Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

BARIKI Auren Soja Complete Hausa Novel

  __ _*BARIKI Auren Soja Complete Hausa Novel*_ ‍✈ _Auren soja_‍✈ _written by fenerh_ Maman Ammar   *Dedicated to* Fiddousi mainasara *Allahamdulilahi Ala kulli halem ina godiya ga Allah mai kowa mai komai da ya bani ikon dawowa a cikin sabon labari na wato BARIKI Auren soja duk kan yabo da godiya su tabbata ga Allah madaukakin sarki wanda ya bani ikon rubuta wannan labari Alkhairin dake cikin shi Allah yasa Alumma su Amfana dashi kuskuren dake ciki Allah ka gafarta min Ameen* *KADUNA* N.D.A BARRACK convoy ne na sojoji a Jere na hilux sai wata jeep katuwa guda daya a tsakiyar su, Katon gate d'in suka shiga na w'anda gaba daya sojojin dake wurin suka kame Alamar girmama wa ga wanda ke cikin jeep din mai ruwan kalar sojoji,   Jiniya kawai ke tashi Alamar koma waye a ciki babba ne a Aikin, jerin manyan gidajen suka nufa w'anda daga gani na manyan sojoji ne dake cikin barikin wanda sune farkon shigowa, Gidan da yafi kowanne girma suka tsayar da motocin, kuratan sojojin suka fito dauke da bindigogin su tareda kamewa domin jiran Fitowar ogan nasu,   Gaban motar aka bude gefen mai zaman banza wani soja ya fito rike da brief case da kuma manyan wayoyi har ma da jakar laptop duka a hannun shi,   Shi ya bude kofar bayan tare da sarawa da hannun shi daya Alamar girma mawa, w'anda ni a zatona shine ogan saidai ganin wanda yasako kafar shi a waje ai tuni na yi saurin boyewa bayan manyan itacen fulawoyin dake harabar gidan, Wani kyakkyawa kuma kakkarfan matashi ne fari tas dashi ya fito daga bayan motar sanye cikin kakin green na soja, Wanda da Alama da wuya ya kai shekara Arba'in a duniya, ga kakin ya mugun fitoda kwarjinin shi har ma da kara bayyanar da kyanshi a zahiri,   Cikin takun shi mai cike da kasaita da kuzari irin nasu na sojoji jarumai, ya fara takawa domin shiga cikin gidan nashi, Nayi matukar jin mamakin ganin wannan karamin matashin ana bashi girma duk inda ya wuce, General Muhammad Abdullah kenan G.O.C I DIV Nigerian Army Kaduna Mutum mai matukar kwarjini da cikar haiba kana ganin shi kasan yana gina jikin shi ta hanyar training da kuma Abinci mai lafiya, Yakai namiji ta ko ina domin samun kyakkyawan namiji sosai wanda ko wacce mace zataso ta mallaki irin shi,   Kofar gidan nashi ma sojoji ne masu tsaron lafiyar shi, ciki suka shiga shida PA dinshi wanda daga gani Akwai y'ar da mai karfi a tsakanin su da kuma Aminci,   Juyowa yayi cike da bada umarni ya kalle shi "Ahmed take care of them am going to take a bath and rest u can go to your house and rest too, " tank you sir ya fada tareda mikamai kayan shi ya juya domin isa nashi gidan, Motar ogan nasu ya bude ya Ciro bandir din kudi ya mika wa sojojin da suka rako ogan, Sunyi matukar farin ciki shiyasa suke matukar kaunar megidan nasu domin Akwai kyauta kusan kullum sai ya basu kudi su raba, Kafin su wuce, Shima PA din da aka kira da Ahmed ya wuce gidan shi wanda yake gaba kadan da gidan ogan nashi wanda kana gani kasan boys quarters ne duk da suma ba laifi sun tsaru Amma ba kamar gidajen manyan ba, Wata kyakkyawar mace ce ta fito da gudu tareda dan karamin yaronta ta tareshi da murna fal fuskar ta, Da sauri ya riketa da hannu daya shima fuskar shi cike da fara a dajin dad'in ganin farin ciki a fuskar Matar tashi,   "Madam dina ya Akayi kike irin wannan gudu haka kin manta da Ajiya ta ne kikeso kimun Asara? Kankame shi tayi gam tareda fara hawaye w'anda kana gani kasan na farin ciki ne. Da kuma jin dadi, Dagowa tayi tareda Jan hannun shi suka shiga cikin falon su tana cewa " Dadyn Auwal ka tayani murna yau munyi waya da baba harda Mama yau da kanshi zai kawomin Yasmin Ahmed baba ya daina fushi dani, Ta karasa tana fashe wa da kuka, kan kujerun dake falon ya jata tareda rungume su gam ita da yaron shi yana mai lallashin ta daga gani kasan Akwai wata akasa da har yakesa shi jin tausayin Matar tashi,   "Am sory Maryam nasan nine sanadin komai Amma ki daina damun kanki bazan taba juya miki bayaba kuma gashi kinga su baba sun hakura har zai kawo mana uwar rigima da kanshi, To kija mata kunne karta zo tana leka min gidan oga don nasan tasa mai ido, ya furta cike da dariya domin kawar mata da damuwar ta,   Dariya tasa itama tareda goge fuskar ta " ai Yasmin Akwai tsiwa ita wai y'anda mata ke shiga da fitane yasa ta tsane shi kuma ko ganin shi bata taba yiba Amma ta mugun sashi gaba da Zagi, "Hmm pray for him ni kaina ina son oga yayi Aure ko zai rage kwaso mata gidan shi, duk da nasan wasu suke kawo Kansu Amma inaso Allah ya bashi ikon daina wa, Ameen tace tareda zamewa ta fara kwance mai boot din kafar shi ya rungume yaron shi dakyau a kirjin shi, " mama tace kar inyaye Auwal inbari har inhaihu tunda bai kaiba, "haka nafada miki tun farko ai kika kiji yanzu tunda mama ta fada zakiji ai,   Dariya tayi tareda mikewa rikeda takalmin domin fita dasu susha iska, bin bayan ta yayi da kallo yana maijin son Matar tashi har cikin b'argon shi,   Muhammad na shiga falon shi yaci karo da takalmin mace, ya kwalawa kukun shi kira tareda ajiye kayan dake hannun shi akan kujerar dake lafiyayyan falon nashi da ya mugun kaya tuwa da kayan Alatu, Da gudu ya fito yana " yes sir "Emanuel who came? " oga na da madam way day give me money come, Wani irin mugun kallo ya watsa mai tareda cewa "you are very stupid didn't I warn you ? " sory sir ya fada yana kamewa kafin yace wani Abu yaji tace "hy M.A ta fada cikeda yanga da kara'i raya gaba daya surar jikinta a bayyane yake don kusan rabin kirjinta da sukayi ruku'u a bayyane suke, Matsowa tayi tareda rungume shitsam wanda yayi sanadiyyar watsawa Emanuel mugun kallon da ya kwasa a guje yayi kitchen din gidan,   Saurin janyeta yayi tareda daure fuskar shida Sam dama ba Alamar fara'a atare da ita, " why the you come? Marai raicewa tayi tareda cewa "come on baby I miss you so much that's is why I came,   Kafin ya bude baki yayi magana wata budurwa ta fito daga cikin dakin baccin shi sanye da T-shirt dinshi na Como flag rigar ko cinyar ta bata rufe ba domin idan tayi kyakkyawan motsi za a iya ganin pant dinta, Wani irin kallo ya bita dashi tareda kwalawa Emanuel kira cike da bakin ciki, Da gudu ya fito rike da cooking spoon yana sarawa " yes sir, wani irin disgusting look yake aika mai kafin ya ce, "Are you stupid,? " no sir Am sory "na she tell me say..... " come on keep quite, ya fada yana mai ture su duka cike da fada "now All of you out of my house, you All no my rules no one comes to my house without my permission, " and you I will del with you letter, ya nuna Emanuel da hannu kafin ya wuce ciki, binshi sukayi da kallo domin sun saba da halin shi na wulakanci don haka kowacce ta kama gabanta kafin ya jona su da mugayen kuratan yaran shi, Wanka yayi kawai ya haye gado domin ya sauke farali a office kuma bayajin yunwa he just need to rest before going out, ______________________ A zaune suke a barandar kofar apartment dinsu suna shan iska shida iyalin shi kana ganin y'anda yake tarai rayar ta kasan Akwai soyayya mai karfi a tare dasu,   Gefe daya d'an karamin yaron sune ke wasa akan d'an keken shi na yara, Kara shigewa tayi jikin shi tsam, "Ya Akayi ne farin cikin Ahmed? Murmushi tayi tareda fara yimai shagwaba, " wallahi na matsu Yasmin batazo ba inaso inga babana Baban Auwal, "k'arki damu maman Auwal dina komai yazo karshe insha Allah, Tsayuwar mashin din da ya dakko ta yasa tayi saurin mikewa tareda rugawa da gudu ta rungume ta, Itama cike da zumudi ko akwatin ta bata d'auka ba ta rugo suka rungume juna cike da so irin na yan uwan da suka mugun shakuwa da kuma son junan su,   Daka gansu kaga jini daya saidai Yasmin tafi Maryam kyau nesa ba kusa ba duk da ita din kyakkyawa ce sosai Amma Yasmin tafita don ita farinta har wani daukar ido yakeyi, Yarinyar kamar Aljana ga jikinta dai dai da ita, saida suka gama murnar su sannan ta kalle ta " ina babana? "Wallahi baba ya tafi zaria Anki rashi wurin aiki shiyasa nazo ni kadai Amma yace shi zaizo daukata,   Wani iri tayi domin taso ganin mahaifin nata sosai tasa rai, tsaye yayi tareda nan nade hannu yana zabga murmushi domin ganin Abinda sukeyi, Shi ya matso tareda Sallamar mai mashin din ya kallesu to mushiga daga ciki idan kun gama murnar ni ko gani na kanwata batayiba wannan karon nayi fushi, " lah yayana wallahi tsabar murnar ganin rabin jiki ko boy dina Bangani ba sai yanzu ta ruga tareda rungume shi tsab "I miss you my boy,   Ta fada with so much excitement yayi dariya shima yaron kamar ya ganeta A kan kujerun da suka tashi ra zauna tareda zubawa kofar katon gate din ido, " Aunty ina bunsurun can gidan? Saurin rufe mata baki tayi "kiyi shiru kar Baban Auwal ya jiki wallahi kina zagar mai oga, " ai Aunty ban taba ganin namiji mai d'an banzan son mata ba irin shi wallahi ana fadan sojoji na kwashe kwashe nashi karshe ne, Shiyasa bana ko kaunar ganin shi A Rayuwata I hate him to the extend, "Ikon Allah wai maikarfi na bara ina ruwanki da bawan Allah da baruwan shi da harkar mutane kuma bai ko San Allah ya tsiroki ba Amma kinsa mai ido,   " ai Bazai ma San daniba har abada d'an iskan mtsww ta mike tareda nufar cikin gidan domin maganar shi kawai tasa ranta ya baci,   Dariya kawai Maryam tayi domin tasan halin y'ar kanwar tata, ta shiga ciki itama,   Tare sukaci Abinci suna hira atsaka nin su kafin ta fito mata da tsarabar da takawo ma yaron ta na kayan wasa da kuma kayan sawa masu kyau, Sai su kubewa da Daddawa da sauran kayan gargajiya irin na bahaushe daga mama domin tasan basa samu a bariki,   Saida tayi wanka ta shirya cikin kana nan kaya San nan ta dora after dress akai domin tana son tafita tasha iska a wajen gidan dama ta saba duk tazo nan ne wurin zaman ta tana karewa bariki kallo,   Yaron ta ta d'auka ta fito tana tafiya a hankali kamar bataso hannun ta rike da wayar ta hot 8 ta zauna tana karewa gidajen kallo kafin ta sauke akan katon cikin su wato na oga kwata kwata,   Emanuel ne ya fito daga gate din hangota da yayi yasa ya zo da sauri bakin shi har kunne, "My friend don come, ya fada with so much excitement da jin dad'in ganin ta domin sun saba sosai kuma shine ummul khaba isin da yasa ta kara tsanar M.A domin shike bata labarin komai,   Washe mai fararen hakoran ta tayi cike da jin dadi tace " yes woo friend how are you? "Fine mam hope you are not going back and leav me here again? " yeah I will but I will spend one month here with my friend, ta fada tana dariya,   Da yake ba wani kan gado gareshi ba ya ce "come escort me na oga send me' itama kan narawa tace ok Am coming Ciki ta koma tareda janyo hijabi ta dora akan kayan jikinta ta saba yaron ta akafada tace Aunty zamuje yawo da EMA, Kallon ta tayi kafin tace " keda EMA ko sai gyaran Allah kun hadu kun dace wallahi, "He is very funny and friendly wallahi inajin dad'in hira dashi Akwai shafta " kodai gulma ? Keda yayanki ba ruwana   Fita tayi tana dariya sunyi tafiya mai nisa yana gabza mata labari da kuma Abinda ya faru dazu shida ogan shi yaja ya tsaya tareda dora hannu aka, "Ewo I don die I forget wetin oga tell me wo ' come mo we go back and ask him, kallon shi takeyi cike da mamakin wautar shi ko waye ya dauke shi a aiki oho,   Da sauri sauri suka juyo domin yasan yayi laifi karya kara wani, Shikuwa M.A da ya dauki lokaci yana jiran Emanuel ya kawomai sako yaji shiru kuma yanaso ya fita dole ya fito ya tsaya sanye cikin tree quarter da t-shirt na Como flag yayi masifar yin kyau ga wani Annuri da haske dake bayyane a fuskar shi,   Isowar Ahmed wurin shi yasa ya fara mai magana cike da takaici, " you have to find better cook for me I don't like this guy at All can you imaging him letting Kate and that stupid girl chioma in my house? Dariya Ahmed yayi kafin yace "oga sun cika naci ne wallahi bebs din nan naga ka gama yayin su Amma sunki hakura,   " ni bansan me yasa duk Yarinyar da na sake mata fuska sau daya ba sai ta nace min, "farin jini ne oga, Ahmed ya fada cikin dariya, " kodai rashin class I hate that kind of girls, "am idan mun fito daga gidan Hajiya zamu biya unguwar shanu inason inyi renewing wasu'   Yafada tareda yin wani tsadadden murmushin shi mai kyau, dariya Ahmed yayi " oga Karfa mu samo wasu karfen kafar kuma kuma kasan zuby ta kusa zuwa karka hada rigima,   Dariya yayi sosai tunawa da zubyn tashi da yayi domin tsohuwar budurwar shice kuma itace y'ar gidan ministern kudi Yarinyar naji da kyau da gata sun dade tare da juna suna Kwasar muguwar soyayya atsaka nin su, Bata kaunar ganin shi da ko wacce mace duk da itama tana nata Rung's din a kasar wajen da take karatu,   Karaso wa sukayi itada Emanuel suna Kwasar dariya, tunda suka matso yake kallon ta yana mamakin wace mahaukaciyar ce take hira haka da Emanuel gata daga gani kamar tanada hankali,   Tana hango mijin yayar tata da wani a wurin tayi saurin tsayawa daga nesa domin tasan da shine ogan nasu da ake fada kuma wannan ne karon farko da ta fara ganin shi fuska da fuska, "Amma anyi kyan dan maciji ta furta a hankali tareda zabga mai harara da kuma tsaki, w'anda ya ganta sarai domin kallon ta yakeyi sosai batareda ya cire idon shi akan taba,   " she is very beautiful but psycho daga gani kyan ne kawai Amma batada hankali, "Oga I forget wetin you sen......" You are mada Emanuel give me my money ' ya furta cike da jin haushi ya fada motar shi tareda kallon Ahmed "let go before I do something bad here,   Fadawa motar yayi tareda tayarwa domin shine zaija motar ogan na gefen shi yana matsa waya, " wai me ka aikeshi ne ? "Forget that mad man, saida ya matso kusa da Yasmin ya d'an tsaya tareda sauke glass kadan, Kanwata zan shiga gari me kike so? Kawar da kanta tayi domin batason kallon fuskar wannan gayen ko kadan mai kama da Aljani, " bakomai yaya na sai kadawo' "yau baza Asha ice cream din ba da two one two bread ? Dariya kawai tayi har hakoran ta suka bayyana tace bye tareda nufar gidan na y'ar uwar ta, Domin Sam bata son ko minti daya tayi da wannan mutumin, saida sukayi nisa yace " kanwar kace wannan? "Eh sistan maman Auwal ce, " Amma dai kamar itama kalar Emanuel din ce ko ? Dariya yayi tareda cewa "kawai tana son mutane ne kuma sun dade da sabawa dashi tun farkon zuwanta,   " Hmm kawai yace tareda ci gaba da d'anna wayar shi har suka isa lafiyayyar unguwar ta malali dake cikin garin na Kaduna Bakin wani tafkeken gate ya yi horn mai gadi ya wangale mishi ya kutsa hancin katuwar jeep din, tasowa sojojin sukayi tareda Sara mai domin har mai gadin gidan soja ne, Da kanshi ya bude motar ya fito tareda nufar cikin gidan da tundaga bakin kofa yake jiyo hayaniya, yana bude