa da ni din mai tsiwa ce, mai kuma hayaniya ce. Amma jininmu ya ha'du sosai. Kusan tun soyayyar kuruciya ce ta rikide ta zama ta gaske. Dalibi ne a jami'ar tarayya ta Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi. Ajinsa uku sawess yake yi a cikin Jos. Sannan ya yi sa'a ma'aikaci ne a karamar hukuma da aka dauke shi aiki da sakandire a lokacin kawunsa kanin mahaifiyarsa kansila ne a yankin gundumar Toro. Na isa gare shi, yana sanye cikin farin yadi fari k'al. Wato duk samarin gidanmu babu mai tsabtar Yaya J. Ina jin da'din k'iransa da Yaya J. Na lura shima ba karamin son sunan yake yi ba. Ni ka'dai ce nake fa'da masa hakan kuma. Kusan halayyarmu daya ni da shi, domin nima tsabta ce da ni, har fa'di ake yi aljanun tsabta ne da ni. Baya ga haka muna da son y'anuwanmu, bama jin k'yashi wajen salwantar da duk abi da yake namu ne akan d'an-uwanmu, har rashin girman jikinmu iri d'aya ne. Shine d'a na farko a bangaren Baban Tsakiya. Mutane da yawa suna fa'din kama muke yi ni da shi, ni kuma bana ganin kamar kawia dai yanayinmu ne daya tunda shi din ba wani girma ne da shi ba, haka yake dan madaidaici avarage height ne. Haka nima duk cikin y'anmatan da muka taso ko wacce ta fini tsayi, bani da tsayi, nafi kusa da gajerta. Ina da gashi sosai, sannan ina da manyan idanuwa baya ga hakan fara ce sosai. Yadda nake yar cif cif sai nake matu'kar daukar hankalin mutane. Kullum idan zan fita sai Gwaggo ta ce ban da wulakanci Yabi, domin al'adar gidanmu ne yarinya bata kammala karatun sakandire. Shekaru sha biyar ake aurar wa, amma mu da alamu za'a bari mu kammala duk da dai Dada ta fara fa'din mu shirya dama kuma ita ce take matsa lambar sai an yi aure. Ya zuba mini ido babu walwala jikina ya yi sanyi na yi kasa da kaina ina fa'din "wannan kallon tuhumar fa Yaya J?" Ya saki gauron numfashi ya ce "kin kama kanki da kanki Yabi. Jiya ma fa sai da kuka tsaya da yaron nan dan gidan Sarkin k'ofa ko?". Na yi murmushi na ce "Ai dai baka ji me na ce masa ba". Na fa'da cikin shagwaba shagwaba. Ya sake yin kasa da murya ya ce "Ban ji ba, amma yanzu fa'da mini na ji". Na yi k'asa da kaina na ce "Na fa'da masa cewar ni bana sonsa akwai wani bawan Allan da ya riga shi yin wuf da zuciyar Yabin Marina". Ina kallonsa ya dan murmusa ya ce "Waye wannan bawan Allan?" Na dago amma ban kalle shi ba a dalilin hasken kwai na kanmu. Na juyar da fuska na ce "Yaya J mana". A wannan karon murmushi mai sauti ya yi. Ya nisa ya ce "Yauwa Yabin J, kin biya ni. Amma idan kina son ki burge ni, ki daina ma sauraronsa ba shi kawai ba, kowanne namiji ma. Sannan ki daina fa'da dazu ma sai da kika yi dambe da Saratu. Kin ta'ba gani na ina dambe?" Na girgiza kai tare da cewa "Ha'kuri ne ya yi maka yawa, ni kuwa bani da shi, domin duk wacce ta ta'ba ni ba zan k'yale ba" Ya girgiza kai ya ce "Ha'kuri fa falala ne da shi Yabi". Na girgiza kai na ce "To ka dinga yi mini addu'a na shiga sahun masu ha'kurin domin kuwa ni duk wanda ya ta'ba ni idan ban rama ba sai nake ganin na zama sullutu". Ya murmusa sosai domin ba mai dabi'ar k'yal-k'yala dariya ba ne. Ya zuba mini ido ya ce "Wai Goggo ce ta haife ki, al'amarin Ubangiji da girma yake. Waton idan kika rama baki zama sullutu ba?". Da hanzari na ce "Ras Yaya J domin dai kai din shaida ne na yadda ake kaffa kaffa da ni, da duk kayana". Ya zuba mini ido ya ce "Allah ka sanyawa Yabi ha'kuri da juriya, a mayar mini ita ta zama mai shanye dukkan kalubale da ha'kuri da kuma kawaici". Na ce "Gaskiya Yaya J kada mu yi haka da kai, roka mini na zama yar gwagwarmaya mana, sai kawai ka roka mini na zama mai ha'kuri komai aka yi mini sai dai na yi kuka, ko ya yi ta cina a zuciyata, watarana sai dai kawai a budi ido aga Yabi ta ha'du da jinya ko ta mace ma gaba'daya. To ni ba zan zama hakan ba". Ya gyara tsayuwarsa ya ce "Kinsan darajar ha'kuri kuwa Asiya?" Na kalle shi domin bai cika fa'din zahirin sunana ba, tunda ya fahimci ina son inkiyata ta Yabi shi kenan ya wajabta ma kansa fa'da mini duk da dai yafi son Asiya. Domin an sha dakuwa da ni akan ce mini Asiya, ina ganin duk wanda ba zai ce mini Yabi ba, to hassada yake yi mini, tunda an yi dawafi da ni a ciki, an yi tsayuwar arfa da ni, an yi jifan shaidan da ni, an yi sa'ayi da ni to mene ne na tauye mini Hajjin?" Ban bashi amsa ba ya ce "W anda Ubangiji ya masa baiwar ha'kuri to ina tabbatar miki an ba shi arzikin duniya da lahira, ba kuma abin da ba zai cimma ba a rayuwarsa, daure ki zama jaruma amma ba jarumtar rashin ha'kuri ba". Na girgiza kai ina murmushi domin dai ban gamsu ba. Har yau da na fara mallakar hankalina ban ga ribar ha'kurin da mahaifiyata take yi ba. Ban ga ribar kawaici da ha'kurin da mahaifinmu yake yiwa zumunci ba. Ban ga ribar ha'kurin da Yaya Ummi take da mijinta da uwargidanta ba. Tunda har yau ita ce a wahale, kuskure ka'dan zata yi ya mata tijara a tsakar gida a gaban kowa tamkar ba ita ce mai k'uruciya ba. Dan haka na k'udire a raina ba wanda zai nemi ta'ba ni, na k'yale shi, zan yi komai dan na tabbatar ban bari na zama gajeriyar katanga mai da'din k'etara ba. Yanayina ya tabbatar masa ban yarda zan iya yin hakan ba. Ya girgiza kai ya ce "Ai shikenan sai dai zan cigaba da yi miki addu'ar dace wa da babban arzikin duniya wato Ha'kuri". Na yi dariya na ce "Dama addu'ar na zama hamshakiyar y'ar kasuwa kake yi mini, ta yadda kasuwacina zai d'auke mini hankali daga dukkan wani rashin ha'kurina da kake ga ni". Da sauri ya ce "Ina yi miki Yabina! Da ikon Ubangiji komai kika kasa sai kin sayar, kullum sai na roka miki Ubangiji ya baki dauwamammiyar sana'a da zaki tsufa kina cin gajiyarta". Da'di ya kama ni, domin Yaya J ne kawai ya fahimci irin yadda nake son na zama shahararrriyar y'ar kasuwa. Ya miko mini tsarabar Jos leda biyu da ya ajiye a bayan k'yauren shiga shashinmu. Na karb'a ina godiya sosai. Na tabbatar Atile ce da kuma turare, tunda sune abu mafi soyuwa a mini kyautarsu. Fahimtar hakan da ya yi, sai ya dimanci yi mini tsarabarsu. Shine ya fara koya mini amfani da turaren Far-away. Daga haka muka yi sallamah. Kai tsaye dakin uwata na nufa ban koma wajen Dada ba. *Akwai kayayyakin gyara mace sosai irin na kasar Chad.* *Akwai maganin sanyi sadidan* *Ku tuntube ni a wannan lambar* *08032773332.* ✍️ *BAK'AR TA'ADA* *NA* *SURAYYA DAHIRU GWARAM* *(MRS M.I.NASHE)*. *Marubuciyar* *Halin Yau* *Sabo da kaza* •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI* *IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*. *SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI* *AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN* *AKWIA PACKAGE DIN AMARYA* *AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO* *AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*. *INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA* *MASU SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332* *DAN ALLAH SERIOUS BUYERS* https://www.wattpad.com/1381521145?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp.w4b&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=SurayyaIbrahim1&wp_originator=2c15XL0D2bIzHhiZQM1Ufz9MWPlKieRkWxJuGH2P9gX0b9XHQk5Jym8fxiz%2BPI0TAhOUhwh2GWl2lunKDNI2ObmS%2B%2FfL1BUVY3%2Ft%2BNKg%2B0D0iEZNLOPdWH9AZxOaGd51 https://arewabooks.com/book?id=64e93a53984f91b3605ae432 *Ina makaranta labaran Books ɗin Ayshat Ɗansabo lemu, marubuciyar TAIMIYYAH DA NUFIN ALLAH kai har ma da sauran daɗaɗan littafanta? Marubuciyar na muku albishir da cewa sabon littafinta mai suna ƘADDARAR ZOYA ya fara sauka da zafinsa,labarin ƘADDARAR ZOYA labari ne da ya faru a gaske ba ƙageggen labari bane.Don haka kar ku bari ayi wannan tafiyar babu ku a cikinta,labarin zai zo muku akan 500 Whatsapp group sai VIP group on Telegram 1k.Ku tuntuɓi marubuciyar akan lambarta 08167768704 domin samun free pages na labarin kai tsaye, kafin ku kai ga yin payment.Kar ku manta it's a true life story,don haka ku hanzarta shiga cikin tafiyar da babu danasanin bin alƙaminsa....✍* 5&6. A zaune na tarar da ita tana kullin siga, da yake tana auno rabin kwano tana k'ullawa, idan an zo siyan koko ana siya. Ikilima tana gefenta tana faman barci. Na ajiye ledar a gabanta. Ta kalle ni ta ce "Yabi na sha fa'da miki, jikina na bani sha'aninku da Jabiru ba mai yiwuwa ba ne, ba sa'an auren ki ba ne, gara ki tsaya akan Abdulrashid zai fi mana sau'ki da kwanciyar hankali". Na yi shiru, amma zuciyata sai tsalle take yi. Babban tashin hankalina a duniya shine Gwaggo ta ce mini aurena da Yaya J ba zai yiwu ba. Na yi k'asa da kaina a hankali na ce "Gwaggo fa'da mini dame ya fini da kike ganin yafi k'arfina?" Ta murmusa ka'dan ta ce "Saboda Babanki ba shi da arziki, sun tsere mana, sannan uwarsa tana da buri a kansa, bayan haka ga Mama k'ut take da uwarsa, dan haka zata yi dukkan mai yiwuwa ta sake b'ata lamarin tunda akwai haske a tare da shi, ba zata so wannan hasken a tare da ke ba. Sanin kanki ne kuma mutanen gidan nan baza su dauke ki su ba shi ba, tunda kuna da yawa, zasu yi kwarya tabi kwarya ne a tsakani. Da ace ke din diyar Baban kasuwa ce to, da ba fargabar da zan yi". Na numfasa k'irjina ya daure ainun. Na dinga tambayar kaina shin zan iya rabuwa da Yaya J? Da gaske har lalacewar zumunci ya kai za a iya hanamu aure ba tare da wani dalili gamshasshe ba? Ashe har za'a iya ture karfin jini saboda kawai dan-uwanka ba shi da wadatar abin duniya? Na sauke nannauyan numfashi na ce "Ki daina damuwa Gwaggo! Ban tsananta ba, ban kuma dage sai shi ba. Ki cigaba da yi mini addu'a". Ta sake kafe ni da ido ta ce " Ina yi miki addu'a sosai Yabi, amma zata yi tasiri ka'dai idan kin barwa Allah ya yi miki zabi, kin kuma yak'i zuciyarki akan Jabiru. Ina nufin ki rage zurfafa a al'amariinsa." A sanyaye na ce "To Gwaggo". Sai kuma na zauna ina taya ta k'ulla sigan ina bata labarin yadda ta kaya a tsakanina da Dada. Ta nisa ta ce "Ba kya jin magana ne, ban da hakan mene ne zaki dinga janyo wa tana yi miki mugun fata? Kinsan kuwa bakinta zai kama ki domin ita ma uwa ce a wajen ki". Jikina ya sake yin sanyi, na dinga yin addu'ar Allah yasa na daina tanka mata akan Shehu tunda mafi yawa saboda hakan take fusata. Ta ke tsanata mini, har take yi mini mummunar addu'a. Washagari takwas saura muka d'unguma zuwa makarantarmu ta jeka ka dawo ta gwamnatin jahar Bauchi. Ajin mu hudu wato ss1. Ko wacce tana cikin tsafta, duk inda muka wuce sai an kallemu wataran akan kunnenmu mu ke jiyo yadda ake fadin "y'an Marina ne, kasan yawa ne dasu tamkar tsaki." Ko muji an ce "kai wato gidan Marina akwai zuka zukan zaratan y'anmata fa." Muna tafe ina tambayar Basira da Nazira jiya Dada ta d'ora musu karatun kuwa bayan na tafi?. Nasiba ta ce "Bayan kin bata mata rai yaushe zata iya yin karatu? Kin san kullum sai ta ce haramun ne yin karatun addini a cikin fishi ko a cikin rashin tsarki". Muka k'yal-k'yalale da dariya gaba'daya. Muka isa makaranta hatta Malamai kwarjini muke yi musu saboda yawanmu da kuma yadda muke kama da juna baya ga hakan tare ake ganinmu tamkar kashin awaki alhalin a gidajenmu babu wannan soyayyar da jin kai da ake gani a tare da mu. Lokacin tashi yayi muka dawo a jiga ce a dalilin rana ake yi duk da zafin ranarmu da sau'ki akan ta Bauchi da Jigawa. Wajibi ne idan zamu tafi sai mun shiga mun gaida Dada, haka nan idan mun dawo. Tsabar saka ido da kwakkafin baiwar Allan nan duk wacce bata je ba sai ta ga ne, hakan kuma na iya zama sanadin rikici a gidan, domin bai zame mata komai ba, ta kira uwar yarinya ta yi mata tass, ta ce da sa hannunta y'arta ta raina ta. Kuma abin mamakin idan baka kama sunanta ba, to da kai da wacce bata je ba daidai kuke. Ina tsaye suka dinga shiga suna fitobwa ba abin da ake ji sai "Dada mun dawo, sannu da gida" . Yayin da ita kuma take kama sunan kowa tana cewa "Sannunku da dawowa, lale da y'anmata Dada". Sanin da na yi garina da tsakuwa da ita, ya sanya nake jingirta wa sai na je gabanta sosai ta yadda zata shaida ni da kyau. Tunda kullum sai na je, amma idan ta so ci mana mutunci ni da Gwaggo sai ta ce ban je ba, ko kuma na yi mata gaisuwar gadara da wulakanci daga bakin k'ofa Dan haka da na k'ara wayo sai nake isa gabanta mu hada ido sosai sannan na yi gaisuwar. A gajiye na k'arisa k'ofarmu na tarar da bacin rai domin tsagwaya na tarar an yi a matsayin abincin rana, wani irin nau'in abinci ne da ake sirfa dawa sai a dafa a ci da manja. Na tsani abincin ba dan babu da'di ba, sai dan kawai bana so. Na zauna a tsakar d'akin Gwaggo ina kunci sosai. Ta shigo ta kalle ni ta ce "ban ga kin cire inifom din naki, kin yi sallah kin zuba abinci ba?" Na tumbatsa da fishi ban tanka ba. Ta kafe ni da ido ta ce "Yabi kullum aka yi tsagwaya sai kin tayar mini da hankali? Sanin kan ki ne mahaifinku ya saka takunkunmin siyo abinci a waje ko a ro'ko a wani waje. Me yasa ba zaki rufe ido ki ci dan ta yi miki maganin yunwa ba? Idan kin yi ha'kuri ai wataran barin gidan zaki yi, ranar da Allah ya kai ki dakinki komai kike so sai ki yi wanda bai wuce wadatar mijinki ba". Cikin bacin rai na ce "Ki taimake ni ki bar ni na jika gari na sha, Allah ya sani yunwa nake ji kamar na mutu". A sanyaye ta ce "To ki jika amma nafi son ki dinga ci tunda idan kin ci din ba illah take miki ba." Haka na jika gari na bu'de jakar makaranta na dauko gyada maro na bushe na zuba, ina sha, ina fa'din "ba dan na k'osa ba, da Iklima ta siyo mini madara, to aikenta bana me sauri bane ko wanda yake a matse irina, domin shad'arta ta yi yawa". Gwaggo ta girgiza kai ta ce "Ke dai duk salon k'wadayi kin san shi, ki dinga bin duniya a sannu sannu Yabi". Na yi dariya na ce "Gwaggo tuni aka daina bin duniya a sannu. Saboda gaggawar mutanen cikinta ba zasu bar mai binta a sannu ya kai ga gaci ba, yanzu da nake yin kitso na ha'da da lalle ba gashi muna d'an samun taro da k'wabo ba, da sannu nake bi iya kitson kawai zan yi Gwaggo. Yanzun ma so nake na koyi wata sana'ar na sake ha'da wa domin ina da burin na samu ku'di masu nauyi na jiyar da ke da'di, na jiyar da su Iklima". Ta girgiza kai ta murmusa ta ce "Na gode sosai Yabina! Allah ya ida nufi, amma dai ki bi a sannu da ikon Ubangiji komai zai saukaka a gareki, kullum sai na rokar muku kada a jarrabe ku da rashin abincin a gidan aurenku kamar yadda aka jarrabi Yayarku, ita ma ina fatan da'di ya biyo bayan wannan wahalar da take ciki". A sanyaye na ce "Allah ya amsa bakinki Gwaggo". Ina kammala wa na yi haramar sallar azahar, sannan na shiga wanka dan shirin tafiya Islamiya. Dai-dai lokacin Babanmu ya dawo daga wajen sana'arsa. Gwaggo ce mai girki ta hau hidimar kai masa abinci, a raina sai kiyastawa nake yi ina ma ina da hali na dinga soya masa miya mai d'auke da naman kaji ko na shanu zuk'u zuk'u a ciki. Din ya dinga ci da abinci. Na fito na gan shi zaune a rumfa akan tabarma jikinsa duk ya yi futu futu, ga alamun gajiya mai yawa a tare da shi. Tausayinsa ya tsirga mini, cikin rauni na ce "Sannu Baba, sannu da kokari". Ya dan sassauta ya ce "Sannun ka dai Yabi Asiya". Na dan murmusa domin shi ka'dai ne yake ha'da mini sunan guda biyu. Tunda ya fahimci ina bacin rai idan ba'a ce mini Yabi ba, sai ya kankare kirana da gayan Asiya. Na wuce shi na fa'da d'akin Mama wajen Nazira. Na tarar itama shirya wa take yi. Tare muka fito muka risina muna cewa "mun tafi Baba". Ya amsa da cewa "A dawo lafiya, ku kula da kanku". Muka shiga sashin Baban Tsakiya muka fito da su Firdausi da Saratu. Amma wani irin abu ya tsirga mini mai nauyin gaske, ba dan komai ba illah ganin da na yi Baban Tsakiya yana cin dafadukan shinkafa gefe kuma kunshin balangu ne, ga pure water mai sanyi a gefensa cikin yar bak'ar leda da alamu shi ya shigo da su. A banzan ce ya amsa gaisuwarmu tamkar ma bai ganemu ba. Na tuna gabzar da muka baro Baban Marina yana ci zufa tana yanko masa. A hankali na ce "Àllah ga Yabi! Ka buda mata hanyoyin arziki ta jiyar da iyayenta da'din duniya". Kafin muje k'ofar Baban kasuwa muka yi kicibus da Maijidda, ta fito. Na ji da'din hakan domin shi kam ma tsiyatakunsa sun fi na Baban Tsakiya yawa. Gaba'daya muka d'unguma k'ofar Dada dan yi mata sallama da kuma biya wa Nasiba. D'aya bayan d'aya muke gaisuwar tamkar masu neman tabarraki, kuma dole sai an kama sunanta idan ba hakan ba sai ta dauke kai tabbacin bata karbi gaisuwar ba. Abin da zai biyo baya kuwa ba mai sau'ki ba ne. **** An idar da sallar isha dukkan mun hallara a k'ofar Dada. Sai jiranta muke ta kammala nafilfilinta ta d'ora mana karatu, domin karatun nata ba k'aramin nisha'di yake sanya mu ba. Ta idar ta dinga jan dogon carbinta wanda kafin ka kammala jan k'afa d'aya ma lokaci ne mai yawa. Amma haka muka jira ta kammala. A fili ta cika addu'arta da salatil fatih. Dada tsohuwa ce da bata samu ilimi sosai ba, amma Ubangiji ya cika zuciyarta da son addini, ta rabauta da yawan yin istigifari, matsalarta guda tana da son zuciya, matu'kar zaka bata abin duniya to zata juya gaskiya ta koma karya. Hakan kuma ya yi tasiri a zukatan ahalinta, domin kuwa a tsakaninmu ma mun k'ullaci yadda take fifita Nasiba akanmu, ta yadda ta fimu gata da iko a gidanmu. Kowa yasan Dada tafi son jikokinta da y'ay'anta mata suka haifa, mussaman su Nasiba sannan Bulkachuwa. Saratu ta ce "Dada muna dakon karatun ne, jiya kin ce addu'ar tsari da makarai da miyagu zaki d'ora mana." Ta dan yi tari ka'dan ta ce "Hakkun Saratu". Ta numfasa ta ce zan biya sau uku daga nan sai ku dinga fa'da bayan na fa'da." Muka amsa da cewa "To". Ta yi Basmalah, ta yi salati ga Annabi, sannan ta nemi tabarrakin SHEHU. Na yunkura zan yi magana sai kawai na yi maza na saka hannu na kame bakina. Da karsashi ta ce *"Wa makaru, wa makaru, Wallahu kairan makirina".* Na amsa karatun nata ina ganin kuskuren ciki ka'dan ne. Muna saurare har ta biya sau uku kamar yadda ta fa'da. Sannan muka koma tana yi, muna amsawa har kuma ta ce mu yi da kanmu. Muka dinga yi har muka rike dama kuma mun biya ayar a islamiyya. Ina son na yi mata gyara amma ina jin tsoron abin da zai biyo baya. Ganin mun ri'ke sai ta ce "To zan baku addu'ar farin jinin samari, ku yawaita yinta atafe kuke, ko a zaune ko kuma a kwance". Muka yi shiru dan nuna kunya. Ta numfasa ta ce *"Ya tifa risubuha ragadan".* Muka k'yal-k'yalale da dariya, na kasa daurewa na ce *"Min kulli.."* kafin na karasa ta ce "Lah! Ai iya inda na tsaya, zaku dakata, duk wacce ta yi karambanin cika ayar to ta kuka da kanta. Domin maza kala kala zasu yi ta bin ta har mazan dabbobi sai sun bi'de ta da sunan soyayya saboda karfin addu'ar, kunsan Annabi Isibu aka saukar wa ayar." Muka kasa cewa uffan domin kowa dariya ce a bakinsa yake gimtse wa". Ta kalli Nazira, Saratu, da Nasiba ta ce ku dimance ta babu kakkautawa kune masu nauyin jini, ke Yabi ba sai kin yi ba, ku kuma ragowan saffa saffa zaku dinga yi tunda kuna samun mane ma." Nasiba ta bata rai ta ce "wanne irin nauyin jini kike magana Dada? Duka duka fa shekarunmu sha shida ne wasu ma basu cika ba, ban da dai ana auren wuri a gidan nan ina ma muka isa a samu a sahun y'anmata a wannan zamanin?". Dada ta ce "A wajena kun wuce y'anmata ma kun zama iyayen mata, tunda ba wacce bata yin wanki duk watan duniya, ni kam kullum sai na yi tuba sama da sau dari uku, tare da addu'ar Allah ya cika mini burina wajen sallar layya ace ko wacce maneminta ya tsaya duk sai mu tattara mu rabu da ku salin alin. Amma a duk sadda na hango zugar ku gabana faduwa yake yi, inta shiga firgicin yadda sallolimmu suke goriya a madakata basa isa gaban Zati". Cikin dariya na ce "Wai a ina kike koyon wadannan karatun naki irin na makafi ne?". Haka kawai na fa'da ta rusa ihun da ya janyo hankalin ahalin gidanmu, mu kuwa gaba'daya muka zuba mata ido muna mamakinta, yayin da jikina ya yi mugun sanyi, zuciyata ta shiga kaiwa da komowa cikin fargaba mai yawa. Cikin kankanin lokaci dukkan iyayenmu maza sun bayyana, wasu daga cikin matan gidan suma sai iso wa suke yi cikin zullumi duk da dai ta kan yi irin haka sa'i, sa'i. Tana kukan tana fa'din "Yabi ce, Yabi ta zage ni, ta mini gorin mijina makaho ne". Mamaki ya sake kama mu, domin sai a ranar muka san kakanmu Alh Garba wai ashe ya makance a karshe karshen rayuwarsa, duk cikinmu ma ba wadda ta san shi bare har a yi mata gori, sannan dama ana gorin ciwo ne?" Haka Baban kasuwa da yake jin shine a saman kowa, ya hau cin mutuncina yana fa'din ba zai yiwu kullum sai na tozarta uwarsu ba. Zai dauki mummuna mataki a kaina ya ga take takena so nake na gagari kowa, to shi ba zai zame masa komai ba akan mahaifiyarsa ya kore ni daga gidan, ko kuma ya dauke Dada su bar mini gidan, idan ya so iyayena su shata jan layi da shi. Baban Marina kuwa cikin sanyi yake fa'din "Haba Iliya yaushe zan haifi y'ar da zata shiga tsakaninmu, komai zaka yi mata ai ka isa ne". Baban Tsakiya ya ce "A a ai yaran yanzu basu da kunya balle mutunci baka ganin yadda ta saka uwarmu kuka to mu kuma idan muka ce zamu shiga shirgin ya'yanka ai sai dai su rufe mu da duka tunda a cikin idonsu muke ganin bakincikin da suke yi da mu, tamkar dai mune muka hanaka ka sake tara arziki, ko muka hanasu yin zuciyar tallafa maka. Ban da lalace wa Musa ka'dai bai isa ya ri'ke kofarka ba? Ya'yanka wajen hudu ko biyar ne a daki amma duk wula'kantattu ne, basa taimaka maka da komai, amma abin kaico sun raina kokarinmu akan ka." Baban Marina ya sunkuyar da kai kasa gwanin tausayi yana fa'din sai ha'kuri da yaran yau, ni kuma har yau din nan basu fiye mini ku ba". Na kalli Nazira na ga hawaye na tsere akan fuskarta, na sake kallon ragowar, su Firdausi kowa idonta a bushe tabbacin basu da kaico akan cin mutuncin da iyayensu suke yiwa ubanmu. Na kasa hawaye a dalilin ba'kin cikin da yake cina yafi gaban hawaye. Ba abu mai ciwo irin wanda ba za'a barka ka keta shi ba, ya tisa iyayenka a gabanka da cin mutunci akan idonka. Na sake kai idona kan Dada da take matsar hawaye, na dinga mamakin yadda ta tara mini jama'a haka. Na gama yarda kafatalin jikokinta ba wacce take jiran kiris akanta iri na. Duk yadda Nasiba take zage wa suna yin sa in sa, hakanan kowa a cikinmu tana mayar mata da magana amma ba wanda take mayar da laifinta garma sai ni. Tausayin mahaifina ya yi matu'kar kama ni ta yadda kannensa suka tsaya a gabansa suke fa'da masa maganganun da komin sanyin halinsa sai sun mintsine shi. Kirjina ya sake nauyi akan wanda ya yi dazu da naga Baban Tsakiya yana cin da'di a kofarsu amma mu muna cin abinci irin na yan