falon gaba daya suka koma wacce ta natsu kamar ruwa ya cinyesu,   Y'an matane guda uku a cikin falon sau wata dattijuwa bai cikar haiba da kamala faratas da ita tana Jan carbi sanye take da less lafiyayye dinkin buba,   Sallamar shi yasa Matar ta dago kanta domin ita Sam hankalin ta baya kan yaran zuciyar ta tay nisa sosai, Washe bakin ta tayi wanda ya bayyanar da hakorin makkan dake gaban hakoranta guda biyu na gold suna sheki,   Saida ya zauna kusa da ita akasa kafin yace "ina wuni momy na? " lafiya lau yanzu nake son insa Fatima ta kiramin kai a waya danaji shiru,     "Gani nazo momy kema kinsan dole inzo inganki kullum sai dai idan da Akwai matsala ko aiki ya rikeni kuma ai Zanfada miki,   " ina wuni ya Muhammad, yan matan suka hada baki wurin fada ya waiga tareda zabga musu harara "dama zaman da kukeyi kenan saboda kusa jinin uwata ya hau sai haushi kukeyi kamar karnuka a cikin gida kowacce fuska kamar tayi dambe da toka kun tasa min ita a gaba kuna ta iface iface, ." banson dibar Albarka Muhammadu kai Bakayi Aure naga Matar ka ba bare insa ran jikoki ya'yan ka ba kila sai na mutu sannan yaran dake debe min kewa ka sasu agaba da kyara,   Dukan su wani irin bakin cikine ya rufesu wai duk kwalliyar da suka caba shine zai ce kamar sunyi danbe da toka lallai wannan gayen zasuga Matar Auren shi, Tashi sukayi sum sum suka shige kafin ya kara labto musu wata bakar maganar, Shigowar Ahmed ne yasa momy tasaki fara'a "Amadu dama tare kuke? " eh mama ina wuni? "Lafiya lau d'an Albarka ya iyali, ? Ina labarin y'ar Albarka Yasmin? " ai momy dazu kuwa tazo bariki tazo mana hutu, "Ai yar nan nada hankali sai daya kawai da kukazo tayi mugun shiga zuciya ta, kallon Momyn nashi yayi kafin ya kalli Ahmed yace " who is Yasmin? "Oga that my sister, tabe baki yayi kafin yace yaushe kukazo nan har momy ta ganta? Last time datazo ka aikoni lokacin zata tafi muka biyo nan kafin in sauke ta gida, Shiru kawai yayi domin yasan halin Momyn shi idan taso mutum, " Muhammadu yaushe zanga Auren ka ? Idan Bakada zabine ni inmaka zabi kuma nasan zakayi farin ciki, . "Momy Muyi magana mai ma ana don Allah Mubar wannan, " oh wannan batada ma'sna kenan ? "Muhammadu idan lafiya ce Bakada ka fada min anemi magani shekarar ka talatin da bakwai yanzu kakusa arbain kullum ba wai yarinta kake karawa ba shekarun ka natafiya ne fa, Amadu ka fadawa Abokin ka ko mai gidanka zance ne oho domin nasan baida wani Abokin da zai iya fadawa matsalar shi sama dakai, "In Akwai matsala kufada min, ta fada cike da damuwa aranta, saurin riko hannun ta yayi tareda rage murya a hankali, " momy na kiyimin hakuri zanyi kok'arin yin hakan idan na shirya banason inyi Auren da zan shiga damuwa insa Kaina a matsala momy kitayani Addu'a kawai,   Tashi yayi tareda kallon Ahmed da idanun shi da sukayi ja saboda tausayin mahaifiyar tashi "muje ko dafatan bakwa bukatar komai? Ya tanbaye ta Amma ido kawai ta zuba mai domin babbar bukatar ta itace Auren tilon d'an nata ta kuma ga jinin shi a duniya,   Yana fadawa motar ya jefar da wayar shi ya dafe goshin shi da yafara Sara mai Ahmed ya tayar da ita sai da suka tsaya bakin unguwar shanu sannan yace " oga Gasu nan fa sai ka zaba, Daga jajayen idanun shi yayi ya zuba wurin matan dake Jere akan titi da shiga kamar Tsirara   Fita Ahmed yayi saida yayi ma wata magana tareda Ciro bandir din kudi ya bata ya dawo cikin motar "oga na yi making Arrangement din,   " ok muje mess ", ya fada kai tsaye suka wuce batareda sun tafi da ita ba,   Karfe kusan tara nadare suka dawo, kasan cewar lokacin zafine kusan mafi. Yawancin mutane kan fito waje domin shan iska duk da kuwa Akwai wutar lantarki ta ko ina ga A.c Amma sanin kowane iskar ubangiji tafi kowace iskar bature ni ima tareda Amfani a jikin dan Adam,   Hirar su sukeyi irin ta y'an Uwa gefe data bowl ne dauke da chips Yasmin ta Ajiye agefen ta wandone ajikinta dogo mai fadi sosai da wata tea shirt mai guntun hannu ta kamata tsam kanta sanye da hular net kafar ta kuwa silipas ne sabo tayi matukar yin kyau sosai duk da bawai kwalliya tayi ba, Amma she look very Adorable kamar ka sace ta ka gudu Babyn ta hadu sosai kamar y'ar Aljana ga kirjin nan cike tab da dukiyar Fulani daga kasa kuwa zakasan Allah yayi halitta a wurin nan mai daukar hankali,   Maryam ta kalle ta " Yasmin kije ki saka hijabi kinga yadda mijin maman Amla ya kasa shiga cikin gida tun dazu saboda ganin ki a nan kuma ga shigar dake jikin ki,   "Kyale tsinan ne Matar shi naciki tana jiran shi Amma ya tsaya kallo na Ayya kuwa sai na haukata shi, " nidai ki rufamin Asiri kina ganin Matar nida ita saidai gaisuwa daga nesa saboda tsabar kishi tun zuwan ki na farko tazo nan tayi min magana "wai me yasa mukeson kawo kannin mu mata bariki neman maza?   " Kwal uba kika ce mata mene? "Hakuri na bata nace nidai ba neman miji kika zoyi ba zumunci ya kawoki tayi hakuri,   " ai wallahi sai nayi maganin ta Allah ya kai mu gobe bari ma kigani tun yanzu in dana tarko, Mikewa tayi cikin salon daukar hankali har tana girgiza kirjin ta wanda suka yi d'an rawa kadan da saida numfashin shi yayi skipped sannan ta duk'a ta dauki bowl din chips din da takeci,   Ta kalli y'ar uwar ta "muje ciki Aunty ai munsha iska sosai ga boy na yayi bacci, baza mai duwai wukan ta tayi da gangan saida ta saka kafar ta cikin falon ta juyo tareda jefa mai blow kiss har da kashe mai ido daya cike da salon daukar magana   Ta fada cikin falon, kusan sumewa yayi a tsaye yakai hannun shi saitin wandon shi ya dafe saida ya dauki lokaci kafin ya daure fuska tamau ya shige cikin gidan nashi shima dauke da kudurin samun wannan Aljanar Yarinyar daga gani yar hannu ce,   Ita kuwa tana shiga ta kyal kyale da dariyar mugunta " ai zaki ga BARIKI maman Amla, "Dariyar me kikeyi Yasmin? Ina fatan ba wani mugun Abin zaki kulla ba domin nasan halinki sarai dariyar ki ba Alkhairi bace, " kai Aunty na ba komai kawai inajin nishad'i ne' "Hmmm Allah yasa, ta wuce masaukin ta wato dakin y'ar uwarta domin bin lafiyar gado saidai kwanciyar ta keda wuya ba Abinda ya fado mata sai fuskar wannan gayen,   " me yasa kake neman mata? Shine kawai ta samu bakin ta da furtawa tarasa dalilin da yasa taji kawai tsanar shi ta ragu a cikin ranta tunda ta ga fuskar shi a karon farko,   Kirar jikin shi domin ta hango irin muscles din da ya Ajiye na karfi w'anda tasan ba shakka idan ya riki namiji zai ji jiki bare mace, His face look innocent he look pure but why is he like that? Saurin runtse idanun ta tayi tareda yin Addu'a har barawon ya dauke ta,   *"farkon farawa kenan my fans ina fatan wannan labari nawa da na faro ya baku ni shadin da kuke bukatar samu ya kuma ilmantar daku ya fadakar*   *"ku ci gaba da biyoni nidin ce dai "UMMU AMMAR Aunty Fener ku kuma Matar soja* _*BARIKI*_ _Auren soja_ _written by fenerh_ Maman Ammar   *Dedicated to* Fiddousi mainasara 3&4 Kasan cewar ta saba tashi da wuri, yasa ko a gidan y'ar uwar tata ta tashi tun karfe shida tafara gyara musu gidan, Ita ta shirya breakfast na gargajiya koko da kosai domin basa rabo da ni kak'ken wake a firij domin k'arin safe,   Saida ta kammala da wannan ta kwashi kayan su ta fita domin d'aurayewa, tana fitowa taci karo da maman Amla na tsaye tana kallon gidan nasu,   Daga murya tayi tareda cewa "ina kwana maman Amla mun sameku lafiya? Wata irin muguwar harara ta zabga mata tareda maka mata mugun tsaki ta shige tareda cewa " karuwan banza masu kwace mazan mutane kawai,   Dariya Yasmin tayi ta girgiza kai "zakiga karuwa ganin idon ki karamar y'ar bariki sai na koya miki darasi,     Tafada can kasan zuciyar ta domin batason tayi wata hayaniya da Matar Aure Ace tayi rashin kunya Amma sai ta gasa ta a ruwan sanyi zata koya mata hankali, Wankin ta tayi ta shanya kasan cewar ba yawa ta koma ciki lokacin har Ahmed ya shirya cikin kakin shi ya fito fes Maryam na rike da hannun shi tana cewa, ....yanzu dear Bazaka sha ko tea ba? " Nop nayi latti kuma kinga mun makara yau, Shigowar ta yasa suka kalleta ganin ta rike da bocket "Yasmin har kintashi? " ina kwanan ku ta fada tareda kallon mijin yayar ta "ni ai tun karfe shida Natashi da yake ku yan gayu ne kalli karfe takwas fa yanzu,   " eh bakyason matata ta huta ne ? "Inaso y'ar uwata ta huta don haka nayi mata Aikin komai har breakfast nayi muku yau, " wow kanwata godiya nake bari ingani yafada yana matsawa wurin d'an karamin table dinsu ya bude flask yaga koko da kosai, "Gaskiya kin burgeni kanwata a zuba min idan naje office zansha Acan nayi latti oga na jira na yanzu,. Juyawa kawai tayi ta nemi flask me kyau ta zuba mai koko da kosan yayar ta karba ta rakashi har waje kafin ta dawo cikin gidan,   Kukan yaron Yane yasa ta nufi cikin dakin ta dakko shi dakan ta tayi mai wanka ta shirya shi kafin yasha nonon shi,     Shirya wa tayi cikin kwalliyar ta mai matukar kyau da daukar hankalin duk wani namiji, riga da wandone tasaka sunfito da surar ta mai kyau duk da rigar takai har guiwar ta,   Ta yafa d'an karamin mayafi ta fito tana zuba kamshi da kuma kyalli, Taku take kamar wata Sarauniyar kyau tsabar jin kanta datakeyi,   Y'ar uwar ta ma saida tace " yayi Autar Mama wannan irin kyau haka saikace suruki na zai zo? Murmushi tayi kafin tace "kin manta kinada suruki a kusa Baban Amla,   " aa Yasmin kirufa min Asiri k'arki tafi kibarni da rigimar Matar nan don y'ar bala'i ce ta karshe wallahi, "takai karshen ta kuwa Aunty watch and see,   ...nidai aa ki fita hanyar ta kawai, " hmm kawai tace tayi waje' "ina zakije? " shan iska zanfita "ki rufa min Asiri ki sanya hijabi Yasmin kinsan halin sojoji kuwa? " wanda duk ya sa rai yasha wuya domin gani nan bari nan wallahi bani ba soja, shiru kawai tayi ta bita da kallo har ta fice,       Tana fitowa Emanuel na fitowa daga cikin gidan ya washe baki tareda nufota jikin shi na rawa"my friend ' "Yes wo good morning EMA, ya zauna gab da ita tareda zuba mata idanu domin tayi mugun yimai kyau, " chiii friend this kind fine no be small ting wo if my oga saw you Ahh,,, Ya fada yana cizon yatsa basar da shirmen shi tayi tareda kawo wata hirar "why are you not going to office? " na because I dey cook for oga so I no dey go office,   "Friend oga bring one Celine Dione yerstaday no shape no boobs noting I don no wetin he go enjoy there wo?   Wani irin kallo ta watsa mai domin ya fara bata haushi da mu gayen hirar shin nan da baya gajiya kowa ya tanbaye shi oho? Ta manta ita ke tanbayar shi a da can saboda gulma, kuma ita yau bata bukata impact zaman jiran Baban Amla takeyi Alakar sa idon can ta juya bata ta oga MA yanzu,   Ganin taki bashi fuska ya canja magana " I beg friend help me na oga say ma I cook kuka soup for him before he come back,   Kallon shi kawai tayi domin ya ishe ta da magana gashi da mugun nacin tsiya bata taba dana sanin sake mai fuska ba irin yau,   Cewa tayi ya tafi kawai zatazo ta nuna mai da fatan ogan shi Bazai dawo ya sameta ba yayi saurin girgiza kai "no oga no go comeback now till one O'Clock,   Saida ta fadawa Aunty Maryam ta fito suka wuce tare yana ta faman zabga mata magana,   Tundaga harabar gidan ta fara baza idanu fulawoyin da aka zagaye gidan sunyi matukar burgeta bata taba sanin haka wurin yakeba don bata taba matsawa ko jikin gate din dake zagaye da Bob ware ba ginin na tsakiyar shi, Wani irin ni ima ke kadawa da ita ga kamshin furanni kala kala ga kayan mar mari zagaye da gidan irin su lemo gwanda mangwaro ayba har ma dasu gwaba,   Tsarin wurin ya matukar burgeta " hmm gidan mutum daya d'an iska yafi kuma kowa tsula iskan ci ogan y'an iska, ta fada aranta,   Falon gidan kuwa ai sai shuru kawai domin tsarin gidan gaba daya kamar Akwai mace saboda kyale kyale ga shi kalar komai favourite dinta purple and white,   Daga gefen kitchen din step da zai kaika upstairs din ne she wish zata iya hawa saman shima taga tsiyar dake ciki,   Maganar EMA ta dawo da ita ta bishi cikin kitchen din da ta kira Aljanar mace domin tana mugun son ganin kitchen a tsare ga wannan ya tsaru kamar a turai komai na bukatar macen data San kan kitchen Akwai a ciki,   Ajiyar zuciya ta sauke tareda ku durin idan zatayi Aure haka zata tsara nata insha Allah,   Da taimakon EMA ta hada komai ta shirya musu lafiyayyar miyar kuka da taji namomi zuku zuku aciki sai kamshin garlic da citta ke tashi domin sunada komai na Amfanin gargajiya da Alama ogan nason harkar gargajiya,   Shi kuwa EMA baki har kunne sai zuba yake mata kamar kanya har ta matsu tabar gidan tana kammalawa tace zata wuce ya rakota sai godiya yakeyi kamar ya ari baki, "Tank you friend you save me today from my oga suna bude kofar shigowa wata sisi ta shigo kyakkyawa ce ba laifi ga wanka iya wanka domin less din jikin ta kadai zai nuna ma kudi sun koka Anan,   Komai na jikin ta kudi ne har Bangle's da jakar hanun ta Abin kallo ne sai walwali take tana zabga kamshi,   Wani irin kallo suke watsawa juna domin kowa na hango kyan kowa ita Yasmin Yarinyar burgeta tayi domin tana son mace mai daukar wanka kuma wannan tayi ba karya,   Ita kuwa zuby wani irin hade fuska tayi tana mata wani irin kallon ke wacece kafin ta bude baki cikin masifa tace,   " Emanuel who the hell is this? Tuni jikin shi ya fara rawa "sory madam na my friend I call her ne to help.......   " quiet ke kuma kiji nan nan gidan mijin da zan Aura ne ban y'arda ko wacce mace ta shigomin cikin shiba ni na tsara gidana kuma banason mace na rabar shi   Kinzo da kazaman kafar ki har cikin gidana to kar in kuma ganin ki daga yau stay away from my husband house,   Me neman kuka ai jikin Yasmin har rawa yakeyi ta gyara tsayuwar ta dakyau harda jijiga jikin da saida zuby tayi Addu'ar Allah yasa Muhammad bai taba ganin wannan Yarinyar ba,   "Ke wacece da zaki zo har cikin falo na kina min ihun wai gidan mijin ki lallai karuwan cin ki ya girma   " kin shigo min gidan Aure har kinada gut da zakice wai gidan mijin ki to ni Matar shi ce sai ki jira ya Auro ki kafin Kizo kiyimin gadara kuma yanzu kibar min gida kafin inhada ki da kuratan sojojin dake wajen gate din nan,   Wani irin tsuma jikin zuby ya farayi tuni hawaye suka wanke mata fuska wani irin kishi ne ya tokare mata kirji,   Kafin ta iya bude baki tayi magana kawai Yasmin ta turata waje ta datse kofar har tana huci kamar da gaske gidan tane,   EMA suman tsaye yayi ya dora hannu akai ya zama kamar statue duk da ba hausa yakeji ba yasan what ever Yasmin is saying is not right at All   "Chineke me friend na oga love wo na him girl friend she come from abroad you don kill me......   