fursuna, kuma suna da halin tallafa wa. Amma sun runtse idonsu. Haka Baban Marina ya dinga bawa Dada da sauran y'ay'anta ha'kurin katobarar da na yi tamkar dai shi din ba uwarsa ba ce. Sai lokacin hawaye mai ciwo ya goce mini, ina jin tsanar mutanan da a baki Baffanina ne. Maganar gaskiya kuma na fi jin ciwon Baban kasuwa. Haka suka fice suna kumfar bakin na fitine su, na fitini y'ay'ensu, tunda ba'a sati ba a doku da ni ba a cikin gidan. Rainin da aka yi mana ne ya sanya dukkan mutanan gidan suke ganin zasu mayar da mu gidadawa, shiyasa ni kuma na lashi takobin duk wanda ya nemi ta'ba ni, ko taba wani cikin yan k'ofarmu la shakka ni ya ta'ba domin zan siyi fa'dan ne ya dawo kaina, duk yadda nake yar shafal amma Ubangiji ya hore mini wani irin karfi tamkar shari'a, ko dan da dukkan zuciyata nake yin fa'dan ne oho. Yadda nake tare wa kannena fa'da da muke daki d'aya haka nake tarewa na yaran Inna amaryar Babanmu babu banbanci. Hatta Nazira da take yayata ni nake tare mata fa'da domin duk wanda ya fa'da mata maganar banza zan yi ruwa na yi tsaki na shiga na dinga yarfa bak'ar magana har sai abin ya juye kaina. Duk yadda nake jin haushin Mama bai shafi son da nake yiwa Nazira ba. Domin yar-uwata ce da uba ya ha'damu, idan da abin da na tsana ban kuma yarda da shi ba shine yan'ubanci. Ina matu'kar takaicin yadda wai gidanku daya da mutum, cikinku daya, gadonku daya amma babu yarda da amana a tsakaninku. Duk wani alherinka baka son dan-uba ya ji, zaka iya fa'dawa bare matsalarka amma ban da dan-uwanka da uba daya ya hada ku. Kuma mafi yawa iyaye mata ne suke bari yaransu su shiga cikin rikicin da ba nasu ba. Da ace Nazira tana biye hudubar Mama da tuni ta gurbata mana zumunci da soyayyarmu, mun koma muna adawa da junanmu. Wai uwa ce zaka ji tana zayyane wa y'ay'anta laifin kishiyarta, ko kuma laifin y'a ko d'an da ba nata ba. Da ace iyaye mata zasu dinga ha'diye rikicin kishi a tsakaninsu, suna boye rashin jituwarsu a gaban yaransu, sannan idan matsala ta faru suna barinta a tsakaninsu da an samu sassauci wajen yan ubancin da ake yi a yau. Idan d'an kishiya ya yi miki laifi ko ta yi miki, daure ki ha'diye ba sai kin baza wa yaranki da basu sani ba, gudun haddasa gabar da baki san iyakacinta ba. Ko wanne d'a a duniya gaibu ne, ba wanda yasan me gobe zata zo da shi, ba lallai d'an da kika haifa ya samu daukaka ba, wata'kila sai d'an miji ya samu daukaka fiye da yaranki, adalcin ki ne zai sa Ubangiji ya sarrafa zuciyarsa ya ji k'anki, haka nan ke ma babu jin kunya ko nauyin kin yi abubuwa a baya marasa da'di. Na sani mutanan yau bamu cika gode wa da yaba kokarin abokan zamanmu ba, muhimmi dai mu yi adalci a tsakanin zaman kishi da yaranmu, ko ba a shiri ya zama akwai sassauci da ha'diye bacin rai, shi adalci yana haifar da farin-ciki da yalwar arziki da hadin kai a cikin gida. Addinin musulunci cewa ya yi ko wanne musulmi dan-uwan musulmi ne, bare kuma wanda jini mai k'arfi ya ratsa a tsakaninku. Daga shakiki sai li-Abbi a duniyar musulunci da zumunci amma mutanan yau mun dauki wata irin *Bak'ar Ta'ada* ta mayar da dan-uba abokin gaba kuma makiyi. Da kaina na jinjina wa kaina da duk wacce bata da wannan mummunar manufar a ranta. Madallah da mutanan da suka yarda Ubangiji ne yake zaba mana mutanan da zasu zama iyayenmu da yan'uwanmu. Alhamdulillah, Allah ka bamu ha'kuri da juriya wajen mua'amalantar mutanan da ka d'ora mana hakk'in zumunta da su. *Kafin lokacin zaku iya fara payment ta yadda idan an kammala free pages babu dogon jinkiri.* *Madallah da masoyan RUBUTUNMU*. *Madallah masu sauke hakki komin kankantar sa, madallah da masu k'arfafa guiwarmu*. *Fatan alheri ga masu kiyaye hakkin sana'ar y'anuwansu*. *500 for regular* *1k for VIP* *2384876855* *Surayya Ibrahim* *ZENITH BANK* ✍️ *BAK'AR TA'ADA* *NA* *SURAYYA DAHIRU GWARAM* *(MRS M.I.NASHE)*. *Marubuciyar* *Halin Yau* *Sabo da kaza*. •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI* *IDAN KINA DA KANWA KO DIYAR DA ZAKI AURAR. TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*. *SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI* *AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN* *AKWIA PACKAGE DIN AMARYA* *AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO* *AKWAI GORAN TULA SYRUP* *AKWAI GORAN TULA FRUIT* *AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*. *INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA* *MASU SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332* *DAN ALLAH SERIOUS BUYER'S ONLY* *Ina makaranta labaran Books ɗin Ayshat Ɗansabo lemu, marubuciyar TAIMIYYAH DA NUFIN ALLAH kai har ma da sauran daɗaɗan littafanta? Marubuciyar na muku albishir da cewa sabon littafinta mai suna ƘADDARAR ZOYA ya fara sauka da zafinsa,labarin ƘADDARAR ZOYA labari ne da ya faru a gaske ba ƙageggen labari bane.Don haka kar ku bari ayi wannan tafiyar babu ku a cikinta,labarin zai zo muku akan 500 Whatsapp group sai VIP group on Telegram 1k.Ku tuntuɓi marubuciyar akan lambarta 08167768704 domin samun free pages na labarin kai tsaye, kafin ku kai ga yin payment.Kar ku manta it's a true life story,don haka ku hanzarta shiga cikin tafiyar da babu danasanin bin alƙaminsa....✍*   *Shafin nan kyauta ne sukutum ga mamana* *Hajiya Hadiza Sodangi* *Na gode sosai Ubangiji ya shirya zuria* 7&8. Maganar Baban Marina ta dawo da ni tunanin da nake yi. Kamar a sama na ji ya ce "Na gode miki Asiya! Duk yadda nake jan kunnenki akan b'atawa Dada rai, da kuma dukan yaran gidan nan ba kya ji, saboda kin riga kin zama y'ar kuka. Uwarki kullum cikin yi miki kashedi akan shiga fa'dan yara da kuma tsokanar Dada, amma duk a iska ko? Na gode sosai da wannan bacin rai da kika sanya ni, Allah ya shirye ki". Ya tsugunna gaban Dada ya ce "Ki yi ha'kuri! Halin Asiya ni kaina ha'kuri nake yi da ita, amma zan dauki mataki akan ta'ba ki da take yi". Ta kyabe baki ta ce "To ka fara dan takidin aurensu. Jiya mun tattauna da kannenka sun ce su babu matsala ko yaushe auren ya zo a shirye suke, kai dai za'a fa'dawa ka fara tanadin tunda yaran ka har biyu ne". Ya yi gyara murya cikin k'arfin hali ya ce "Babu damuwa Dada ina saka rai Ubangiji zai kawo mini hanyar da zan samu na yi musu iya abin da zan iya." Ta murmusa tamkar ba ita ce mai kuka tana face majina ba. Ta ce "To babu laifi Allah ya basu na gari, masu kuma ha'kuri, domin mai yakana ne zai iya zama da Yabi dan wuyar zamanta ya kai inda ya kai, ba inda ta baro uwarta". Cikin sanyin jiki Baba ya mike yana cewa"Dada sai da safe mu kwana lafiya". Ta amsa masa da fa'din "Allah ya tashe mu lafiya". Na mike, Nazira ma ta biyo ni muka fice, ba tare da mun ce uffan ba. Domin na sake fusata da ta ce sun tattauna da kannensa amma shi ba'a saka shi cikin zaman ba. Muna jin ta tana fa'din "Wanda Allah ya bashi tsawon rai zai yi kallon tak'ama a wajen ki Yabi. Yarinya da ke amma kusan ke kike juya shashinku gaba'daya. Kina tashi Yayarki ta biki zungui zungui ko sallama ta kasa yi mini saboda tana rarrashin zuciyarki?". Ban juya ba, bare na tanka mata, balle kuma Nazira da take da sau'kin hali. Muna shiga shashinmu muka yi turus a dalilin halin da muka ga mahaifinmu a ciki, zaune yake akan tabarma a tsakargida. Sai fifita Gwaggo take yi masa, gumi na yanko masa babu kakkautawa. Muka isa gabansa, muka tsugunna, baki na rawa na ce "Sannu Babanmu! Abin mamaki sai ya daga mini hannu tabbacin ya amsa gaisuwar tawa. Nazira ma ta yi masa sannu ya amsa ta hanyar gyada mata kai. Mama ta fito daga bandaki ta kalle ni ta ce "Wannan ja'irar yarinyar sai kin zama sanadin mayar da kananun ya'yansa marayu, fitananniya tabtacciya. Ai duk gwanin na iya a rana ya ke" Ta ja tsaki mai tsanani ta wuce d'akinta. Bata jima da shiga ba ta k'walawa Nazira kira, ta mike a hanzarce ta nufi dakin nasu. Daidai lokacin Baba ya dan samu sau'kin zufar da take karyo masa. Ya yafito ni, jiki na rawa na isa gabansa. Ga mamakina sai ya mik'o mini hannunsa na dama. Hannu bibbiyu na ri'ke hannun nasa, cikin barin jiki gaba'daya. A sanyaye ya ce "Ina alfahari da ke Yabi! Kafatalin ya'yana ke nake da tabbaci akan ba zaki cigaba da yin mini *Bak'ar Ta'ada* ta y'an ubanci ba, na tabbatar da hakan. Ina saka rai ta dalilinki yarana zasu dawo tsintsiya. Na so ace da wuri na haife ki Yabi. Da al'amuran da suka dame ni basu yi mini tsananin da nake ciki ba. Amma Alhamdulillah! Ubangijinmu baya kuskure na gode masa, ina kuma tuba a gare shi." Hawaye tuni ya goce mini dukkan zuciyata a jagule take da tsananin tausayin Mahaifina da a yau nake ganin wani irin tashin hankali da raunin da ban ta'ba ganinsa a ciki ba. Gwaggo tana fifita, tana kuma share k'walla.y Ya numfasa ya ce "Idan na mutu Yabi, duk runtsi ku gaisa da yan'uwana, ko ba zasu taimakeku ba, to lallai ku dinga saka su a cikin al'muranku, idan kina yi, sannu a hankali zaki samu wanda zasu yi koyi da ke, tunda tun yanzu al'amura sun haska ke ce mai tsayayyen ra'ayi wanda yafi kusa da kyau da kuma dace wa." Murya na rawa na ce "Mu sasu a alamuranmu ko da ba zasu taimakemu ba, ko da idan mun fa'da musun ba zasu dauki al'amarin namu da girma ba?" Ya sake damk'e hannuna ya ce "Haka nake so Yabi". Da karfin zuciya na ce "Da Ikon Ubangiji zan yi yak'i da dukkan zuciyata na yi hakan. Amma ina ro'kon arziki ka mini afuwa, ka yafe mini muzancin da na janyo maka dazu". Ya girgiza kai ya ce "Baki yi laifi ba, na sani. Sannan su d'in ma bana son ki d'auki abin da suka yi mini a matsayin muzanci ko tozarci, na sani baki da sauki, kina da ru'ko, dan haka na umarce ki, ki manta komai". Na murmusa hawaye na kwaranyo wa na ce "Shi kenan Babanmu! Allah ya kara maka lafiya da nisan kwana, yadda a ke mini habaicin tunda aka haife ni ka tsiyace, ina ro'kon Ubangiji kullum, ya saka idan na girma na samu sanadin da arzikinka zai dawo ta dalilina fiye da wadda ka rasa a shekarar da na iso duniya". Ya ce "Rabu da maganar jahilai, ko iya hakan na ga ni ai na gode, sanadin sana'arki na daina fargabar a tambaye ni ku'din sabulu a gidana. Alherin da kika janyo mini mai yawa ne, mafi farin-ciki a ciki shine wanda kike yarda ya'yan da na haifa duka daya ne a wajenki ta fuskantar mua'amala ta zahiri." Da'di ya tsirga mini ban ta'ba zaton Baba ya fahimci yadda nake da ra'ayin rikau akan kannena ba, bansan ya fahimci ina tare musu fa'da ba, hakanan ban san hakan yana yi masa da'di ba, tunda kullum a cikin kirarin bani da hakuri yake. Sannan kuma baya ta'ba nuna mini ina abin a yaba, sai dai ya ce ai duka yan'uwane tunda ragowar ma y'ay'ansa ne da yan'uwansa suka haifa masa. Cikin son na sake k'arfafa nasa guiwa na ce "Duk d'an da ka haifa ina jin sonsa har cikin zuciyata Baba". Idonsa ya ciko da k'wallah cikin k'arfin hali ya ce "Allah ka shirya mini yarana, ka saukaka musu, ka basu lafiya, ka cika zuciyarsu da tsoronka, ka jefa soyayya da tausayin juna a tsakaninsu. Allah ya yi miki albarka Yabi". Daga ni har Gwaggo muka hau fa'din "Ameen ameen". Na kalli Gwaggo na ga hawaye ya goce mata, jikina ya sake yin sanyi, domin ita din wata irin mace ce mai k'arfin zuciya k'warai da gaske, abin da zai saka ta yi kuka to kuwa ya girgiza ta ba ka'dan ba, duk tsananin da take fuskanta a rayuwar gidanmu ban ta'ba ganin ta yi kuka ba. Na yi kasa da kaina cikin rauni mai yawa na ce "Ameen Baba! Allah ya kara maka lafiya da nisan kwana mai albarka. Na gode sosai". Duk muka yi shiru kowa na cikin alhini. A hakan Nazira ta fito rai a bace da gani Mama sababin yadda ta like mini ta yi mata. Kusa da ni ta zauna, cikin sanyin murya ta ce "Sannu Baba". Murya ba amo ya ce "Sannu kadai Nazira, Allah ya kara miki ha'kuri kin ji. Ki cigaba da jajirce wa a kan gaskiya ko da hakan ya ci karo da ra'ayin kowa, ku so junanku, ku binne a tsakaninku, kin fi Yabi ha'kuri, a duk sadda kika ga zata yi aikin nadama yi amfani da fikon da kika yi mata ki dakatar da ita, komin runtsi kada ki bari ta dauki hukunci cikin fishi. Ke kuma Yabi kul kika ki jin shawararta, idan ta ce yi ha'kuri, to na roki ki bar abin nan komin girmansa. Ina jaddada muku ne dan ku ri'ke su da kyau, ko babu ni idan kuka ri'ke maganganuna ba zaku ta'be ba. Allah ya yi muku albarka ya ha'da ku da maza na gari, ya raba ku da sharrin shaidan a cikin zumunta". Muka amsa da Ameen amen cikin sanyin jiki. Nazira ta mika hannu ta karb'i Maficin hannun Gwaggo ta cigaba da yi masa fifita, duk da gumin ya yi sau'ki. Har lokacin kuma bai saki hannuna ba. Ya jima kafin ya saki hannuna yana sake cewa "Na hore ki da ha'kuri Yabi! Ku zauna da yan'uwana lafiya, ku mutunta su, ku gaishe su da girmama wa". Na gyada kai yayin da Nazira ta ce "Duk yadda kake so hakan zamu yi, amma ka taimake mu ka daina sanya damuwa a ranka Baba! Fatanamu mu ganka a tsaye akan kafafuwanka, idan muna ganinka cikin walwala ba abin da zai dame mu sosai." Haka muka kwanta ni da Nazira tana ta jan kunnena na kiyayi Dada, tunda zata iya yin ha'din kitifo har ya zama sanadin da za'a samu damar cin zarafin Babanmu akan idonmu. Tun daga wannan ranar na kame bakina a gaban Dada, duk karatun da zata yi bana tankawa, haka nan ban cika zama na yi doguwar magana da ita ba. Zanje gaishe ta babu fashi, kuma sai na tabbatar mun ha'da ido sannan zan kama sunanta na gaishe ta. Na daina jan magana a tsakaninmu ne kawai. Sannan na soke zuwa hirar dare, amma matu'kar zata d'ora karatu sai ta sa an kira ni. Janye war da na yi da ita kuma sai ya dame ta, amma ta kasa bu'de baki ta yi magana. Tunda Nazira ma ba wani sake wa take yi ba, balle ta yi mata korafi. *** Karshen wata Yaya J ya dawo. Mun taso daga Islamiya muka ganshi zaune akan dandamalin kofar gidanmu. Sanye yake cikin kananun Kaya da suka yi matu'kar kar'barsa, sai kamshin turaren Dagmar yake tashi sannu a hankali. Dukkan y'anmatan suka hau rige-rigen gaishe shi, yayin da ni na sunkuyar da kai kasa alamun kunya. Na zo wucewa ta gefensa na saci kallonsa ai kuwa karaf muka hada ido, wani irin abu ya tsikare ni, kwalliya da tsabtar Yaya J ko mace ce ta kai a sata a masu tsabta, sannan kankantarsa tana sawa na ji mun dace da juna. Domin da ka'dan ya zarta ni cika ido da tsayi. Babban abin burgewa mai nutsuwa ne, sannan mai ha'kuri ne, bashi da hayaniya ko ka'dan. Da sauri na janye idon nawa, murmushi yana subuce mini wanda ban shirya yinsa ba, na tsananin shauki ne. Na wuce ba tare da na yi gaisuwar ba. Cikin raha ya ce "Nasiba ki koya wa Asiyan Toro gaisuwa tunda ta zama bak'auya". Da dariya ta ce "Yaya Jabir kaine da fa'din Asiyan Toro yau? Babu ruwana a shirginka da Yabi". Ya k'yal-k'yale da dariya ya ce "Tsoron ta kike ji ne Nasiba? Kin fita tirinya fa, to kuma ya za'a yi ne tunda ku biyu zan ha'da na aure rana guda?". Ta yi maza ta ce "Lallai kuwa ka shiryawa darun Yabi domin har ka tafi ba zata saurare ka ba, ni kuma ba zan taya ka rarrashi ba". Ta wuce ni da sauri ta shige shashin Dada. Ni kuma na wuce shashinmu a dalilin yau Nazira ba ta samu damar zuwa ba, saboda tana fama da ciwon mara. Zuciyata har wani tukiki take yi na tsananin bacin ran kalaman Yaya J. Wai zai ha'da ni da Nasiba ya aura. Na yi tsuka na ce "Sai dai ya aureta ita ka'dai. Dama na san dunbula dunbulan kirjinta na iya tafiya da shi, ba'kin ciki ya sake turnike ni a dalilin ni ba mai cikar k'irji ba ce. Har yanzu bana saka breziya sai dai half best, domin a manne suke a kirjina yan kananu da kadan suka fi tsakuwa. Amma Nazira da Nasiba kam kirjinsu a cike yake sosai. Wataran har rayawa nake yi ko dai na fara shan ruwan baru ne ko zan yi sa'a su fito su cika mini kirji ni ma. Amma sai na kasa, mussaman da sai na ro'ko ruwan kuma sai nake ganin kamar za'a gane dalilin shan da zan yi. Da daddare ya dinga aiken na zo amma na yi mirsisi na ki fita. Washagari a zauren Dada na tarar da shi. Na sani sammakon tashi ya yi dan ya hadu da ni. Domin shi ba ma'abocin tashi sassafe bane, da zarar ya dawo daga sallar asubahi idan ya kwanta sai tara yake tashi. Nazira ta gaishe shi ta shige, yayin da na dauke kai fuska murtuk zan wuce shi. Ya yi maza ya sha gabana yana fa'din "Haba Yabin J baki san wasa ba ne? Na yi bakam tamkar dai ban fahimci da ni yake magana ba. Na yi kasa da kaina. Ya sassauta murya ya ce "Yanzu Ashe zaki iya mini irin wannan fishin Yabi?" Na dago na kalla shi na ce "Oh wai ka yi zaton ba zan iya ba? To kuwa ka dauka zan yi maka fiye da hakan domin zan iya shafe babinka gaba'daya." Ya jima yana kallona cikin ki'dima. Ya yi k'arfin halin cewa "Me ya yi zafi haka, daga wasa?" Na sake d'aure fuska na ce "Bansan wasa ba, ban iya shi ba, ban kuma ta'ba daukan al'amarinka a matsayin wasa ba, bare har na yi maka tsokanar da zaka ji ka tozarta". "Hakane, na kuma gasgata ki, yanzu ki yi ha'kuri ba zan sake miki irin hakan ba kin ji". Na jijjiga kaina tare da yin wata irin shakiyar dariya na ce "Ha'kurin ma ban iya shi ba. Ba kuma zan koyo shi a dalilin cin fuskar da aka yi mini ba. Na riga na barwa Nasiba kai, dan haka ka manta da wata Yabin Marina". Ya yi tsam cikin kaduwa wata'kila yana mamakin yadda kishi yake kutsowa tunda ga kasan zuciyata ne, kallon yarinya k'arama yake yi mini, sai dai bai san yar shekaru goma ma zata yi kishin abin da take so ba, bare ni da nake da shekaru sha sha biyar, na ke harun sha shida. Ya lankwashe murya cikin rarrashi ya ce "Ai na yi zaton ina da wata alfarma ta daban a wajen ki, ban ta'ba zaton zan yi miki laifin da zaki shafe ni a zuciyar ki ba. Yau dai daya tak da na sab'a miki, ki daure ki mini uzziri, ni kuma na yi al'kawarin ba zaki sake kama ni da laifi irin wannan ba". Na dauke kai na ce "To idan na yi ha'kuri na ce maka komai ya wuce, ya zan yi da tafasar da zuciyata take yi idan na ga Nasiba? Ya zan yi na goge amincin da zuciyata ta yi akan ita kake so bani ba, tunda ita din ta fini zama y'anmata?" Tsananin mamakin da na ba shi ya sanya ya kasa magana na tsawon lokaci. Sai da ya jima kafin ya numfasa ya ce "Ni fa ba wacce take burgeni nan duniya idan ba Yabin Marina ba. Kinsan dai ina tsokanar Nasiba tun fil'azal tunda abokiyar wasanmu ce, yar mace da dan namiji muke. A kaikaice na ce "Oh oh, ashe dama ana wasa har irin haka? To kuma wai ya matsayin wannan *Bak'ar Ta'adar* a shari'a tunda ba'a wasa da maganar aure?" Ya dan tunzura ka'dan ya ce "Ke Yabi". Nima na ce "Ke Yabi ko kuma ke gaskiyar magana?" Ya girgiza kai ya ce "Shi kenan na gode, na gode sosai da yadda kika ajiye ni". Ya fice ya bar ni, kafin na shiga wajen Dada Bulkachuwa ya fito daga dakinsa. Ya yi fitoh irin na tantiran yan-iska ya kalle ni ya ce "Asiya Toro rikakkiyar budurwa". Ya kwashe da dariyar iyashege ko me ya tuna kuma sai ya gintse dariyar tasa. A fili ya ce "Ban da ma shan koko d'aukar rai ne, ta yaya kamar Jabir da yake ganin Bigger babes zai tsaya wajen kwailaye irin Asiya Toro? Ya wuce yana sake fa'din " Soyayya da kananun yara menene a cikinsa ban da raini da ba'kinciki, yar yarinyar da bata gama iya wanka ba ma sai ta caccaba maka magana son ranta, abin ba'kinciki kuma dole ka rarrasheta ko ka hadu da gallazawar zuciya." *Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame* *Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea* *Akwai pop corn* *07036662633* Na yi kwafa a dalilin yadda furucinsa suka sake sawa na washe shi. A dole na shiga ciki na gaida Dada. Ina kallon yadda Nasiba take rawar jikin zuba masa ruwa a buta, dan ya yi brush. A raina na ce wannan fa shine shan kokon. Sai da ta gama barebaren yi masa hidima sannan muka fito muka wuce makaranta. Gaba'daya wannan zuwan na Yaya J ban yarda mun shirya ba, haka ya koma Jos. Ni kuma ina k'arfafawa kaina gwara mini Abdulrashid kamar yadda Gwaggo take so, domin ni da kaina ban san waya fi sona a tsakaninsu ba. Sai dai me? Juma'a da maghariba muna tsakar gidanmu sai jin ihun yara muka yi suna "Oyoyo Yaya Jabir, oyoyo". Nazira ta ce "wannan dawowar taki ce Yabi. Na ro'ke ki huce hakanan ai ya garu". Na tabe baki na ce "Rabu da shi, nifa dama ina ta neman hanyar da zan yakice shi a raina, ki ga fa irin yadda Baban Tsakiya ya yi wa Baban Marina, akan idonmu". Ta fesar da iskar takaici ta ce "Amma Baban ya ce ba ruwanmu da kasafinsa da yan'uwansa, a gabanki ya tabbatar bamu fi yan'uwansa a gunsa ba. Aure ai kaddara da rabo ne Yabi. Ban da haka da wani namijin bai isa auren wacce yake aure ba, sai kaddara ta ba shi, haka nan wata macen bata isa mijinta ya kalle ta da nufin soyayya ba, amma saboda karfin kaddara da rabo sai kiga ta zame masa mata kuma uwar ya'yansa. Matu'kar Yaya Jabir mijinki ne, sai kaddara ta sanya aurenku ya yiwu komin k'in da iyayensa zasu yiwa al'amarin. Mu da muka yi sa'a ma dukkan iyayenmu suna da ransu, kullum kuma suna roka mana mu dace da maza na gari, na yi imanin Ubangiji ba zai juyar da addu'arsu ba, hakan kuma ba zai hana mu ga kalubale a cikin ko wanne zabi ba, domin sunnar rayuwa ce komai na da irin nasa cikas din, sai dai albarkacin addu'ar iyaye sai ki ga komai ya saukaka. Jikina ya yi sanyi, na kasa bu'de baki na ce komai. Ta ru'ko hannuna sosai ta ce "Ki yi ha'kuri kin ji Uktina". Na nisa na ce "Na yi ha'kuri saboda ke, amma ki fa'da masa bana son irin wannan wasan, bana so". Cikin jin da'din na yarda da maganarta ta ce "Madallah da K'anwata kuma kawata YABIN J". Na murmusa a raina kuma sai addu'a nake yi mata ita ma Ubangiji ya kawo mata saurayin da zan taya ta sonsa, domin hatta Abdulrashid da ba wani sonsa take yi ba, bata ta'ba kushe shi ba, illah iyaka tafi son Yaya J. Idan ina yi mata d'an bikin ita bakin ganga ce, domin a gabansa bata ta'ba nuna masa akwai wanda take supporting sama da shi. Sai ta murmusa ta ce "Tunda har zuciyar Yabina tana dan sonsa ai kuwa yafi karfin na wula'kanta shi, baya ga haka son ki yake yi, dan haka nake girmama shi. Amma ai bazan so shi na bar Yaya J ba domin yafi shi cancantar ya same ki". Bata ta'ba nuna k'yashi ko takaicin ina da samari ita bata da su ba, duk da ta fini zama cikakkiyar budurwa. Ni da kaina na sani Nazira tana cikin Yan ka'dan da Ubangiji ya wanke musu zuciya akan k'yashi. Allah kenan! Sarkin hikima sai ya bawa bak'ar uwa karimi ko karimar yarinyar da za'a yi ta yi mata alfarma saboda kunyarsu. Hakan ce ta kasance domin sau tari sai na yi yun'kurin yiwa Mama iyashege irin ta dan yau dan ta fahimci dan Babanmu da Gwaggo suna shayinta, tunda laya ce ita, ni kuma mai zamani ce dole kuwa ta kiyaye ni. Nauyin Nazira ka'dai yake sawa nake hadiyar dukkan matsatsin da take sanyamu. Domin na riga na ajiye alakar matar Babana ce tunda bata ta'ba yi mini karar ni din y'arta ce ko ta mijinta ba. Ana idar da sallar isha ya aiko na je. Yana jingine jikin katanga hannuwansa biyu a kirjinsa, sanye cikin shadda shud'iya kalar sararin samaniya. Sai kamshi yake yi. Na rakube gefe guda ba tare da na ce kanzil ba. Ya matso kusa da inda nake ya ce "Assalamu alaikum Yabi". Murya babu amo na ce "Wa'alaika Salam". Ya ce "ki yi ha'kuri, na yi kuskure, tunda na gane da gaske ba kya son irin wannan wasan bazan sake yi miki ba shi kenan?". Na yi kasa da kaina, ba tare da na ce komai ba. Ya numfasa ya ce "Kin yi shiru". Cikin yauki domin da k'yar na ce "Ya wuce". Ya murmusa ya ce "Yabina sarkin ginshira, da rikici". Na kawar da fuskata gefe ban ce uffan ba. Ya dan damu ya fara fa'din "Kin ce "Ya wuce amma kin k'i sakar mini fuska, saboda ke fa na dawo". Fuska ba walwala na ce "Ya wuce mana, mantawa ai sai a hankali, yo ban da ma dai ina ganin mutuncin ka ai da an rabu ke nan, ina ruwana da duk wanda zai nuna mini yana son wata dan ta fini tirinya". Ya kame baki alamun mamakina. Tsawon shudewar mintina sannan ya iya ce wa "Yabin Marina ho". Na sake tsuke fuska. Murya ba amo ya ce "Ba tone tone zamu yi ba, ai kin gama magana tunda na yi sa'a kina ganin mutuncina. Na gode miki da wannan karamcin, ina son ki fiye da komai". Ya lankwashe murya ya ce "Mutunci da soyayya idan suka hadu fa'din irin al'amuran da zasu haifar na nutsuwa ma bata lokaci ne Yabin J".   *Annur food Delicious* *Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.* *Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa* *HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna* *Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya* *08039183880* ✍️ *BAK'AR TA'ADA* *NA* *SURAYYA DAHIRU GWARAM* *(MRS M.I.NASHE)*. *Marubuciyar* *Halin Yau* *Sabo da kaza*. •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI* *IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*. *SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI* *AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN* *AKWIA PACKAGE DIN AMARYA* *AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO* *AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*. *AKWAI GORAN TULA SYRUP* *AKWAI GORAN TULA FRUIT* *INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA* *MASU SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332* *DAN ALLAH SERIOUS BUYER'S ONLY*. *Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko kuma kina sha'awar yin register da su. Ki tuntubi babbar dealer din su Aisha lame* *Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea* *Akwai pop corn mai kore dukkan kwadayi*. *07036662633* https://arewabooks.com/chapter?id=64ff47e14ba2e11c69ef3f2f 9&10. Na sunkuyar da kaina k'asa alamun kunya, gane hakan da ya yi, sai ya mayar da hankalinsa wajen kwarzanta ni, tare da maganganun masu taushi da nuna kurewar matsayin mutum. A hakan har ya samu na dawo masa Yabin J bata Marina marar ragayya idan an tabo ta ba. Domin sai da kunyarsa da nake ji ta dawo, walwalar da fuskata take yi idan ina gabansa ta dawo. Hakanan shaukin da zuciyata take yi ya bayyana. Sai goma saura ya tafi bayan ya bani ledar atile da kuma turare, wannan karon har da takalmi mai kyau. Ina shiga gidan na ci burki a dalilin maganganun da suka ja hankalina. Muryar Mama nake ji daga dakinta tana cewa "Da gangan kake zuba mata ido take yin yadda ta ga dama. Jiyan nan yarinyar nan ta muzanta gyatumarka, amma tana shigowa ka bita da addu'ar da ban ta'ba jin ka yiwa wata cikin manyan ya'yanka ba. Ba wacce ta samu lasisin tara samari a gidan nan sai Yabi, nan Indo ta yi farinjii fiye da nata, sai ka fititke akan sai dai ta zabi guda daya, amma wannan da yake y'ar tijara ce ka barta ta zamo wa uwarta haja, dan kuwa nasan baka samun abin da take roro musu. Saboda ba'kin cikin kada wasu su ci. Yau Jabir ya kawo musu, jibi Audurashid, gata malamin makarantarsu". A hankali na ji muryar Baba yana ce wa "D'a ai mallakin uwarsa ne Habiba, duk abin da uwa ta ci ko ta samu a sanadin y'ay'anta bai zama abin a yi magana a kansa ba domin ta cancanci dukkan sadaukarwa daga wajensu. Ban da Dada da take da ra'ayin auren wuri wai duka nawa ma suke ne? Inda za'a bar ni da ra'ayina kamar yadda ake barina da hidimarsu da ba wacce zan aurar sai ta kammala sakandire bare Yabi mai karamin jiki ce". Ta harzuka ta ce "Waton ba zaka dai dakatar da su, ka bar guda daya ba ko? Wai yaushe ka zama mai son zuciya ne haka? Jikina ya yi sanyi da irin amsar da ya bata. Ya ce "Kinsan talauci ba abin da baya sawa, bana haufin shine ya mayar da ni mai son zuciyar, kamar yadda kika mayar da ni banza ko wacce magana zaki fada mini babu fargaba. Kin ta'ba jin na yi magana akan yadda yaranki ke ka'dai suke nufa da tallafinsu, ai saboda nasan uwa mafi uba ce ko da kuwa uban sarki ne". Ban sake jin harshenta ba, na wuce a raina ina ta murnar Babanmu ya fara gwada k'arfin halin taka mata burki, duk da a yanzu ma babu garantin ba zai lallabata ba. Domin ta riga ta jarraba shi ainun. Washagari asabar da wuri na tashi na ha'da kayan wankin dakinmu gaba'daya. Na aiki Anas ya siyo mini sabulu da omo tun daren jiya dama. Na fara wanki, yayin da shi kuma yake janyo mini ruwa a rijiyar bayan shashinmu. Kafin karfe takwas din safe na kammala na shanya su reras. Tuni kuma Inna ta kammala abin karin kumallo. Na karbo mana namu dumamen tuwon da Nazira, ga kuma kokon a jug da kullum Gwaggo sai ta bawa duk wanda yake son sha a gidan. Kusan kullum sai na tambayi ko ribar nawa take samu? Yadda bana gajiya da tambayar itama bata gajiyawa wajen cemin "Wanda ake sha ne ribata". A duk sadda ta fa'di hakan ban cika fahimtar rufin asiri ba ne sai kawai na kalli ita din mace ce mai yin hidima a inda ba'a ganin darajarta. Kafin Nazira ta gama wanke baki na k'osa domin indai na yi wanki to bani da jarumtar ri'ke yunwa sai na ji tamkar an mini yasa a cikina. Ta tarar tuni na fara cin tuwon. Ta zauna tana fa'din "Yabi sark'a, yanzu da ni ce na fara ci ban jira ki ba, sai kowa ya ji kwakwazon ki" Na rausayar da kai tare da fa'din Ayyah Addah Nazi kinsan bana shiri da yunwa ko kadan. Muna karyawa ina bata labarin yadda ta kaya a tsakaninmu da Yaya J. Ta murmusa ta ce "Yabi duniya! Yanzu Yaya Jabir din ma ba zaki dinga raga masa ba? Na dan daure fuska na ce "Ai matu'kar zai tsokano ni tabbas zan ajiye komai na yamutsa shi inta kama a rabu ma shi kenan. Ba zan dauki wula'kanci ba ko ka'dan. Ta girgiza kai tare da cewa"Allah ka shirya mini Yabina". Dai dai lokacin Baba ya fito da nufin fita. Muka gaishe shi ya amsa yana cewa Nazira da Asiya albarka ta kewaye mini ku". Cikin farin-ciki mai yawa muke fa'din ameen Babanmu". Amma sai na sake cewa "Babanmu Asiya fah?" Ya murmusa ya ce " Ho Yabi! Da ikon Allah sai kun sauke farali daga ke har y'ar-uwarki. Sai kin zama Hajiyar ta sosai". Cikin karadi na ce "Ai kuwa dai Babanmu "Dawafi na mussaman zamu yi maka!" Ya fice yana dariya. Babanmu wani irin uba ne da yake wasa da raha a tsakaninsa da y'a'yansa, babbar matsalarsa kawai Mama ce, domin yanzun nan sai ta saka ya ci mutuncinka ko na uwarka akan idonka dan ma an yi sa'a abin ya dan fara sau'ki, na sani kuma karfin addu'ar da muke yi ne mu da Gwaggo". Kwanaki suna ta shude wa har muka yi jarabawar zangon karatu na uku. Muna tafe kowa da sakamakonsa a hannunsa, Nasiba da su Firdausi sai murna suke yi a dalilin sakamakonsu ya yi kyau. Nazira ma babu laifi domin ta sha biyu ta zo. Amma ni kam sakamakona ba zai nunu ba domin kuwa ta arba'in da takwas na zo a cikin mu hamsin da bakwai. Kowa ya nuna sakamakonsa a tsakaninmu. Amma ni na boye nawa kamar yadda na saba. Muna tafe Maijidda sai fa'di take "Akan me za ki dinga ganin results dinmu amma ke ba zaki yarda a ga na ki ba?" Na gallah mata harara na ce "Saboda mahaifina bai fara gani ba, ba kuwa wanda yafi cancantar ya fara gani sai shi". Ta tunzura ta ce "Kins an Allah yau sai na ga ni, ai na sani ta karshen aji kike yi. Ban da class master din ajin naku saurayinki ne ai demotion ne ya kamace ki Asiya". Na fusata kwarai da gaske na ce "Tabdi jam! Yabi kika je fa wa wannan maganar?" Ba shakka ta ce "An fa'da miki Asiya. Kin dauka ina jin tsoron ki ne? Idan ba jakar aji kika dauka ba to miko mini sakamakon ki kamar yadda na baki nawa kika ga ni". Na girgiza kai da tare da yin k'wafa mai tsananin gaske. Nazira kuwa sai fa'di take "ba ruwanki da al'amarin Yabi fa Maijidda". Ta ce "Na shiga komai zata yi, ta yi ina daidai da ita". Ban ce komai ba sai da muka isa zauren Gidanmu ba zato na shake Maijidda da dukkan k'arfina, ina kai mata duka ko ta ina. Kafin ta yi yun'kurin ramawa na jibge ta sosai, sannan kuma muka ci gaba da gwabza wa. Aka rasa mai rabamu domin duk wacce ta ta'ba ni kanta fa'dan zai koma sun san haka dabi'ata take. Nazira sau fa'di take Yabi sake ta, amma bata ri'ke ni ba, domin ta san ce wa zan yi bata taya ni fa'da, ta taimake ni ba tunda bata kishina, akan me zata ri'ke ni? Na turmushe ta ke nan na debo k'asa ina shirin cika mata bakin da ya yi mini izgilanci sai ga Bulkachuwa ya shigo. Ya hau fa'din ke Asiya Toro wanne irin abu kike yi haka ne?" Ganin na fara kokarin danna mata a baki ya sanya shi iso wa garemu, bai jira komai ba ya saka hannunwan sa ya cira ni cak kamar y'ar tsana ya yi wurgi da ni. Na yi sa'a na dire akan sayyadata. Da yake a hassale nake sai na durfafe shi ina cewa "To kai ma din ai ba tsoronka nake ji ba, ka zo ka zaune mana a gida ka uzzira mana haba.?" Na kalli yadda ya harzuka amma ko gezau ban yi ba, duk da ban fi iya cikinsa ba. Ya kalli Nazira ya ce "Me ya ha'da su?" Ta tsara masa yadda aka yi ba ragi babu kari. Ya juya ga Maijidda da take hawaye ga jini a hancinta tabbacin habo ne ya goce. Ya ce "Dube ki gansamemiya da ke amma wannan y'ar tsakon ta lallasaki haka, wanne irin mutuwar zuciya ce ta same ki?" Na galla masa harara tare da murguda baki na ce "To ni komin girman gardi ma ba zai hana na zubar masa da jini ba, bare kuma mace yar-uwata". Ya nuna kansa ya ce "Asiya Toro ni kike tunanin zaki buga?". Na ce "Ba dan ha'da jiki da kai sai ballagazaye ba, ba abin da zai hana na zage mu gwabza y'ar k'ashi Wallahi". Ya nuna ni da yatsa ya ce "Asiya Billahillazi zan sumar da ke, yar iska marar mutunci kawai.". Yana rufe baki na ce "Ga ka nan babban dan-iska mai shiga fa'dan mata, yabi bayan wacce take da abin da zai lallaba ya cuce ta." Ya yo kaina yana fa'din ashe "Izgilancinki mai girma ne haka?" Ga mamakinsa sai kawai na yi shirin kai masa naushi tamkar bacaniya. Wannan dunukule hannu da saitin da na yi, ya yi matu'kar bashi dariya da tu'ajjibin k'arfi halina. Ya tsaya ya ce dambe zaki yi da ni? Na ce "Allah suturu bu'kui na yi dambe da mai daudar zunubi irin ka, kuma ni ba ballagaza ba ce, kawai zan kare kaina ne daga cutarwar ka". Ya jima bai ce komai sai ya kalle ni ya ce "shahsa da bata iya komai ba, sai fa'da da rashin kunya a aji kuwa ita ce dalkiya". Ba'kin ciki ya mamaye ni, idona ya ciko da hawayen takaici na ce "Na gode wa Allah da na yarda ina zuwa makarantar, wani ma tsabar akuyanci korarsa aka yi daga karatun nasa. Me za'a yi da mai halin bunsuru?" Ya rasa yadda zai yi da ni sai kawai ya shammace ni ya dauke jakata yi wuf ya zaro takardar sakamakon da take a farko farko. Ya juya zuwa waje ya bu'de ya ga yadda jan biro suke mamaye sakamakon. A karshe ya ga ta yadda na zo sannan ya mayar ya shigo ya kalli yadda na tumbatsa ya ce "Anya Asiya ba dusa kike ci ba kuwa? Ace har kin doshi hamsin? Gaskiya ina taya Baba ba'kin cikin asarar ku'din taran da ya wanzu yana baki". Cikin rawar murya na ce "Bulkachuwa Yadda ka tozarta ni a gaban wanda suke son na tozarta in sha Allah sai an tozarta budurwarka fiye da yadda ka mini, da ikon Ubangiji sai ka ha'du da sharrin mace, sai ka muzanta a idon duniya". Ya make kafa'da alamun ko a jikinsa tare da cewa "Yabi yanga mai kwakwalwar kifi". Ganin hakan ya sanya Maijidda ta mike tana jin karfi yana shigar ta tunda ta ji abin da take son ji. Ta mini gwalo tare da cewa "Na ji dai, dama nasan baki tsinana komai ba". Ta shige wajen Dada da saurin ta. Yayin da ragowar suke fa'din "Yi ha'kuri Yabi, ai kin nuna mata ruwa ba sa'an kwando bane. Ba gashi ta tsere ba". Na jijjiga kai na ce "Ai dan ta ga Bulkachuwa ya tsaya mata ne". Yayin da shi kuma ya ce "Ba dole na tsaya mata ba, tunda ke din karfinki na aljanu ne, na tabbatar ba ke ka'dai kike fa'da ba, kina samun tallafin aljani mai kilabo da gwaigwai". Duk wajen aka fashe da dariya illah ni dana sake fusata na daga murya "Ina ce wa "Allah ka dora wa matar Bulkachuwa aljanun da zata dinga daga shi sama tana danfara shi da k'asa". Ya wuce yana fa'din "Duk bala'in aljani ba zai shigo mini gida ba, domin hafiza zan aura mai hazakar gaske a ilimin boko da na addini. Safiya da marairaice ta yi ta tofe mini gidan da azkhar, idan kin ga aljanu sun yi tasiri, sai a gidan wanda basa mayar da kai a wajen bautar Allah irin ki". Na wuce shi zuwa shashin Dada. Na tarar da Maijidda tana ta kuka yayin da Dada take sakacen hakori da tsinken zabori hankalinta a kwance. Na bu'de baki na ce "Dada sannu da gida, mun dawo". Ta amsa ba alamun damuwa a tare da ita. Na juya na tafi sai na ji kukan Maijidda ya karu tana cewa "Kin bar ta tafi baki bi mini kadina ba?" Na yi tsam dan na jiyo amsar Dada. Kamar ba zata tanka ba sai kuma na ji tana ce wa "Na k'i na yi mata maganar. Yar kankanuwa a gabanki, sannan kin bata kwanaki arba'in cif amma kin kasa kwatar kanki a hannunta sannan dan asaranci ki ce na tare miki fa'da? Ai kinsan fa'dan ta baya mutuwa akan me zaki tsokano abin da yafi karfinki?" Maijidda da bata yi zaton haka Dada zata ce ba, domin mun saba yin fa'da da yan k'ofarsu ta basu gaskiya ko da kuwa ni ce mai gaskiya. Dada ta ja tsaki ta ce "Sadda nake cikin shekarun kuruciyata haka nake nima duk girman mace bata bani tsoro, haka nan duk wanda ya mini kan ice sai na yi masa na kara. Sai yanzu na fahimci wannan tijarar ta Yabi sawuna ta biyo domin komin sharrin mai sharri ba zai ce ubanta mafadaci ba ne ko kuma uwarta. Dukkan iyayenta sanyin kalau ne, dan kuwa inta sune kiyama ba zata tsaya ba." Kukan Maijidda ya tsananta ta dinga yi tana ce wa "Ai dai kinsan bata isa ta kai ni k'asa ba, dunbular mini kirji ta yi ta yakushe ni a wajen." Salati Dada ta dauka tana cewa "Ikon Rabbani, tarihi na maimaita kansa ni Fadimatu. Wallahi Maijidda sadda aka mini auren fari ina kankanuwa aka kai ni babban gida, matar wan miji ta saka ni a gaba, duka, kyara zagi. Har na fara girma a cikin fargabar wannan baiwar Allah na ke. Ai kuwa da tura ta kai bango na fara rama abin da take yi mini. Har muka kai jallin da muka fara dokuwa, sai dai kashi take bani da yake ta fini sosai, ai sai kawai nake fakar ido idan muna damben ina mintsinin nonuwanta ko na na cije su. Shi kenan na yi maganin gallazawarta, ta shiga kiyayata. Yau ga Magajiyata na samu a haulata". Ta fa'da tana tafa hannu tana sake jan salati. Na wuce ina son yin dariya amma ba'kin cikin Bulkachuwa ya dabaibaye ni. Na wuce shashinmu ina jaddada wa kaina ko a gaban Baban kasuwa ne Maijidda ta tsokano ni sai mun sake cire raini, bare Dada. Bamu jima da dawowa ba sai ga mahaifiyar Maijidda da kanta ta kawo togaciya. Fadi take "Tura ta kai bango kullum Yabi sai ta yi mini sanadin bacin rai jiyan nan ma sai da ta dakar mini Kaltume akan sun samu sabani da Ismail, akan me zata tisa mini yara a gaba irin haka?" Ha'kuri kawai Gwaggo take ta bata, Inna da ta rage tsananta gaba da ni a dalilin ina yiwa yaranta hidima tamkar yan dakinmu, sannan ba mai tab'asu a waje matu'kar ina wajen sai hakan yayi tasiri, ta rage daukar zugar Mama. Dan haka sai ta ce "Ban da ke ma Abu da shiga shirgin yara ina ce Maijidda ta girmi Yabi ne? Sannan idan kinsa ha'kuri anjima ka'dan zaki iya ganinsu tare". Nan da na ta harzuka ta ce "To Yabi ni kaina ai sai ta dake ni tunda fa'dan yan-iska take yi, ban da dai ta riga ta rik'a ta yaya zata dinga dumbular kirjin y'anmata, tabbas dayan biyu ne, ko dai niyyar kisa take yi ko kuma ta shiga sahun masu *Bak'ar Ta'adar* neman mata." *Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko kuma kina sha'awar yin register da su. Ki tuntubi babbar dealer din su Aisha lame* *Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea* *Akwai pop corn mai kore dukkan kwadayi*. *07036662633*. Gwaggo ta ce "Dutse a tsakaninmu da duk masu wannan al'amarin, muna neman tsarin Allah da su, muna kuma nema musu shiriyarsa." Ta ce "ASMA'U Wallahi kin siffatu da agwagwa, ace wai baki isa ki sarrafa y'ar cikinki ba, ta gallabi kowa a gidan amma ba k'ya yi mata fa'da, saboda tana samun ku'di shiyasa ta gagareku? Sai ayi ta fankamar ku'din kitso da na lalle ne, alhalin munsan samarin da suke mata layi ne suke bata. Wallahi idan ba sa'a kika yi ba sai Yabi ta hana ki shan ruwa kamar yadda ta fitine mu". Na fito na ce "Umma ya isa haka nan, ba zai yiwu fa kizo k'ofarmu ki zagi Gwaggo ba". Ta mini dakuwa ta ce gidanku tabbataciyar yarinya marar albarka". Tana rufe baki na ce "yarinya tana bayan uwarta Wallahi, albarka kuwa da ikon Ubangiji sai na yi ta". Gwaggo ta yo kaina na ki guduwa tasan kuma matu'kar ta kawo mini duka ban gudu ba, na riga na shiga yanayin da nake bu'katar a kashe ni kawai na huta. Inna ta yi maza ta karbe itacen hannun Gwaggo tana fa'din "Wannan ai sai ki sabauta ta". Yayin da Umma Abu ta juya tana fa'din "Zaman babban gida ko masifa, ba dama a ganka da haske sai an tisa ka a gaba da ba'kin ciki da hassada tamkar dai kai ofne ka tare wa mutum nasa arzikin". Tana fita Gwaggo ta kalli inda nake a tsaye kik'am tana fa'din "Kin ji da'di ai da wannan wula'kancin da kika janyo mana". Ban ce komai ba, sannan kuma ban ji a raina cewar zan koyi ha'kurin dole idan an ta'ba ni ba. Wannan rikicin yana cikin al'amura masu tsananin gaske da ya faru. Domin da daddare babu kunya bare kawaici Baban kasuwa ya gurfanar da mahaifina a gaban Dada yana ta sababin ya gaji da yadda na takura wa ya'yansa amma ubana ya kasa tsawatarwa. Da yake Dada bata iya tsallake umarninsa sai kuwa tabi bayansa. Ta dinga fa'din ai tsoron zuciyata yake yi. Cikin rishin kuka Baban kasuwa ya ce "Ki gafarce ni Dada! Wani satin zan koma gidana dana kammala gina wa tun bara, amma na kasa tashi saboda ke, to yanzu kam zan tashi na gaji da wannan masifar Wallahi". Dada ta ce "Wallahi ko ubanta ba zai tashe ka ba tunda matsayinku guda a cikin gidan bare kuma ita. Share hawayenka ita ce zata bar mini gidan". Na sake kasa kunne domin tunda aka aiko cewar Babanmu ya zo in ji Dada nasan karata za'a kai sai na bi bayansa ba tare da yasan ina binsa ba. Na makale a soron Dada ina addu'ar kada Allah ya kawo Bulkachuwa tunda dakinsa a cikin soron yake. Ta ce "ka fa'dawa Yabi ta tsayar da miji da dukkan yaran ma. Na umarce ku, ku aurar da su nan da watanni biyu". Baban kasuwa ya ce "Shi kenan" Ya fice ya barta da Babanmu." Ganin zai fito ya gan ni sai na yi maza na fice daga soron na tsaya a bakin k'ofar shashinmu. Ya zo wuce wa ya dallaro mini ido da sabuwar tocilayit dinsa da alamu suka nuna yau ya zuba mata sabbin batira saboda tsananin hasken ta. Na dauke kai tare da saka hannunwana na rufe fuskata dan rage wa kaina kaifin hasken da ya dauke mini ido. Takaicin rashin gaishe shi ya sanya ya ce "Asiya ce?" Na dauke kai a shak'e na ce "Yabi ce?" Ya kuwa bu'de murya ya ce "Ja'irar yarinya mai mugun y'anci dama nasan ke ce zaki gan ni ki mini irin wannan iyashegen. Na ce ba, zaki yiwa ubanki Sani hakan?" Na dauke kai ina kunkunin fa'din "Ai kai ma ba zaka yiwa su Maijidda irin hakan ba". "Me kika ce? Bude Baki sosai ki fa'di abin da kike ce wa shedaniya." Ganin Baban Tsakiya dawo ya nufo mu dan ya shiga wajensa ya sanya Baban kasuwa ya d'auki k'arfaffan salati. Ganinmu hakan ya sanya Baban Tsakiya ya dakata ya ce "ya ya ne Iliya?" Ai kuwa ya hau rattab'a masa bayanin da aka yi masa na karya akan fad'anmu da Maijidda. Wani abin mamaki a gabana ya lauya zance yana fa'din a gabansa ma, na zage shi yanzu nan. Da kunnensa ya ji ina zaginsa. Baban Tsakiya yana bu'de baki sai ce wa ya yi "Tuni fa na d'iga alamar tambaya akan yarinyar nan domin wacce ta saba cudanya da maza ne take irin wannan dibar albarka." Gabana ya yanke ya fa'di wacce irin magana ce mai muni ta fito a bakin kanin mahaifina kuma uban wanda nake burin aure?" Na yunkura da nufin mayar masa da zazzafar magana sai kuma na tuna girman aika aikar da zan janyo wa kaina da uwata. Na sani mahaifina ba zai d'auki al'amarin da sauki ba, domin kuwa zai ce tunda na iya zagin dan-uwansa shima zan zage shi, hukuncin da zai biyo baya kuwa na tabbatar zai zama mai tsananin gaske. Na ha'diye maganar na juya na tafi na barsu dan kada na yi subutul kalam. Sai na sake juyo muryar Baban kasuwa yana sake cewa "Na kagu a samu mai tsautsayin daukar kara da kiyashi ya zo ya kwashe ta, ko zamu sarara da musibarta domin ta riga ta zame mana tamkar annoba" . Baban Tsakiya ya ce "Lallai kuwa kara da kiyashi daukar marar sani, na tausaya wa ahalin gidan Sarkin gida q tunda ina ganin d'ansu a wajenta" "To namu d'an fa? In ji Baban kasuwa. Baban Tsakiya ya yi wata irin dariya ya ce "Ta yaro ai kyau take yi bata k'arko, yaushe kana ganin kashi a jikin mutum, za kuma ka yi kuskuren bari naka ya dauki abin nan?" Kai-tsaye dakin Gwaggo na fa'da na zauna akan tabarmar da take shinfide, yayin da take zaune gefe daya, yanayinta ya nuna a takure take ma'ana tana cikin zullumin kiran da aka yiwa Babanmu me zai haifar mata. Na sassauta murya na ce "Gwaggo ki yi ha'kuri dan Allah" Ta muskuta ta ce "Idan ban yi ha'kuri ba ya ya zan yi ne Yabi? Ai a gabanki aka tabbatar mini ni agwagwa ce akan ki. Kinsan me hakan yake nufi kuwa?" Manufa kina gaba ina bin ki a baya, saboda gudun zuciyarki da nake yi. Ace yanzu kullum a cikin d'aukar wa kanki baki kike, sai ka ce ke kad'ai ce a gidan? Ga yar'uwarki nan ban ta'ba jin an kawo togaciyar Nazira ba. Amma ke idan ba'a kawo k'ararki ba, sai idan baki fita ba, ko kuma kin ha'du da masu alkunya, anya Yabi kina ganin kin hau turba mai b'ille wa? Jikina ya yi sanyi sosai na ce "Duk fa'dan da nake yi kowanne takala ta ake yi, ba wanda nake yin sa na rashin gaskiya, amma ki yi ha'kuri zan yi kokarin koyo ha'kuri idan an nemi ganin rikicina". Ta kafe ni da ido tana cewa "koya ma zaki yi Yabi? To fa'da mini zuwa yaushe zaki fara bita?" Na yi kasa da kaina na ce "Addu'a zaki tsananta yi mini a sanya ni cikin bayi masu ha'kuri da kawaicin cutarwar mutane. Amma a zahiri saboda ke zan yarda na zama mai kawaicin tunda abin da kike so ke nan. Domin ni dai har yau ban ga ranar da ha'kurinki ya miki ba, ban ga kuma ranar da kawaicin Babanmu yayi masa ba, tunda yau an kai dan-uwansa ne mai kirana da lalatacciya mai bin maza". Na fa'da hawaye na kwace mini ba tare da na shirya zubarsu ba. *Annur food Delicious* *Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.