Tuni yafara paret tsaki ta yi tareda bude kofar ta leka taga ta tafi ta fito tayi wucewar ta gidan y'ar uwar ta ko ajikin ta,     A zaune yake a cikin office dinshi sanye da kakin shi yayi wani irin kyau a ciki gefen shi pistol ce da kuma system din shi har ma dasu tabs din shi akan table din ya dora kafafun shi dake sanye da boot dinshi masu sheki akai,   Kanshi a sama yana tunanin maganar shi da Momyn shi jiya, ta shigo cikin office din kamar yaki ta buga kofar jikin ta na rawa, Har saida yayi saurin mikewa cikin hanzari ya janyo pistol dake gefen shi, ganin fuskar ta yasa yaji ranshi ya mugun baci, . Komawa yayi ya zauna kawai batareda yace mata ci kanki ba ta fara magana, " ka kyauta Muhammad na kiraka yakai sau uku jiya kaki daga min waya, Bayan na fada maka zan dawo a jiya baka damu ba sannan d'an wulakanci na iso ko ka neme ni......any way nagano matsalar wato Aure kayi Muhammad bayan tafiya ta bayan kayi min Alkawarin Aure yanzu duk halaccin da nayi ma irin sakayyar da zaka biyani da ita kenan?   "All......." Quite don't you there couse me ke kika Ajiye ni ? Auren ki nayi ni nace ki jirani ? Na fada miki sai ke zan Aura ? How thare you banged into my office like this?   "Duk Rung's din da kikeyi a can na sani kar ki rena min hankali kuma Aure da kike magana.... Shiru yayi tareda kare matse fuska " eh nayi Aure kiyi Abinda zakiyi kuma yanzu kifitar min a office kafin inyi loosing control inci ubanki a nan '   Wani irin kuka ta fashe dashi kamar zata hadiye zuciya ta juya zata fita tana rufe baki yace "wait, tsaya wa tayi cak domin tayi tunanin hakuri zai bata,   " stay away from my wife and my house, da gudu tafice bako waiwaye duk inda ta wuce yaran shi kallon ta sukeyi domin kowa ya Santa dashi kuma sun San irin y'anda oga,ke mugun ji da ita to yau me ya faru,   Tana ficewa ya zauna kan kujera yana fitar da huci kamar kumurcin maciji yana tunani ko wace shegiya ce ta shigo mai gida har zuby ta ganta,?   Zaici uban Emanuel yau sai ya kulle shi don uban shi, baiso ya ma zuby haka ba Amma ai tasan bayason mace tayi mai gadara da rashin da'a shi yasa ya mata haka amma zai lallashe ta letter,   Intercoms ya danna Ahmed ya shigo saramai yayi ya koma gefe yana jiran umarni "ka hada min connection din TV inason inga wace ce a gidana?   " ok sir domin Akwai connection da yake ganin komai dake faruwa a gidan nashi Abinka da zamani,   Janyo tan din dake gaban shi yayi danna kawai yafara viewing Abinda ya faru na yau Ahmed zare idanu yayi waje lokacin da video ya fara aiki,   Goshin shi ya dafe cike da kaduwa "wannan Yarinyar zata kashe ni waya aiketa gidan oga,?   MA kuwa tagumi yayi yana karewa karfin halin ta kallo mamakin ta ya mugun cika shi, " og a....... Ahmed ya fada bakin shi na rawa zai bashi hakuri yayi saurin daga mai hannu tareda da nuna mai kofa yace ya fita kawai,   Jikin shi yayi sanyi ya fita shi kuwa ya kalli video din yakai sau uku yana repeat din shi dressing dinta yake karewa kallo har zuwa y'anda ta baje mai cikin kitchen ta hada mai miya a natse cikin kwarewa da kuma tsantsar tsabta,     Stop yasa dai dai lokacin da ta jijiga jikinta a gaban zuby zata zabga masifa d'an karamin bakinta ya tsurawa ido har zuwa lips din masu sheki da kuma idanun ta masu kama da fish lashes dinta sunyi zaro zaro ga gefen fuskar ta suma akwance tana sheki da Alamar taji gyara,   Samun kanshi yayi da jin nishadi karfe sha biyu ya bar office yace su tafi gida shima bai San dalilin shi na son komawar ba kasan cewar shi mutum mai son Aikin shi baya son wasa ko kadan,   Gefen mutane biyu kuwa sai zullumi sukeyi domin basu San me ogan nasu zaiyi ba yau wato EMA da Ahmed,   Motar su na tsaya wa sojojin shi suka bude mai motar ya fito kawai ya samu kanshi da wai gawa kofar gidan Ahmed din bakowa a wurin,   Saida gaban Ahmed ya fadi domin yasan wa yake kallo Yarinyar nan tajamun gidan ya shiga EMA tuni ya tsure tun jin jiniyar motar ta ogan don yasan lokacin dawowar shi baiyi ba   Tundaga kofar falon ya cire rigar saman ta kaki ya rataya a wani abin rataya kaya ya zauna a kan kujera tareda dora kafa daya kan daya yana girgiza wa,   Ahmed na shigomai da kayan shi ya nufi hanyar fita tsayar dashi yayi tareda bashi umarnin yayi serving dinshi Abinci,   Kallon shi yayi domin baiyi tunanin zaici Abincin da yana gani Yasmin ta hada shi ba, da sauri ya nufi kitchen ya samu EMA na sintiri hannu saman kai ya daka mai tsawa,   Ya natsu tareda bashi umarnin aje ya shirya table din oga, sanin halin EMA yanzu zai kuma tafka wani shirmen yasa ya hada mai komai da kanshi ya zuba ya jera a kan table din dake gefen shi ya zuba mai komai tareda dakko mai ruwa mai sanyi har da coke ya Ajiye a gefe sannan ya fita domin zuwa jawa uwar rigima kunne,   Tashi yayi ya zubawa plate din miyar idanu tayi gwanin sha'awa miyar batayi mugun yauki ba yasa mu kanshi da daukar spoon ya deba yakai bakin shi saida ya rintse idanun shi tsabar dad'in da ya ratsa shi,   Bai San lokacin da ya shanye miyar tas ba batareda ya ko kalli tuwon semon da EMA ya tuka mai ba ya dauki ruwa ya kora yaji ya koshi tab kamar yaci wani Abu,   Gaskiya girki hannu ne sirri ne kuma ga duk macen da tasan me takeyi ko ruwa ta dafa na tea zakaji shi daban   Ko takan EMA bai biba ya haye sama ya fada wanka EMA na ganin ya tashi ya fito ya tattara kayan yayi kitchen da gudu tareda Addu'ar kar ya shiga hannun oga,   *UMMU AMMAR* [8/30, 2:56 PM] Feenerh Wrtr: _*BARIKI*_ _Auren soja_ _written by fenerh_ Maman Ammar   *Dedicated to* Fiddousi mainasara 5&6 ......Ahmed na shiga gidan nashi ya sameta a baje ita da yaron ta a falon sai cin Abin cinta takeyi hankali kwance shi kuma ta jefa shi a zullumi,   Gaishe shi tayi ya zauna a kusa da ita tareda daukar yaron shi "ina Maryam take? " Aunty na hutawa bacci takeyi bari in kawo ma Abinci, Ta fada tana shirin mikewa yace "no zo Muyi magana Yasmin, yakira sunan ta tasan kwanan zancen don haka ko a jikin ta ta koma ta zauna tareda zabga mai na mujiya,   Dariya ya yi ganin reaction dinta, " Yasmin haka kikeyi a school? "Kallon Bangane ba tayi mai, " eh naga kinada mugun karfin hali ne wanda ba haka Maryam take ba ita matata batason fitina bata son matsala Amma ke naga idan ma matsalar batazo ba da kanki kike tara kai ki kirata tazo,   "Yaya Ahmed Nafasan me kake son fada' ta fada tana turo baki " hhhh yayi dariya kafin ya cigaba, "Nasan kinsan me kikayi ai, " Amma so kike a kulle ni ne kinsan laifin zai iya komawa Kaina? "Oga nane kuma Yarinyar da kika yima wulakanci bakisan tsakanin su ba " oga Muhammad na matukar jida ita tanada muhim manci a rayuwar shi ita kadai ce macen da ya dade da ita kuma nake sa ran zai iya Auren ta duk da bansan zuciyar shi ba amma kowa yasan kusan cin su, "To ni ya Ahmed ina ruwa na dasu ? " me kikaje yi gidan oga dazu? "Nifa taimako nayi Emanuel ne.... Ta yi mai bayanin y'anda sukayi dashi yayi shiru,   " amma Yasmin duk barikin nan kirasa wanda zakiyi mutumci dashi sai EMA? "Kaji yaya to sai inki mai sona? " aa ban fada ba nidai a kiyaye kar ajamin matsala da aiki na,   Tashi tayi kawai tare da duba sakon da yashigo wayar ta , wani murmushin mugun ta tayi kafin ta yi tsaki "zanci ubanki maman Amla sai nasa jinin ki ya hau,   Dama bayan Fitowar ta daga gidan MA tayi karo da Baban Amla sukayi musayar number yace zai kirata suyi hira da dare Ganin sakon da ya turo mata yanzu yasa ta kara d'ana tarko, _zan kiraki Anjima Muyi hira face to face domin kin tafi da zuciya ta har ma da murad'i na_   Reply ta tura mai _saika zo ina nan ina jiran ka I love you_ Ta tura tana tun tsura dariya, ai kuwa jiki na rawa ya kirata kai tsaye a lokacin yana zaune da Matar shi ya mike ya fito don kawai yaji muryar ta,   Ba bata lokaci ta d'auka tare da karya murya " Aslm Alkm "Wslm gimbiya kin rikita ni gaba daya na matsu ban ganki ba pls ki leko ko sau daya inyi tozali da kyakkyawar fuskar ki ko zanji dad'i, Wata irin dariya tayi mai tafiya da ruhi tace " Karka damu zaka ganni sai ma ka gaji da gani na' "Allah kar ya nufe ni da gajiya da ganin ki gimbiya,   " sai Anjima yanzu ina busy ne' "ok bye gimbiya ta, ta katse wayar tareda tunawa da bakar fuskar shi tace " god forbid bad thing,     Karfe takwas na daren ranar yasha wanka tareda nufo kofar gidan nasu ya kirata a waya, Tana zaune suna hira da Aunty Maryam ta ce "ina zuwa Aunty nayi bako,   " zaro ido tayi waje "yaushe kika fara kula samari Yasmin? " kaji Aunty ban isa bane? "Am nineteen fa going to twenty, Naji kije kidawo kifada min waye? " ok ta fada saida ta koma ciki ta kara gyara fuskar ta tareda fesa turare mai laushin kamshi sannan ta yafo gyale akan doguwar rigar jikin ta,   Tayi matukar yin kyau kamar ka sace ta ka gudu ta fito cikin taku dai dai, yana hango Fitowar ta ya kashe ta da ido kamar ya hadiye ta yakeji Babyn ta mugun tafiya da tunanin ruhin shi,   "Barka da fitowa gimbiyar Umar, murmushi tayi itama tareda cewa barka da dare'   Namiji muna fuki saida ya kalli kofar gidan shi sannan ya ce mu dan matsa can nan haske yayi yawa banason sa ido, batareda ta damu ba suka matsa d'an gaba kadan wanda tana hango harabar gidan na Oga kwata kwata kuma idan ba karya idanun ta ke mata ba tana hango mutum ta saman benen ta waje wurin da Akayi domin shan iska kuma idan mutum na wurin yana iya hango duk Abubuwan dake faruwa akusa ,   Sharewa tayi kawai suka fara zuba hira kasan cewar ta mai son zance tuni ta saki jiki da shi har tana dariya, hasken wayar shi ya haska fuskar ta, " gimbiya ina fatan ba w'anda ya riga ni ko? "Aa ni banida saurayi banda lokacin kowa, ta fada " kai Amma ni mai sa'a ne Ashe,   Gyara tsayuwar shi yayi tareda d'an riko gefen gyalen ta "baby kin fa hadu sosai Allah yayi miki kira mai kyau komai yaji, Shiyasa gaba daya kika tafi da ima nina, " Anzo wajen ta fada tareda kok'arin janye gyalen ta Amma da yake d'an duniya ne tuni ya rike hannun ta tamau, Wani irin laushi yaji a hannun kamar na jariri ya lumshe idanu "wow gimbiya hannun ki keda wannan laushin Inaga....... Fisge hannun ta tayi cikin fushi tareda matsawa kadan " bana son irin haka fa shiyasa naki kula samarin yanzun nan kai ma zamu bata idan ka kuma irin haka, "Oh gimbiya sai kace rainon kyauye? Keda nake ganin ki a waye ''ba irin wannan waye war nayi ba don haka saida safe, Ta juya cike da takaicin rike mata hannu da yayi d'an iska gobe zan cika aiki na in watsar da kai shege,   Kiran ta yake tayi amma ko juyowa batayi ba tayi shigewar ta gida, Muhammad kuwa tun lokacin da ya haska fuskar ta yaga irin dariyar da takeyi yaji zuciyar shi tayi mai baki ya miki tareda dunkule hannun shi kamar zai daki mutum Ganin ya riko hannun ta ai tuni ya wuce cikin gidan don ji yayi jinin shi na harbawa kamar zai tsiyaye a jinin shi,   Daga karshe wurin motsa jikin shi ya nufa yafara daga wani heavyweight da ko za a hada mu mu goma baza mu iya daga shi ba,   Saida ya hada gumi kamar w'anda ya fito filin daga ya mike tareda daukar ruwa mai sanyi ya sheka wa kanshi,   Towel ya d'auka ya fara tsane jikin shi dake tsiyaya kafin ya wurgar a zafafe ya jefar ya nufi bathroom ya sakarwa kanshi shower batareda ya cire gajeran wandon jikin shi ba, Saida ya dauki lokaci mai tsawo a tsakiyar ruwan kafin ya fito daure da towel ya fada gado, bai taba tsintar zuciyar shi so restless ba irin yau meke damun shi ?   Ya rasa me yasa shi jin yanayin da yake ciki kodan sunyi fada ne da zuby? Runtse idon shi yayi gam tareda dunkule Hannayen shi yana maida numfashi mai zafi ji yake kanshi na juya wa,   Jin ankwanta a bayan shi yasa shi saurin zabura ya juyo domin ganin wace shegiyar ce ta isa da har ta shigo mai gida batareda ya kirata ba kuma for that matter har bedroom dinshi, Ganin fuskar zuby yasa ya d'an yi cool dwan ya maida wukar fadan komawa jikin shi tayi tareda sa mai kuka ,   "Me yasa zaka hora ni haka Muhammad ? Kasan ina matukar kaunar ka me yasa zaka yimun haka ? Na tanbayi Ahmed yace mun kanwar shi ce ba Matar ka ba ce Am sorry baby for what I did, " a jiyar zuciya ya sauke tareda cireta a jikin shi yace "is ok kinsan banason raini ai " riko hanun shi tayi masu burgeta saboda wasu jijiyoyi da suka shata ko ina kana gani kasan na karfi ne tareda motsa jiki, Kallon shi takeyi wani iri Kamar hoto domin ba haka yake ba ya canja "meke damun ka Muhammad dina? " waya bata baka rai ? Nasan Muhammad din zubaida ba haka yake ba why the sudden change? "Ni ba wani canji ke ke ganin haka, " ok ya isa ni dai hakuri nazo bayar wa don haka let me take a bath and come you no I really miss you ta fada tana daga gira,   Saurin tsayar da ita yayi "no need ki koma gida bana bukatar komai sai hutu yau please no aguement,   Sanin hali yasa taja ta tsaya tareda zuba mai ido kafin ta dauki key din motar ta ta fita kawai kafin ya kuma hawa,   Runtse idanun shi yayi gam yarasa meke damun shi ji yake kamar ya mike ya dawo da zuby amma ina yasan zataso ya taba ta shi kuma yagaji da wahalar da jikin shi batareda ya samu Abin da yakeso ba, " wai haka ne matan suke? To meye zaisa yayi Aure tunda shidai har yau baiji wani Abin da zaisa yace zaiyi Aure ba, sex food what ? Shidai yasan ko mace goma yakeso a rana zai samu but meye dadi a cikin su duk Abin daya ne shi har yau bai samu ruwan da zai kashe mai kishi ba har yau gobarar cikin shi na ci   Shi mace ma duk wadda ya taba bayajin wani feelings he is just using them to reduced the fluid __________ Umar ya kirata yafi sau goma taki dagawa Shikuwa a halin yanzu baijin zai iya hakura da ita har dai da yaji irin taushin dake jikin ta yasha cudanya da mata Amma ita da ban ce shi gaba daya ma ya canja akalar zuciyar daga samun biyan bukata zuwa mallakar ta gaba daya Auren ta zaiyi kawai, A ranar Sam Matar shi bata gane mai ba domin ya mugun daure mata fuska karshe ma ko makwanci yaki hada wa da ita,   Falo ya dawo sai faman text yake turawa Yasmin na lallashi Amma ina tama yi nisa ita a bacci tareda ku durin cin uban maman Amla da safe,   Tana tashi da sakon nin shi tayi karo dariyar mugunta tayi mai kafin ta tura mai msg _Zamu hadu kafin kaje aiki by_ Ta fara taya y'ar uwar ta aiki tana cike da nishadi w'anda saida Maryam tayi magana "Yasmin me ke faruwa? Nifa ban gane miki ba Sam ' " bakomai Aunty na kawai naji dad'in wannan ziyarar da na kawo muku ne jina nake cikin farin ciki tun zuwa na, Hmm kawai Maryam tace kafin tace.... "Allah yasa ba wani Abun kike hadawa ba , Ameen ta Amsa saida suka kammala Aikin gidan ta fada wanka shirya wa tayi cikin wata riga da wandon Pakistan purple wandon fari tayi matukar yin kyau ta gyara gashin ta mai tsawo tareda dunkule shi gyale fari d'an karami ta yafa ta fesa turare ta fito,   Wani sheki takeyi ga kayan sunyi matukar karbar ta rigar ta d'an kamata ta West ga wandon pencil silipas ts sanya masu d'an