* *Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa* *HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna* *Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya* *08039183880* *VIP 1k, regular 500.* *2384876855* *Surayya Ibrahim* *Zenith Bank.* *Shaidar biya ta* *08032773332.* *BAK'AR TA'ADA* *NA* *SURAYYA DAHIRU GWARAM* *(MRS M.I.NASHE)*. *Marubuciyar* *Halin Yau* *Sabo da kaza*. *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ──────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.}``` ✏️ ____________(✪)______________ https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *Annur food Delicious* *Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.* *Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa* *HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna* *Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya* *08039183880* 11&12. A ki'dime Gwaggo ta ce "Baban Kasuwa ne ya fada miki hakan Yabi?". Na girgiza kai na ce " A a Baban Tsakiya ne". "Tirk'ashi" Gwaggo ta fa'da a hautsine. Na sunkuyar da kaina k'asa ina jin wani irin al'amarin tashin hankali na ratsa ni. Da kaina nake jin shekaruna sun yi k'aranci na dinga fuskantar irin wannan rikita rikitar. Na rasa dalilin da ya sanya nake da ba'kin jini a cikin gidanmu. Hatta a k'ofarmu mak'iyan da nake da su sun wuce misali. Domin kafatalin y'an d'akin Mama Nazira ce take sona fisabidillahi, sai ko Yaya Salamatu ita ma kuma ba yadda za'a yi alheri ya samu ta doshe ni da shi, sai dai Nazira, tana dai bani kuncen kayanta da suka sha ruwa ainun. Ni kuma murna nake yi domin tafi sauran yi mini adalci da sassauci. Mama kuwa da tana da ikon da zata kore ni a gidan da tuni ta yi hakan tsabar yadda ta washi ta bude ido ta gan ni, mussaman yanzu da sana'ata take sake kafuwa. Y'an dakinmu ne bana fuskantar adawarsu sai dai muna yawan haura wa sama da su a dalilinsu na ce wa ina daga wa Gwaggo hankali tunda kusan kullum sai na janyo mata bacin rai. Inna kuwa tare wa yaranta fa'da da nake yi ne ya sanya na kubuta daga nata kaidin. A hankali ta ce "Ai kuwa ribar ha'kurina gashi nan a bayyane tunda ban yarda na tafi na barku kun yi rayuwar ni y'asu a dalilin rashin uwa ba. Kina gani ina nan din ma ya ya kuka kare ne, bare kuma na zubar da ku na tafi? Ashe yanzu yadda yayunki suke dawainyar rike gidan nan bai isa abin alfaharina ba? A bayyane yake kafatalin ya'yan gidan nan ba wanda Babanku yake mora irin yaran dakin nan. Ai kuwa ko iya hakan na ga ni ba abin da zan ce da Allah sai godiya. Domin wasu da yawa yaran nasu basu amfani kansu ba bare waninsu ya amfanesu. Ubangiji ba abin da bai yi mini ba, na gode masa, kema na hore ki ri'ke ha'kuri ba abin da hakuri ba zai baki ba. Ta ri'ke kaina ta ce "Àllah ya miki albarka, ya sassauta miki al'amuranki. Ina fatan Ubangijin da yake sarrafa zuciya, ya sarrafa taki ta zama mai sassauci da afuwa". Kuka ya k'wace mini sosai ina cewa "Ameen Gwaggo". Ba komai yake sanya ni d'imuwa ba irin maganar Baban Tsakiya. Maganarsa ishara ce akan aurena da Yaya J ba zai yiwu ba. Zuciyata ta yi nauyi ainun. Na shiga rud'ani mai yawa, na sani idan har zan yi aiki da lura kamata ya yi na nisanci d'ansa tunda har yake neman maraba da ni a cikin gidanmu, ina kuma ace na zama cikin ahalinsa? Mutumin da bakinsa yake ambaton jaje da alhini ga ahalin wanda d'ansu zai kwashe ni. Bansan yadda aka yi ba na tsinci kaina da fashe wa da matsanancin kuka. Saboda fishin Baban kasuwa ya sanya Baban Tsakiya tsayawa ya mini irin wannan tozarcin da zai yi wahalar gaske na sake ganin girmansa. Na samu kaina da tambayar anya kuwa Babanmu ba dan uba ba ne a tsakaninsu? Sai nake ayyana ai ko y'ay'an Baffanni suke (cousins) bai kamata su dinga yi masa irin wannan kaskancin ba, dan kawai sun fishi wadatar abin duniya. Balle kuma girman nasaba irin ta uba guda, sai dai kuma babu haufi cikinsu daya ma'ana Dada ce ta yi nakudarsa tun gabbannin a yi tasu. Babban farin cikina d'aya, bai rasa wadatar zuciya ba, tunda duk tsananin wahala ba zai bu'de baki ya ce su taimake shi ba. Idan sun yi niyya akan kansu sun yi masa kyauta to zai kar'ba, amma idan zamu kwana mu yini bamu ci ba, ba dai ya ce wane ga halin da nake ciki ba, sai dai idan ya'yan cikinsa ne. Har ya k'wammace ya fa'da wa aminisa Alhaji Tanimu tsananin da yake ciki, ya tsananta. Matu'kar kuma zai fa'da masa to kuwa zai sauke masa buhun masara, dawa, dana gero. Sau tari kallon wadatar da ake yiwa su Baban Kasuwa yake hana masu k'arfi tallafa wa Babanmu. Sannan mutanan yau suna da dabi'ar k'in taimaka wa matu'kar ba ro'konsu ka yi ba, yayin da mafi yawa aka fi taimako da azumi, shima fake wa ake yi da sunan neman lada alhali a ku'din zakkar da Allah ya wajaba a fitar ne suke siyan kayan abinci suna rarraba wa. Oh mutanan yau mun rungumi *Bakaken Ta'adodi* daban daban. Allah ya shirye mu kawai. Muryar Inna na ji cikin sigar umarni ta ce "Ki cire Jabiru a ranki, nasan zai yi matu'kar wahalar gaske wannan al'amarin bai zama sanadin yin shamaki a tsakaninki da shi ba. Ina son ki ninka jarumtar ki, tun kafin su miki 'kwalele da shi." Kafin na bu'de baki sai ganin Baban Marina muka yi ya shigo a fusace yana fa'din "Ina Asiya?" Da rawar murya na ce "Ga ni Babanmu". Ya ce "zo ki fice ki bar mini gida tunda har zaki iya tsaya wa gar da gar ki zagi Badamasi da Iliya akan idonsu. Ai bansan zaki iya irin wannan dib'ar albarkar ba. Na dauka abin naki akwai lissafi a ciki amma tunda kina ganin idan kin yi karo tsakanin kwai da dutse zai miki daidai sai ki je ki yi a wani gidan, amma ba a nan ba. Ban haifi d'an da zai zagi dan-uwana akan idonsa na bar shi ba. Na sha fa'da miki babu ruwan ki da shiga tsakanina da y'anuwana. Amma sam kin k'i ji" Cikin kuka na ce "Ka yi ha'kuri Babanmu! Ba yadda aka fa'da maka al'amarin ya kasance ba. Ban zage su ba, har abada kuma ba zan zage su ba, kada ka kore ni a gidanka, zai iya zama sanadin tabarbare war al'amura masu yawa, ka mini dukkan hukuncin da zaka gamsu. Ka taimaki kanka, ka kuma tserar da ni fa'da wa halaka akan wad'anda basa nufin ka da alheri". Ya jijjiga kai ya ce "Yabi ki yawaita hamdala da baki zo a cikin mutanan farko ba, lah shakka da irinku ne masu kafiya akan ra'ayinku ko da ya ci karo da gaskiya. Na ji ba zan kore ki ba, amma dole ki yi nisa da gidan nan tun ban fusata na miki baki ba, tunda ba'kin cikin da kika cusa mini a sanadin musayar yawun da kika yi da iyayenki ba mai sau'ki ba ne, akan kannena mahaifiyata take mini mugun baki. Yabi kibi a sannu fa." Na sake tsorata na ce "Àllah ya huci zuciyarka Baba, Allah ya shiga cikin al'muranka, ya iya maka da iyawarsa". Nan da nan ya sauka ya hau fa'din "ameen". Gobe ki shirya ki tafi gidan Salisu har sai na nemi ki, saura can din ma ki nemi gigita masa zaman lafiya a gidansa, dan nasan zaki gano masa laifukan da iyalinsa take yi wanda shi yake yin uzziri a cikinsu". Na yi kasa da kaina na kasa cewa komai. Washagari kuwa Gwaggo da kanta ta shirya mini kayana a ledar biba tana ta jaddada mini idan na kuskura na yi rikici da matarsa to ba tantama da ita na yi. A sanyaye na ce "Komai zan ga ni zan runtse idona babu ruwana, ko da kuwa zata tsokane ni." Wani irin salama ya shiga Gwaggo ta dinga fa'din "Yauwa Yabina Allah ya sassauta miki". Anas ne ya fara yi mini gaba da kayana. Yayin da zamu tafi da Nazira da Iki idan anjima. Nazira sai kuka take akan tafiyar da zan yi na barta. Na yi shirin zuwa gaida Dada wanda rashin zuwa wannan gaisuwar ba k'aramin abu take mayar da shi ba. Babu kuzari na ce "Nazira mu je mu gaida Dada". Ta girgiza kai tare da cewa "je ki kawai, bana jin dadi anjima na leka". Na ce "Tom na tafi, ina jin da'di tare da k'arfafa wa kaina guiwar ko na rasa soyayyar kowa a fuskar zumunci ina da yakinin ba zan rasa soyayyar Nazira ba. Tana sona fiye da zatona, haka nima nake sonta tamkar yadda nake son shakikiyata Yaya Ummi. Tun daga bayan katangar Dada nake jin tashin muryoyinta da na Ya'yanta Na karasa har cikin soron sosai na dinga jin kumfar bakin da Baba Maryo uwar Nasiba take yi akan ba zata ta'ba yarda a dauki Nasiba a bawa Tijjani ba. Kuka take yi wiwi. Tana cewa "sai dai a ga laifina a banza, amma wannan ha'din ba mai yiwu wa ba ne." Yayin da Babah ta Bulkachuwa take fa'din "Ai ban ga laifinki ba, gaskiyar magana kika fa'da. Kuma dama mutum shi yake mutunta kansa, da ya nutsu ya zama mutumin kirki ina ce a ko ina zai nemi aure a ba shi?. Yanzu kuwa da ya zama abin da ya zama a cikin danginsa ma gudunsa za'a yi bare a waje". Dada ta ce "Ya isa haka, ba cece-kuce zaku yi mini ba. Na rufe wannan maganar, na yi zaton auren nasa da ita zai kawo masa dai-daito tunda tana sonsa, idan aka yi sa'a sai ya shiryu, ruwan wankan aure ka'dai maganin wanda ko wacce suka fand'are ne. Amma tunda abin zai zama tashin hankali a bar maganar haka nan Nasiba ba matarsa ba ce." Kafin na yi wani motsi sai jin muryar Baban Tsakiya ya yi yana fa'din "Kazalika wannan yar iskar yarinyar ba matar Jabir ba ce, ko bayan raina idan aka bari ya aure ta Wallahi Allah ya isa, na fa'da a gabanku, kuma yanzu ma idan na tashi zan je na sami Yaya Sani na tabbatar masa babu maganar aure, mun gama magana da Iliya, Maijidda zai aura. Domin ba zan yadda ya dauko mini majuniniyar yarinyar nan ta zo ta tarwatsa mini zuri'a ba". Daidai lokacin na yi sallama na gaida Dada sannan na gaishe su a jamma'u. Babar Bulkachuwa ce ta amsa cikin karfin hali tana danne bacin ran da ya ke kutso mata. Nima na yi jarumtar cewa "Ashe kin zo Babah?" Ta ce " Na zo dazun nan kin san sammakon zuwa nake yi saboda motar Jos muke shigowa. Na yi yake na ce "Sannu da zuwa". Na mike da nufin tafiya sai kuwa Baban Tsakiya ya ce "Dawo ki zauna. Na zauna ina kallonsa k'ir domin ya riga ya wanke mini a zuciyata. Ya kausasa murya ya ce "ki hanzarta turo wanda kuka shirya domin kuwa watan jibi da saba'a zaku bar gidan nan". Cikin son nuna masa iyaka na ce "To ai Jabir naka muka daidaita da shi, wannan satin zai iso garin, wajenka zan turo shi, ko wajen Baban Kasuwa?" Ya zabura ya mini dakuwa ya ce "Marar kunya, marar mutunci ki zagi dan-uwana, ki mini tsaki a gabana ki yi zaton kuma zaki zama surukuta, ko dai bayan sharholiyar da kike yi har shayeshaye kike had'a wa da shi? To saurara ki ji! Jabir ba zai auri wanda zata zagi ubansa ba." Babu fargaba na ce "Na karbi wannan hukuncin da hannu biyu Baba, ban kuma saka ka cikin masu son rai ba, domin na yi laifin da na cancancin hakan. Alfarma d'aya nake ro'ko a wajenku tunda ni ce bani da tarbiya, to ku musanya wa Yaya Jabir ni da Nazira domin dukkanku nan ba wanda zai zargeta da rashin tarbiya ko sharholiyar da ni nake yi". Nan da nan Baban kasuwa ya ce "Anki a bashi ita din dan uwarki, makira, algunguma, Maijidda ce matarsa har a kiyama kuwa". Ga mamakina sai na mike na tsinci kaina da cewa "Gaskiya Baban Marina ne ba a so, shi kuma har yana kora ta saboda ku. Ba komai Ubangiji ya sanya alheri". Har na fice ba wanda ya iya bu'de baki ya ce mini kala tsabar kad'uwar da suka yi da furucina. Baban Tsakiya ne cikin fishi ya ce "Ba shakka dangin uwar yarinyar nan akwai majununai". Na so na tsaya na ce "ko wanne d'a yafi gadon dangin ubansa, dan ya gane sune majununai ba mutanan Kangire ba. Sai dai kuma duk iyashegena ai wata fuskar tafi gaban mari, kannen ubana ne, ta ko wacce fuska idan na yi musayar yawu da su ni ce bani da gaskiya. Sai kawai na had'iye. Ina fitowa na yi kicibus da Bulkachuwa yana tsaye da buta a hannunsa, tabbacin daga bayi ya fito. Na tabbatar kuma ya ji komai har maganganun da aka yi a kansa da Nasiba. Domin gaba'daya manyan idanuwansa sun kad'a, sun yi jajur. Na wuce shi ban sake kallonsa ba, kallonsa ka'dai ya sanya na ji tamkar na yi amai tsabar yadda na washe shi. Wannan abin da na yi ya sake ki'dima wadannan bayin Allah domin dukkansu ba wanda maganar bata shige shi ba. A ranar na koma gidan Yaya Salisu ban san wainar da ake toyawa a gidan Marina ba. Zama nake yi irin na taka tsantsan a gidan, ba dan komai ba sai togaciyar da aka yi ta yi mini a gida. Da safe zan yi wanke wanke da shara, na yiwa dansu wanka shi kenan sai na shige daki. Idan ta gama abinci zata mini zubin auki. Yadda nake gudun bata mata, hakan ita ma take kaffa kaffa dan kada na ga beken ta, ko idan na koma gida na bada ba'kin labari a kanta. Ranar da na yi kwanaki hudu sai ga Nazira da Iklima. Muka yi hira, sun kusa tafiya Nazira ta ce da Iklima ta fita ta jira ta a waje. Ba musu Iki ta fita. Ta sassauta murya tabbacin bata son a ji maganar ta ce "Kinsan me yake faruwa kuwa a gida?" Na girgiza kai ina fa'din a ina zan sani Adda Nazi?" Ta sake yin kasa da murya ta ce "wata yarinya ce ta yi cikin shege har ta kusa haihuwa fa, to ana ta shari'a, da ta lissafo wadanda suke mua'amalantar ta har da Yaya Bulkachuwa yanzu haka kullum sai sun je kotu". Zuciyata ta harba da tsananin gaske, na ce "Tijjani gaskiya baya kyauta mana, gaba'daya sai ya gama ruguza darajar gidanmu alhalin shi ba dan gidan ba ne". Nazira ta ce "Hmm abin sai ha'kuri ba ki ga yadda ya zama ba, ya kuma kafe akan ciki ba nasa ba ne ba zai kar'ba ba. Babah ta Bulkachuwa ita ma ta zama abin tausayi sosai tsabar ba'kin ciki." Hawaye ya balle mini wata irin damuwa ta shige ni, kishin zumunta ya murde ni, ko yaya ba zaka so ganin jininka a cikin tozarci ba. Mun jima a hakan kowa da k'wallarsa ta ce "Jiya Malam Yunus Econs ya aiko a bashi izinin neman aurena kinsan tunda matarsa ta rasu a wajen haihuwa har yanzu bai sake wani auren ba, ga yaron nan tuni ya shekara biyu." Na ru'ko ta ina fa'din "Kai na yi murna sosai Allah ya tabbatar da alheri mutumin kirki ne, na amince Adda Nazi ta so shi ta bashi dama, Allah sanya albarka a tafiyar". Muka fito ina musu rakiya tana ce wa "Abdul sau uku yana zuwa amma Baba bai bari an fa'da masa inda kike ba." *GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI* *IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*. *SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI* *AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN* *AKWIA PACKAGE DIN AMARYA* *AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO* *AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*. *AKWAI GORAN TULA SYRUP* *AKWAI GORAN TULA FRUIT* *INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA* *, SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332* *DAN ALLAH SERIOUS BUYER'S*. Na ce zai bari ne, domin ko Yaya Jabir ne autan maza na bar shi Nazira". Ta ru'ko hannuna ta ce "Madallah da zuciyar Yabin Marina! Ni nasan zuciyarta ba zata cigaba da son wanda zata yi kuka a hannun ahalinsa ba, ba zata so wanda ubansa yake k'yamarmu ba, in sha Allah sai kin auri wanda ya fishi komai, aurensa da Maijidda kuma bama adawa. Sai kuma kuka ya goce mata, nima hawaye ya sake zubo mini, domin idan na ce bana sonsa ko abin bai dame ni ba na yi k'arya. Amma zan nuna wa su Baban Tsakiya ni din yar halak ce ina kishin ubana, ina kuma kishin kaina. Babban rufin asirin da Allah ya yi mini shine dama ina da Abdulrashid. Su biyun duk ina sonsu amma nafi son Yaya J. Yafi daukar hankalina matu'ka da gaske sai dai zan iya rayuwa da Abdul ba tare da na takura ba. Sai da muka yi kukanmu son ranmu sannan muka je gidan Yaya Salamatu, muka bata labarin halin da ake ciki. A sanyaye ta ce "Babanmu ne basa so fa, gara miki ma hakan, Allah ya kawo miki mafi alheri me za'a yi ma da auren dangi irin namu ne?" Mun jima sosai sannan muka tafi, bayan na bata labarin Malam Yunus da yake son Nazira. Ta yi murna, ta yi farin-ciki, ta bamu dari biyar mu hau mashin. Bayan ta bawa Nazira kaya a leda ta kaiwa Mamansu. Na koma gidan Yaya Salisu, su kuma suka wuce gida. Kwanana shida da barin gida sai ga Yaya J a gidan Yaya Salisu. A matu'kar birkice na ganshi. Ya kasa mini magana, tsawon lokaci kafin ya ce "Me yasa haka Yabi?" Ba walwala na ce "me yasa, me ke nan?" Ya ce "na dauka ko baki ha'da komai da su Baban Tsakiya ba zasu ci darajata bare kuma iyayenki ne da zasu daura miki aure". Na bata rai na ce "Bana ma bukatar su mini walittaka Jabir, domin komin kashin Babanmu da ake ga ni, Ubangiji ya azurta shi da yara mazan da zasu maye mana gurbin kowa. Kai ko ba ni da yan'uwa maza a cikin gidan Wallahi Ammar da Bulkachuwa zasu iya daura mini aure duk da kasancewarsu ya'yan mata ne, amma idan har ya kasance sai ku to lah shakka zan iya saka hula na wakilci kaina ko kuma na samu alkali ko liman". Jikinsa ya yi matu'kar yin laushi. A sanyaye ya ce "Ni yanzu mene ne laifina a nan Yabi?' Yana rufe baki na ce "Rashin biyayyar ka. Na tabbatar an fa'da maka ka kiyaye ni, domin ban cancanci ka aure ni ba, saboda mahaifina ba shi da daudar duniya". Ya yi kasa da kansa ya ce "Ni da ke muke magana ki daina sako mini manyanmu domin wannan ba dabi'a ce mai kyau ba. Na gallah masa harara na ce "Madallah" Na tsuke bakina na yi gum. Ya marairaice ya ce "Yabi kada ki bari a bada kofar da za'a yi mana farraku, ina son ki, ina kaunar kasance wa da ke, jikina na bani kamar ma na kusa barin duniyar nan, ki taushi zuciyarki kada ki zalunci wanda yake tsananin sonki Yabi. Ban miki komai ba, kada ki hukunta ni da laifin da bani na yi miki shi ba". Jikina ya yi sanyi. Na kasa magana domin gaba'daya ya d'aure ni da jijiyoyin jikina. Zufar da take karyo masa ta sanya na sake jin sonsa na taso mini. Kafin na yi magana sai kawai na tuno maganganun mahaifinsa a kaina, wai ni da nake matsayin y'arsa, yar dan-uwansa amma ya jefe ni da mafi munin kalma wai ina bin maza, ke nan karuwa ce? Bayan ga hakan kuma ya ci mutuncin mahaifina wanda wansa ne. Take na ji karshen jakanci ne na cigaba da mua'amalantar jininsa da sunan soyayya. Mussaman da ya ce yana tausayin zuri'ar da d'ansu zai kwaso musu ni. Na dago cikin karfin zuciya na ce "Jabir mu yi datse wannan soyayyar ka ji, na rantse maka tun jiya na shak'e ta, na kwashe mata karama. Babanka ya tabbatar mini Maijidda ya za'ba maka, domin ita ce arzikin ubanta yayi daidai da shi, ban yi ba'kin ciki ba, domin kullum zabin Allah muke nema. Alhamdulillah! Na karbi wannan kaddarar da hannu bibbyu, domin Ubangiji na bar wa al'amarin, ya yi mana za'bi da kansa. Amma zan roke ka Yaya Jabir ka yi iya kokarinka wajen taka burki a ta'ba mutuncin Baban Marina da ahalinsa. Ina jin tsoron kada wannan matsalar ta yi girman da ba zata gyaru ba. Ina jin tsoron kada a wayi gari a ga gidan Marina ya zama sansanin yaki a tsakanin jini guda". A matu'kar birkice ya ce "Allah kada ya kaddara mini ganin hakan Yabi! Ina fatan mutuwa ta riske ni kafin wannan lokacin" Na girgiza kai na ce Shi kenan". Ya marairaice ya ce "Na tsugunna miki Yabi Asiya? Ki taimake ni, ki fahimce ni, idan kin kwantar da hankalinki ai za'a a samu sulhu ta sanadin aurenmu. Sai mu kawo dai-daito, an yi abin da yafi haka muni, kuma an dawo an shirya, kada ki tsananta, ki yanke mini hukuncin da babu laifina. Allah da kansa baya kama mu da laifin iyayenmu ko na y'ay'anmu. Daure ki ji tausayina, na rantse idan kin bani ha'din kai ba abin da zai sa na bar ki komai za'a yi kuwa" . Na girgiza kai na ce "Idan na yi hakan ba sonka nake da gaske ba. A gaban iyayenmu Baban Tsakiya ya ce "Idan aka baka aurena Àllah ya isa. Baya ga hakan kuma ya tsane ni, tsanar da ya danganta ni da karuwa ce ni, kuma ya ce na zage su, hakan ya janyo ubana ya kore ni saboda shi kullum yana sonsu, yana musu kyakkawan zato". Daga haka kuma sai kuka ya subuce mini. Bai hana ni yi ba, shima kuma idonsa ya ciko jijiyar kansa ta yi rud'u rud'u tabbacin yana cikin rud'u mai girma. Da murya kuka na ce "Maijidda ta fini kyau, ta fini gata tunda Babanta mai ku'di ne, ta fini komai, ka karbi zabin iyayenka na tabbatar Ubangijin adalci zai juya maka al'amarint fiye da al'amarina, tunda ka yi biyayya. Zan fa'da maka gaskiya ko zan yaudari kowa bazan yaudare ka ba. Kana da muhimmanci a rayuwata, da gaske ina ganin mutuncin ka. Na roki arzikin ka rabu da ni, na riga na ha'kura da kai Wallahi, maganar soyayya kam ta kau". Ya numfasa ya ce "Oh! Haka kaddara ta za'ba mini? Na so ace kin saurare ni, na so ace kin bani dama mun ha'da hannu da k'arfe mun yaki wannan *BAK'AR TA'ADAR* da take neman zame wa alummarmu tamkar wutar jeji. Ina cikin zullumin yadda zumuncin yau ya koma tsakanin masu kumbar susa. Ina cikin takaicin yadda aka jahilci d'an-uba. Ina matu'kar so a ce kin zama matata ta yadda zamu kawo cigaba ta fuskar zumunci a cikin zuri'armu ta hanyar mua'amalantar kowa da girmama wa. Amma babu komai, mu ci gaba da addu'a Allah baya juyar da addu'ar masu kyakkawar manufa". Ya saka hannu ya zaro hankicif ya fara goge zufar tashin hankali da take yanko masa, kalaman sa ba k'aramin sukurkuta ni suka yi ba. Amma na yi jarumtar waske wa domin har cikin zuciyata nake jin ban cancanci na zama cikin ahalin Baban Tsakiya ba. Ya kasa cewa tsawon lokaci sannan ya yi karfin halin cewa "Fatan alheri mai yawa gare ki Yabin J". Sai ya dawo da sauri cikin rawar murya ya ce "Yanzu kin mini adalci idan kika jingina sunan ki da wani na? Yanzu kin manta komai, bani da wata alfarma a wajen ki?" Na yi kasa da kaina na ce "Alfarmomi masu yawa kuwa . "Kai na fara so, kai kawai nake yiwa uzziri da sassauci bayan iyayena, sannan idan akwai wanda na yarda da son da yake mini to kuwa kai ne. Sai dai ko kusa bazan yaudari kaina ba. Iyaye girmansu yawa ne da su, Annabi (S.A.W) ya yi ta jan hakankalinmu akan mubi su. Idan kuwa hakane zan gwada maka cikakkiyar soyayya ta hanyar dora ka akan turba sahihiya, iyayenka duka biyu basa son almarinka da ni. Dan haka ka bar son zuciyarka, ka musu biyayya, na yi imani Ubangiji ba zai barka haka ba". Daga haka na fashe da azababben kuka. Jikinsa ya dinga kyarma ya ce "Na sani kina sona. Na roki arzikin, ki mini uzziri, kar ki ce mu rabu, mu bar wa Allah ya yi mana za'bi, mu yi addu'a mu ga ni. Jikina bai bani akwai namijin da zai aure mini ke alhalin ina numfashi a wannan duniyar ba". *Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame* *Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea* *Akwai pop corn* *07036662633*. *BAKAR TA'ADA* *NA* *SURAYYA DAHIRU GWARAM* *(MRS M.I.NASHE)* *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ──────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.