tudu ta dauki wayar ta ta kirashi,   A lokacin zaune yake Matar shi sai zuba take amma hankalin shi na kan wayar shi duk da yayi late Amma Bazai taba tafiya bai ganta ba,,   Motoci tagani a kofar katon gate din a Jere hilux biyu da kuma wata Benz Army colour a tsakiya sojoji ne a tsaye da bindi gogi kamar zasu ci babu dauke kanta tayi duk da taji tsoro saida ta kusa kofar gidan na Umar ta kirashi " ka fito ina waje,   Wani irib zabura yayi kamar wani maye ya fito batareda yako kalli Matar shi ba jikin shi na rawa , meke damun Baban Amla ne wai ta fada tareda biyo bayan shi,   Lokacin har ya karaso kusa da ita kamar zai rungumo ta "gimbiya kin sani cikin wani hali wallahi na horu da yawa a Gaskiya kin gama tafiya da zuciyar Umar,   Murmushi tayi na mugunta domin hankalin ta na kofar gidan nashi kuma ta hango Matar shi tsaye ta dora hannu akai hawaye na zuba,   Karaso wa tayi kamar guguwa ta matso " Amma Allah ya isa tsakani na dake wallahi karuwa kawai masu shigowa bariki domin kwace mazan mutane a haka zaku kare tsinan nu,   Wani irin tsawa ya buga mata tareda yi mata tsatstsauran gargadi "hauwa ki wuce kafin yanzu in canja Shawara akan ki wallahi, Tasan halin shi dole ta wuce cikin gidan tana kuka kafin ya nad'a mata na jaki tana wucewa Yasmin ta juya zata tafi domin burin ta ya cika tasan yanzu can ta matse musu ko ya lallashi Matar shi ko yayi biyu babu,   Shan gaban ta yayi jikin shi na rawa " Yasmin please kiyi hakuri zan ja mata kunne k'arki tafi ki barni cikin damuwa,   Tsayawa tayi cikin daure fuska "aini ban ma San kanada Aure ba da ban saurare ka tun farko ba kuma indai wannan ce Matar ka wallahi ban Auren ka don ba tun yau ts saba Zagina ba don haka ka kama kanka dani kafin in hada ka da yaya na,   " what is happening? Taji muryar Ahmed saurin juyawa tayi wurin shi "Yauwa ya Ahmed ka shiga tsakani na da wannan mutumin yasa min ido ka man iyaka dashi ko dole ne in soshi tayi shigewar ta cikin gidan batareda ta ko saurari Ahmed din ba,,   Muhammad da ya fito daga gidan shi har ya shiga cikin motar shi yaga duk Abin da ya faru yana hango su daga cikin motar har Fitowar Ahmed da wucewar ta ciki, This girl is unbelievable meke damun ta ta hada shi da budurwar shi yanzu kuma miji da mata bayan sun gama shan soyayyar su,   Isowar Ahmed cikin motar yasa shi dawowa cikin dogon tunanin da yakeyi gaida shi yayi cikin respect irin nasu na sojoji sannan aka rufe motar suka kama hanya,   Sai bayan sun isa office ya kirashi office, " Ahmed meke faruwa ne dazu I saw everything me ka fadawa Umar? Me yake tsakanin su da sister ka?   "Oga wai yana sonta ne kuma yanzu tace ya fita hanyar ta ni ban gane me ke faruwa ba shima nace ya jirani har mu dawo gida Muyi magana domin nasan halin Yasmin,   " Yasmin'''' ya furta sunan can kasan zuciyar shi sunan ta Akwai dad'i sosai,   Ka fada mai karya kuma gangan cin zuwa gidanka tunda tace ya kyale ta ba a so dole don haka warn him before I do something about it   "Ok sir I will do so , ya sallame shi tareda maida bayan shi bayan kujera ya runtse idanun shi yana wani irin murmushi " what a woman Yarinyar nan me take nufi da rayuwar suda ta shigo bariki ?   *I don't no kuci gaba da biyo ni,"*   *UMMU AMMAR* [8/30, 2:56 PM] Feenerh Wrtr: _*BARIKI*_ _Auren soja_ _written by fenerh_ Maman Ammar   *Dedicated to* Fiddousi mainasara (¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯)   тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.com/pro__writers?s=09 7&8 Maryam batasan wainar da ake toyawa ba saida Maman Amla ta zo gidan da kanta tana uban kuka, Har kasa tasa guiwoyin ta tana rokon Maryam don Allah su bar mata mijin ta gaba daya yace idan bai samu Yasmin ba itama zata barmai gida,   Abin ya bama Aunty Maryam mamaki ganin ko a jikin Yasmin yasa tasan Akwai wata akasa tayi saurin kallon y'anda ta juya musu baya,   "Yasmin meke faruwa ? " AUNTY ki tanbaye ta ita data zo miki gida da kuka , kuma tasan banbacin karuwan gida dana bariki yau ba boka ba malam mujiya kwakwal war mijin mace idan tayi wasa kuma wallahi tayi gidan su,   Baki Maryam ta saki kafin ta lallashi Maman Amla ta tafi tareda kwantar mata da hankali bayan ta rakata "ki kyale Yasmin haka take kuma tanada wanda zata Aura d'an uwan mu ne kawai ta daga miki hankali ne,   Wani dadi taji tareda ba wa Aunty Maryam hakuri akan zagin ta datayi " kiyi hakuri Maman Auwal bazan kuma fitina dake ba insha Allahu,   Koda ta shigo gidan kasa ce mata komai tayi saidai idanu kawai don tasan halin y'ar kanwar tata idan ta matsa sai yanzu tace zatayi mata yaji gwara ta bari idan tayi niya zata fada mata da kanta,   *tushen labari* 2years back, Tafe suke a kan hanyar su ta dawowa daga makaranta sanye suke a cikin fararen kaya da d'an karamin hijabi sai bakin low pass a lamar dai malaman jinya ne su   Kyawa wane su sosai duk da kana ganin su kasan yaya da k'anwa ne Amma Akwai shakuwa mai girma a tsakanin su   Saidai kanwar tafi yayar nesa ba kusa ba kuma kirar jikin su Akwai banbanci domin Maryam nada jiki kadan ita kuma Yasmin jikin ta d'an dai dai ne,   Zasuyi matukar burgeka idan kaga y'anda suke tafiyar su kamar wasu kawaye, Motace tasha gaban su fara tas kirar Lexus sukayi saurin tsayawa cak,.   Fitowa yayi sanye cikin kakin shi yayi matukar yin kyau kanshi ba hula ya fara basu hakuri, "Y'an mata Kuyi hakuri na tsayar da ku akan hanya, wani irin mugun kallo Yasmin ta watsa mai " kadai yi niyyar kashe mu Allah ne baiyi ba saboda ka ganka soja to Allah ya fika , ta furta tana mai murguda mai baki, Saurin riko hannun ta Maryam tayi Alamar ya isa mana, dariya yayi ya kalli Maryam "kibawa kawar mu ko kanwar muce hakuri naga tanada tsiwa,   " kayi hakuri ba komai ta rikota suka kama hanya da niyar wucewa yayi saurin shan gaban su " don Allah meye sunan ki ? Ya fada yana kallon Maryam, ta fada mai kai tsaye yayi "suna mai daraja don Allah wane unguwa kuke ne yau nakai kwana uku ina ganin ku a dai dai nan hanyar kuma saboda ku nake biyo wa yau nakasa hakuri ne a yimin uzuri inzo gidan k....   ...karma ka fara wallahi don Aunty nada mijin Aure ni kuwa ko maza sun kare ban Auren soja don haka bamu hanya ko inbangaje ka wallahi,   Finciko hannun Maryam tayi sukayi gida batareda ta kuma kallon inda yake ba, Maryam na wai wayen shi domin gayen ya matukar burgeta ga kakin ya karbeshi sosai,   Shiga motar shi yayi ya rika binsu har saida yaga gidan su ya koma barrack w'anda su kuma suna isa kofar gidan su sukaci karo da Ismail wato w'anda. Maryam din zata Aura,   Karo na farko da taji takaicin Amince was Auren da iyayen su keda burin hadawa, Tasowa yayi yana musu barka da zuwa, Yasmin ce tayi carab tace " ai wallahi ya sama'ila idan baka dakko mu sai anyi ma fashi a hanya wataran kaga wani mayen soja yau ya biyo ma mata,   Dariya yayi "kai Yasmin kin cika mita nasan meye matsalar ki daga yau na gama interview dina ni zanrika dakko ku insha Allah,   Maryam dai wuce wa tayi batare da ko gaishe shi ba, yasan halin ta na rashin son magana don haka bai cika damuwa da shariyar ta ba,     Karfe takwas na dare suna zaune a tsakar gidan nasu dai dai na rufin Asiri aka aiko ana kiran Maryam, saida gaban ta ya fadi ganin irin kallon da Baban ta yayi mata kuma suna matukar tsoron mahaifin nasu bayason wasa,   " Maryam waye kika bashi izinin zuwa gidana bayan kinsan kinada miji a kasa? "Wallahi baba bakowa, " to bari inga kowaye,   Yana fita Mama ta ce "Yasmin waye yazo wurin y'ar uwarki? " mama ni yazan San ko waye ? "Nasan tare kuke ai koma waye zaki sani,   " nidai bansan waye ba, "to ku kiyaye kafin ku hadu da fushin babanku Kunsan burin shi akan ku ita kuma tasan tanada mijin Aure don haka ta kiyaye,   Shiru kawai sukayi har Baban ya dawo ya ce wani soja ne wai sunan shi Ahmed ya mun bayanin wai yana son Maryam ne toh nabashi hakuri bayan nayi mai bayanin tanada mijin Aure,   Wani iri taji har cikin ranta zataso ace ta Auri wannan bawan Allah mai suna Ahmed ya tafi da ita lokaci daya gashi ita bamai iya magana bace,   Kwana biyu Abin ya tsaya mata arai sosai har wani zazzabi ke shirin kamata gaba daya tayi sukuku da ita Yasmin tayi tanbaya har ta gaji Amma ba Amsa,   Shima gefen shi hakan take domin ya mugun damuwa soyayyar Maryam ta yi mai mugun kamu bayajin zai iya hakura da soyayyar ta gashi baida ko numbar wayar ta bare yaji muryar ta, Damuwa tayi mai yawa har takai ga ogan shi ya tanbaye shi lafiya? Jin juna suke kamar yan Uwa ko Abokai don haka bai boye mai komai ba " hmm saboda mace kake hana kanka natsuwa? Toh ita y'ar gidan uban waye da Baban ta zai ce ya bawa wani ita?   "If you really love her get her pregnant sai muga y'anda zata Auri wani kaga dole su baka ai, kallon ogan yayi " sau daya fa nasamu damar magana da ita,   "Ina gidan su yake ? Suna unguwar Dosa ne " ok karka damu I will help you get her,   Bayan sati daya ta dawo daga makaranta ita kadai ce saboda Yasmin bata jeba tana fama da ciwon ciki, ta fito daga cikin school din nasu dake tudun wada,   Ganin motar ranar a gaban ta yasa tayi saurin daga idanun ta ta zuba mai yana zaune a cikin motar kamar zai cinyeta da idanu,   Kafin ya fito ya dawo dayan gefen da take tsaye ya bude mata tareda bata umarni, "ki shiga Muyi magana Maryam,   Ba musu ta shiga tareda rufe kofar da yake tinted ne bamai hangosu, Ya shiga shima tareda riko hannun ta da yakusa sata suma saboda wani irin shock da taji, Wannan ne karon farko da wani namiji ya taba rike mata hannu haka " Maryam ya kira sunan ta dago kanta kawai tayi idanun ta na cikowa,   "Kinga halin da soyayyar ki ta jefani' ko Abinci bana iya ci kawai tafiya nakeyi Amma bana cikin hayya cina Maryam bazan iya hakura dake ba banason wani ya Aure ki I want you,   Ki taimaki marayan Allah k'arki sani cikin gararin Rayuwa, kuka ta fashe dashi da yasa baisan lokacin da ya rungumota zuwa jikin shi ba gaba dayan ta tadawo kan kafar shi,   Wani irin rudewa yayi jikin shi ya fara rawa, " Maryam ki Aure ni don. Allah, ya dago fuskar ta ya zuba mata ido "kina sona? Kai ta daga mai kawai " to ki fadawa baba ni kikeso ya barni na Aure ki zakiyi farin ciki, "bazan iya ba ' Ta furta mai. A hankali, Ajiyar zuciya ya sauke   " zan koma wurin baba yau bazan iya hakura dake ba ina sonki sosai ko bakyason Aure na? ",inaso, ta fada kissing goshin ta yayi kafin ya maida ita mazaunin ta kamar wata baby ya gyara belt din sit dinshi, " muje inkai ki gida, tace "aa kar baba ya ganni a motar ka kabarni zan hau napep, " aa bazan bar matana na hawa motar haya ba, ya hau kan titin batareda ya saurare ta ba,.   Tun daga nesa ta hango mahaifin ta a kofar gidan jingine da jikin y'ar karamar civic dinshi yana magana da Ismail, wani irin faduwa gaban ta yayi ta fara juya kai "don Allah mu koma kaga baba da ya Ismail a tsaye, Jin sunan w'anda takira yasa ya bude motar cikin fushi ya nufesu Dukawa. Yayi ya gaida Baban kafin yayiwa Ismail wani irin mugun kallo, " Ahmed Kaine yau a gidan mu ya aiki, baba ya fada tareda bashi hannu, Yace "Alhmdulillah naga Maryam ne a hanya na rage mata hanya nakawo ta gida yafada yana nuna mai Maryam din data fito jikin ta narawa ta gaida Baban nata dake. Binta da kallo,   Ismail kuwa dukar da kanshi kawai yayi batareda yace komai ba, Gaishe su tayi ta shige jikin ta narawa,   A tsakar gidan ta tarad su suna hira Yasmin tayi filo da kafar Mama, ta gaida mama ta wuce da sauri cikin dakin su, Yasmin ce ta mike tareda binta dakin " Aunty lafiya? "Me kika gani? " naga kin shigo a sittin ne ko kallo na bakiyi ba, "Ba komai ya jikin ki? " naji sauki, ya lectures yau me Akayi? "Ki duba jakata ina zuwa in watsa ruwa zafi ta fada tana fita dakin zuwa waje,   Tanajin Shigowar Baban nasu ta ki fitowa cikin bandakin domin tasan sauran saidai maganar da taji yanayi ce yasa ta fashe wa da kuka, saurin rufe bakin ta tayi da hannu kar su jita,   " nace Ismail ya fara shiri watan da zamu shiga zandaura musu Aure da Maryam, yake fadawa mama, "Alhaji bayan kace sai sun gama school of nurse din kuma me yasa ka canja Shawara? " gani nayi Maryam na shirin kaini ga kunya shiyasa nace zanyi mata Auren ita Yasmin idan ta kammala sai tafito da miji tayi Auren,   "Allah yasa Alkhairi tafada batareda lamarin yayi mata dad'i ba saidai halin girma irin na iyayan my mata nagari da kara yasa bata nuna maiba, Ita kanta Yasmin jikin ta yayi sanyi duk da tasan wannan ne burin Baban su a Rayuwa hada Auren Maryam da Ismail, Alhaji lawal mai turare shine sunan mahaifin nasu shi dan Asalin garin Zango ne su biyu iyayen su suka haifa shida kanin shi Mahmud sun taso cikin kaunar juna har lokacin da Alhaji lawal ya kammala karatun shi ya fara aiki da ma aikatar nipost dake nan Kaduna ya dawo cikin gari tareda Auren Matar shi guda daya da kuma d'an kanin nashi tilo,   Tun Ismail na karami Allah ya dorawa Alhaji lawal kaunar yaron tun ma bai haifi nashi ba, kuma d'an uwan shi ya mallaka maishi halas malak Mama saudatu ita ce Matar shi daya mai halin kwarai ta rike shi Amana tun bata fara haihuwa ba har Allah ya bata haihuwar Maryam,   Bayan shekara biyu Allah ya kuma bata Fatima wato Yasmin kenan kasan cewar ta ci sunan kakarta ta wajen uba,   Rashin son maganar Maryam ya faro tun tana karama zaka d'auka kurma ce shiyasa ma bata fara karatu da wuri ba har saida Yasmin ta isa shiga makaranta aka hada su, A gurguje sunyi karatun su tundaga primary har matakin secondary kafin su shiga makarantar koyon Aikin jinya wato school of nurse, Wanda a nan ne suka hadu da Ahmed bayan maganar Auren ta da Ismail tayi karfi sosai, A haka kwanaki ke tafiya har lokacin da baba yasa ya yi a lokacin Maryam duk ta tsiyaye a tsaye tsabar tunani da damuwa kullum mahaifiyar ta tanbayar ta takeyi duk da tana kara irin ta y'ar farko Amma saida ta cire kunya ta sata a daki,   "Ki fada min Abinda ke damun ki nice mahaifiyar ki Bakida wanda ya fini kuka tasa mai cin rai kafin ta bude baki " mama Ahmed nakeso banason ya Ismail ki sa baki baba ya barmu Muyi Aure dashi ina son shi sosai,   Shiru mama tayi tareda zuba mata ido tama kasa cewa komai tasan cewa maganar babbace tunda duk karar Maryam ta bude bakin ta fada lallai kuwa tana son shi sosai, Tashi tayi fita dakin megidan ta sameshi ta zauna cikin ladabi, Baban Ismail Alfarma nake nema don girman Allah, juyowa yayi sosai ya zuba mata ido "ina jinki saude wace irin Alfarma ce?   " akan zancen Auren nan ne don Allah ka hada Ismail da Yasmin tunda ita batada w'anda takeso ka bawa Yarinyar can zabin ta,   Zuba mata ido yayi kafin ya mike kawai ya nufi dakin su Maryam din tana ganin shi ta zabura jikin ta na rawa "Maryam baki y'arda da zabi na ba ko?   