}``` ✏️ ____________(✪)______________ https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *ALBISHIRINKU* *MASOYAN LITTAFAN MARUBUCIYA HAFSAT C SODANGI*! *DUBA DA YADDA KUKE KEWAR RUBUTUNTA YA SANYA TA YI SHIRIN SAKE DAWOWA DAN TA SAKE MUKU WANI RUBUTUN SABO DAL* *AMMA KAFIN HAKAN TA DAWO MUKU DA TSOFAFFIN LITTAFAN TA ZUWA KAN WAYA, DAN KU SAKE BITA TARE DA NAZARIN KYAWAWAN SAKON DA TAKE NUFIN ISARWA GAREMU*. *A YANZU HAKA LITTAFAI HUDU NE RIGIS* *WAYYO DUNIYA 1-3* *KYAUTATA 1-3* *DAGA K'IN GASKIYA 1-3* *MATA MASU DUNIYA 1-3* *KO WANNE 1K NE AMMA AKWAI DISCOUNT IDAN ZA'A SIYA SAMA DA GUDA DAYA* *MISALI GUDA BIYU-1500* *GUDA UKU 2500* *GUDA HUDU 3500* *ZA'A TURA KUDIN TA ASUSUN MARUBUCIYAR KAMAR HAKA* *0082739293, ACCESS BANK HAFSAT YUNUS ABDULLAHI* *SAI A TURO MINI SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR 08032773332* *SAI NA BADA LITTAFIN DA AKE SO* *MADALLAH DA KARFAFA GUIWARKU* *MADALLAH DA SOYAYYARKU GA RUBUTUNMU* *AKWAI LITTAFANTA SAMA DA GUDA GOMA DA A YANZU SUKE SOFT COPIES, KAWAI KI TAMBAYI DUK WANDA KIKE NEMA A WAJENA CIKIN LITTAFANTA NA BAYA*. *Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame* *Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea* *Akwai pop corn* *07036662633* 13&14. Da azama na shige cikin gidan na bar shi domin na samu sau'kin halin da nake ciki. Kuka na dinga yi tamkar zuciyata zata fa'do k'asa, bansan son Yaya J ya tumbatsa a zuciyata irin hakan ba sai yau, domin sai na tsinci kaina da addu'ar na zama gawa kafin igiyar aure ta d'auresu da Maijidda. A wannan daren barci rabi rabi na yi shi. Washagari da hantsi sai ga shi ya dawo, kallo d'aya na yi masa na gane yana cikin zullumi mai yawa domin gaba'daya ya zube ya sake fige wa. Yaya Salisu da ba shi da matsala da kansa ya masa iso har cikin falon gidan da yake dakuna uku ne a jere falle falle. Na fito a sanyaye sanye da hijabi idanuwana a kumbure a dalilin kuka da rashin barci. Na zauna a kujerar da ta yi nesa da wacce yake zaune. Tsawon lokaci muna zaune jigum jigum, tamkar masu makoki, daga karshe dai ya k'osa cikin murya marar amo ya ce " Yabi babu gaisuwa ne?" Kaina a kasa na ce akwai gaisuwar da tafi nema maka amincin da na yi? Shin ka raina sallamar ne?" Ya girgiza kai ya ce "Hakkun Yabi. Kin fini kusa da daidai, kin yi barci kuwa?". Kaina a k'asa na ce "Me zai hana Yabin Marina barci a wannan duniyar? Sai mutuwa, ko ciwo". A matu'kar sanyaye ya ce "Idan kuwa hakane ki shirya kwanan zaune domin kullu nafsin za'ikatul maut. A kowanne lokaci muna iya rasa mutane mafiya daraja a rayuwarmu, ko kuma a jarrabemu da ciwo mai hana runtsawa. Fata dai Allah ya bamu ikon cinye dukkan jarabawowin da suke dunfaromu. Ban da dai dan-adam an jarrabe shi da tsoron mutuwa, mene ne abu mai da'di a cikin wannan duniyar da a kullum tsanani da bacin rai suke sake yiwa mumini k'awanya?" Ban tanka masa ba, domin kuwa gaba'daya zuciyata babu sukuni, kuma cike take da ba'kin ciki mai nauyi. Cikin alhini ya ce "Yabi ban yi zaton munin dambarwar da take faruwa ta kai lalacewar da ta yi ba! Na gamsu, na ha'kura da aurenki a yanzu, dan na tsaremu daga fa'dawa halaka. Amma na rantse miki babu wata macen da zan sota irin son da nake yi miki, zan kuma dauwama a cikinsa. Tsoron hakkkm iyaye ne kawai zai sanya na yarda na yi aure kuma na mua'amalaci matar cikin adalci. Amma ban ha'kura da ke ba, zan cigaba da kokarina har sai Ubangiji ya mini taimakon tabbatar da aurenmu. Hawaye ya balle masa tamkar ba namiji ba. Da rawar murya ya ce "Akwai bukatar mu tsananta addu'a a cikin zumuncin Gidanmu Yabi. Daga jiya zuwa yau na fahimci BAK'AR TA'ADAR wariyar launin fata, ta yi kane kane a cikin gidan". Na dago idona jage jage da hawaye na ce "Komai zai dai-daita idan arzikin Baban Marina ya dawo, ko idan ya'yansa suka kawo k'arfi." A kasalance ya ce "Ba wannan ce matsalar ba kawai. Shin menene ribar hana ni auren ki?" Na dago na ce "Saboda ana ganin zan samu cigaba, ana ganin ban cancanci na samu irin wannan darajar ba, bai kuma kyautu ayi wa Baban Marina irin wannan zumuncin ba tunda ba za'a amfana da shi ba, an kuma rufe ido an mance irin amfanar sa da aka yi a shekarun baya". Ya yi shiru ya ce "ban gamsu ba, idan kuma wannan ne hujjar da gaske? Menene dalilin da zai sa ba za'a bawa Bulkachuwa auren Nasiba ba? Ai duk lalacewarsa jininmu ne. Idan za'a hana shi mace a cikin danginsa to ina za'a bashi? kawai halin da ya jefa kansa ne ya sanya baya iya tanadi. Amma idan aka bashi mace na tabbatar indai yana samun nutsuwa da ita, zai nutsu ya zama mutum na sosai, sannan zai daina zalama da tsilla tsillar da yake yi tunda yana da tasa ta halal a dakinsa ." Duk da matsananciyar damuwar da nake ciki sai da maganganunsa suka jefa ni cikin kunya da takura. Na kasa magana. Ya sake cewa "To saboda Allah idan ba'a taimake shi a cikin danginsa an rufa masa asiri, an tsaya kai da fata wajen ganin al'amarinsa ya kintsu ba, me za'a yi masa? A wajene ake son ayi masa irin wannan sadaukarwar da kishin kai? Babban tashin hankalin ita Nasiban sonsa take yi kamar ta kai kanta dakinsa. Da ace bata sonsa na zan ga laifin kowa ba. Shin wanne irin zamani muke ciki ne mai cike da son zuciya?" Nan ma na kasa cewa uffan domin tunanina ya riga ya tsuke, ban sani ba ko dan har yanzu ban gama fahimtar al'amuran da shi ya fahimta a tsakanin yammacin jiya zuwa yau ba. Ko dan ya fini shekaru, ya kuma fini ilimi da hangen nesa ne oho. Gaba'daya a rikice yake, k'warai kwamacalar da take cikin gidanmu ta gigita shi. Nasan bai san haka abin ya tsananta ba, tunda ba kasafai yake zaman garin ba. Ya jima kafin ya sake cewa komai. Ya mike ya zura hannunsa a aljihunsa. Ya ce "Bansan me zan ce miki ba, amma nasan zan rayu da son ki a raina muddin rai. Zan kuma rayu tamkar wanda ya rasa bangare guda a jikinsa. Ina fatan Ubangijinmu Allahu ya sanya mu cikin masu soyayya dan Allah. Har kuma yanzu da nake miki wannan jawabin ban cire alkalamina a cikin tawada ba. Ban cire rai cewar kaddara tana iya bani damar mallakar ki a matsayin matata ba. Ina neman alfarma, komin kankantar damar da zamu samu ta cikar burinmu kada laifin da bani na yi ba, ya shafi hakan Yabi. Ina da burin idan mun yi aure na mayar da ke makaranta ki zurfafa a ilimummuka daban daban. Amma ko yanzu ma ban fitar da rai ba, lokaci zai zo da zaki tsaya ki yi karatu tuk'uru, ki cire shiriritar da kike yi. Mu tsananta addu'a, mu barwa Allah ya yi mana zabin da ba zamu koka ba. Kin fini gaskiya duk al'amarin da babu saka albarkar iyaye to tsinannen al'amari ne. Fatan alheri gareki Yabin J". Ya fice da sauri. Jikina ya yi matu'kar sanyi, domin na tabbatar akwai abin da Yaya J ya ga ni a cikin zumuncin Gidanmu da ya warware masa duk wani confidence dinsa. Na kagu na samu labarin irin wainar da ake toyawa a gidan Marina. Na rasa yadda zan yi, domin Yaya Salisu ba mai zama ya tattauna magana da mutane ba ne. Na matsu kwarai na ga Nazira domin a bakinta zan ji komai kuma babu k'arya ko karin gishiri a cikin kalamunta. Kwanaki suka yi ta shudewa, ban samu ganin Nazira ba, ban kuma ji labarin komai ba. Abin da yake damuna daya ne takunkunmin hana ni zuwa gida da aka sanya mini. A hakan har na shafe kwanaki ashirin da biyar a gidan Yaya Salisu. Na riga na kai k'ololuwar gajiya da son jin makoma ta. Gashi ba wanda ya zo daga gidanmu. Dan ma ina samun y'an kitso da k'unshi, suna biyo ni, haka na unguwar ma suke yi mini layi. Rannan da na gaji, sai kawai na zari jiki na doshi gida a sayyadata duk da tazarar gidan Yaya Salisu zuwa Gidanmu tafiya ce mai tsayi ainun. Tunda na kusa k'arisa wa na fara jin jikina na kakkarwa, ga kuma luguden da zuciyata take yi tamkar ta faso ta fito. Bakina na ambaton sunan Allah, duk da idan ance na fa'di me nake fa'di ba zan iya tantance wa ba. Na fa'da zauren na yi kicibus da Baban Tsakiya, zai fita, da alamun rashin sukuni a tare da shi. A farko kamar ba zan gaishe shi ba. Bansan ya aka yi ba, cikin rawar murya na ce "Baban Tsakiya ina yini?" Ina daga tsaye ban rusuna ba. Ya mini dak'uwar da ta zame masa dabi'a ya ce "Baban farko ba na Tsakiya ba. Wato ke tabbataciyar yarinya ko? Sai kin ha'da da inkiya saboda ba kya mini kallon arziki.l? Zan ga mai daura miki aure, sai dai Ubanki ya waklice ki da kansa. Kuma indai ina numfashi duk wanda ya zo neman auren ki sai na fa'da masa rashin d'aarki da hatsabibanci irin na ki, domin fadar gaskiya a neman aure jihadi ne kabiran". Na yi k'asa da kaina ba tare da na ce komai ba. Ya juya ya tafi yana ta yi mini sababi da kwashe albarka da fatan tsiya iri iri. Na jingine a jinkin garun ina tambayar kaina "Wai haka kowa yake fuskantar bacin rai da danginsa ko kuwa iya ni ce? *GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI* *IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*. *SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI* *AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN* *AKWIA PACKAGE DIN AMARYA* *AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO* *AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*. *AKWAI GORAN TULA SYRUP* *AKWAI GORAN TULA FRUIT* *INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA* *, SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332* *DAN ALLAH*. Take na tuno Nazira bata fuskantar tsanani irin nawa a wajen Baffannin namu. Amma kuma ko ka'dan bata samun sakin fuska da alherin da suke yiwa ya'yansu. Na sake tafiya dogon tunanin yadda Baban Marina yake mua'amalantar nasu yaran. Mua'amala ce ta sassauci da ja a jika. Domin duk talaucinsa, yana k'ok'arin siyan albasa ko su mangwaro ya ce mu mika kofofinsu. Hakanan indai zai yi aski sai ya ha'da da ya'yansu an musu ya biya. Bayan nan duk wani rikicin da ya'yansu zasu rakito shine zai yi ta zarya yana bada ha'kuri har sai komai ya daidaita. Amma su ba ruwansu damu, wani ikon Allah Yaya Musa da yake a lalace sun fi sonsa, sun fi yinsa, sun fi tattalin farin-cikinsa. Na jijjiga kai a fili kuma sai na ce "Allah haska kofar Baban Marina, Allah ka jibanci al'amarinsa da na ya'yansa. Na shige cikin gida ban doshi k'ofar Dada ba. Yanayin da na tarar da Babanmu da ahalinsa ya sake sanyaya mini jiki. Na shiga bakina da sallama na isa kan tabarmar da suke zaune na tsugunna ina gaishe shi cikin girmama wa. Ba walwala Baba ya ce "Asiya me kika zo yi? Ba na ce sai na neme ki ba?" Da rawar murya na ce "A mini afuwa Baba! Na kasa jure ji daga gareku ne." A sanyaye ya ce "Na miki afuwa Yabi zo ki zauna. Da rarrafe na karisa kusa da shi a dalilin rawar da jikina yake yi ya sake ta'azzara. "Na yi godiya Baba Allah ya k'ara maka lafiya, ya shirya maka zuri'a, Allah ya mayar da ahalinka wasu masu fa'da aji". Ya yi murmushin da babu nisha'di. A sanyaye ya ce "Ameen Yabi! Duk yadda zan yi ba zan iya cire miki wannan BAK'AR TA'ADAR k'ullaci da ta shiga ranki ba. Amma abin da zan fa'da muku duk taku, duk wanda bai mutunta y'anuwana ba, to nima kar ya mutunta ni". Jikina ya yi sanyi, na yi kasa da kaina, na kasa cewa komai. "Yabi". Ya k'ira ni murya babu amo. Na amsa a hanzarce "Na'am Babanmu". Ya yi gyaran murya ya ce "Nan da kwanaki goma sha biyu auren y'anuwan ki. A duk wanda kuka taso ke da Nasiba ne kawai babu ku a cikinsu. Da gobe zan je na sanar da ke maganar a nutse cikin kwanciyar hankali. Na tura wa iyayen Abdulrashid su turo ayi magana to bansan inda aka haihu a ragaya ba, sai suka aiko mini da sun yi wa d'ansu mata tuntuni, ba da yawunsu yake neman auren y'ata ba." Jikina ya sake daukar bari a dalilin idan na fahimci maganar Babanmu kenan zan rasa Yaya J da kuma Abdul tashi guda, wannan shine biyu babu, kamun gafiyar b'aidu. Na tattaro dukkan jarumta na yafa a dukkan sassan jikina da fuskata. Na ce "Babu damuwa! Allah ya sanya alheri. Amma Baba har da Adda Nazi kenan?" Na fa'da cike da karsashi irin na tsananin karfin hali. Ya ce "Da ita Yabi, sai dai bana jin za'a yi tariya da ita, domin ban mallaki komai na aurenta ba, tunda titsiye aka yi mini." Na kalli dukkan yaran gidanmu masu hankalin suna wajen hatta Yaya Musa kuwa. Hawaye ya b'alle mini na ce "A a Babanmu da ikon Ubangiji a ranar zata tare. Na kalli Yaya Salamatu na ce "Yaya" Sai kuma na fashe kuka sosai. Dukkansu matan sai suka taya ni kukan in ban da Yaya Ummi da take Jin zafin yadda nake damuwa da lamarinsu alhalin ita ma ba sonta suke yi ba in aka dauke Naziran. Da rauni Yaya Salamatu ta ce "su uku sun kawo dubu sha biyar biyar, yan dakinsu kenan. Sai ummi ta kawo dubu biyar, Ni kuma na bayar da ashirin maigidana kuma ya bada buhun masara da na shinkafa ayi hidimar biki da su". Su Salisu kuwa sun ha'da hamsin a tsakaninsu dan haka dari da ashirin ne a k'asa kacal". Nan da nan na zaro magana tamkar babbar mace na ce "Ai kuwa sun isa Yaya, kuje ku siyo mata katifa da labule da ledar tsakar daki. Na kunce hannun zanina na kunce na fito da kudi kimanin dubu sha bakwai da dari takwas. Na ce ga nawa a siya mata bargo da zanin gado. Su Mama ku fito da kwanuka da tukunya. A kai ta a hakan da ikon Ubangiji watarana sai ta yiwa wani kayan daki na alfarma, ai duniya ce mai rawar y'an mata na gaba ya koma baya". Hatta Mama a wannan ranar na ga kallon sassauci da adalci take yi mini, domin da ta ga na sake dauko bankina na mik'a wa Nazira na ce "Ki fasa ki yi dinkin fitar biki nasan zasu ishe ki tunda kinsan mu din masu k'aramin karfi ne, masu nema a wajen Àllah." A fili take fa'din "Yabi da Nazira sai Allah". Baba kuwa zuba mini ido ya yi, tsawon lokaci kafin hawaye ya goce masa. Duk muka ha'du aka yi ta kuka tamkar an ce ya mutu ne. Domin ita kanta Mama da take ha'da kai da matan su Baban Tsakiya suna sake tsananta mana, ta sha mamaki da ta ga suna yiwa ya'yansu hidimar aure basu yi kara sun saka da Nazira ba. Wata'kila a haukanta zasu yi ko saboda da ita. Da rawar murya Baba ya ke fa'din "Allah ka sake jefa soyayya da tausayi a tsakanin ya'yana, Ubangiji na gode maka". Yaya Indo ta kira Malam Yunus ta fa'da masa ku'din lefe ya bayar yadda zai iya ba sai ya yi ba , domin kuwa muma abin da zamu iya za'a yi. Da yake ba yaro bane ainun, sai ya gamsu ya ce zai yi mata lefen yadda ya sauwaka, sannan zai bawa Yaya Salisu ku'din da ya sauwaka shi mutunci ya gani dan haka komai zai yi. Ba wanda ya san me ake ciki domin kowa ya zuba ido yana jira aje ganin dakunan amare Yayin da ta bangarena nake ta danne damuwar auren da Yaya J zai yi da Maijidda. Ita ka'dai ce amaryar da bata da kuzari a dalilin babu ha'din kai ko zumudin ango, komai sai dai mahaifinta ko na angon su yi mata. Gefe guda kuma Nasiba ta susuce domin ba karamin son Bulkachuwa take yi ba, wanda aka ce ya fito kuma a dangin Babanta sun ce bai shirya ba sai bad'i. Bulkachuwa kuwa yarinyar da suke takaddama ta haihu an yi gwajin halittar dan Adam bashi da alaka da jaririn. Sai dai an yi masa hukuncin bulala tamanin tunda ya amsa da bakinsa ya ta'ba takarta. Wannan lamarin, da bulalar ya yi matu'kar sururuta shi. Ya zama abin tausayi, duk wani iyashegensa ya zubar da rabi. Kowa ya ganshi sai ya tausaya masa. Hatta ni da bama ga maciji sai da na yi masa jaje. cike da alhini, ya dinga fa'din na gode "Asiya Toro, ki yafe mini, a duk sadda na tuna addu'ar da kika yi mini cikin fishi da kika ce sai na hadu da sharrin mace, sai na ce ashe dai Asiya bayan samun tallafin dan aljani yayin fa'da, har baki idan kika yiwa banu adam sai sun taimake ki, ya zama wajabat. Shiyasa na k'udire zan roke ki, ki mini addu'a na zama yadda mutane na gari suke". Na girgiza kai na wuce shi "Ina cewa "Allah ya shirye ka Tijjani". Ya d'aga murya ya ce "Da biyu kika yi wannan addu'a domin da zuciyarki fes take da ni Yaya Tijjani zaki ce". Ban tsaya ba, bare na tanka shi, a zuciyata kuwa ina fa'din mashiririci, ba sauya wa zaka yi ba, borin kunya ne kawai, ka zubar da mutuncinka a idon kannenka da iyayenka, Allah ya shirye ka kawai. Shikenan sai na dawo gida, muna ta shirin bikin Nazira. Auren da ya zo tamkar dirar mikiya, ya yi matu'kar rage mini tashin hankalin da nake ciki. Kitso da lalle nake yi babu hutu, tun safe idan na zauna sai magariba, sallah kawai take tayar da ni. Haka nake mika ku'din ga Baba ina fa'din "A dinga siyan kayan cefanen biki Baba" Da farin-ciki yake fa'din "Madallah da Yabi Asiya". Kallo daya za'a mini a gane ina cikin tasku kawai boye wa nake yi, sannan son Babanmu ya fita kunya da tozarta da ake son ya yi, ya danne wanccan damuwar. Domin yadda nake kishin Babanmu da yan k'ofarmu bana jin anan kusa za'a samu mai yin hakan. Shiyasa na cire son jiki, da lalaci nake sana'a, Ubangiji kuma ya haska, ya saka mini hannu, domin a rana ina hada dubu shida zuwa bakwai, mussamna idan kwanakin da ake yin biki ne. Da ce a birnin Kano nake yarfa kunshin nan ai da ku'di masu nauyi zan dinga ha'da wa, amma hakan ma na gode sosai, tunda mafi yawa manyan mata idan sun zo basa bayar da iya ku'din sai sun mini k'ari. Bana kuma jin k'yashin na bayar da komai dan mu yi hidimar mu cikin rufin asiri. Duk yadda Yaya J yake son mu ha'du na rufe kofofin da zasu sa mu kebe. Ranar litinin dukkanmu muna wajen Dada. Ana ta hira, na yi lakwas a dalilin bani da kuzari, ba k'aramin cizona auren J da Maijidda yake yi ba, har addu'a nake yi kada a wayi gari aga zuciyata ta buga a dalilin ba'kin ciki. Kwana nake yi ina kuka, ina kalubalantar wannan hukuncin da aka zartar mini tare da tsanar Baban Tsakiya da Baban Kasuwa. Tabbas a idona su din ba kowa bane face mutane masu son kai kuma y'an jari hujja. Dada sai farin-ciki take zata aurar da jikokinta kusan goma. Ta kalle ni ta ce ",Ke da Nasiba ne aurenku ya yi gardama, ga shi kune fitanannu." Ban kula ta ba domin abin da yake zuciyata fadinsa da ciwonsa sai ni da mahaliccina. Balle Nasiba da ta bari halin da take ciki ya bayyana a komai na ta. Ni mamakin da take bani wai akan Bulkachuwa take wannan ba'kin cikin, sannan abin kaicon shi bai ce yana sonta ba, kawai ya lura da yadda take mararinsa sai yake amfani da hakan yana sata tana yi masa bauta. Misali komin dare zai kawo indomie ya ce ta dafa masa, ko kuma ya ce ta dafa masa ruwan wanka, ko shayi. Haka idan zai fita zai bata mukullin dakinsa ta je ta gyara masa. Bai zame masa komai ba, ya kawo mata kayansa matu'kar zai ga tana wanki, yana fa'din "Ga karo". Bata damuwa hakan zata karba, ta wanke, ta goge. Shi kenan sai yake sassauta mata ya daina yarfa ta. Ita kuma ta dauki son duniya ta d'ora masa bata ko lura da rashin nagartarsa, duk kuma wanda zai zo da nufin yana sonta bata sauararansa, sai Dada ta yi mata wuta wuta. Matu'kar kuwa yana gida ba zata yarda ta fita ba, duk tijarar Dada kuwa. Tunda mahaifiyarta ta ce bai cancanci a bashi aurenta ba, ya dauke mata wuta, ya daina kula ta, ya koma muzurai ne a tsakaninsu shi kenan sai ta k'aratanwa kanta walwala, tunda ba yadda bata yi ba, ya fahimce ta shi kuma ya taurare. Saura kwanaki biyu aure domin tuni gidan ya fara cika da jama'a ana ta hidima tuni an yi wa amare jere. Da ni aka je jeren Adda Nazi, na dinga k'walla a dalilin irin rufin asirin da Ubangiji ya yi mana. Komai ya yi, ba wanda ya zaci za'a samu hakan. Na dawo Yaya J ya rutsa ni a soro. Murya a dushe ya ce "Yabi mene ne ya yi zafi ne, shin gaba zamu yi?" Da sauri na ce "Eh mu yi gabar kawai, yafi mini sauki da na saurare ka." Ya numfasa ya ce "Oh no! Kada ki yi mini hakan, ya miko mini leda mai dan dama. Na dauke kai na ce "Bana bukatar komai na ka". Ya rausayar da kai ya ce "saboda zumunci na baki fah". Na ce "To kuwa bana so, domin na shafe alakar da ta ha'damu". Ya fusata, sai kuma ya ha'diye dukkan fishin ya ce "To karbi dan Allah, dan soyayyar da nake yi miki". Na mika hannu na kar'ba ba tare da na ce uffan ba. Ya sassauta ya ce "Wannan auren ba zabina ba ne Yabi, ba abin da zuciyata ta za'ba mini ba ne. Dan haka zan yiwa kaina auren da zuciyata take so take kuma muradi. Na rok'e ki, kada ki juya mini baya. Kada ki haramta mini farin ciki a zuciyata da rayuwata." Yana diga aya sai kawai na rushe masa da kuka mai tsananin gaske. Fadi nake "Lallai kuwa wato zan yi ta zaman jiran ka ko? To ko dai kallon Yabin mahaukata kake mini ba ta Marina ba?" Ya ki'dima ya ce "me ya kawo wannan maganar? To ai ni ko a turu nake kallon ki ra'ayil aini, zan cigaba da son ki babu gazawa, cikin kowanne hali son ki nake yi, zan kuma cigaba da son ki YABIN J". Na ha'diye kukan da nake yi. Na zuba masa ido na ce "Na gode da soyayyar ka, Allah ya bada lada". Kafin ya yi magana Bulkachuwa ya shigo, ya kalle mu kamar ba zai yi magana ba, sai kuma ya kasa ha'diye maganar ya ce "Poor baby haka kawai kin zuba ido an k'wace miki abin da yake na ki ne, ni fa akan abin da nake so sai dai ayi kare jini, biri jini da ni." Ya kalli J ya ce "Jabir ka daina tare yarinyar nan tunda dai an baka wata ka karba, bar ta ta ji da suyar da kirijinta yake yi mata kawai". Yaya J ya daure fuska ya ce "Menene hakan kuma Bulkachuwa?" Ai kuwa ya ce "Gaskiya ce mana Jabir, ni yanzu da aka hana ni Nasiba ka ga na damu ne? Ai saboda dama soyayyar ba mai karfi ainun ba ce. Da son ya zama so deep da komai zai faru, ba zan yarda na musanya ta da wata ba". *Dukkan littafan Saliha Abubakar Abdullah Zaria akwai su in soft copies a hannuna.* Takaicinsa ya shake Yaya J. Ya nuna shi da yatsa ya ce "Bana son irin haka Bulkachuwa". Ya make kafa'da alamun ko oho ya wuce yana sake fa'din "Ato ai gaskiyar magana kenan, ku barta ta ji da bacin ran da take ciki mana, ai kowa yasan tana sonka, akan idonta da na iyayenta aka dauki wata aka baka, ka karba da sunan biyayya, amma ka kasa gwada kwanjin ayi maka alfarmar ka ha'de su biyun ka yi wuf da su. Sai kuma ka dinga tare ta kana tayar mata da hankali a wofi. Ita ma k'uruciya ce ya sanya take zubar da hawaye akan ka. Ni yanzu da na fahimci inda aka ajiye ni, na sake yiwa Nasiba kallon soyayya ne? Duk nacin ta bana sauraron ta". Daga haka ya fice gaba'daya. Yayin da Ba'kin ciki mai tsananin gaske ya dabaibaye Yaya J. Ya ce "Ban da ma idon ka babu kunya Bulkachuwa har ka iya tsayawa ka ce zaka fa'da wa wani dai-dai? Ina ka santa, ai kanka zaka fara yiwa bitar gaskiyar kafin wani, wanda tsoron Allah baya iya hana shi aikata kaba'ira, shine zai yi kishin ana bata wa wata lokaci, kai kuma *BAK'AR TA'ADAR* lalata y'ay'an jama'ar da kake yi fa? Ko an ce maka daga sama suka fad'o babu mai kishinsu?" *Annur food Delicious* *Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.* *Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa* *HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna* *Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya* *08039183880* ✍️ *BAKAR TA'ADA* *NA* *SURAYYA DAHIRU GWARAM* *(MRS M.I.NASHE)* *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ──────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.}``` ✏️ ____________(✪)______________ https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *KUN TUNA MAI GYARAN GUDUYO?* *INA NUFIN FASEELAT BABBAR DILA TA G.H.T.* *KO WANNE NAU'IN KAYAN GHT TANA SIYAR DA SU AKAN FARASHI MAI RANGWAME* *KAWAI KU TUNTUBE TA A WANNAN LAMBAR DAN GANIN JERIN KAYAN DA TAKE DA SU* *TUN DAGA KAN SUPPLEMENT, SABULAI DA LIPTON*. *MASANIYA CE AKAN KAYAN G.H.T.* *DOMIN TA SAMU KARRAMA WA DAGA KAMFANIN A BANA*. *HANZARTA KI TUNTUBETA DAN SIYA DAI DAI KO SARI.* *07039269802* *Follow me @Arewa books* https://arewabooks.com/chapter?id=6504c04660ef31f52af5ad6c *VIP 1k* *Regular 500 via* *2384876855* *Surayya Ibrahim* *Zenith Bank.* *08032773332*. *Free pages na daf da tsinke wa* *Ku zo ku shiga tafiyar Yabi. Sa'adan Mk da Guduyon Gudale tuni suna cikin paid group*. 15&16. Bulkachuwa ya juyo ya ce "Tir da masu gori, Albarkar Annabi ba zaka samu Asiya Toro ba, tunda kallon kitse nake yiwa rogo, marar mutunci kawai". Ya juya ya yi tafiyarsa a tunzure. Ya juyo da nufin yi mini magana sai kawai na d'aga masa hannu na ce "Kada ka ce mini komai Yaya J. Wannan maganar fa, gaskiya ce tsagwaro. Na roki arzikin ka bar ni na ji da damuwata". Na juya na tafi. Na bar shi yana fa'din "Kaicon Bulkachuwa, ko har yaushe yasan mutuncin gaskiyar da har yake wannan zugar?" Ina shiga d'akin Gwaggo na zube na fashe da kukan da ya ja hankalinta k'warai da gaske. Ta jani jikinta ta ce "To mene ne kuma? Kin yi k'ok'ari, kin yi ha'kuri, sake daure wa mana, komai zai wuce fa". Na saka hannuna na rike ta sosai, baki na rawa na ce "Yi mini addu'a Gwaggo, ki yafe mini bacin ran da na yi ta sanya ki. Ina jin mutuwa zan yi." "Ba zaki mutu ba Yabi. In sha Allah! Ubangiji ba zai bar ki hakan ba, ai yasan an zalunce ki, amma daure ki cigaba da nuna jarumta, ki cigaba da sha'aninki tamkar baki da wata damuwa." Na ce "Abin ne yake neman fin k'arfina". Na fa'da, kuka na sake kwace mini. Ta dinga bubbuga bayana tana fa'din "yadda aka yi din ne akwai tozarci a ciki, amma ni dama bana son wannan ha'din domin tsananin da zaki fuskanta mai girma ne. Allah ya sa haka ne mafi alheri. Share hawayenki ki d'oro alwallah ki yi ta nafila tunda hantsi ne yanzu." Na kuwa mike ina share idon nawa, na fita da zummar yin alwallah. Na dawo na tarar da ita, tana ganin kayan da suke cikin ledar. Leshi mai kyau, da mayafin da ya dace da shi, da doguwar riga abaya, da takalmi da jakarsa, sai tarkacen sark'a da abin hannu ga kayan kwalliya da turaruka. Da envelope mai dauke da wasika da kudin dinki. Gwaggo ta ce "Wannan kaya masu daraja haka? Ajiye wa za'a yi sai Babanku ya ga ni". Na tayar da sallah ban ce komai ba. Mama da zata dafawa Nazira kazar aure har da Maijidda ta hada ta dafawa. Ina kallo yadda ta samo tattabaru ta hada da saiwowi ta sake dafa musu. Haka Gwaggo ta maze kamar bata gane ba. *Mai bukatar saiwowin dahuwar kaza ko na tattabaru da sauran kaya na mussaman ta mini magana akan lambata 08032773332*. Ina ji, ina ga ni aka daura auren Yaya J d'ina, da Maijidda. A ranar kam buya na yi, a makwabta na yi kukan da ban ta'ba yin irinsa ba. Na dinga jin wani irin abu tamkar zai fasa mini zuciya gaba'daya. Fa'di nake "Ya Allah! Ya Allah". Idan na tuna nagarta da sanyin halinsa sai na ga ba karamar asara na tafka ba, wacce na saddakar ba zan mayar da irinta ba. Har dare ba wanda yasan inda nake, sai da na ji dirin isowar motar daukan amare sannan na fito. Dan ba zai yiwu ace ban raka Nazira d'akinta ba. Da na fahimci Nazira za'a fara kai wa domin motocin kai ta ne suka fara iso wa sai kawai na fa'da daya daga cikin motocin. Sai a dakinta muka ha'du. Duk yadda ta ke lullube a cikin mayafi said da ta riko hannuna ta ri'ke gam tana sake kankame shi tabbacin farin-cikin da take ciki bai sa ta manta tawa damuwar ba. Sai da kowa ya watse aka bar ni da ita, domin dai bamu da wasu kawayen da zasu kai mana dogon dare. Ta kalle ni ta ce "Mu yi ha'kuri Yabi, kara daure wa, idan muna ganin ki a hakan ba wanda zai samu sukuni. Kinga ma yunwa nake ji, tun jiya da muka ci abinci ban sake saka komai a bakina ba, ba wanda hankalinsa ya kai a bawa amarya abinci, na sani da kina kusa da ni da kin bani". Na ce "Afuwan Adda Nazi, amma ai yanzun nan Malam Yunus zai shayar da ke nama da madara". Ta galla mini harara tare da fa'din aku sarkin magana". Na mike domin na ji ana fa'din mai motar ya dawo. Da k'yar ta bar ni na tafi, tana kuka, ina yi. Kwanaki ukun da suka biyo bayan bikinsu Yaya J sun fi ko wanne tsauri a gare ni. Sa'ar da na yi ma ba a gidan aka yi masa gini ba, a can bayan gari ne da kansa ya gina abinsa sai dai da tallafin Baban Tsakiya. K'aramin gida mai fasali na ban sha'awa, ba burin da banci akan wannan gidan ba. Ko bandakin gidanmu da yake sani takaici, da zarar na tuno bandakina a cikin daki yake a gidan Yaya J sai komai ya wanke mini, na yi ta zumudin zuwan lokacin da zamu yi aure, ashe dai wasikar jaki nake tsara wa. Tayals a ko ina, ga furanni har da fasadabir ya shuka mini, ga bishiyar mangawaro da ni na bayar da kwallon ya shuka, ita ma ta kama sosai. Amma tashi guda aka ruguza mini komai, Maijidda na cikinsa an kuma sake kawata mata gidan da kayan alfarma domin takanas aka tafi Jos aka siyo mata furnitures, ko yaran Baban Tsakiya su Firdausi basu samu gatan ta ba. Haka na dinga rama tamkar ku'din guzuri. Ban samu sassauci ba sai da aka doshi kwanaki ashirin da auren a dalilin na koma zuwa makarantar boko mun shiga aji shida. Da k'yar Dada ta bari muka koma. Gaba'daya na zama shiru shiru, idan ba kure ni aka yi ba, na daina fa'da, ko yara na gani sai dai na rabasu na yi musu sulhu. Amma na daina rama wa wani duka, bare ni na doku da kaina. Duk da yadda na canja ba yaron da yake kuka sabo da ni, ban tsira a wajen mutan Gidanmu ba. Gaisuwata da kyar Baffanina suke amsa wa. Na rasa laifina, zamu gansu tare da Nasiba mu gaishe su, su amsa ta ta gaisuwar cikin walwala har suna ambaton sunan ta amma ban da ni. Na fa'dawa Gwaggo ta ce "Na cigaba da gaishe su kada na gaji suna da hakkin na mutuntatasu. A sanyaye na ce "Gwaggo ni bani da hakkin su sakar mini fuska su mua'amalance ni da mutunci tunda jininsu ce ba agola ba? Nasiba fa ba yar gidan nan ba ce, amma ace ta fini a wajensu?" A duk sadda na yi mata wannan k'orafin dauke kai take yi ta ce "To ai laifukan da kika yi musu ne, da yawa, sannan ita Nasiba ko ba y'ar gidan ba ce amma tana da wata alfarma tunda a ko ina ana son y'ay'an da yar'uwa mace ta haifa, ke ma ai har da halin ki ya sanya suke yi miki hakan". Idan ta fa'di hakan sai kawai na kalle ta na yi shiru, domin na sani ta fa'da ne dan kawai na fahimci girmansu. Ba dan suna yi mini adalci ba. Har sati uku sannan na warware na rungumi zuwa makaranta duk da karatun ma sai a hankali saboda kewar Nazira na damuna. Dada kuwa fa'di take na fito da miji domin wanda za'a bawa Nasiba ya ce "Kowanne lokaci zai iya gama gidansa ba sai bad'i ba, ita kuwa ranar auren Nasiba ita ce rana ta, ko na fito da miji, ko a bani Malam Nata'ala shine damo sarkin ha'kurin da zai jure wa dukkan iya shegena. Malam Nata'ala dattijo ne da yake zaune a unguwarmu mutumin kirki ne kwarai da gaske matansa biyu da yara da dama, tsanagaya ce da shi ma'ana Malami ne mai almajirai. Ban wani dauki maganarsa da Dada ta ambata da muhimmanci ba, illah k'anzon kurege. Kwanci tashi asarar mai rai har aka cinye kwanakin wata da auren su Nazira. Har lokacin kuma ban yarda na je gidanta ba duk nacin aikar da take akan tana nema na. Ikilima ce take zuwa akai akai duk sadda ta je kuma akwai abin da zata bata ta kawo mini na ci ko na sha. Ga wasiku birjik tunda bani da waya duk da an kawo mini har uku amma Baban Marina ya ce "Baya son mu ri'ke waya. Duk yadda Yaya J yake nacin mu hadu gaba'daya na tsike zuciyata, domin yanzu haushinsa nake ji ba ka'dan ba. Kan dole ya koma makaranta tunda ya kammala sawes din da yake yi a Jos. Ina cikin wannan yanayin da na cire komai a raina nake iyakacin bakin kokarina wajen mayar da hankali a karatuna, sai dai ba wani fahimta nake sosai ba. Na dai yi sa'a zan iya karatu da rubutu. Na gama fahimtar ni din basirata a wajen kirkirar abin ado ne, misali idan na samu kan mace mai gashi zan b'ata lokaci na yarfa mata kitson da kowa sai ya ce "wow". Haka kuma duk gunjin gashi sai na kitse shi, zana adon lalle kuwa tamkar wanda aka bu'de mini ido. To yanzu da nake sake koyon kwalliyar da ake ya yi, ban jima da fara koyo ba amma har hannuna ya fara fa'da wa. Dan haka na daina takura wa kaina sai dai ina ta kokari dan na samu na ci jarabawar kammala sakandire. Ranar asabar tun safe nake ta murnar zan je gidan Nazira, tunda muka zo duniya bamu ta'ba rabuwa na lokaci mai yawa haka ba. Mutum uku kawai na yarda zan yi wa kitso, duk masu zuwa lalle kuwa ha'kuri nake basu, sai d'aya da take unguwar Nazira, layinsu d'aya domin Naziran ce ta turo mini ita. Dan haka na saka mata lallen a gurguje na barta da nufin ta same ni gidan Naziran na yi mata kitso a can. Da murna nake komai domin Allah ya sani ina son Nazira, ina samun farin-ciki idan ina tare da ita. Har Malaminmu na tarar yana dakon iso wa ta, ga abinci an shirya mini tamkar wata babbar bak'uwa ta mussaman. Spaghetti ce da miyar kifi, saboda ita ce favorite dina. Ga kuma zobo ya sha ha'di an fasa masa k'ank'ara, gefe kuma babbar kula ce shake da pure water da aka jefa masa k'ank'ara yini guda aka yi mini tanadinsa. Da farin-ciki yake taya amaryarsa marabta ta. Ta rungume ni tana k'walla da mitar ashe zan iya yin watsi da ita na tsawon wannan lokacin? Da dariya na ce "Babanmu ne ya ce "Ba zan dinga yi miki sintiri a gida ba". Malam Yunus ya ce "Ba wani sintiri idan kin so ma ki tattaro kayanki ni bazan gaza ba". Na yi dariya ina fa'din "Na gode da karamci, Allah ya sanya alheri". Ya fice ya barmu tare da cewa "Ameen Asiya". Tunda muka zauna hira muke yi, ba a gama wani zancen ba za'a sake, a kama wani. Na bata labarin yadda muka yi da Dada akan Malam Nata'ala. Ta dinga dariya tana tintsira wa tamkar ta samu tab'i. K'wallar dariya a idonta ta ce "Lallai ma tsohuwar nan, ke ce za'a bawa wannan tsohon?" Na taya ta dariya tare da cewa "To ba namiji ba ne? Kuma ai ta ga ya dace da ni ne, tunda ana kore mini duk wanda ya zo da niyyar aure na". Ta yi shiru ta ce "Kawai lokacin yin auren ne da saura, amma ba dai Alaramma ba." Muka shiga hirar duniya, muka ci abinci, muna santi a fili na ce "Na ji da'din ganinki Addah Nazi, Allah ya kara miki kwanciyar hankali, ya kawo zuri'a dayyiba". Ta ce "Ameen Yabi! Yanzu addu'ata mafi yawa taki ce Àllah ya kawo miki miji na gari". Na yi shiru. Ta ce"Baki amsa ba?". Idona ya cika dam da ruwa na ce "Baban Tsakiya ya lashi takobin duk wanda ya zo sai ya b'ata ni, ya fa'di munanan dabi'una kin ga kuwa aure ai zai yi mini wuya tunda kanin mahaifina ne yake fa'din munanan kalami a kaina." Ta yi shiru sai kuma ta ce ",Ba abin da yafi k'arfin addu'a Yabi! Fa'da kawai yake yi ba zai yi hakan ba". Na hade fuska na ce "bana son haka, wanne irin zance kike yi? Kema kin san gaskiya, zai yi abin da yafi haka in dai Alle Badamasi ne" Dariya ta subuce wa Nazira ainun, tana yi tana nuna ni da yatsa tare da ce wa "Ho Yabi". Tsawon lokaci muna hira tana ta bani labarin aure. Na dube ta na ce "Ya ya maganar da ake fa'da na ha'duwar farko, ya take kaya wa?" Ta galla mini harara ta nuna kanta ta ce "Ni kika yi wa wannan tambayar?" Na k'yal-k'yale da dariya ina fa'din "Adda Nazi manya. Yo wa nake da ita da zan tambaya, kawai fa'da mini Malama". Ta leka ta ga ko Iki na jinmu, sai ta ga game take yi a wayarta a falo, mu kuma muna uwar daki. Ta ce "Kawo kunnenki ki ji". Da rawar jiki na mika mata, ai kuwa ta gantsara mini cizo. Na saki kara a ki'dime. Ita kuma ta ci magani tana fa'din "Maganin mai son jin almarin da bai shafe shi ba, maganin mai son jin abin da Allah ya sakaye shi, maganin mai son ya ji sirrin da Annabi ya tsine wa mai bayyana shi". Ai kuwa na fara hawaye ina shesshe ka. Nan da nan ta hau shafa kafa'data tana fa'din "Yi ha'kuri mana Yabina a hankali fa na yi miki, menene zaki zubar da hawayenki?" Na zum'bura baki ina fa'din "Mun bata gaskiya! Kuma dan kin zama babba ce ai dai kinsan fa'da na." Ta yi murmushi ta ce "Ni ban girma ba." Muka yi dariya gaba'daya. Sai lokacin wacce na bari a gida da k'unshi, ta biyo ni, akan na yi mata kitso. Muka fara, yayin da Ikilima ta hau wanke wanke ita kuma Nazira ta hau gyara wajen da muka yi dabdala. Da zan taho ta hado ni da kayan kwalliya masu yawa har Ina fa'din ta kwashe mini kayan ai. Da sabuwar doguwar riga da ko sata bata yi ba, da sabon takalmi. Na kalleta na ce "Ki rage kayan sun yi yawa Adda Nazi". Ta ce "Idan ina da fiye da hakan baki zan yi Yabi". Na jijjiga kai na kasa cewa komai na yi gaba na bar Iki tana dauko mini. Muna tafe ni da Iklima muna hirarmu na ce "Idan kin gaji dai, ki bani na karbi kayan." Ta ce "zan iya Adda Yabi". Muna tafe wani Alhaji sai binmu yake a hankali a cikin dankareriyar motarsa. Duk hon dinsa ban yarda mun tsaya ba. Har muka je gida, bai fasa ba. Muka shige gida, ya yi parking. Dai-dai lokacin Bulkachuwa ya danno kai. Na shige na bar Iki tana lekensa. Ba wani jima wa ta shigo da sauri tana fa'din "Adda Yabi wai ke ya biyo. Yaya Bulkachuwa ya fa'da masa babu maganar wani a kanki, ya bashi ku'di, ya kuma aiko shi wajen ki". Tana rufe baki sai ko ya shigo, daga tsaye ya gaida Gwaggo da Inna yana fa'din "Asiya Toro zo mana". Na yi kamar bazan kula shi ba, sai da Gwaggo ta ce "Yabi wai Yayanki ba magana yake yi miki ba ne? Ni fa bana son wannan wula'kancin na ki". Na mike ina fa'din "Shi ai Tijjani kayan haushinsa yawa ne da shi." Ya yi dariya ya ce "Ashe duk yadda na yi ba'kin jini a wajen Jabir akan ki ban wanke laifina na baya ba?" Muka dan fita wajen k'ofa. Ya sassauta ya ce "Kin ga Àllah ya dubi takaicin da aka cusa miki Asiya Toro! Kin zargo babban kifi. Wannan mutumin son ki yake yi da aure, kwamshinan harkokin addini ne na jahar nan, sannan babban dan kasuwa ne. Mutumin kirki ne, kin ga abin da ya ba ni". Ya nuna mini rafar dubu guda. Na zaro ido na ce "Billahillazi dan yankan kai ne Tijjani! Ban da hakan daga haduwa ya baka dubu dari?" Ya yi dariya ya ce "Kin san istigifari nawa na yi yau kuwa? Na yi yafi dubu goma, Ubangiji kuwa ya yi al'kawarin warware mana komai matu'kar muka dimanci istigifari har da bude kofofin arziki. Bana haufi Ubangiji ne ya turo mini arziki ta hannunsa. Ki yiwa kanki fa'da Asiya kin ga dai ba shiri muke yi da ke ba, amma na fi jin ciwon abin da aka yi miki sama da wanda aka yi mini. Ki saurare shi, ki yi addu'ar zabin Allah. Idan kin samu nutsuwa ki ba shi dama azo a yi auren ki ko kya samu sau'kin masifar gidan nan. Nima kin ga wannan ku'din ajiye wa zan yi wani satin zan bayar akai mini ku'din aure, ko wannan yar'uwar ta ki zata shafa mini lafiya". Na sauya fuska na ce "Nasiba fa bata da laifi Tijjani". Ya kwabe fuska ya ce "To ai ni kuma ko ita ce ka'dai ta rage a duniyar nan na haramta wa kaina ita. Bulkachuwa bai yi wannan arahar ba, ba za'a ci mutuncinsa, a tozarta shi kuma ya lik'e ba". Ya mik'o mini dalleliyar waya a kwalinta ya ce "Da caji da kuma layi a ciki ki kunna zai kira ki." Ya hade hannu alamun rarrashi ya ce pls ki saurare shi ko za'a dace". Na ce "Baba fa ya hana ni rike waya, yanzu haka akwai sabbin wayoyina a ajiye, da wacce Yaya J ya siyo mini, da ta wajen Abdulrashid har biyu. Wai sai na kammala makaranta, ko idan na yi aure na ri'ke". Ya ce "Wannan dai kin ga Babban mutum ne Yabi, ga shi kowa ya yi masa shaidar nagarta. Ki boye ta ba sai an ga ni ba, bana son ya kubuce miki. Bauchi zai kai ki, ba zai ajiye ki anan ba, ko ma Abuja. Babbar waya ce ki yiwa Allah kada ki bari ta salwanta". Ya juya na bi shi da ido ina raya ina ma yadda ake zuba masa kyakkawar sura kuma cikakkiya haka yake da kyakkawar dabi'a da nagarta. Inda a ce shine yake da dabiun Yaya J da ya zama komai an hada masa. Mafi yawan lokacin ina yawan ayyana da Yaya J ne yake ingarma kaman Bulkachuwa da an yi namiji tsayayye mai kyakkawar manufa. Amma halayyar Bulkachuwa shine nak'asunsa, mussaman na yadda yake iya keta alfarmar shari'a yana aikata kaba'ira, ga rashin ta ido, ga shigar iyashege, yau har barima na ga ni makale a kunnensa, gashin kai ya sha tiri (dying) gashinsa mai kyau ne irin na fulanin Bulkachuwa amma ya mayar da shi cibiri cibiri tsabar fitina da son yaudare y'anmatan da ba susan ciwon kansu ba, ga kafiya akan ra'ayinsa, ko k'uda ya shafa masa lafiya wajen naci. *Annur food Delicious* *Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.* *Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa* *HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna* *Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya* *08039183880* Amma akwai tausayi mussaman idan ya ga kina kuka, to kin karya masa lagonsa, sannan yanzu ya fara sanin kishin kansa har yana taya wani ciwon abin da aka yi masa. Ashe da ya fita wajen Baban Marina ya raka wannan mutumin da ko sunansa ban sani ba, ya nemi a bashi izinin fara magana da ni. Baba ya ce "Ya bashi damar neman yardata, amma idan ban amince ba, ba zai mini dole ba. Shi kenan sai Alhaji Mustapha Zaki yake zuwa, ni da kaina kunyar yadda nake yar mitsil a gabansa nake yi. Dogo ne sosai yana kuma da jiki, ga tumbi sai dai tumbin bai yi muni da yawa ba, ustazu ne sosai domin ya tsayar da gemun sunnah. Ku'di yake sakar mini da suturu na alfarma, ga kuma mutunta ahalin gidanmu. Dada kanta sonsa take yi a dalilin idan zai zo sai ya kawo mata rafar sabbin ku'di, y'an 100, da na 50, da na 20. Yana cewa gashi ta ajiye canji a hannunta, duk zuwa kuwa. Ga ledar tufa da kilishi. Nawa kuwa y'an 500 da 200 ne. Bulkachuwa ya zama magayak'insa. Kullum sai ya masa kamfen, fa'di yake "Gidan ki daban zai baki Asiya, idan kika yi sa'a ma Umrar bana da ke za'a yi, aikin hajji kuwa tabbas ne. Ba ruwanki da tsufansa, lallaba ki zai yi. Ni kaina alherin da nake samu a jikinsa ba ka'dan ba ne. Kin ga "Na kalli hannunsa da yake karkada wa. Mukulli na ga ni ya ce "Mashin ya ba ni sabo dal, gwamnatin jahar Bauchi take raba wa matasa, shine ya saka sunana. Dan Allah Asiya ki so mutumin nan, oh wani hanin ga Allah baiwa. Yarinya kin tako arziki, na tabbatar Gwaggo data haife ki da akwai wutar Nepa a time din Wallahi. Na miki murna ma da wannan dan tsurut din bai same ki ba. Ai ke babbar mace ce, sai manyan maza, amma yana tafiya tamkar iska ta hure, kirjinsa duk bai fi allona na makarantar tsangaya ba". Na b'ata rai na ce "Yaya J din kake yiwa haka akan bare? Sannan nima ai y'ar tsurut ce ta ina na zama babbar mace?" Ya murmusa ya ce "Ba sai na bu'de maganar ba, ke ma kinsan yadda ake miki layi ai akwai sirri na mussaman a tare da ke. Na'kasunki biyu ne tsayayyiyar zuciya, kuma taurarriya, da fitsara, dole handle dinki sai tsayyayen namiji k'arfaffa ba lusari irinsa ba". Na sake b'ata rai na ce "To yadda kake ganin zuciyata, tasa har tafi tawa tsayuwa da jarumta". "Ke tafi can, me kika sani? Wai har yau son Jabir kike yi? Tabdi jam lallai so ba k'arya ba ne. Jiya fa na gan shi goye da Maijidda a mashin ina ga d'an yawon shan iska suka fito". Nan da nan idona ya k'ada sosai hawaye ya cika su, ya mike yana fa'din "So sorry Asiya Toro. Ki gode Allah da ya kawo miki Honarable Zaki. Domin da ki yi kuka a inda kike so, gara ki yi a inda ake son ki, da ki yi kuka a gidan cin abinci gara ki yi kuka a gidan daula sosai, domin mu maza da kika ganmu so baya hanamu murza kanku". Na girgiza kai na ce "Zan amince ne idan kai ma ka yarda zaka shirya da Nasiba, ni shaida ce akan ba wanda take kula wa saboda kai". Ya bata fuska ya ce "Kin san Allah? Zan ci mutuncinki Asiya Toro! Kada ki saurare shi mana, shawara na baki saboda ina nufin ki da alheri, idan baki so ba, ki sallame shi, ki jira wanda zaki dinga kuka a gaban murhun gawayi, da kishiya. Ga kuma ba'kin cikin da zaki kunsa a wajen ahalinsa, shasha da bata san me ya dace ba". *Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubi babbar dealer din su Aisha lame* *Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea* *Akwai pop corn* *07036662633*. ✍️ *BAKAR TA'ADA* *NA* *SURAYYA DAHIRU GWARAM* *(MRS M.I.NASHE)* *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ──────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.}``` ✏️ ____________(✪)______________ https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *ALBISHIRINKU* *MASOYAN LITTAFAN MARUBUCIYA HAFSAT C SODANGI*! *DUBA DA YADDA KUKE KEWAR RUBUTUNTA YA SANYA TA YI SHIRIN SAKE DAWOWA DAN TA SAKE MUKU WANI RUBUTUN SABO DAL* *AMMA KAFIN HAKAN TA DAWO MUKU DA TSOFAFFIN LITTAFAN TA ZUWA KAN WAYA, DAN KU SAKE BITA TARE DA NAZARIN KYAWAWAN SAKON DA TAKE NUFIN ISARWA GAREMU*. *A YANZU HAKA LITTAFAI HUDU NE RIGIS* *WAYYO DUNIYA 1-3* *KYAUTATA 1-3* *DAGA K'IN GASKIYA 1-3* *MATA MASU DUNIYA 1-3* *KO WANNE 1K NE AMMA AKWAI DISCOUNT IDAN ZA'A SIYA SAMA DA GUDA DAYA* *MISALI GUDA BIYU-1500* *GUDA UKU 2500* *GUDA HUDU 3500* *ZA'A TURA KUDIN TA ASUSUN MARUBUCIYAR KAMAR HAKA* *0082739293, ACCESS BANK HAFSAT YUNUS ABDULLAHI* *SAI A TURO MINI SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR 08032773332* *SAI NA BADA LITTAFIN DA AKE SO* *MADALLAH DA KARFAFA GUIWARKU* *MADALLAH DA SOYAYYARKU GA RUBUTUNMU* *AKWAI LITTAFANTA SAMA DA GUDA GOMA DA A YANZU SUKE SOFT COPIES, KAWAI KI TAMBAYI DUK WANDA KIKE NEMA A WAJENA CIKIN LITTAFANTA NA BAYA*. *Saura kiris shaufakan kyauta su k'are* *Turka turkar da ke cikin labarin nan kabiran ne. Har yanzu shimfi'da kawai muke yi bamu kutsa labarin ba tukun*. *HANZARTA ki shiga tafiyar dan karfafa guiwarki ga marubuciya da karatun cikin SALAMA.