Kina so ki watsa min kasa a ido har zaki iya aiko uwar ki wurina ta fada min bakyason dana sai wani bare kuma soja " toh shi kenan kije ki Aure shi Amma ki sani ba hannu na a ciki kuma bada yawu na ba kuma na gode wa Allah da yasa bake kadai bace Yata don haka zan hada mama na da Ismail nasan ita bazata bani kunya ba, Wani irin kuka tasa jikin ta na rawa "baba kayi haku.." Ki yimin shiru kuma ranar Aurenki da nasa ba fashi kije ki nemi wani uban ya daura miki Auren Amma nidai kin gama zama a gidana,   Ya fita Abinshi ranshi matukar bace ya kira Yasmin tareda neman Alfarmar ta y'arda da Auren Ismail, Abin yazo mata a bazata Amma kodan ta taimaki y'ar uwar ta dole ta y'arda, saidai ta nemi Alfarmar Baban ta ya barta ta karasa karatun ta kafin ya mata Auren ya kuma Amince, Gefen Ismail kuwa ba wata matsala domin shi a yanzu tuni dama yafara son Yasmin din don Bazai iya furtawa Baban bane don haka canji yafi yimai dadi sosai,   Baban su Mahmud shine yayi ruwa yayi tsaki har aka daura Auren Maryam da Ahmed kuma mahaifin ta yace bashi baita kuma karta tako mai gida bai kuma y'arda kowa yayi hulda da ita ba duk da irin lallashin da kanin nashi yayi ta yi Amma fur yaki,   Shiyasa Yasmin take sato jiki tazo wurin y'ar uwar ta , sai bayan ta haifi Auwal ne baba ya fara sakko wa jin labarin ta kuma samun wani ciki ba tareda d'an ya shekara ba yasa ya fauwala wa ubangiji yasan cewa rabon haihuwa ne sanadi da yanzu yayi jikoki a kan titi, Wannan shine d'an taka'i taccen tarihin Abinda ya faru sai kuci gaba da biyoni domin jin yazata kaya da Auren Yasmin din taku"   *Matar soja* [8/30, 2:56 PM] Feenerh Wrtr: _*BARIKI*_ _Auren soja_ _written by fenerh_ Maman Ammar   *Dedicated to* Fiddousi mainasara (¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯)   тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.com/pro__writers?s=09 7&8 Maryam batasan wainar da ake toyawa ba saida Maman Amla ta zo gidan da kanta tana uban kuka, Har kasa tasa guiwoyin ta tana rokon Maryam don Allah su bar mata mijin ta gaba daya yace idan bai samu Yasmin ba itama zata barmai gida,   Abin ya bama Aunty Maryam mamaki ganin ko a jikin Yasmin yasa tasan Akwai wata akasa tayi saurin kallon y'anda ta juya musu baya,   "Yasmin meke faruwa ? " AUNTY ki tanbaye ta ita data zo miki gida da kuka , kuma tasan banbacin karuwan gida dana bariki yau ba boka ba malam mujiya kwakwal war mijin mace idan tayi wasa kuma wallahi tayi gidan su,   Baki Maryam ta saki kafin ta lallashi Maman Amla ta tafi tareda kwantar mata da hankali bayan ta rakata "ki kyale Yasmin haka take kuma tanada wanda zata Aura d'an uwan mu ne kawai ta daga miki hankali ne,   Wani dadi taji tareda ba wa Aunty Maryam hakuri akan zagin ta datayi " kiyi hakuri Maman Auwal bazan kuma fitina dake ba insha Allahu,   Koda ta shigo gidan kasa ce mata komai tayi saidai idanu kawai don tasan halin y'ar kanwar tata idan ta matsa sai yanzu tace zatayi mata yaji gwara ta bari idan tayi niya zata fada mata da kanta,   *tushen labari* 2years back, Tafe suke a kan hanyar su ta dawowa daga makaranta sanye suke a cikin fararen kaya da d'an karamin hijabi sai bakin low pass a lamar dai malaman jinya ne su   Kyawa wane su sosai duk da kana ganin su kasan yaya da k'anwa ne Amma Akwai shakuwa mai girma a tsakanin su   Saidai kanwar tafi yayar nesa ba kusa ba kuma kirar jikin su Akwai banbanci domin Maryam nada jiki kadan ita kuma Yasmin jikin ta d'an dai dai ne,   Zasuyi matukar burgeka idan kaga y'anda suke tafiyar su kamar wasu kawaye, Motace tasha gaban su fara tas kirar Lexus sukayi saurin tsayawa cak,.   Fitowa yayi sanye cikin kakin shi yayi matukar yin kyau kanshi ba hula ya fara basu hakuri, "Y'an mata Kuyi hakuri na tsayar da ku akan hanya, wani irin mugun kallo Yasmin ta watsa mai " kadai yi niyyar kashe mu Allah ne baiyi ba saboda ka ganka soja to Allah ya fika , ta furta tana mai murguda mai baki, Saurin riko hannun ta Maryam tayi Alamar ya isa mana, dariya yayi ya kalli Maryam "kibawa kawar mu ko kanwar muce hakuri naga tanada tsiwa,   " kayi hakuri ba komai ta rikota suka kama hanya da niyar wucewa yayi saurin shan gaban su " don Allah meye sunan ki ? Ya fada yana kallon Maryam, ta fada mai kai tsaye yayi "suna mai daraja don Allah wane unguwa kuke ne yau nakai kwana uku ina ganin ku a dai dai nan hanyar kuma saboda ku nake biyo wa yau nakasa hakuri ne a yimin uzuri inzo gidan k....   ...karma ka fara wallahi don Aunty nada mijin Aure ni kuwa ko maza sun kare ban Auren soja don haka bamu hanya ko inbangaje ka wallahi,   Finciko hannun Maryam tayi sukayi gida batareda ta kuma kallon inda yake ba, Maryam na wai wayen shi domin gayen ya matukar burgeta ga kakin ya karbeshi sosai,   Shiga motar shi yayi ya rika binsu har saida yaga gidan su ya koma barrack w'anda su kuma suna isa kofar gidan su sukaci karo da Ismail wato w'anda. Maryam din zata Aura,   Karo na farko da taji takaicin Amince was Auren da iyayen su keda burin hadawa, Tasowa yayi yana musu barka da zuwa, Yasmin ce tayi carab tace " ai wallahi ya sama'ila idan baka dakko mu sai anyi ma fashi a hanya wataran kaga wani mayen soja yau ya biyo ma mata,   Dariya yayi "kai Yasmin kin cika mita nasan meye matsalar ki daga yau na gama interview dina ni zanrika dakko ku insha Allah,   Maryam dai wuce wa tayi batare da ko gaishe shi ba, yasan halin ta na rashin son magana don haka bai cika damuwa da shariyar ta ba,     Karfe takwas na dare suna zaune a tsakar gidan nasu dai dai na rufin Asiri aka aiko ana kiran Maryam, saida gaban ta ya fadi ganin irin kallon da Baban ta yayi mata kuma suna matukar tsoron mahaifin nasu bayason wasa,   " Maryam waye kika bashi izinin zuwa gidana bayan kinsan kinada miji a kasa? "Wallahi baba bakowa, " to bari inga kowaye,   Yana fita Mama ta ce "Yasmin waye yazo wurin y'ar uwarki? " mama ni yazan San ko waye ? "Nasan tare kuke ai koma waye zaki sani,   " nidai bansan waye ba, "to ku kiyaye kafin ku hadu da fushin babanku Kunsan burin shi akan ku ita kuma tasan tanada mijin Aure don haka ta kiyaye,   Shiru kawai sukayi har Baban ya dawo ya ce wani soja ne wai sunan shi Ahmed ya mun bayanin wai yana son Maryam ne toh nabashi hakuri bayan nayi mai bayanin tanada mijin Aure,   Wani iri taji har cikin ranta zataso ace ta Auri wannan bawan Allah mai suna Ahmed ya tafi da ita lokaci daya gashi ita bamai iya magana bace,   Kwana biyu Abin ya tsaya mata arai sosai har wani zazzabi ke shirin kamata gaba daya tayi sukuku da ita Yasmin tayi tanbaya har ta gaji Amma ba Amsa,   Shima gefen shi hakan take domin ya mugun damuwa soyayyar Maryam ta yi mai mugun kamu bayajin zai iya hakura da soyayyar ta gashi baida ko numbar wayar ta bare yaji muryar ta, Damuwa tayi mai yawa har takai ga ogan shi ya tanbaye shi lafiya? Jin juna suke kamar yan Uwa ko Abokai don haka bai boye mai komai ba " hmm saboda mace kake hana kanka natsuwa? Toh ita y'ar gidan uban waye da Baban ta zai ce ya bawa wani ita?   "If you really love her get her pregnant sai muga y'anda zata Auri wani kaga dole su baka ai, kallon ogan yayi " sau daya fa nasamu damar magana da ita,   "Ina gidan su yake ? Suna unguwar Dosa ne " ok karka damu I will help you get her,   Bayan sati daya ta dawo daga makaranta ita kadai ce saboda Yasmin bata jeba tana fama da ciwon ciki, ta fito daga cikin school din nasu dake tudun wada,   Ganin motar ranar a gaban ta yasa tayi saurin daga idanun ta ta zuba mai yana zaune a cikin motar kamar zai cinyeta da idanu,   Kafin ya fito ya dawo dayan gefen da take tsaye ya bude mata tareda bata umarni, "ki shiga Muyi magana Maryam,   Ba musu ta shiga tareda rufe kofar da yake tinted ne bamai hangosu, Ya shiga shima tareda riko hannun ta da yakusa sata suma saboda wani irin shock da taji, Wannan ne karon farko da wani namiji ya taba rike mata hannu haka " Maryam ya kira sunan ta dago kanta kawai tayi idanun ta na cikowa,   "Kinga halin da soyayyar ki ta jefani' ko Abinci bana iya ci kawai tafiya nakeyi Amma bana cikin hayya cina Maryam bazan iya hakura dake ba banason wani ya Aure ki I want you,   Ki taimaki marayan Allah k'arki sani cikin gararin Rayuwa, kuka ta fashe dashi da yasa baisan lokacin da ya rungumota zuwa jikin shi ba gaba dayan ta tadawo kan kafar shi,   Wani irin rudewa yayi jikin shi ya fara rawa, " Maryam ki Aure ni don. Allah, ya dago fuskar ta ya zuba mata ido "kina sona? Kai ta daga mai kawai " to ki fadawa baba ni kikeso ya barni na Aure ki zakiyi farin ciki, "bazan iya ba ' Ta furta mai. A hankali, Ajiyar zuciya ya sauke   " zan koma wurin baba yau bazan iya hakura dake ba ina sonki sosai ko bakyason Aure na? ",inaso, ta fada kissing goshin ta yayi kafin ya maida ita mazaunin ta kamar wata baby ya gyara belt din sit dinshi, " muje inkai ki gida, tace "aa kar baba ya ganni a motar ka kabarni zan hau napep, " aa bazan bar matana na hawa motar haya ba, ya hau kan titin batareda ya saurare ta ba,.   Tun daga nesa ta hango mahaifin ta a kofar gidan jingine da jikin y'ar karamar civic dinshi yana magana da Ismail, wani irin faduwa gaban ta yayi ta fara juya kai "don Allah mu koma kaga baba da ya Ismail a tsaye, Jin sunan w'anda takira yasa ya bude motar cikin fushi ya nufesu Dukawa. Yayi ya gaida Baban kafin yayiwa Ismail wani irin mugun kallo, " Ahmed Kaine yau a gidan mu ya aiki, baba ya fada tareda bashi hannu, Yace "Alhmdulillah naga Maryam ne a hanya na rage mata hanya nakawo ta gida yafada yana nuna mai Maryam din data fito jikin ta narawa ta gaida Baban nata dake. Binta da kallo,   Ismail kuwa dukar da kanshi kawai yayi batareda yace komai ba, Gaishe su tayi ta shige jikin ta narawa,   A tsakar gidan ta tarad su suna hira Yasmin tayi filo da kafar Mama, ta gaida mama ta wuce da sauri cikin dakin su, Yasmin ce ta mike tareda binta dakin " Aunty lafiya? "Me kika gani? " naga kin shigo a sittin ne ko kallo na bakiyi ba, "Ba komai ya jikin ki? " naji sauki, ya lectures yau me Akayi? "Ki duba jakata ina zuwa in watsa ruwa zafi ta fada tana fita dakin zuwa waje,   Tanajin Shigowar Baban nasu ta ki fitowa cikin bandakin domin tasan sauran saidai maganar da taji yanayi ce yasa ta fashe wa da kuka, saurin rufe bakin ta tayi da hannu kar su jita,   " nace Ismail ya fara shiri watan da zamu shiga zandaura musu Aure da Maryam, yake fadawa mama, "Alhaji bayan kace sai sun gama school of nurse din kuma me yasa ka canja Shawara? " gani nayi Maryam na shirin kaini ga kunya shiyasa nace zanyi mata Auren ita Yasmin idan ta kammala sai tafito da miji tayi Auren,   "Allah yasa Alkhairi tafada batareda lamarin yayi mata dad'i ba saidai halin girma irin na iyayan my mata nagari da kara yasa bata nuna maiba, Ita kanta Yasmin jikin ta yayi sanyi duk da tasan wannan ne burin Baban su a Rayuwa hada Auren Maryam da Ismail, Alhaji lawal mai turare shine sunan mahaifin nasu shi dan Asalin garin Zango ne su biyu iyayen su suka haifa shida kanin shi Mahmud sun taso cikin kaunar juna har lokacin da Alhaji lawal ya kammala karatun shi ya fara aiki da ma aikatar nipost dake nan Kaduna ya dawo cikin gari tareda Auren Matar shi guda daya da kuma d'an kanin nashi tilo,   Tun Ismail na karami Allah ya dorawa Alhaji lawal kaunar yaron tun ma bai haifi nashi ba, kuma d'an uwan shi ya mallaka maishi halas malak Mama saudatu ita ce Matar shi daya mai halin kwarai ta rike shi Amana tun bata fara haihuwa ba har Allah ya bata haihuwar Maryam,   Bayan shekara biyu Allah ya kuma bata Fatima wato Yasmin kenan kasan cewar ta ci sunan kakarta ta wajen uba,   Rashin son maganar Maryam ya faro tun tana karama zaka d'auka kurma ce shiyasa ma bata fara karatu da wuri ba har saida Yasmin ta isa shiga makaranta aka hada su, A gurguje sunyi karatun su tundaga primary har matakin secondary kafin su shiga makarantar koyon Aikin jinya wato school of nurse, Wanda a nan ne suka hadu da Ahmed bayan maganar Auren ta da Ismail tayi karfi sosai, A haka kwanaki ke tafiya har lokacin da baba yasa ya yi a lokacin Maryam duk ta tsiyaye a tsaye tsabar tunani da damuwa kullum mahaifiyar ta tanbayar ta takeyi duk da tana kara irin ta y'ar farko Amma saida ta cire kunya ta sata a daki,   "Ki fada min Abinda ke damun ki nice mahaifiyar ki Bakida wanda ya fini kuka tasa mai cin rai kafin ta bude baki " mama Ahmed nakeso banason ya Ismail ki sa baki baba ya barmu Muyi Aure dashi ina son shi sosai,   Shiru mama tayi tareda zuba mata ido tama kasa cewa komai tasan cewa maganar babbace tunda duk karar Maryam ta bude bakin ta fada lallai kuwa tana son shi sosai, Tashi tayi fita dakin megidan ta sameshi ta zauna cikin ladabi, Baban Ismail Alfarma nake nema don girman Allah, juyowa yayi sosai ya zuba mata ido "ina jinki saude wace irin Alfarma ce?   " akan zancen Auren nan ne don Allah ka hada Ismail da Yasmin tunda ita batada w'anda takeso ka bawa Yarinyar can zabin ta,   Zuba mata ido yayi kafin ya mike kawai ya nufi dakin su Maryam din tana ganin shi ta zabura jikin ta na rawa "Maryam baki y'arda da zabi na ba ko?   