* *Kudin karatun ki 500/1k* *Via 2384876855* *Surayya Ibrahim Dahiru* *Zenith Bank*. *Ko* *7061488065* *Surayya Dahiru Ibrahim* *Opay Bank*. 17&18. Na bishi da ido yana tafiya cikin gajeren wando tiri k'wata, da riga t shirt mai kama da singeleti. Ko kunya baya ji. Na girgiza kai ban ce komai ba dan nasan da dukkan zuciyarsa ya yi magana. Kwanaki suka yi ta shud'ewa har aka samu wata uku da auren ahalin gidanmu, dai-dai da wata biyu da haduwata da kwamishina. Zuwa lokacin alherin da ya same mu ba ka'dan ba ne. Domin ta hannun Yaya Salisu ya saka an gyara mana band'akin k'ofarmu an zamanantar da shi, an yiwa kofar kwaskwarima ta farfad'o sosai. Sannan ya karbi takardun Yaya Salisu da Yaya Rabi'u da alk'warin zai nema musu aikin yi. Hatta Yaya Musa sai da ya saka ya samu tallafin injin nik'a da na markade, kuma Alhamdulillah yana zama wajen sana'ar. Tun Babanmu yana fa'din hidimar ta yi yawa mussamna yadda ake sauke mana kayan abinci, wannan kam duka kofofin gidan ake sauke wa. Har ya koma yin shiru domin dai kwamshina bai fasa ba, sai dai ma ya ce "Tallafi ko samo aikin yi ga matasa ai hakkinsu ne domin y'an jahar Bauchi ne, hanya kawai na yi musu, ko ba ta sanadin Yabi ba, matu'kar ina da damar yin hakan ai nima hakki ne a kaina na yi hakan." Nan da nan na canja tunda cimar Gidanmu ta canja, ga kayan kwalliya da dangin shower gel masu kyau. Domin dukkan setin kayan Oriflame na siye su ta online. A hannun Aisha lame 07036662633 tunda na bude account saboda manyan mata masu yin transfer din kudin lalle. Sutura kuwa duk zuwa sai ya kawo mini su, manyan zannu wa da leshi. Na sake zama so cute, ga fata tana sheki ga kuma sutura ta d'aukar hankali. Hijabai har sun mini yawa duk da ina bawa Nazira da Yaya Ummi, bai ta'ba kawo mini mayafi ba, sai dai abayoyi kaloli daban daban, hakan ya tabbatar mini mai ra'ayin kiyaye ka'idojin shari'a ne. Su Gwaggo kuwa komai zai kawo uku ne tare yake musu babu banbanci, hakan ya sake daga darajarta domin kuwa duk y'ay'an d'akin Mama bata bari ko sabulu suna kawo uku. Sai dai ita ka'dai, idan yan arzikin suna kusa ta samm musu, idan basa kusa sai ta bawa Inna a boye, Gwaggo kuwa ko labari. Bakin Mama ya mutu murus sai dai dama tun abin da na yi a auren Nazira ta saukaka al'amura masu yawa. Ba sai kuma aka fara cece-kucen auren kwadayi za'a yi mini ba, ban da haka ta ina za'a dauki yar mitsitsiya kamata a bawa wannan mutum da idan na tsaya a gabansa sai a zaci yarsa ce bama ta fari ba. Su Baban Tsakiya suka fara raddi, domin ba karamin gyagije wa ahalin Baban Marina muka fara ba. Dada ta fara taka tsantsan da lamarina, tunda yanzu tana samun kayan ciye ciye da ku'di saboda ni, ga turare da atamfofi da ya kawo mata har sau uku. Ni da kaina na gamsu ku'di suna kan gaba wajen magance tozarcin d'an-adam, haka nan suna saka wa a ga girman ka aji tsoron zuciyar ka ko da baka da siffa mai kyau. A raina sai k'yamar wannan *BAK'AR TA'ADAR* nake yi. Domin na hakikance rashin wadata ya sanya aka mayar da ubanmu ya koma k'arami a cikin gidanmu, wai daga d'an zuwan Kwamshina har an fara raga masa, inda ace shine mai ku'din ko wani cikin y'ay'ansa fa? Sai dai Baban Tsakiya da na Kasuwa basu sanya wa lamarin albarka ba, asalima fadi suke a ina na hadu da shi? Ba d'an gari ba? A sharholiyarmu muka ha'du kawai. A raina bana sonsa, bana burin aurensa, amma ya zan yi? Tunda shi ka'dai ne ya tsaya ya na sona a yanzu, sannan gaskiya na gaji da zaman Gidanmu ba dan komai ba, sai dan yadda nake shan matsin lambar na fito da miji da kuma k'iyayya da aibantawa. Sannan tunda ake yin hassada a lamarin, sai na kudire zan sadaukar da komai na aure shi, ko dan ya zame mana garkuwa a k'ofarmu tunda mutumin kirki ne wanda ya siffantu da dabi'aun addini. Rannan kwatsam na fito daga inda nake koyon kwalliya sai ganin Yaya J na yi a zaune kan wani dutse da alamu suka nuna dakona yake yi. Na zo zan wuce ta gabansa tunda ba zai yiwu na koma na fasa tafiyar ba. Sanye nake da k'aton hijabina har kasa irin wadda ake ya yi mai hula ta baya. Ban ce masa k'ala kanzil ba, asalima ban nuna na ganshi ko na san shi ba. Da azama ya biyo ni a fusace ya ce "Yabi ashe zaki iya ganina ki mini irin wannan wula'kancin?" Ban ce komai ba, ban kuma fasa tafiya ta ba. Yana bina yana fa'din "Tun jiya ban runtsa ba, ba abin da nake so irin na ganki na tambaye ki abin da ya rikita mini al'amura". Na tsaya cak na ce "Tambaye ni Jabir, ina jin ka". Ya zuba mini ido, nima na zuba masa tsawon lokaci, ga mamakina sai kawai abin da na binne a kansa ya nemi taso mini da k'arfin gaske. Na yi maza na dauke kaina, tare da sake d'aure fuska. A sanyaye ya ce "Da gaske ne Mustapha Zaki yana son ki?" Ba ja in ja na ce "Da gaske ne". Ya kadu amma sai ya ce "Ke nan kin amince masa?" Na kalle shi cikin ido, na ce "ko ban amince dan ra'din kaina ba, idan kaddara ta amince masa ai shike nan kamar yadda kaddara ta amince maka zama da Maijidda". Na yi gaba na fara tafiya, ya biyo ni yana fa'din"me kike nufi Yabi?" Ban kula shi ba, domin gaba'daya wani irin abu ya cushe mini zuciya da mak'oshi. Sai fa'di yake "Kina nufin zaki aure shi ke nan?" A tunzure na juyo na ce "A a ba aurensa zan yi ba, debe mini kewa zai yi, kafin a sahale maka ka nemi aure na". Ya girgiza kai ya ce "Wacce irin magana ce haka Yabi?" Kai tsaye na ce "Mai da'di kuma ta gaskiya". Ya rasa yadda zai yi, hankalinsa ya kai k'ololuwar tashi. Ya saki gauron numfashi ya ce "To ni kuma mene ne makomata ke nan? Na kadu na ce "Ban gane ba? Nusar da ni." Kai tsaye ya ce "Ina nufin ya maganar tawa soyayyar, ya batun aurenmu?" Na kafe shi da ido cikin tsananin kad'uwa. Kawai tambayar kaina nake yi "Ko dai ya samu mental disorder ne? Amma sai na shanye mamakina na ce "Jabir ke nan". Da sauri ya ce "ki ha'da ki ce Jabir Badamasi Toro, ba komai ba ne watarana In sha Allah zaki dawo da yayan domin ko kin yanke alakar da ta ha'damu ai baki isa ki wanke jinin da ya cakudamu ba" Na daure fuska ainun ban ce k'ala ba. Ya ce "Fa'da mini inda kika ajiye ni Yabi! Ina son ki, ina son na rayu da ke, ki yiwa Allah kada ki zalunci zuciyoyinmu, ki mini adalci ko da kina mini kallon azzalumi." Na murmusa na ce " Wanne irin adalci kake nufin na yi maka?" Ba nauyi ya ce "ki aure ni Yabi, ki bani damar da zan rayu da ke". Ido cikin ido na ce "To kuma ya zaka yi da Maijidda da aka baka dan ana ganin ta fini nagarta, kuma y'ar babbar k'ofa ce?" Ya ha'de rai ya ce "Ni da ke ne anan ba ruwanki da kowa, ni nake tsaye a gabanbki, kin sani kuma ina son ki, ina kaunar ki, idan kin bani dama ina da sauran dama uku a gaba da shari'a ta bani". Na jinjina k'arfin halinsa na murmusa na ce "zaka ha'da ni da Maijidda kishi? D'iyar attajiri irin Baban Kasuwa da ta fak'iri irin Baban Marina?" Ya naushi hanunsa ya ce "Kina da bak'ar magana Yabi! Ki yi kokarin kiyaye harshen ki, gubar harshe ta fi ta maciji dafi". Na yi gajeriyar dariya na ce ", Gaskiya na fa'da amma tunda ba'a sonta, to na janye" Nan da nan ya sace ya ce "To ki yafe mini, ina son ki, idan har kika ba ni dama zan tsaya miki, ba zaki yi kuka da ni ba. Zan fafata da duk wanda ya nemi shatale farin-cikinki da iznin Lillahi." Idona ya k'ada tsakanina da Allah ina matu'kar son Yaya J ba kowa zai fahimci hakan ba sai wanda suka yi soyayyar k'uruciya ta rikide ta zama ta gaske, irin wannan soyayyar tana matu'kar tasiri a cikin zuciyar banu adam. Amma na sani idan zan yaudari kowa, bazan yaudari kaina ba. Ba za'a ta'ba bari ya aure ni ba. Bayan k'iyayyar ubana to ni kaina wata irin kiyayya iyayensa suke mini wanda basu ki su gan ni da abin kunya ba. Dan haka hawaye ya b'alle mini, da rawar murya na ce "Yaya J ba kowanne Dan Adam ba ne yake nasarar rayuwa da wanda yake so. Mata da yawa ba wanda suke so k'addara ta aura musu ba, hakan nan mazan. Yarda da k'addara kuma sharadi ne na cikar imani. Ka sani, na sani ba za'a ta'ba barinka ka aure ni ba. Na tabbatar za'a bari ka auro ukun da kake kirari a ko'ina amma kuma ba za'a bari ka aure ni ka'dai ba, na gamsu kana sona, nima kuma har yau din nan ban so wani kamar ka ba, ba kuma zan so din ba. Mu yi addu'a Ubangiji ya sanyamu cikin masu soyayya dominsa wanda sakamakon hakan Aljannah ce". Idonsa ya k'ada ya ce "kin yi magana ta hankali Yabin J. Rabon da na samu aminci irin na yau, tun kafin ki juya mini baya. Abin da nake so da ke na yarda na gasgata ki, amma ki bani dama na sake jarraba wa ko za'a dace a wannan karon, zan yi iya kokarina dan na same ki, ai na yi biyayyar a farko". Na murmusa na ce "Shari'a bata hana hakan ba, amma zan ji nauyi mai yawa a ce ina kishi da Maijidda! Sai kuka ya subuce mini na gaske". A rikice ya ce "Wallahi zan iya rabuwa da ita matu'kar ita ce cikas din cikar burin ranmu. Sai dai ace na aikata *BAK'AR TA'ADAH* na saki aure akan wata macen da bata zo hannuna ba". Na girgiza kai na ce "Ba za'a kai ga hakan ba". A hanzarce ya ce "To ki huce da ni, ki bani damar auren ki". Hawaye na zuba na ce "Na baka Yaya J. Nan da sati biyu ka fito, idan har ya wuce baka bayyana a gaban Baban Tsakiya da Baban Kasuwa da nufin ka je neman aurena gabansu ba, ka tabbatar magana ta k'are a tsakaninmu ta soyayya har abada, na kuma baka dukkan damar da zan iya, sai dai ka sani ba zaka ha'da ni zama da ita a gida guda ba". Ga mamakina sai gani na yi ya zube a kasa yana sujjada. Ya dago ya ce "Alhamdulillah! Alhamdulillah! Alhamdulillah. Zaki ji sakona kuwa daga yanzu zuwa ko wanne lokaci. Sannan na miki al'kawarin a Bauchi zan nema miki inda zaki zauna kafin na samu halin gina miki naki gidan". Ya tako mini har titi ya tarar mini Napep ya biya, na tafi yana d'ago mini hannu cikin matsanancin farin-ciki. Ni kaina wani irin shauki ke fizgata mai danne dukkan bacin rai. Na manta k'iyayyar da Baban Tsakiya yake mini azima ce. Sannan Baban kasuwa ba yadda za a yi ya goyi bayan ayi wa diyarsa kishiya da ni. Amma dukkanmu hankalinmu ya gushe duk da ni din gatse na yi masa, amma TASIRIN soyayyar da nake yi masa ta taso mini haik'an ta saukar mini da farin-ciki mai tsananin gaske. Har nake fatan al'amarinmu ya kasance. Na isa gida na ci abinci na yi sallah na hau kitso tunda mutum uku na tarar suna jirana. Da yake a cikin nisha'di nake kafin ka ce kwabo duk na kitse musu. Hatta Gwaggo sai da ta fahimci irin walwalar da nake ciki, rabon da ta ganni hakan tun komai bai tabarbare mini ba. Ina idar da sallar isha na nufi wajen Dada. Na tarar ta idar da sallar ita ma tana jan dogon carbinta. Ni da Nasiba muke hirarmu, akan makaranta. Dada ta shafa addu'a. Muka gaishe ta ta amsa da walwala a dalilin yanzu shiri take yi da ni tunda tana samun alheri a dalilina. A sanyaye Nasiba ta ce "Kin daina d'ora mana karatu dai Dada". Ta murmusa ta ce "To kuwa yau zamu yi. Zan d'ora muku addu'ar da idan kuka lazumce ta babu ku babu yunwa ila yaumil k'iyamati, ina nufin duk tsanani, Ubangiji zai yassare muku abin da zaku ci". Nan da nan na nutsu domin idan na ji ingancinta na d'orawa Yaya Ummi domin ita kam tana wahala kafin ta k'oshi. Ta gyara zama ta ce " *ALLAHUMMA RABBANA ANZIR ALAINA MA'IDATUN MINAS SAMA'I TAKULU LAANA IDDAL LI AUWALI WAL AKIRI...*" Da sauri na ce "Ai mun haddace tuni, a cikin suratul ma'ida take Ashe haka take da falala Dada". Ta washe baki ta ce "Ai wani bajimin Malami ya tabbatar mana matu'kar zaka biya wannan addu'a to haularka ba dai su rasa abinci ba bare kuma kai da kake bitar ta". Na 'kyal-k'yale da dariya domin ni na dakatar da ita ne saboda kurakurai da na ji a ciki. Tunda ba yarda zata yi na gyara mata ba. Ta ce to "Kun ga ni, ni da ku ne anan zan d'ora muku wata muhimmiyar addu'a, sadakar da zaku bayar ku yiwa Annabi salati, ku nema wa Shehu karin karama". Cikin zakuwa muka ce "To". Ta yi kasa da murya ta ce " ku dimanci *Ya ladifu* Idan kun yi dari ba daya a cikon na dari ku rufe da fa'din *"Allahu ladifin bil ibadihi, yar-Razaku man ya shaa'u Wallahu Qawiyin Azim*". Karon farko da Dada ta biya karatun da babu kuskure, da haka na dage nake ta biya wa a zuwan koyo nake yi, ita kuma sai fa'di take, tana sake gyara mini". Muka kammala tana jaddada mu ri'ke adduoin nan falalarsu ta kai matu'kar shahara.Ya ladifu kundin sirri ne, gashi babu wahalar fa'da. Na maze domin tsokanar ta zan yi, dan na ga reactions d'inta. Na ce "Dada ki daina jan carbi fa, babu kyau Annabi ya ce mu yi da yatsun hannunmu domin su mana shaida ranar gobe". Ta b'ata fuska kamar ba zata yi magana ba, sai kuma ta kufula ta ce "Asiya tun kafin a haifi Ubanki nake jan jarbi, duk wani sabon addini da kuke son kawo wa na raini Wallahi ba zai yi tasiri a wajenmu ba". Nasiba ta fashe da dariya yayin da nake jira ta tara mini gayya irin wanda ta mini watannin baya, amma na ji muk'us. Na jijjiga kai a raina sai fa'di nake "Allah ka sake bawa Yabi tsaron da ba za'a dinga tozarta ta ba." Ta ja robar maganinta da Honarabil ya kawo mata na warwarewar gajiyar tsufa da kara kuzari. Sai kuma na daidaita siga da bugawar zuciya duka daga kamfanin G.H.T. Na murmusa ina tuna a wajen FASEELAT ba zai kai kudin da na ga ni a manne a jikinsu ba. Na Santa a littafin Guduyo. Nemi dukkan nau'in kayan ght daga gare ta cikin RANGWAME. *07039269802* Muna cikin haka sai ga Yaya J. Ya sha kwalliya da wani farin yadi, d'inkin ya zauna masa sosai. Ga kamshin turaren Dagmar ya baibayemu. Cikin farin-ciki Dada take fadin maraba da Jabiru angon Maijidda". Zuciyata ta buga da k'arfi, shi kuma ya dan diriri ce. Ya waske da ce wa "Angon Dada dai, ai ke ce ta karfen". Ta yi dariya ta ce "Yaudara ke nan." Ya gaishe ta ta amsa da walwala tana tambayar amaryarsa. Ya bata amsa da ce wa"Tana lafiya a gajar ce. Ya shige cikin dakinta yana cewa "Zo mu yi sirri Dada". Ta rarrafa ta bishi domin kuwa mutuminta ne baya rabuwa da kawo mata tsire da turare. Ita kuwa duk wanda zai mata ungo tana mutunta shi. Muka ci gaba da hirarmu wacce galibi Nasiba tana fa'da mini ciwon da take ji akan sharewar da Bulkachuwa ya yi mata. Fa'di take "Dan Allah laifina ne? Inda ya fahimce ni, da ya k'arfafa soyayyarmu ai komai za'a mini bazan kula kowa ba, amma daga maganar fatar baki ya d'ife, ya ce kada na kuma shiga sha'aninsa. Da yana sona ba zai yi irin wannan fishin ba." Ta fa'da k'walla na zubo mata. Jikina ya yi sanyi ainun domin kuwa Bulkachuwa ya riga ya yi rantsuwar ya yanke hulda da ita. Kamar daga sama na ji muryar Dada cikin karadi tana cewa "Ina! Jabiru ka zo da *BAK'AR TA'ADAH* Mai wahalar tabbatuwa, ta ya ya zaka ha'da mini jikoki kishi? Dama kuma ba jituwa suke yi ba. Ha'kuri zaka yi da Yabi domin tuni ta samu miji ita ma, dattijon arziki irin albarka." A sanyaye na ji yo shi yana ce wa "Idan ban samu goyon bayan ki ba akwai matsala Dada. Kin sani Yabi nake so tun fil'azal. Amma saboda na yi biyayya ya sanya na karbi auren Maijidda. Yanzu da nake son na cike wanccan burin nawa ba sai a taimake ni ba?". Ya dinga magiya, tamkar zai fashe da kuka. Cikin kad'uwa ta ce "Jabiru ka zo da babban al'amarin da yafi Dutsen dala nauyi. Bana jin iyayenku ma zasu amince maka, ka bar maganar nan tun baka tono wani bacin ran ba". Ba shakka ko nauyi ya ce "Ba zan barta ba Dada! Domin da zan iya barinta da ko ke baza ki ji ba. Idan ba zaki taimake ni ba, to ki mini adalci kada ki b'ata al'amarin a gaban iyayenmu". Ta ce "ita Yabi ta gamsu zata aure ka ka had'asu da Maijidda?" Da sauri ya ce "Ina da tabbacin soyayyarmu ba zata yi zangwayenwar da babu alfarma ko fahimta ba, ban tuntu'beta ba, amma ina da yakinin ba zata juya mini baya ba". Tsawon lokaci sun yi jigum jigum, muma da muka bar maganarmu muka kashe kunne muna jiyosu, jikinmu ya yi la'asar". Nasiba ta ce "Tabbas soyayyar da take ta gaskiya kuma k'arfaffa ce ake yin afuwa da sassauci a cikinta." Na kasa cewa komai domin hausa ta yi cikin hikima. Da Bulkachuwa take. Bansan ya aka yi ba, kawai sai ganinsa na yi ya fito ya fice a hanzarce. Sai ga Dada ma ta fito cikin rashin sukuni. Ta zauna jiki a sanyaye. Ta kasa jure wa ta kalle ni ta ce "Yabi Jabiru zai ballo wani irin tashin hankali, kada ki sake ki saurare shi. Ki rike Alhaji nan yafi miki, ina tsoron abin da zai biyo baya." Na yi k'uri ina kallonta a zahiri gaskiya ta fa'da tashin hankali zai iya biyo baya. Amma kuma a zuciyata sai nake ganin son zuciya ne kawai yasa ba zata goya masa baya ba. Dan kawai Maijidda d'iyar shalelenta ne, kuma mawadacin gidanmu. Dan sai yanzu na fahimci ba fa wai ku'di ne da Baban Kasuwa ba, kawai a gidanmu ne yafi kowa wadata, saboda talakawa ne mu na sosai. Me yasa a farko bata hana a bashi ita ba, tunda tasan ni yake so? Me yasa a wanccan lokacin ba ta yi zaton hakan zai zama tashin hankali a dalilin gaba da kullaci da zai shiga zukatan y'an gidan gaba'daya ba?. Duk yadda nake da ba'kin jinin a cikin ya'nuwana sai da suka yi kishin abin da aka yi mini, suka yarda ubanmu aka tozarta. Tashin hankali tuni an shige shi ai, kawai sa'ar da aka yi Baban Marina mai sassauci ne, shi yake ta tsawatarwa dan kada mu kullaci y'anuwansa ko muce zamu rainasu. Amma iyakacin wula'kanci da kaskanci an yi mana. Ba kuma wanda ya k'alubalanci hakan sai Baba ta Bulkachuwa ita ma kuma bata da power kamar Babanmu. Duk da a cikin rufin asiri take, dai-dai gwargwado tana dan tagazawa wajen yiwa Dada hidima. Haka nan ita ka'daice kafatalin yan'uwan Babanmu zata aiko da wani abu da sallah ta ce a bawa y'ay'ansa. Wani lokacin sark'a da yan kunne, ko hijabai, ko y'an takalma masu sau'ki haka. Dan ko sallar da ta wuce da hijabanta muka je sallar idi ni da Nazira. Amma Baba Maryo uwarsu Nasiba da bata iya tsinana komai har a Dadan ma ita take zuba mulki, haka nan komai aka yiwa Dada na dangin sutura ko wani abu mai k'yau karshe sai ya zama nata ko na y'ay'anta, ita kuma saboda auta ce da ta shiga rai. *BAK'AK'EN TA'ADODI* masu yawa na faruwa a gidanmu da dole duk kawaicinka sai zuciyarka ta motsa sa'i da lokaci. ✍️ *Ina tallata muku kayan gyara na mussaman na mutanan Sudan da chadi*. *Saiwowin dahuwar tattabaru* *Saiwowin dahuwar kaza* *Saiwowin Tsumi da Zaki dafa da kanki, ki ajiye ki sha sosai ya ratsa miki jiki* *Y'aya'n gadali na mussaman* *Hadadden daka emergency* *Tsumin kwakwa da zuma* *Turaren matsi na tsugunno* *Maganin sanyi sadidan na mara har ma da gabobi* *Gumba* *Goran tula syrup and fruits* *Tsumin Goran tula na asali* *Duk zaku same su da RANGWAME kuma na asali me ba karabiti ba.* *Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*. *Tuntube ni a wannan lambar* *08032773332* ✍️ *BAKAR TA'ADA* *NA* *SURAYYA DAHIRU GWARAM* *(MRS M.I.NASHE)* *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ──────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.}``` ✏️ ____________(✪)______________ https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•   *Annur food Delicious* *Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.* *Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa* *HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna* *Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya* *08039183880* *Last free page* *500regular page* *VIP 1k twice pages* *2384876855* *Surayya Ibrahim Dahiru* *Zenith Bank*. *Ko* *7061488065* *Surayya Dahiru Ibrahim.* *Opay Bank.* *08032773332*. 19&20. Jin na yi shiru tsawon lokaci a dalilin tunanin da nake ta yi. Ya sanya Dada ta ce "Yabi da alama zaki bawa Jabiru ha'din kai". Na yi murmushi na ce "A a sai dai na yi imani Ubangiji ne yake shirya komai, dan haka shi na barwa al'amurana ya yi mini zab'i. Dama kuma ban k'ullace shi ba domin ba shine ya mini laifi ba, sannan Dada idan har auren Maijidda da aka sanya ya yi ya bar ni, bai zama abin kaico da rikici ba, ashe kuwa nawa auren da yake hak'ilon yi a yanzu adalci ne da tsantsar gaskiya". Jikin Dada ya yi tub'us tabbacin tasan gaskiya na fad'a. Da k'yar ta ce "Ana barin halak dan kunya Yabi". Are yi murmushin da yake nuna ba wananan maganar. Ta sake ce wa "Kuma yanzu wannan dattijon arzikin sai ki bar shi, duk dawainyar da yake faman yi dake da dukkan dangin ki?" Na sake murmushi na ce "To ai aure gaibu ne, sannan Allah ne ya gadar wa maza su yi ta hidima da macen da suke so dan su ja ra'ayinta. Abin farin cikin ba rok'arsa nake yi ba, haka nan wani nawa bai ta'ba rok'arsa ba." Ta yi shiru ta rasa me zata ce kuma. Sai ta hau addu'a da kamun k'afa a wajen Shehu kada zuri'arta ta rikice a dalilin wannan al'amarin. Har k'asan raina da al'amarin zai yiwu ba wani nauyin da zan ji, domin nawa ne aka k'wace mini saboda kawai zuciyar ahalin gidanmu a cike take da gilli da ba'kin ciki mai yawa. Kwanaki biyu kullum sai na ga Yaya J ya zo gidanmu, kusan a nan yake yini, ba shi k'ofarsu ba shi a wajen Dada. Rashin sukunin da nake ga ni a tare da shi, ya tabbatar mini kasafin ya cud'e fiye da zatonsa. Bai kuma neme ni ba. Kwanaki suka yi ta shud'e wa har aka samu kwanaki bakwai babu tartibiyar maganar Yaya J. Dama na sani mawuyacin abu ne su amince, sai dai dan ya ce zai iya ha'diye gatari ne, shi yasa na sakar masa k'ota ko zai dace ya ha'diye, bayan ya sha kakarin tagwaitakar riskar ajali. Ina cikin wannan yanayin sai ga wani b'acin ran, gidan da Bulkachuwa ya tura su Baba akai masa ku'din aure suka shafa wa idonsu toka suka ce basu san wannan maganar ba, ba zasu dauki y'arsu su bawa wanda aka bulale a bainar nasi bisa k'azamin laifi irin wannan ba, kuma marar tartibiyar sana'a. A sanyaye su Baba suka dawo babu kuzari. Dukkan iyayenmu ukun nan sun ji ciwon abin da aka yi musu. Amma ba wanda ya hango irin wannan tozarcin mai ciwo suka yiwa Babanmu ta hanyar hana Yaya J aure na. Shi kuma Baban Kasuwa ya dauki tasa y'ar ya ba shi. A gabana Baban Marina yake yiwa Bulkachuwa bayanin halin da ake ciki, cikin alhini da bacin rai. Ba wata damuwa mai yawa ya ce "Babu damuwa Baba! Ban damu ba, domin an hana ni aure a cikin gidan nan ma. Dan haka dan waje sun hana ni ba zai zama abin kaico ko tashin hankali a gare ni ba. Ciwon da nake ji daya ne! Da na yarda da hukuncin Allah. Na amince aka mini bulala sai kuma na zama abin k'yama a idon al'umma. A wauta ta imani na yi, domin na yi biyayya ga abin da Allah ya zartar ba tare da bin ra'ayin turawa na yiwa hukuncin Ubangiji tawili ba. Na sani na yi laifin da ku kanku na zubar da darajar gidanku, amma ina yiwa Allah kyakkawan zato zai katange ni daga sake aikata wa tunda na yarda da hukuncinsa, na zabi tereren duniya akan na lahira. Matu'kar kuwa mutane zasu ci gaba da nuna irin wannan *BAK'AR TA'ADAR* Akan mai laifin da ya d'aura d'amarar taubatun nasuha ba shakka zasu dauwamar da mutum cikin b'ata, tunda idan ya dawo kan sahihiyar turba, ba zasu karbe shi ba, ba zai tsira daga yamididinsu ba." Baba ya kasa ce masa k'ala domin jikinsa ya yi sanyi da kalaman na Bulkachuwa. Ni kaina da nake gefensu ina wa Baban Marina wanki ba k'aramin sanyaya jikina kalamunsa suka yi ba. Na sani gaskiya ya fa'da, hana shi aure da ake yi kuma ba shine mafita ba, illah bashi lasisin sake dulmiya cikin zunubin da ake k'yamarsa. Baya ga hakan basu taimaki y'ay'ansu ba, tunda dukkan y'anmata nasa da aka hana shi auren su sonsa suke tamkar su bashi kyautar kansu, ashe kuwa idan ya so lalata rayuwar yaran nasu cikin ruwan sanyi zai yi hakan, tunda Ubangiji ya kyautata masa halittarsa k'warai da gaske . Dan haka zai iya amfani da son da suke masa ya lalatasu a banza, idan kuma hakan ta faru zai yi wahalar gaske ya karbi aurensu domin komin lalace war namiji baya son lalatacciya. Cigaba aka samu ko tabarbare wa? A wannan rana na fahimci ashe cikakken mutum ne mai nutsuwa, kawai sharholiyar ce ta yi masa k'awanya. Ya katse shirun da Baba ya yi ta hanyar ce wa "Baba na gode sosai, zan cigaba da istigifari, idan al'amura suka sake daidaita mini zan fara sana'a, zan je Bulkachuwa na nemi aure ina da tabbacin a dangin mahaifina ko nafi hakan lalace wa zan samu mai k'arfin halin da zai bani aure tare da fatan auren ya zame mini sanadin shiriya da bud'ewar arziki." Ya mike ya tafi yana sake godiya sosai. Ajiyar zuciya kawai Baban Marina yake yi, na lura ba k'aramin ki'dima ya shiga akan al'amarin ba. Murya babu amo ya ce "Yabi idan kina son Alhaji ki ce masa ya turo wakilansa, idan kuma ba kya sonsa to ki fa'da mini zan sallame shi". Na yi k'asa da kaina na kasa amsa masa, daga haka kuma sai ya fita, na bishi da ido amma tunanin a yadda jikin Baba ya mutu murus akan al'amarin Bulkachuwa da ace Adda Nazira ba ta yi aure ba, Babanmu na iya juya wa nak'asunsa baya, ya bashi auren ta. A fili na furta "Alhamdulillah da Allah ya sanya ta yi auren ta ta barranta da auren tantiri ma'abocin *BAKAKEN TA'ADODI*. Haka kawai sai zuciyata ta buga da tsananin gaske, a dalilin ayyana wa da na yi, wata'kila fa idan ban tsayar da miji ba, Baba yana iya cewa ya bashi ni. Nan da nan na tsirtar da yawu saboda kyankyaminsa da ya taso mini. Gashi dai zabgegen saurayi ne dogo cak mai murdadden jiki tamkar ya fito cikin Kyawawan Tirkawa(Turkish). Amma kwata kwata baya burge ni duk da farar fatarsa da bak'ar sumarsa, da suke rudar y'anmata. Asalima Y'ar tsama muke yi, sassaucin rikicinmu a dalilin kwamshina ne, domin sosai yake yi masa alheri. Ya karbi takardunsa, samun aikin ne dai shiru, amma ana saka rai tunda kwamshina baya wasa kuma mutuminsa ne. Tuni Yaya Salisu ya samu aiki a asibitin Toro a matsayin accountant na asibitin tunda dama bangaren ya karanta. Yaya Rabi'u da Bulkachuwa ne shiru amma akwai kyakkawan zaton suma zai samo musu. Wananan dalilin ne ya sanya ya daina tsokanata ta hanyar muzanta ni. *Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame* *Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea* *Akwai pop corn* *07036662633* A fili na furta "dutse a tsakanina da Bulkachuwa ya Rabb". Ina wankin ina jaddada wa kaina matu'kar Yaya J bai yi yun'kuri mai k'arfi ba, to nan da lokaci kankani zan bawa kwamishina dama ya fito tun zuciyar Baba bata ayyana masa wani al'amarin da zai iya kassara ni, ya dauwamar da ni a cikin ba'kin ciki mai tsananin gaske ba. Na kammala wankina. Mama ta fito ta ce "Yabi anjima zan aike ki gidan Nazira". A ladafce cikin murna na ce "To" Domin kuwa ha'din baki muka yi da Naziran, saboda na yi ta tambayar Baba zani gidanta yana hana wa, basan me yasa yake hana ni zuwa ba, amma bai ta'ba yin k'orafin zuwa koyon sana'ar da nake fita ba kullum. Duk kuwa da ce wa ake yi shargalle nake yi da sunan koyon sana'a. Shiyasa Nazira ta ce wa Mama ta bani kwanuka na kai mata kar aba wa marar wayo ya yi b'arinsu su yi lamba. Tunda idan ita ce ta aike ni Baban ba zai hana ba, ba kuma zai tambayi aiken menene ba. Dan haka a gurguje na shirya na tafi. Muna zaune ina bata labarin yadda muka yi da J. Ta galla mini harara ta ce "um um uhum. Ashe dai Yabin bata san ciwon kanta ba. Har wane ne Jabir kuma? Idonta ya ciko ta ce "Allah ka sanya sai bayan raina zaki zama matarsa!. Jikina ya sabe da rawa na ce " Addda Nazi! Cikin gigita domin ban ta'ba ganin fishi mai yawa a tare da ita irin hakan ba, ita din mai ha'kuri ce, mai kuma sanyin hali ce tamkar dai ba daga tsatson Mama ta duro ba. Murya na rawa na ce "mene ne na wannan mugun fatan Nazira?" Idonta taf cike da hawaye ta ce "Da kin fahimci yadda na k'yamci al'amarin, da baki zo gabana da wannan maganar mai bak'i tamkar zunubi ba. Ban iya fishi ba, shi yasa nake kaffa kaffa da duk abin da zai ha'da ni rikici da jama'a, domin ni kaina ina tsoron fishina ina kuma yawaita neman tsarin Allah da shi. Amma zan fa'da miki, matu'kar kina son ganin fishina da barranta kaina daga al'amarinki to ki cigaba da yi mini wannan maganar da nake fatan ajalina ya riske ni kafin ta wanzu". Sai ta fashe da kuka sosai. Cikin kuma kukan take cewa "Yanzu duk ba'kin cikin da aka cusa wa ubanmu, duk yadda aka wula'kanta ki, dan ke ce asararriya har ki kalli dan Baban Tsakiya da sunan soyayya irin ta aure? Na rantse miki da Allah idan ace Jabir ne ka'dai namiji a duniya gara ki tabbata babu aure, ko ni na mutu ki maye wa mijina madadina da dai Yaya Jabir ya same ki. A haukanki Baban Tsakiya zai bar shi ne? Ko kuwa kwantaccen tunaninki ya fa'da miki Baban Kasuwa zai bashi aurenki alhalin tasa y'ar ce matarsa? Kaico da wannan maganar da kika nufo ni da ita. Nima cikin kuka na ce ",Takura mini ya yi shine na yi masa gatse dan ya shafa mini lafiya." Ta ja tsaki mai tsananin gaske tare da fa'din "Amma shine kike rawar jikin fa'da mini, idan ba kya so me ya sanya zaki yi mararin sanar mini?" Ta nisa ta zarce da fa'din "Idan zaki ha'kura da shi ki hakura Yabi. Domin Jabir ba mijinki bane, na tabbatar duk sanyayyar zuciyar Baban Marina ba zai ta'ba bawa Jabir aurenki ba, ban da dai ma mai k'arfin halin jure damuwa ne da kuma kawaici da tuni bai ha'du da ciwon shanyewar barin jiki ba a dalilin abin da yan'uwansa suka yi masa. Ashe duk zafin ranki, da kishinmu da kike yi a banza ne a kuma fatar baki ce? Wallahi matu'kar zaki nemi zama ahalin gidan Baban Tsakiya ki tabbatar kin fita daga namu ahalin Yabi" Ta tashi ta bar ni tana kuka sosai. Jikina ya mutu wato ba k'aramin gaba ba ce ta shiga dangimu ba kenan? Duk ha'kuri da kawaicin Nazira ita ce take fadin tsauraran kalmomi akan zumunta irin haka? To idan har Nazira mai sau'kin hali da k'ullaci zata yi hakan to ina ga Yaya Ummi shakikiyata kuma mai ra'ayin rikau?. Domin ita hatta zumuncina da Nazira adawa take yi da shi tana ganin ita ce tafi kusa da ni, ita ta cancanci mu yi irin wannan soyayyar, ta kasa fahimtar tazara mai yawa ce a tsakanina da ita, Nazira kuwa tare muka taso tamkar tagwaye, kuma Ubangiji ya jefa mana soyayyar juna duk da k'unbiya k'unbiya irin ta iyaye mata da kishi yake haifar wa. Bare kuma mazan Gidanmu. Yaya Rabi'u shine sa'an Yaya J tare suka taso, bayan jini da ya ha'dasu, abokanta suke yi sosai, amma Yaya Rabi'u da kansa bayan an yiwa J aure da Maijidda na ji yana fa'dar bai k'i wani a duniya har cikin zuciyarsa irin Baffanninmu ba, yana kuma fatan kada a k'addara auren zumunci a tsakanin y'an k'ofarmu da tasu ila yaumil k'iyamati. A sanyaye na bita uwar d'akinta na dinga rarrashinta da k'yar na shawo kanta ta ha'diye kukan nata tamkar yarinya y'ar k'arama haka ta koma mini. Wannan yinin bai yi wani armashi ba tunda zuciyarta ta riga ta baci. Har na dawo gidanmu a takure nake jin kaina, domin ban ji da'din yadda Nazira bata sake mini kamar yadda nake so ba. Na iso gida na tarar da Yaya J gurfane a gaban Baban Tsakiya kansa a k'asa da alamun kuka yake yana fa'din yayi masa alfarma ya bar shi ya yi abin da Allah ya hallata masa. Ba sassauci ko nauyin ganina ya ce "Na gama magana idan baka gamsu ba, ka je ka nemi wanda zai shige maka gaba, babu damuwa, amma fa babu albarkata a ciki". Na shige da sauri, ina ambaton "Innalillahi wa inna ilaihir Rajiun". Ina shiga gida sallar almuru kawai na gabatar na dauki waya na k'ira kwamishina na ce "Baba ya ce ka turo waliyyainka". Ya dinga murna yana sanya alheri da albarka, tare da addu'ar Allah ya sanya yadda na aminta da shi, kada ya kunya ta a idona. Na ajiye wayar ina mamakin ni kuwa a duniya me na tsare wa Baban Tsakiya ne? Na dinga Jin haushin kaina yadda na makance ina son Jabir! A yau na yarda na gamsu tazarar da take tsakaninmu tamkar tazarar sama da kasa ne . Ba zan ce bana son Yaya J ba, domin kuwa ikon zuciyata ba'a hannuna yake ba. Amma na yarda da maganar Nazira ko shi ka'dai ne namiji a duniya to haramun ne a gare ni. Bayan Baban Marina ya dawo gida bayan sallar isha a tsakar gida Inna ta shimfida masa tabarma a dalilin zafi da ake fama da shi. Ya kammala cin abincin da ta gabatar masa kenan. Ya kalli ni duk da muna da tazara ya ce "Yabi zo nan". Zuciyata ta harba da tsananin gaske. Na matsa kusa da shi kamar yadda ya yi mini umarni. Babu sukuni ya ce "Ya ya maganar Alhaji?" Kaina a kasa na ce "Na isar da sakon na ka". Ina rufe baki ya ce "Madallah da Yabi! Ubangiji ya tsare ki, ya sanya albarka a dukkan sha'aninki". Farin-ciki ya mamaye ni, na amsa da ameen da karsashi. Ya sallame Ni. Na shiga dakinmu na tarar da Gwaggo tana ta kulla siganta hankali kwance. A zuciyata ina ta jinjina mata na yadda bata raina riba duk kanknatar ta. Domin sigan nan mafi yawa sai ta yi ciko duk sadda za'a auno mata. Idan na ce ta bari, sai ta ce da bata siyar wa, da ba zamu sha yadda muke so ba. A hankali na ce "Sannu da kokari Gwaggo! Allah dai ya nuna mini ranar da zan hutar da ke zaman kullin sigan nan dan kawai mu saka siga a koko ya ji". Ta yi murmushi tana fa'din Yabi da dogon buri kike, dama ana wuce yin sana'a ne? Na ce "Indai bata kawo ku'di ba. Ta yi murmushi ba tare da ta ce komai ba. Na bu'de baki zan yi maganar sai kawai muka ji sallamar Yaya Jabir a tsakar gidan. Baba ya amsa masa tare da cewa "iso mana Jabiru". Ya zauna a tabarmar ya gaishe shi cikin nutsuwa. Baba ya amsa cikin sakin fuska tare da tambayarsa iyali da karatunsa. Tsawon lokaci Yaya J bai iya cewa Baban komai ba. Sai Baban ne ya ce "Akwai matsala ne Jabiru?". Cikin rauni sosai ya ce "Baba so nake ka bani Yabi na aura". Zuciyata ta buga, na yi matu'kar kasa kunne a kansu, ko kwakkwaran motsi bana son yi. Hatta Gwaggo tsaya wa ta yi tana saurare. Murya da walwala Baba ya ce "Jabiru ka zo inda za'a yi maka komai, ina tabbatar maka da a ce a wani wajen kake son auren da na je na nemo maka. Sai dai da yake y'ar tawa ce shiyasa bazan iya komai ba. Kana da siffar da za'a baka aure babu haufi. Amma akwai mishkiloli da baza su bari na baka Yabi ba. Farko matarka da take hannunka itama y'ata ce da kanina ya haifa. Kasan kuma matan yau basu dauki lamarin kishi da sassauci ba. Ha'dasu kishi zai iya ruguza komai ya mayar dasu abokan gaba, sannan zuri'armu zata dare ne, wasu na bawa Yabi kariya, wasu na bawa Maijidda. Da ace Yabi ka fara aura, ka zo kana son Maijidda daga baya to ina tabbatar maka da sai inda karfina ya kare, domin ina da tasirin da zan lank'awasa ta a zauna lafiya. Amma tunda ka riga ka auri Maijidda a farko, dole a ha'kura da maganar Yabi dan a samu a cigaba da lallaba zumuncin da ya dan yi saura." Tsawon lokaci ban ji Yaya J ya ce komai ba tabbacin ba haka ya so ji ba. Murya ba amo ya ce "Baba kai ne tsanin da nake ganin zan taka dan na samu cikar burina." Baba ya numfasa ya ce "Ai kuwa a wannan karon ba zan zame maka tsanin ba Jabiru. Domin ina sane da yadda Mahaifinka bai amince maka ba, ka yi kankanta da yawa ka jefa kanka a cikin manyan matsaloli, domin auren da kake son yi ba zaka samu nutsuwa da shi ba tunda babu albarkar iyaye, sannan su kansu matan naka ba gode wa kokarinka zasu yi ba, kullum zaka zauna ne cikin zullumin zarge zargensu." Yana dasa aya Yaya J ya ce "Zan jure Baba, zan iya, da sannu Ubangiji zai hore mini su gaba'daya. Sannan ina fatan sanadin wannan auren ya zama silar daidaita al'amura a gidan nan". Ga mamakina sai jin muryar Baban Marina na yi cikin kaushi ya ce "Jabiru ba zan baka ba, na rok'e ka, kar ka kuma dosa ta da wannan tatsuniyar domin ko mak'oshina bata je ba, bare ta shiga zuciyata. Bana son na yi maka abin da zaka mini kallon marar kirki, ko na rashin inganta zumunci, amma idan ka cigaba da dagewa to ba shakka zaka sha mamaki, domin kuwa na riga na haramta soyayyarku a zuciyata, dan haka kai ma ka shafe ta domin ba rayayya bace". Bamu gama fita da mamakin maganganun Baba ba, Yaya J ya sake shayar da mu wani sabon mamakin ta hanyar cewa "To Baba idan kuma Allah bai shafe ta ba, ya raya ta fa?" Takaicinsa ya k'ume Baba ya kasa ce masa komai domin bai ta'ba zaton Yaya J zai iya fada masa hakan ba tunda mutum ne mai biyayya, mai kuma gudun zuciya. A sanyaye ya ce "Kowa ya ki fahimtar halin da nake ciki, me yasa zaka biyesu wajen yin watsi da zumunci Baba? Annabi cewa ya yi mu yiwa wanda basu yi mana ba". A matu'kar zafafe Baban Marina ya ce "To dai ni ne uban Yabi! Ni kuma shari'a ta girmama ta mayar a hakku ya za'ba mata miji, idan kuwa hakane, ko mutuwa ce ta riske ni gabannin na aurar da ita da kaina. To waliyyinta baza su baka ita ba, bare kuma ina fatan a ara mini dama na aurar da ita da kaina. Ka je ka yiwa Mahaifinka biyayya, na gode sosai da soyayyarka. Mu cigaba da addu'a da sannu komai zai dai-daita mana. Amma Yabi kam ba matarka ba ce". Tsawon lokaci bai amsa ba. Ni dai daga sama na ji muryarsa yana cewa "Sai da safe Baba". Ajiyar zuciya mai nauyi na ji Gwaggo ta yi tare da cewa "Alhamdulillah! Ubangiji ka sake nisanta wannan al'amarin kamar yadda ka nisanta gabas da yamma." Na kasa magana, amma dai zuciyata ta yi nauyi, na kuma gamsu da gaske Yaya J yana sona da dukkan zuciyarsa. Gefe guda kuma ina gasgata tsinkayen Nazira da ta ce Baban Marina ma ba zai bashi aurena ba. Na k'udire bazan sake bari mu hadu ba, bare zuciyata ta dinga karaya a dalilin ta so mini da soyayyarsa da nake ta kokarin danne wa da dukkan iya wa ta. Washagari na tashi sukuku ba wanda ya tayar da maganar. Da yamma sai ga kwamshina ya zo, sai da ya fara zuwa wajen Baban Marina a wajen sana'arsa, ya sanar masa nan da kwanaki biyar zai zuro a yi maganar aure da saka rana gaba'daya. Shi yake fa'da mini hakan. A wannan ranar ma kayan da ya kawo mini ba k'aramin yawa ne da su ba. Tunda ga kan sutura, ga provisions tamkar wacce nake rike da kaina. Sai kuma dalleliyar waya da zoben gold wai a matsayin tukuicin amincewa da shi. Tuni Baba ya sallama ya bar ni ina rike waya. Wadanccan ma da ya rike tuni ya fito mini da abina. Dama k'ananu ne sai kawai na ce ya bawa iyayenmu mata tunda uku ne dama. Ni bansan me yake faruwa ba, ashe Yaya J bai fasa sintiri a wajen Mahaifinsa da Dada ba. Da ya kasa samun tallafinsu, sai kawai ya doshi Baban kasuwa mahaifin Maijidda. Nan ma fatattakarsa ya yi tare da alwashin idan mummunar k'addara ta afko aurenmu ya tabbata, to kuwa ya kwana da sanin sai dai ya sako masa Maijidda. Hankali ya fara tashi domin gaba'daya Yaya J ya susuce ya rasa nutsuwa har ta kai Maijidda ta dawo gida a dalilin zaman nasu babu da'di sam, ita kuma ta gaza ha'diye damuwa ta taho, da k'yar Dada ta mayar da ita. Baban Marina da kansa ya fa'da wa Dada da yan'uwansa cewar ranar asabar za'a zo neman auren Yabi, kada su yi nisa. Daga Baban Tsakiya har na Kasuwa suka gabatar da uzzirin suna da daurin aure muhimmi a wannan ranar. A wannan karon hankalin Baban Marina ba k'aramin tashi ya yi da wula'kancin da suke yi masa ba. Ya gabatar da korafinsa gaban Dada cikin kankan da kai ya ce "Ba zai yiwu na dauko wasu daga waje su marabci masu neman auren y'ata ba. Alhalin ga y'anuwana ban da ransu da lafiyarsu, har wanne daurin aure zasu je da yafi al'amarina muhimmanci Dada? Ki shiga cikin wannan maganar, ina jin tsoron kada na kasa jurewa fa." Ita da kanta ta sani ba'a kyautata masa ko ka'dan amma da yake bata iya tsawatar wa wadanccan shiyasa bata iya magana, har komai ya rincab'e. Da rashin walwala ta ce "Zamu zauna da daddare dukkanmu". Da daddare kuwa dukkansu uku suka hadu a gaban mahaifiyarsu, a sanyaye take gabatar da k'orafin da yayansu ya zo da shi. Babu kunya dukkansu suka ce suna kan matsayarsu ba yadda za'a yi suna cikin hankalinsu su jagoranci bawa mai saka d'agaggen wando aure, kema da za'a fito k'arara a fa'da miki ainihin yadda ak'idarsa take da kin k'yamace lamarin wannan mutumin. Mun yi shiru ne kawai dan kada ace hassada muke yi. Ko bamu da kirki, amma waye a jahar nan bai san yadda Mustapha Zaki ya yi k'aurin suna wajen yiwa masu akidar yin maulidi kafar ungulu ba. Duk wani masallaci indai ba na yan kungiyarsa bane sai ya durkushe shi, ke kan ki da yasan yadda kike son shehu da ya d'aure ki saboda zuciyarsa babu alheri." Dada ta kad'u kwarai da gaske. Domin babban b'acin ranta a nemi ta'ba mata mutuncin ra'ayinta. Ita din mai mai zazzafar akida ce akan hakan. Ta fara tafa hannu tana cewa "Ashe hakane? Allah na gode maka da ka kubutar da jinina fa'da wa hannun wanda zai yi mata sanadin rashin samun rabo ranar gobe". Sai ta hau kuka tana sake godiya ga Allah da Annabi. Jikin Baban Marina ya yi matu'kar yin sanyi ta yadda yan'uwansa suka shammace shi, suka gabatar da hujjar da ba mai kankareta a zuciyar Mahaifiyarsu. Ya tabbatar sun dade da kitsa maganar dan sun tabbatar auren ya rushe gaba'daya, kuma wannan hanya ita ce mafi sau'ki da zasu ja hankali gyatumarsu ta lalata komai. A zuciyarsa ya dinga ayyana shin wanne irin zamani muke ciki wanda dan-uwanka ma baya son ya ganka a inuwa? Me ya tare musu ne? Shi ka'dai ne yake fuskantar irin wannan tsananin ko kuwa a ko wacce zuria ce? "Allah kai ne mai zamani, a kawo mana mafita, da sassauci" ya fa'da a ransa. Ya sake kallonsu, yana ganin sun hade sun bar shi daban, sai dai a zahiri ne suke shiri a bad'ini kuwa ba wani taimakon juna a tsakaninsu, tunda kowa iya y'ay'an da ya haifa ne dolensa. Sannan kowannensu boye wa dan-uwansa wadatarsa yake yi. Ya sauke gauron numfashi kafin ya yi magana ya ji Dada tana fa'din "matu'kar ina da iko akan ka ba za'a bashi aure ba, idan kuwa ka kafe sai dai na barka da Ubangijin gizagizai ya bi mini kadina a wajenka". A ki'dime ya ce "Har abada maganar ta mutu, Allah ya yanke mata wahala ya fito mata da wani mafi alheri wanda za'a yi alfahari da shi". Dada ta goge idonta tana fa'din "Ameen". Baban Tsakiya kuwa ya ce "ai y'ar fariya ce , ba zata tsaya a matsayinta ba, dama ya ta kasance? bare yanzu da wannan tsohon banzan ya sake kambaba burinta. Ai idan ba tashi aka yi akan ta ba, sai ta tsofe tana gabanmu tana zuba d'ibar albarka, ko yanzu tana ganin sakamakon hatsabibanci, tunda duk kintsatsse ba zai zo wajenta ba. Har yau ta k'i barin Jabir ya fuskanci matarsa sosai, da sun fara zama lafiya idan har ya yi tozali da Yabi zai gigice. Gashi kuma Maijidda matarsa ce, tunda cikine da ita, idan ba'a bashi aurenta da ake ta munafurci ba, ta ya ya ake so wannan rabon ya bayyana?" Baban kasuwa ya ce " Ai ha'kuri Muna cikinsa, amma sai ace mune da laifi, ban da sha'anin jini tasirinsa yawa ne da shi ai wata shari'a sai a lahira kawai." Dada ta ce "To ni kam ba zaku bar gun nan ba sai an samo wanda za'a ba shi auren Yabi. Domin na fuskanci matsalar gidan nan tana 'damfare da ita." Baban Tsakiya ya sake cafe wa da cewa "Kinsan dai ni da Iliya bamu da mutuncin da zamu yi irin wannan ikon da ita, wannan maganarki ce da ubanta." Cikin rawar murya irin ta sare wa da lamari Baban Marina ya ce "Yau muna watan Safar ko Dada? To matu'kar rayuwata ta kai, watan jibi na gaban maulidi ke nan, zan aurar da ita. Domin ina da wadanda zan basu aurenta su kar'ba, sannan ita ma Ubangiji ya hore mini ita zata ta yi mini biyayya. Ubangiji kuma zai duba manufar kowa a nan ya cusa wa wanda zan ba shi auren ya kar'ba da dukkan zuciyarsa". Dada ta ce "Allah ya tabbatar ya nuna mana lokacin, amma ba za'a tashi ba sai ka fadi wanene, d'an wacce haular ce? Gudun kada a sake kitso da kwarkwata." Baban Tsakiya ya ce "yarinyar nan fa ta riga ta rik'a, idan aka kai ta wani wajen ma mutuncin gidanmu zata zubar, me zai hana a lallaba a bawa wannan yaron kawai, tunda shima yana da tambarin da aure zai yi masa wuyar samu wa?" Baban Kasuwa ya ce "Ni ma tuntuni nake son na fa'di hakan, to amma ina jin tsoron sharrin zuciyar da take raina alheri, yanzun nan sai a juya magana a ce da mugun nufi aka yi kaza". Dada ta ce"Ku yi magana sosai mana, ni duk kun saka ni a duhu ban gane wa kuke nufi ba?" Tirk'ashi Karshen littafi na d'aya. *Gaba'daya wadannan shafuka shimfida ne dan ku fahimci labarin da kyau, asalin labarin da turka turkarsa yana littafi na biyu da na uku* *Bisa soyayyar da kuke yiwa rubutuna ya sanya zan yi muku tsarin VIP. *In Sha Allah babu jira. *Babu posting ranar Lahadi* *Sau biyu za'a yi posting a rana*. *Ku zo mu yi tafiyar da babu nadama* *Zaku dara, zaku koka, jikinku zai tsumu, zuciyoyinku zasu motsu. Tunani kuma zai tafi cancanken me zai faru a gaba*. *Marubuciyar HALIN YAU da SABO DA KAZA* *Yanzu kuma alk'alaminta yana tafe da BAK'AR TA'ADAH* *500regular page* *VIP 1k twice pages* *2384876855* *Surayya Ibrahim Dahiru* *Zenith Bank*. *Ko* *7061488065* *Surayya Dahiru Ibrahim.* *Opay Bank.* *08032773332.* *KUN TUNA MAI GYARAN GUDUYO?* *OK NA NUFIN FASEELAT BABBAR DILA TA G.H.T.* *KO WANNE NAU'IN KAYAN GHT TANA SIYAR DA SU AKAN FARASHI MAI RANGWAME* *KAWAI KU TUNTUBE TA A WANNAN LAMBAR DAN GANIN JERIN KAYAN DA TAKE DA SU* *TUN DAGA KAN SUPPLEMENT, SABULAI DA LIPTON*. *MASANIYA CE AKAN KAMFANIN DOMIN TA SAMU KARRAMA WA DAGA KAMFANIN A BANA, HANZARTA KI TUNTUBETA DAN SIYA DAI DAI KO SARI.* *07039269802 *Surayya Dee* *Yar mutanan Gwaram* ✍️

Post a Comment for "BAKAR TA'ADA BOOK 1 Complete Hausa Novel"