Kina so ki watsa min kasa a ido har zaki iya aiko uwar ki wurina ta fada min bakyason dana sai wani bare kuma soja " toh shi kenan kije ki Aure shi Amma ki sani ba hannu na a ciki kuma bada yawu na ba kuma na gode wa Allah da yasa bake kadai bace Yata don haka zan hada mama na da Ismail nasan ita bazata bani kunya ba, Wani irin kuka tasa jikin ta na rawa "baba kayi haku.." Ki yimin shiru kuma ranar Aurenki da nasa ba fashi kije ki nemi wani uban ya daura miki Auren Amma nidai kin gama zama a gidana,   Ya fita Abinshi ranshi matukar bace ya kira Yasmin tareda neman Alfarmar ta y'arda da Auren Ismail, Abin yazo mata a bazata Amma kodan ta taimaki y'ar uwar ta dole ta y'arda, saidai ta nemi Alfarmar Baban ta ya barta ta karasa karatun ta kafin ya mata Auren ya kuma Amince, Gefen Ismail kuwa ba wata matsala domin shi a yanzu tuni dama yafara son Yasmin din don Bazai iya furtawa Baban bane don haka canji yafi yimai dadi sosai,   Baban su Mahmud shine yayi ruwa yayi tsaki har aka daura Auren Maryam da Ahmed kuma mahaifin ta yace bashi baita kuma karta tako mai gida bai kuma y'arda kowa yayi hulda da ita ba duk da irin lallashin da kanin nashi yayi ta yi Amma fur yaki,   Shiyasa Yasmin take sato jiki tazo wurin y'ar uwar ta , sai bayan ta haifi Auwal ne baba ya fara sakko wa jin labarin ta kuma samun wani ciki ba tareda d'an ya shekara ba yasa ya fauwala wa ubangiji yasan cewa rabon haihuwa ne sanadi da yanzu yayi jikoki a kan titi, Wannan shine d'an taka'i taccen tarihin Abinda ya faru sai kuci gaba da biyoni domin jin yazata kaya da Auren Yasmin din taku"   *Matar soja* [8/30, 2:56 PM] Feenerh Wrtr: _*BARIKI*_ _Auren soja_ _written by fenerh_ Maman Ammar   *Dedicated to* Fiddousi mainasara (¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯)   тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.com/pro__writers?s=09 9&10 Wanene Muhammad Abdullah M.A? Dana ga major Abdullahi Kudan yan Asalin Zaria ne mahaifin shi yayi Aikin soja tun ana Yakin basasa lokacin sune suka yiwa Nigeria hidima,   Mahaifiyar shi Hajiya Hauwa kuwa yar Asalin katsina ce fulanin Asali shiyasa ya gado fari sai dai kirar jikin shi ta mahaifin shine kowa yasan mallawan Zaria da tsawo kamar samu dawa   Ya gaji kyau gaba da baya yanada yayyi biyu mata duk sunyi Aure da yaran su manya ata kaice shine karamin su mahaifin su ya dade da rasuwa saura mahaifiyar su kawai, Yan uwan shi mata duk suna Auren wasu kusoshin gwamnatin Nigeria ba wadda take nema a wurin shi mahaifiyar su na cikin gata sosai shiyasa take daukar yaran jama'a tana tallafa musu,   Tun mahaifin shi nada rai yakeda burin danshi ya yi Aikin soja kuma cikin ikon Allah ya samu gurbi a NDA har ya kammala tareda nasarori da dama har zuwa yanzu,   Da yakai matakin da yake kai na general a kananun shekarun shi domin ba duk soja ne zaikai wannan matsayin ba a under fourty,   Matsalar shi shine rashin yin Aure wanda shi baida burin yin Auren ma A rayuwar shi Sam domin duk abinda yake nema ya mallake shi kudi mulki mata kuwa da kudinka sai ka zaba wasu ma kyauta zasu kawo Kansu,   Saidai har yau baiga macen da ta zauna a rayuwar shi da har zai iya Auren ta ba sai dai zuby itama kawai shakuwa ce da kuma hidima da take mai da Aljihun ta kasan cewar ta y'ar gidan minister saidai wulakanci daban daban take gani akoda yaushe wurin MA,   Saidai bata sani ba yana ganin kimar ta fiye da duk macen da yake Hulda da ita domin yafi sakewa da ita ko a wurin harkar su yana dan samun gamsuwa da ita,   Cigaban labari Kwalliya tayi sosai cikin wata doguwar rigar shadda blue kamar zataje fati ta daura dankwalin a sittin tareda yafa farin mayafi a gefen kafadar ta kana iya hango irin Aikin da gaban rigar yasha da stones suna sheki ga kirjin ta sunyi wani irin cika suna daukar hankali wani farin takalmi ne da kuma y'ar karamar pos dinta ta rike, Hot 8 dinta take dannawa tana tura sako sai murmushi take fitar wa mai kaya tarwa, "Yasmin har kin shirya? Taji muryar Maryam " eh Aunty ina Auwal da Baban shi nifa na matsu bamu tafi ba wallahi, "Wai d'okin zuwa gidan Momyn MA ne haka? " bazaki gane ba Aunty Matar nada kirki kamar ba ita ta haifeshi ba wallahi sainayi sanadin da zatazo taga iskan cin da yake tsulawa a bariki d'an iska kawai,   "Nashigesu don girman Allah Yasmin kirufa mana Asiri ina ruwanki da rayuwar shi ? Nidai inkin San Abinda zakiyi kenan ki hakura bari infadawa Baban Auwal kinfasa,   " aa bazan yiba karki hana ni tafiya ai inada hankali yazan hada Uwa da d'an ta, Fitowar Ahmed da yaron shi yasa shi tsayawa kallon ta "aa kanwa ta irin wannan wanka karkisa ace Amarya na karo wa maman Auwal, " to dafa? Ai nice Amaryar dama, ta fada tana dariya, haka ne fa Kece ta karfen muje yamma nayi ko,   Fita sukayi tana dauke da Auwal a hannun ta Maryam ta rakosu kofar fita kafin ta koma taci gaba da Aikin ta,   Yana hango Fitowar su yana daga saman gidan nashi idanun shi a kafe akanta tana tafiyar ta a natse jikin ta na juyawa kamar tarwad'a   Gaba daya ta gama wucewa da imanin shi ya kasa koda kifta ida nunshi akan ta har saida ta shiga motar yayi Ajiyar zuciya kafin ya janyo wayar shi yayi dialing numbar Ahmed,   Yana d'auka yace "where are you? Muryar shi can kasa Alamar cike yake da kasala, " oga ina gida yanzu dai zamuje gidan momy ne mu gaishe ta ta ce inkai mata Yasmin,   "Wait for me nima gidan zanje, yafada yana mai mikewa, shiru Ahmed yayi domin yasan Akwai matsala yanzu kam idan taji zasu tafi tareda oga,   Juyowa yayi tareda kallon ta tana wasa da yaron " kanwata tafiyar mu ta canja salo fa tareda oga zamu tafi bari in dakko babbar mota a ciki, Ya fada yana fitowa batareda yaji Amsar ta ba, katuwar Hummer jeep din shi Army green ya fito da ita ya faka tareda jiran Fitowar oga kwata kwata,   Cikin shigar kana nan kaya kamar zashi training ya fito tree quarter da kuma wata riga mai hula kalar kaki ya bude gaban motar ya shiga saida suka fito yayi mata horn ta fito kamar bataso ta fara takowa kanta a kasa ta bude bayan motar ta shiga,   Yi yayi kamar bai sanda zuwan ta ba saida Ahmed ya tayar da mota yace "Yasmin ga oga baki gaishe shiba, " dago kanta tayi cikin shirin daukar magana ta watsa mai harara kafin tace "la shine ogan naku? Wallahi da naga yana kwaso mata n.......   "Yasmin shine. Ahmed ya tari numfashin ta da sauri kafin ya kunna radion motar yasaka wani kida mai taushi na wakar Angel of my life,   Janyo earpiece tayi ta sanya a kunnen ta tareda sanya best wakar da take so ta Ado gwanja wakar shi ta a hayye matan Arewa kun kai mata,   Har wani lumshe idanun ta takeyi tsabar jin dad'in wakar shi kuwa tunda tayi magana yaji muryar ta mai zaki ya lumshe idanun shi batareda yaji kalamin ta ba,   Wakar dake tashi ce a cikin motar ga kamshin turarukan su ga na motar sai jin shi yake cikin wani irin yanayi mai wuyar fassara,   Auwal wasan shi kawai yakeyi a gefen ta hannun shi rike da lollipop yana sha, Saida ya tsaya kofar tafkeken gate din yayi horn sojojin suka wangale mai ya sa hancin ta,   Suka rugo tareda bude mai motar ya fito fuskar shi a daure ya basu umarnin su koma bakin Aikin su kai tsaye ya koma gefen da zata fito ya tsaya ya kare ta daga kallon masu gadin nashi,   Saida tayi gaba dauke da yaronta ta bi bayanta tareda Ahmed wani irin kallo yake binta dashi mai cike da ma'anoni kala kala,   Kamar koda yaushe dattijuwar na zaune akasan Capet din ta dora hannun ta akan tun tun din dake kasan hannun ta rike da carbi gefen ta zuby ce zaune kanta akasa,   Gaban ta kayan motsa baki ne a Jere, tun Shigowar shi falon gaban zuby ya fadi shi kuwa hade fuskar shi yayi tareda bata rai sosai,   Yasmin kuwa baki ta saki hango wannan mayyar wato uwar shi ma tasan d'an iska ne tunda ga karuwan har cikin gidan su, "Abin nashi Ashe har da licence ta furta a fili kuma yajita sarai, fuska Hajiya ta saki sosai ganin Yasmin,   " a maraba da Yata Fatima Lale marhabin, ta fada cikin jin dadi yau ga Fatima kai Amadu ka cika Alkawari,   Matsawa tayi kusa da ita tareda zubewa ta gaisheta cike da kunya, shi kuwa gefen zuby ya nufa fuska a matse "what the hell, why did you come hare?   Shiru tayi jikin ta na rawa ta mike tareda daukar Jakarta tace " momy zan tafi, "A sauka lafiya ta fada ba yabo ba fallasa, don ita dai Yarinyar bata yi mata ba,   Mace ba kamun kai haka ki kwaso kafa kizomin gida duk da ina son ganin Auren shi bazan so ya Aure ki ba ta fada a zuciyar ta,   Bin bayan ta yayi suna fita ya fisgo ta ya hada da bango " kina hauka ne kika zo gidan mu? Fisgewa tayi da karfi "eh ina hauka Muhammad, " haukar sonka haba ya kakeson inyi najira ka for so long yanzu kana shirin juya min baya akan wannan Yarinyar da a haihuwar kaji tsab zaka haifi kamar ta wallahi kaban kunya,   Shima Ahmed munafuki yace kanwar shi ce what ever wallahi sai naga bayan ta ba macen da ta isa ta rabeka in kyale ta,   "Kin makaro baby kuma wannan Yarinyar da ki taba ta gwara ki tabani yafi miki sauki kinga y'anda tayi dake ranar ki kiyaye nafada miki I don't take rubbish from women you no, " kayi Abinda zakayi kuma Anjima gidan zanzo wallahi sai na dauki mataki akan ka Muhammad "zakiyi babban kuskure kuwa,   Ya fada yana mai juyawa cikin gidan ya samu Yasmin ta baje sai hirar su sukeyi kamar sun dade da sabawa   Auwal sai wasan shi yakeyi a jikin ta daga gani tanason yaron sosai ya Ayyana, Ko kallon shi momy batayi ba domin tana ciki dashi akan zancen Aure, Zama yayi a gefen ta tareda riko hannun ta " sory mama na ki taya ni Addu'a karkiyi fushi dani Kece garkuwa ta, Dawo da hankalin ta tayi kanshi da kyau"kayi Aure inka naso mu shirya, "momy zanyi in lokaci yayi ki yimun Addu'a, Uwa da da' sai Allah ta saki ranta harda samai Albarka tana mai fatan samun mace ta gari, A zuciyar Yasmin kuwa cewa take " ogan yan iska mace ta gari? Saidai a mafarki kila d'an iska sai y'ar iska irin shi,   Sai kusan magrib suka bar gidan Hajiya tayi mata kyautar super da kayan kwalliya masu tsada harda turaruka   Tayi matukar jin dad'in ziyarar saida suka biyo ta ostrich oga yayi take away na dambun nama dasu pizza sannan sukayi bariki,   Zaka d'auka bai damu da ita ba a cikin motar nan kuwa duk wani motsin ta idanun shi na kanta, Suna tsayawa itace farkon fitowa ta wuce bako sallama da ledar kayan ta Auwal kuwa yayi bacci a kafar MA saida Ahmed ya shigar da motar sannan ya karbeshi ya bashi ledojin take away shima ya je su ci da iyalin shi yayi godiya,   Tana shiga ta fara bawa Maryam labari "Aunty Gaskiya mutumin can katon d'an iska ne " wane mutumin kuma Yasmin sarkin yan daukar magana?   "Ogan ku mana kinsan dashi mukaje gidan maman shi Hmm Abin mamaki karuwar shi muka samu a cikin gidan da gani baiso taje ba......   " ya isa labarin nan Yasmin ina mijina? "Hmm masu miji yana nan zuwa shida my boy ni natafi in watsa ruwa tunda bakyason hirar ga kyautar da na samo ta fada tana mika mata ledar kayan,   Karfe goma yana kwance akan tafkeken gadon shi idanun shi a lumshe ya kasa bacci Yarinyar nan ta tsaya a zuciyar shi sosai   Yarasa me yasa ya kasa cire ta a cikin ranshi shidai ba sonta yakeyi ba kawai baya gajiya da kallon ta ne she is beautiful sannan tsiwar ta na burge shi sosai,   Ina ma zata Amince dashi ya samu kusanci da ita yasan da zata fita akanshi ta barshi yayi bacci don shi ko yaga mace yaji tayi mai yana samun biyan bukata zaiji ya tsane ta,   I will try and get close to her nasan zata fita araina but yasan yanajin kunyar Ahmed Bazai iya yin Abinda zai bata mai rai ba don yasan kanwar Matar shi ce,   Bazama ta iya daukar shi ba he saw her tiny west duk da tana da shape but she can't take him, runtse idanun shi yayi wata irin wutar jaraba na kunnuwa a zuciyar shi da bai taba jin irin taba kodan yayi kwana biyu ne bai nemi mace ba,?   Ganin Abin na neman illata shi yasa ya zabura ya janyo wayar shi numbar zuby ya kira a lokacin tana kwance tana faman kukan juya mata baya da yayi,   Ganin numbar shi yasa tayi saurin picking, murya na rawa tace " hello baby, "zaki iya zuwa yanzu? Ya furta muryar shi na cracking don jin yake kamar numfashin shi zai tsaya tsabar fitina,   Saurin zabura tayi " zanzo baby yanzun nan ta diro daga ita sai kayan baccin jikin ta ta dora after akai ta ziri makullin motar ta tafito security na tanbayar ta ta buga mai tsawa open the get for me, Ko tsoro bataji a haka ta shigo barikin lokacin kusan karfe goma sha daya kasan cewar sojojin sun Santa ba bata lokaci ta shige ciki,   Yana nan kwance idanun shi sun yi mugun yin ja ji yake Kamar zai mutu idan bai rage ruwan dake kwance a marar shi ba,   Tundaga bakin kofar ta fara kwabe kayan jikin ta ta fara taku a haka har ta isa kan gadon yana kife dagashi sai boxer ta haye bayanshi ta kwanta bear chest dinta suka taba bayan shi,   Runtse idanun shi yayi tareda saurin birkito ta jikin shi na rawa, ta fara kok'arin hada bakin su yayi saurin ture ta "you no I don't like it,   " baby please just once kabarni inji test din bakinka please, tsawa ya buga mata idan bazakiyi Abinda ya kawoki ba kibar nan banson damuwa,   "And no sex only romance ok ya fada yana zame boxer dinshi, tuni ta hadiye mugun miyau tareda rungume shi tamau jikin ta na rawa shiyasa take mutuwar son shi har yau bata taba ganin namiji mai kirar Muhammad dinta ba   Komai nashi is perfect kirjin shi mai fadi muscles dinshi farin fatar ga huge machine gun da ta dade bataji test din ta ba tasan halin shi Abinda yace baya canja ra ayi da yau sai ta ka shewa kanta mugun kishin shi koda kuwa bazaiyi da kanshi ba ita zatayi Aikin, . Tadauki lokaci tana Abu daya a jikin shi wanda ji yake Kamar namiji ke tabashi ga fitinar shi na karuwa tuni jikin shi ya dauki zafi   Daga karshe ture ta yayi saboda mugun zazzabin dake rufeshi yaja bargo batareda ya koma kanta ba itama lafewa tayi a jikin shi kamar mage bacci mai shegen dadi ya kwashe ta, Yaushe rabon da tasamu dama irin ta yau,? Haka yaga tsawon daren fuskar Yasmin nayi mai yawo har ma da kirar jikin ta da yake gani a cikin kaya ba a zahiri ba,   Asubar farko ya ture zuby ya fada bathroom saida ya tsarkake jikin shi sannan yayi Alwala ya fito ya shinfida dadduma ya tada Salla,   Yau ko training din da yabi jikin shi bai iya yiba wayar shi ya daga ya kira Ahmed yace yazo gidan shi yanzu,   Gaba daya bayajin dad'in rayuwar shi he feels so restless ji yake kamar yayi ihu saboda damuwa,   Ahmed na zuwa ya ce ya kawo mai first aid box zaiyi Allura domin jikin shi har rawa yakeyi, "Oga Badai diabetes dinka bane ya motsa? Girgiza mai kai kawai yayi jikin shi na rawa don zuwa lokacin idanun shi sun fara rufewa,   Da hanzarin shi ya dakko a ma Ajiyar tashi ya kawo ya mai umarnin ya hada mai jikin Ahmed na rawa yace " oga muje hospital ko inkira doctor Philips ne?   "No don't call any one just make the injection for me I will do it my self " no sir I can't risk your life ni ban iya hadawa ba let me call my sister she is a nurse,   Ya juya da saurin shi batareda ya saurari reply dinshi ba,   Jin yace sister ya runtse jajayen idanun shi a hankali ya furta "if she comes I will surely die today please Ahmed don't call her,   " Akwai ta fa my fan's shin zata zo ta taimaka ? Idan tazo mezai faru karku manta zuby na gidan........ Mu hadu a next page my fans ‍♀   *Matar soja* [8/30, 2:56 PM] Feenerh Wrtr: _*BARIKI*_ _Auren soja_ _written by fenerh_ Maman Ammar   *Dedicated to* Fiddousi mainasara (¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯)   тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.com/pro__writers?s=09 *A Gaskiya comments dinku na karamin karfin guiwar yi muku typin, don haka ina Alfahari daku my fan's kuci gaba da gashi Yasmin na gaishe ku* 11&12 A zaune take bayan ta idar da Salla ta jingina da gadon dakin tana sauraron karatun Alqur'ani mai girma a cikin wayar ta, Ya kwankwasa kofar a hankali, bude idanun ta tayi tareda mikewa ta bude kofar sanye da dogon hijabin ta "Ya Ahmed Kaine da safen nan ince dai lafiya Aunty take? " kalau Kizo don Allah inaso ki taimaka kiyiwa oga Allura bayajin dad'i,   "Ogan yan iskan? Ta fada tana dariya " lallai kace ya shiga hannu yau sai yayi iskancin da tushe mugani, Kasa cewa komai yayi saida takai karshe "muje inkin gama zagin nashi ko, " saboda musulunci kawai wallahi zanje inba haka ba dana barshi ya mutu a rage mugun iri,   Har suka shiga cikin gidan bakinta bai mutu ba , Shikuwa yana nan a kishin gide a inda ya barshi idanun shi a lumshe,   Tundaga nesa bakinta ya mutu murus hango irin kirar jikin shi datayi saida ta hadiye wasu mu gayen miyau, "Tab lallai ma yan matan dake bin gayen nan jarumai ne ai ita wallahi ya riketa kila mutuwa zatayi,   Daga nesa ta tsaya tama kasa kara sawa kusa dashi saida Ahmed ya yi mata magana' ki matso kiyi Aikin ki mana,   a hankali cikin natsuwa take matsowa wurin shi, jin takun Matsowar ta ya kara runtse idanun shi kirjin shi na bugawa da sauri a hankali yake jin numfashin shi na tsayawa na y'an dakiku,   Bayaso ya bude idanun shi ya kalle ta don zata iya hango zahirin Abinda ke tareda zuciyar shi don haka yayi namijin kok'arin da yaki bude idanun nashi,   Kallon shi takeyi dakyau tana karewa kyakkyawar fuskar shi kallo da kuma faffadan kirjin shi mai cike da wata irin suma kwantacciya   Hannun ta na rawa ta bude first aid din tareda tanbayar Ahmed " meke damun shi,? "Inaga sugar dinshi ne ya dan tashi,   Tattaro jarumtar ta tayi tareda gyara zaman hijabin jikin ta tace " bari ingani ko zan iya taimaka mai idan yafi karfina kuje asibiti kawai,   Hannun ta ta daura akan goshin shi domin jin yanayin temperature din jikin shi, a take ya bude idanun shi da yake kok'arin hanasu budewa wani irin mugun shock yaji tundaga kanshi har kasan marar shi,   "Ahmed tell her to stop touching me please" ya furta ba tareda ya shirya Fitowar maganar ba,   Saurin cire hannun ta tayi tareda dafe kugu tana shirin zubo mai magana, "Oga bari ta duba inba haka ba inkira Philip kawai ko mu wuce Asibiti, " no need I will be ok, karka damu nadan lokaci ne,   "Tab yaya fever keson rufeshi jikin shi yayi matukar yin zafi if possible ayi mai Allurar rage zafin jikin kafin yazamar mai matsala yakasa nema..... Kiyi mai ina zuwa Ahmed ya fada tareda fita cikin falon daukar Ruwan Allurar tayi tareda sanya Auduga ta fasa bakin ta zuki ruwan a sirinj Gaba daya idanun shi nakan ta sunyi wani mugun ja kamar wuta, Ta gogi spirit da Auduga ta matso gab dashi " ai wallahi sai nayi ma tunda nazo bazan tafi haka nan kawai ba ta daga kwalbar Allurar "koma wannan ce ko ba ita bace oho nidai yau sai nayi ma Allura, Wani irin murmushi ne ya kufce mai a fuska, " kabani hannun ka intsira ma ni intafi, Ta fada tana girgiza jiki, "saurin kifewa yayi a tree seater din tareda sanya hannun shi ya zame guntun wandon dake jikin shi kadan,   Wani irin zaro idanu tayi waje kamar taga mutuwa tadan ja baya kadan, lallai yau taga iskan ci tayi saurin ajiye Allurar zata juya kenan zuby ta sakko daga saman daga ita sai d'an guntun towel, Kanta a jike da ruwa tana tafe tana hamma, cak Yasmin ta tsaya tana kare mata kallo, " d'an iska wato ya kwana sabon Allah ya tashi da zazzabi wallahi kadan ma ya gani kuma wannan karuwar tashi sai ta kunna ta zatabar gidan,   Saurin komawa tayi ta zari Allura batareda ta taba shiba ta tsira mai, kamar ta tsikari dutse ko motsi baiyi ba,   "Kingama kenan? Ya furta a hankali wanda yayi dai dai da karasowar zuby a kidime' " me zangani haka? Baby lafiya ? Me wannan Abar takeyi a cikin gidan nan? Ko juyowa baiyi ba bare ya bata Amsar maganar ta   Yasmin mai jira tayi wata irin dariya tareda matsowa kusa da zubyn cikin renin hankali "Bakida Amfani ne shiyasa ya kirani inzo intaimaka mai,   " kuma bari kiji gaskiyar zance a gaban shi "ni Matar shi ce idan ma ya fada miki wani zance na daban ne kika kuma y'arda dashi ke kika jiyo,   Nasaba ganin dubun ki a cikin gidan nan basu dameni ba bare ke don haka ki tattara koma tsan ki kibar min gida Ai dai kingan mu har cikin gidan su da idanun ki don haka bana son ganin kafarki a cikin gidan nan again, Ta juya cike da girgiza irin na na hada wuta zata fita, zuby da Yarinyar ta gama kaita bango ta wani irin fisgota ta kamar kara, Wata y'ar karamar kara tasaki da saida ya zabura zaune ya zuba ma ikon Allah ido domin Abin Yarinyar yafara wuce tuna nin shi, " ke karamar y'ar iska waya koya miki bariki Ke y'ar gidan uban waye ? Fisge hannun ta tayi tareda gogewa tace "Allah ya isa kinje kin gama iskan cinki zaki tabamin jiki mai tsarki,   Wani irin wawan marin da saida taga tagwayen taurari ya ziyarci fuskar ta batareda ta shirya ba, Wani irin rudewa M.A yayi tareda saurin tare Yasmin dake shirin zubewa a kasa kuma yayi dai dai da Shigowar Ahmed rike da flask a hannun shi na tea,   Jikin MA na rawa yace " zuby how dare you? "Ya zaka tsaya tanbaya ta bayan komai a gabanka ya faru , " get out "" ya buga mata wani irin mugun tsawa saida ta zabura tayi baya da sauri "Ahmed get her out of my house before I killed her right here,   Hajiya Yasmin kuwa d'an karamin suman wucin gadi tayi kafin ta dawo hayya cinta tasaki wani irin kuka, Ta fara kok'arin burgima jinta a jikin mutum yasa tayi saurin zabura ta mike tana gyara hijabin ta binta yakeyi da kallo mai tattare da ma anoni da dama,   Kana hango tsantsar bacin rai a idanun shi ganin marin da zuby tayiwa Yasmin yasa tuni ya manta da ciwon dake damun shi,   Bubbuga kafa tafarayi " wallahi ya Ahmed saika ramamin kuma yau zan koma gidan mu na rantse bazan y'arda ba katuwar banza ta dakeni,   Kama hanyar fita tayi tana kuka yayi dai dai da Shigowar EMA gidan yaci karo da ita zata fita, "Friend ya fada da karfi yana kok'arin riko hannun ta " wata uwar tsawa Muhammad ya buga mai if you dere touch her I will cut up your hands Yayi saurin matsa mata ta fice , komawa yaya ya zube akan kujerar tareda dafe goshin shi, what a drama Queen this girl is unbelievable,   Wani irin murmushi yake saki tareda tuna irin tsirsmai Allurar muguntar da tayi ya shafo wurin yana girgiza kai wace irin yarinya ce wannan?   What an Angel ya furta a hankali yana shafo goshin shi da har yanzu yana feeling hannun ta a wurin, Bai tabajin hannun mace mai taushin nata ba duk da goshin shi kawai ta taba ya kara runtse idanun shi lokacin da ya tuna fadowar ta jikin shi da zuby ta mareta,   Wani irin harbawa marar shi ta kuma yi yace "this girl is going to end my life for sure, yasan samun ta y'anda yake so ba Abu bane mai sauki,   Yasmin kuwa tana fita ta maida kukan ta tsab tareda kyal kyale wa da dariyar mugun ta " shegiya mai hannun rodi gobe ma ki dawo,   Saurin hade fuska tayi tamau lokacin da ta hango Umar tsaye sanye da kaki yana shirin fita aiki ya hade rai shima ganin gidan da ta futo,   Tana matsowa yasha gaban ta "baki isa ba Yasmin baki isa ki hana zuciya ta sukuni ba kuma kije kina bin oga na yanzu don Allah zaki iya bin oga nine bazaki bani hadin kai ba?   Wani irin bakin ciki ne ya rufe ta tuni taji ranta ya baci fiye da tunani wato shi kallon y'ar iska ma yake mata kenan,?   " eh naga ba sabon Abu bane a bariki kuma ai kowa nason ci gaba idan na bika me zan samu kabarni inbi masu garin in more kabarni inbi maza ba mazan Hajiya ba mijin tace,   Ta girgiza jiki tareda yimai gwalo kuma wannan jikin kwalelen ka ta juya a guje tayi cikin gidan,   Maryam ta tareta "lafiya Yasmin wannan irin gudu? Dariya tayi " nida mijin makociyar ki ne, rike baki Maryam tayi "nidai Allah ya rufa min Asiri dake Yasmin,   " Allah ya rufa mana Asiri dai taji muryar mijin ta dake shigowa, "me ya faru Baban Auwal? Shigewar ta tayi kawai batareda taji korafin shi ba, " kanwata zatasa watara na a kulle ni ko inrasa aiki na'   Ya fada mata duk abinda ya faru har na kwanakin baya duka, Maryam tace "oh Allah Yasmin bata girma ya Ismail nada aiki wallahi,   " Yama kirani yana zuwa yanzu bari infada mata, ta fada tareda shiga dakin nata, har ta tube ta daura guntun towel zata shiga wanka,   Zama tayi gefen gadon tareda zubawa jikin nata ido" Yasmin wane mai kike Amfani dashi ne naga jikin ki na kara fresh?   "Mai na daya ne har yau dove ba canji product din yayi wallahi " Hmm ya Ismail ya kirani yace yanata kiranki wayarki a kashe,   "Oh na manta da zan fita na kashe kinganta nan ta fada tana d'auka tareda kunna wa, " to ki shirya yana nan zuwa yanzu, wani irin tsallen murna tayi domin Allah ya sani Akwai shakuwa mai karfi a tsakanin su   "Wayyo d'an Uwa zai zo dariya Maryam tayi " Yasmin kinason shi sosai ko? Shiru tayi na d'an lokaci "ina sonshi irin na yan Uwa kuma yana matukar bani tausayi wallahi ya cika hakuri kina ganin da aka fasa Auren ku ba w'anda yaji ko maganar shi kuma nasan ya damu,   Shiru Maryam tayi kafin ta mike " ki shirya ki fito kuma don Allah Yasmin ki rage daukar magana kuma ki tuna wallahi badon sanadi da dalili ba baki isa ko kofar gidan Muhammad kibi ba don haka ki kiyaye,   Ta fita, binta da ido tayi tareda cewa "Ai sai dai innabar barikin nan zanfita a hanyar shi kuma wannan Umar din sai na kunna mai gobara a gidan shi zai gane,   Karfe tara ranar sukayi shirin tafiya aiki bayan ya sha magun guna domin yaji karfin yin Aikin shi convoy dinshi na Jere suna jiran shi ya fito cikin shigar shi ta green kakin shi akoda yaushe,   Hannun shi rike da Beret mai dauke da logon gauraka a jiki bayajin shi dai dai har yanzu Amma kasance war shi oga kwata kwata dole ana bukatar shi a office,   Dai dai lokacin Yasmin ta fito daga cikin gidan sanye da riga da sket na purple Atanfa da kuma jan gyale tayi wani irin kyau Kamar ka sace ta,   Taku take dai dai fuskar ta a sake a kamun tana cikin farin ciki ta ja ta tsaya a kofar gidan tareda daukar waya tana duba hanya batareda tako kalli kofar gidan ba,   " Yaya Ismail kana ina ? "Ok ka karaso ina tsaye a waje, ta fada tana kara matsawa domin jiran Isowar tashi, ganin motar shi na matsowa yasa ta kara fadada fara'ar ta kamar gonar Auduga,   Tsayawa yayi cak yana kare mata kallo tundaga kasa har sama batareda ya damu da yaran shi dake jiran shi ba. Ahmed dama shi ya dade da wucewa office ganin ogan nasu yau bai fito da wuri ba,   Tsayuwar motar tareda saurin matsawa ta bude mai tareda riko hannun shi kamar zata shige jikin shi yasa Muhammad saurin fadawa motar ya rufe zuciyar shi na wani mugun racing,   Ji yake kamar zai hadiye zuciya ya mutu wani makoko ne ya tokare mai makoshi ya dakawa driver tsawa ya tuka subar nan,   Ita kuwa bata Masan yana wurin ba ta shiga cikin gidan kai tsaye tareda shi tana zuba mai magana,   " ya Ismail nayi farin cikin zuwanka wallahi yasu mama na? Dariya yayi "tace a gaisheki tunda kin manta da ita ko kira bakyayi,   " wallahi nayi kewar ta sosai Allah sarki Mamana, Maryam ta shigo dauke da Auwal tana murmushin jin kunya ta zauna tareda gaishe shi domin ta dade rabon da su hadu tun Auren ta sai kwanan nan da ya karbi numbar ta a wurin mama suna gaisawa,   "Baba yace a gaishe ku aiki yayi mai yawa shiyasa bai samu shigowa ba, "Yasmin kije ki hado muku breakfast din sai kuci tare ko?   " kai Alhmdulillah mama ta kosar dani kafin infito saboda daga nan zan wuce aiki, banida lokaci da yamma,"ina me gidan yake? "Ya tafi aiki, " come boy ya fada tareda mika hannu ya karbeshi, tashi tayi ta basu waje su dan gana,   Matsowa yayi kusa da ita tareda zuba mata ido kamar zai cinye ta, sai da taji kunya tareda dukar da kanta kasa'   "My Yasmin kinyi kewa ta kuwa? " sosai ya Ismail, "ban y'arda ba tunda bakya ko kirana, " Yasmin nakasa hakuri shiyasa kikaga nayi muku sammako yau bazan iya zuwa aiki batareda na ganki ba, Murmushin ta mai kyau tayi mai "ai na kusa dawo wa don zamu fara project din mu next month, " masha Allah Kice na kusa Angon cewa kenan? "Yasmin na matsu wallahi ina son ganin kin zama matata,   Dariya kawai takeyi bakinta ya mutu, a haka suka taba hira har ya tashi tafiya ya baiwa yaron five k ita kuwa shopping ya kawo mata irin su chocolate da kayan shafa,   Tayi godiya yace zai zo daukar ta sati na sama su koma gida bayan sunyi sallama da Maryam,   M.A dai motar na tsayawa ya fito a sukwane kamar bashine Mara lafiyar nan ba wani irin gumi ke feso mai duk da ni imar dake Akwai,   Yau ba gaisuwar w'anda ya Amsa yana fadawa office ya kulle kanshi ya fara sintiri zuciyar shi na tafasa " what is happening to me?   Ya fada yana naushin iska this girl what is wrong with her me yasa zata yi mai wasa da Rayuwa haka?   Me tafi zuby dashi? "Everything yayi sauri ba kanshi Amsa, tunawa da ganin ta da yayi ta riko hannun wannan gayen yasa shi kuma naushin iska Why did you touch him with your soft hand like that? Yanzu shima yaji irin Abinda yaji kenan,? Wani irin watsar da kayan teble din yayi har ma dasu system din sukayi watsa watsa,   Nan take ya danna intercom tareda bude kofar Ahmed ya shigo, Yayi matukar tsorata da yanayin ogan nashi da kuma y'anda ya bata office din gaba daya,   Wani irin mugun kallo ya watsawa Ahmed wanda saida yaji tsoro, " Ahmed you are very careless,   Ya fada kai tsaye idanun shi kamar zasuyi aman wuta, "what happened sir? " you are asking me? "After you live your house open wato bayan sojoji da ka bari suna hulda da iyalin ka har ma da civilian sunada damar zuwa gidan ka ?   " I don't get you sir? "You want get me ai bayan yanzu naga kanwar ka kusan rungume da wani gaye a kofar gidan ka a motar shi how could you Allowed that happening under your roof? Da haka aka saki Matar da ka Aura tayi zaka aureta? "Oga he is their brother and her husband to be I no is Ismail, " what? Husband to be? "Ya fada cikin wani irin kafewar miyau a bakinshi,   " get out in my office before I send you to mess for month Ahmed ya fada jikin shi har rawa yakeyi, Datse kofar yayi wani irin gumi na wanke shi "husband to be in my foot ya fada yana shurin bango ............... *meye haka fan's Kufito muji ya lamarin zai kasance, nidai kucigaba da biyoni*   *Matar soja* [8/30, 2:56 PM] Feenerh Wrtr: _*BARIKI*_ _Auren soja_ _written by fenerh_ Maman Ammar   *Dedicated to* Fiddousi mainasara (¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯)   тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.com/pro__writers?s=09 *ga badaya wann littafi sadaukarwa ne a gareki jigo na FIDDOUSI MAINASARA Allah ya nuna min ranar Aurenki lfy ina matukar Alfahari dake* 13&14 ....Cikin farin ciki ta kasance a ranar har zuwa yamma saboda zuwan Ismail, itadai tasan ba wani son so take mai ba Amma yanada matukar tasiri a zuciyar ta,   Fitowa tayi mazaunar ta domin shan iska taci karo da idanun Umar dake zaune yana shining boot a kofar gidan shi dama Addu'a yake Allah yasa ta fito don yasan wajen zaman ta akoda yaushe,   Wata uwar harara ta watsa mai tareda manna earpiece a kunne tana sauraran wakar ta a natse batareda ta koma kallon shi ba,   EMA ne ya iso wurin kunshe da gulmar shi a Leda ya zauna tareda kai hannu yana niyyar taba ta tayi saurin bude idanun ta, Dariya yasa ganin y'anda ta tsorata kamar ba itace mai tsiwar nan ba "he friend like say no be you they find my oga trouble fear fear girl,   D'an matse fuska tayi kadan " you scared me I swear, "oh sory, " you no what? Kallon shi kawai takeyi "hmm oga bring another girl wo,   "Mtssw tayi tsaki " that's his on cup of tea, that's is why I hate him so much. " but oga no be bad person , "uhm friend wetin they suck between you and oga Umar look at him,   " forget that one I will teach him a lesson that he will never forget for the rest of his life, "Hahh the way you do with the oga love ehem you no tell me wetin happened today? Mikewa tayi kawai domin zancen ya ishe ta shege mai tsinannen son gulmar tsiya " tayi shigewar ta sakaran na binta da ido, Ayyana wa yakeyi dama zata soshi omo he go enjoy woo this hausa girls fine die,   Oga Muhammad kuwa ai yau kamar asibiti yakejin kanshi tsabar rashin natsuwar da zuciyar shi ke ciki he feels very suffocated he is restless   Shiyasa yayi inviting wata budurwar shi da suka dade da rabuwa ko zai rage damuwar da yake ciki,   Tana zuwa ya fada mata natsuwa yakeso ta bashi yanzu he will give her everything she demands Duk wasan da namiji yake bukata a wurin mace tayi mai Amma but ji yake kamar wuta take watsa mai instead of him to feel relive sai wani uban zazzabi ke rufeshi tsabar rashin gamsuwa,   Wani irin hankado ta yayi daga jikin shi har saida ta fado kasa "pack's your load and leave, ya fada da kyar yana jan numfashin wuya,   Wayar shi ya kuma janyowa yayi searching wata number, tana dagawa yace " come to my hause,   Dama masu nema ai ba bata lokaci itama tazo gidan cikin Adon ta gashi Babyn taji komai gata fara jikin ta ba laifi,   "A gaban shi ta kwabe sikitir ta fara takowa domin yin abinda ya kawota tana wani irin juya jiki kamar wata bar dancer,   Amma kallon ta yake kamar ba mace ba duk da tana da cikar halitta baiji wani sauyi ba ba wani karuwar feelings a dalilin ganin nata da yayi a haka,   Ya runtse idanun shi " Yasmin, ya kira can kasan makoshi he remembered when she shake her body koda tsiwa takeyi he feels it   And her soft hand Hmmm yaja wani irin numfashi "get out in my brain please" ya furta a hankali is impossible to get you in my bed,   Domin shi har gobe bai hango macen da zai Aurs ba kawai a huta ne dasu itama yasan da zai samu ta biya mai bukata zata fita akan shi,   Jin hannun ta a jikin shi yasa yayi saurin bude idanun shi ya watsa mata su kamar zaki domin hannun ta kamar wani dutse yaji da ta taba shi, Tsawa ya buga mata mai karfi" get out you are fired, yana buga tsaki tareda kifewa rub da ciki ya dafe kanshi kamar zai ciji katifar yakeji,   Ranar yakira y'an matan shi ba iyaka kuma kowacce baiji y'anda yakeson jinta ba haka yake korar su batareda sun biya mai bukata ba,   Har karfe biyun dare a zaune yake yana dafe da Mara ga machine gun dinshi ta cika boxer y'anda maitar shi bata kwanta ba haka shima bai yi bacci ba har wayewar gari,     Haka dai abubuwan keta tafiya Yasmin hankalin ta kwance batada wata damuwa tanajin dad'in kasan cewar ta da y'ar uwar ta, Batasan da ruwan tsiron MA ba soyayyar ta take kwasa ita da Ismail dinta,   Wata irin shakuwa ke kara shiga tsakanin su koda yaushe tana manne da waya a kunne, ko kuma suna chart idan yana free,   Yanzu ma a zaune take a falon gidan suna kallo sama sama yaron su na wasan shi hankalin ta rabi na kan wayar hannun ta, Wani murmushi tayi ganin sakon da Ismail ya turo mata _zanzo indauke ki gobe ki shirya nagaji da,rashin ki a kusa dani_   Reply ta tura mai _am sory rabin jiki kasan ina taimakon Aunty ne ta fara nauyi ga hidimar Auwal_   Wayar ya kira ta tashi kawai ta shige dakin da take, "hello heart " me kike cewa ? Bazaki dawo ba saboda cikin Maryam idan kinyi naki wazai taya ki zama ?   Wata irin kunya ce ta rufe ta tayi saurin rufe fuska tareda kashe wayar tana mamakin ismail din nata Yanzu, Sam ya canja ya saki jiki sosai komai fada mata yakeyi kai tsaye as he said yanzu ne yake soyayya Maryam shakuwa ce a lokacin shiyasa koda tayi Aure bai damu ba Amma yanzu ji yake idan bai samu Yasmin ba Akwai matsala,     M.A dai kwanakin nan a cikin wahala suke wuce mai ya rasa inda zai tsoma rayuwar shi a office ko a gida gaba daya ya canza Ahmed kanshi ya rasa mai ye matsalar ogan gashi yanzu matan nashi kusan kullum sai ya gayyaci kusan uku ko hudu saidai kanwar duka ja ce, He needs only her that's Yasmin he agree he wants her koda sau daya ne yasan zai samu natsuwa,   Me zaiyi just to get her close to him? Gashi yau kusan sati daya ko daganesa bai hangota ba. "Zuby ya tuna tun ranar da ya koreta bai kuma komawa kanta ba duk da irin rokon da takeyi mai kullum, Janyo wayar shi yayi tunawa da wani Abu yayi murmushi tareda kiran numbar ta, tana d'auka jiki na rawa tafara mai kuka " tank goodness baby ka kirani Am sory please, "Come kawai ya fada tareda kashe wayar 'wani irin tsalle tayi tareda dirowa ta fara shirin zuwa wajen M.A Dad'i kashe ta at least zata rungumi wannan tsadadden jikin nashi ta manta da duk wani bacin rai,   Shi kuwa ya gama tsara komai shi kadai bayason Ahmed yasan plan dinshi akan kanwar shi yana jinkunyar shi sosai,_he is loyal to him tunda suka hadu bashida wani makusanci da ya y'arda dashi kamar Ahmed,   Zuby na zuwa yayi mata bayanin yanason ta zauna nakwana biyu a gidan, akan ku durin da shikadai yasan shi,.   Wani irin farin ciki taji kamar tayi ihu don dadi zata kwana biyu tareda MA yaushe rabon ta?   " and listing if you try anything stupid I will kill you, yafada mata kai tsaye tareda mikewa ya nufi kitchen wurin Aikin Emanuel,   Sara mai yayi ganin ogan yau a kitchen "what are you preferring ? " oga na rice and stew, "no I want kuka soup and if you cook that kuka soup like day before yerstday I will punished you,   Ya juya tareda Addu'ar Allah yasa ya nemo taimakon Yasmin ta zo gidan shine kawai Addu'ar shi, har ya juya ya dawo " am going out do quick before am back,   "Yes sir ya fada yana sarawa komawa yayi saman shi tareda kulle kofar ya kunna system dake connect da CCTV dake gidan domin ganin komai,   Wanka ta fito batareda ta daura komai ba a jikin ta ta fara matso gadon tana wata irin tafiyar daukar hankali,   Dago kanshi yayi ya kalli kirjin ta da suka yi ruku'u duk da sunada cika amma sunfara rankwafawa ,   Kafe kirjin yayi da ido " me yasa duk Yawancin matan da yake hurda dasu kusan haka nonuwan su ke kwanciya? Meye dalili?   "Ni zan fada muku da liki, cudanya da maza kowane jaki da doki ya cagula ki wata ma a rana zata iya hulda da namiji uku ko fiye kuma kowa sai ya taba, mijin ki na Aure guda daya idan yana tabaki yau da gobe halittar ki na sauyawa tackles of maza da yawa, yan mata ku rike mutuncin kanku Abubuwan da muke gani wallahi bazasu fadu ba sai dai Addu'a Allah ya shirya mana zuri'a,   Ganin tana shirin matso shi yasa ya daga mats hannu tareda nuna mata kujera " sit there ba nakiraki Kizo ki dameni bane ya fada tareda maida hankali kan system din shi, Komawa tayi ta zauna bayan ta daura towel ta zabga uban tagumi tana kallon kyakkyawar fuskar shi dake hade "yaushe ne zata samu ta mallake shi gaba daya ? Yaushe zai y'ar da ya bata matsayin Matar Auren shi,? Wannan ne kawai burinta a Rayuwa yanzu ba Abinda take nema sai kasan cewa Mrs Muhammad Abdullah for ever,   Kamar yadda yayi tunani kuwa da gudu Emanuel ya fita domin ya gwada yafi sau uku yana zubar wa miyar takiyin yadda Yasmin tayi ranar gudaji take yi kuma sai tayi wani irin kitif da ita,   Tayi wanka kenan tagama shirya wa cikin wani tree quarter na mata da rigar shi armless pink color mai zanen fari a gefe kamar na tracksuit, Ta janyo wayar ta domin yin chart da Ismail dinta kenan Aunty Maryam ta shigo, " Yasmin ki zo Abokin barin ki na kira yana nan waje "Emanuel? " waye inba shiba, naga jikin shi na rawa kamar wani mazari, "Hhh ya debo sabuwa kenan bari inje inji, " Kudai kuka sani da gulmar Abinda bai dame ku ba, Hannu tasa ta dunkule sumar kanta data gama gyarawa ta janyo hijabin ta dogo ta sanya mai hannu brown color fuskar ta na wani irin sheki ta saka silipas ta fita,   "EMA how far? ta fada ta na Sakin mai murmushin da yasa shi d'an tsayawa yana kallon ta " ohh friend you are very beautiful, "I no that hope you are not here just to tell me am beautiful? " noo na oga wahala wo today ma na that kuka soup he want,   Daure fuska tayi tareda cewa "and so ? " please I beg you friend I try try he no sweet like your on,   "Look go and try your luck am not going anywhere you no I don't like going there,   Guiwar shi yasa akasa yafara rokon ta tazo ta taimaka mai kafin ya rasa Aikin shi, Jin yace ogan ya fita yasa ta ce suje kawai batareda tunanin komai ba, Tundaga farkon Shigowar ta gidan yayi wata irin wa war Ajiyar zuciya yafara binta da kallo har lokacin da ta shiga kitchen din,   Fuskar ta ya kafe da ido yana kallon natural kyau ba makeup ba komai but she look very beautiful, what a baby dol, Addu'a yakeyi dama ta cire hijabin jikin nata yaga irin dressing din da tayi yau don ya lura Yarinyar Akwai iya dressing, Kamar wata model,   Kamar tasan me yake tunani ta yi saurin cire hijabin tareda daura shi a west din ta ga Emanuel a gefe yayi mugun maida hankali akan ya koyi miyar don yasan next time ko yana tsafi da bakin dodo bazata kuma dawo wa ba don tanayi tana mita akan shine na farko kuma na karshe,   Tunda ga kafar ta yafara kare mata kallo yana hango fararen kafafunta masu laushi har zuwa west dinta duk da ta daura hijab akai, Kafin ya dire kan kafadar ta dake waje saboda rigar Armless ce wani irin Abu yaji ya tokare mai wuya ganin kayan bai kamata ta cire hijabi a gaban Emanuel ba *y'an matan yanzu ai sai dai Addu'a wayewa tasa muna mantawa da Al adun mu na bahaushe ni da idona naga budurwar da tazo wurin saurayin ta a bariki baya gida ta kwabe ta fara yimai girki ga Abokan shi a gidan karshe da shedan ya musu huduba kusan fyade suka yi mata kafin saurayin ya dawo me yasa y'an matan yanzu kuke biyewa samari suna bata muku tarbiya?* Yayi saurin ture system din shi ya diro a gadon yana gyara zaman guntun wandon nashi iya guiwa jikin shi ba riga ya kalli zuby dake kwance ta fara bacci kafin ya fice,   Kitchen din ya nufa cikin sauri, hankali kwance ta baje tana Aikin ta yau har tuwon ita take tukawa da kanta ta kunna kan gas biyu y'anda zatayi sauri,   Jin motsin mutum yasa Emanuel juyowa daga kallon ta da yakeyi tana nuna mai komai, Wani irin razana yayi jiki na rawa na ganin ogan nashi ga kuma Yasmin a gidan "I don die ya fada a ranshi jiki na rawa zai yi magana ya mai Alamar ya fice da ido,   Batasan wainar da ake toya wa ba ita dai taci serious tana nuna mai kawai, Taji shiru batareda Amsar shi ba ta juyo " are you with me ? If you call me again.......... Kawai taga mutum tsaye ya nade hannu tareda harde kafafu ya zuba mata idanun shi da suka kada sukayi ja yana mata wani irin kallo,   Saida cooking spoon din hannun ta ya fadi wani irin rawa jikin ta ya farayi har saida hijab din dake daure a west din ta ya fadi, Kallon jikinta yakeyi tundaga kafarta har zuwa kirjinta dake up and dwan kamar tayi gudu, w'anda ke kara tafiya da jinin jikin shi har ma da ruwan kwakwal war kanshi,   Matsowa ya farayi a hankali yana taku dai dai tayi saurin matsawa jikin sink din kitchen din tareda runtse idanun ta wani irin tsoro ne ya rufe ta, "Na shiga uku don girman Allah kayi hakuri wallahi bazan kuma yi ma rashin kunya ba bazan kuma zuwa gidan ka ba bazan kuma fadawa budurwar ka ni Matar ka bace kuma wallahi Allurar ranar ba mugunta nayi maka ba don girman Allah kayi hakuri bazan karaba kuma zan ba karuwar... Au budurwar ka hakuri......   Wani irin Jan numfashi tayi jin numfashin shi gab da nata ga kamshin shi ya cika mata hanci impact duk da bai taba taba amma she feels his body all around her body, Ya mata runfa ba a ko hango ta ya rufe ta ruf,     Bude idanun ta tayi dake cike da hawaye tayi kamar zata shige cikin sink taga yana mata wani irin kallon da ta rasa na meye,?   " come Always you are welcome, Kizo gidana koda yaushe ya furta akan fuskar ta tanajin wani irin fresh mouth scent a bakin shi, da yasa ta ji jikinta ya mutu murus,   "Ki fadawa ko wacece ke matata ce ba komai I don't care Kizo gidana koda yaushe bazan hanaki ba be my friend please feel free with me,   Wani irin karfin zuciya taji ya zo mata jin irin magan ganun shirmen da yake wani fada mata tayi wani irin matsawa tareda daukar hijabin ta tana shirin gudu,   Yayi carab ya riko tsintsiyar hannun ta saida yaji cikin shi ya juya jin hannun ta ya fisgo ta idanun shi na kasa rinewa,   Ya maida ta jikin sink din " waye ranar na ga kin riko hannun shi da wannan Hannayen? Wani irin kallon tsoro take mai   "Tell me waye shi? Wai Auren shi zakiyi? " don't Mary him he didn't deserve you, Kok'arin kwace kanta takeyi ya manne kirjinshi da ba riga da nata a jikin sink sai Ajiyar zuciya yake sauke wa "baki dace da kowane namiji ba you deserve some one special like you are,   " kan uba wato gayen nan iskan cin shi har akanta yau Zako taci ubanshi wallahi sai ta koya mai hankali, Ita ba y'ar iska bace ba irin matan da yake kwaso wa bace, bakinta ta bude cikin tsiwa tareda saita natsuwar ta,   Duk da yana nan dafe da sin ya sakata a tsakiyar shi yana karema ta kallo he feels her chest on his how full they are ji yake da zata bashi dama zai taba for the first time he feels zaiyi romancing mace da kanshi a kanta,   Saukar da idanun shi yayi dai dai chest din su yana d'an raba jikin su yaji maganar ta mai kama da Kibiya ko mashi,   "My Ismail ka ganshi ranar? My dream man pure heart and clean bai taba tsayawa da ko wace mace ba bare har yayi wani Abin da bai dace da ita ba, He is innocent in and out that's why I love hi........jin bakinta a rufe da wani Abu mai laushi da santsi tareda wani irin d'an dano yasa maganar ta tsayawa,   Kafin ta San same bakin nata yake rufe taji yana bata wani irin soaking kamar zai cire mata tongue     Idanun ta a waje lokacin da ta Ankare da abinda yake faruwa da ita' tsotsar bakinta yakeyi?   Innalillahi yau ta kawo kanta gidan d'an iska wasu irin hawaye ne na bakin ciki suka fara zarya a idonta suna rushing,   Shikuwa jin shi yake kamar yana fly karon farko da yake kissing bakin mace duk huldar shi baya hada baki da mace, ko zuby tayi maitar kissing dinshi har ta gaji,   Gwara da bai taba kiss ba da yasha kowace irin kazanta don kuwa it feels amazing da he can take it any more , her mouth test very sweet, Jin shi yake kamar yanabawa kanshi maganin yunwar dake damun shi na shekaru wani irin mazari jikin shi yakeyi kamar zai zube a wurin,   Hannu tasa tana tureshi tareda kuka can ciki domin bai bata damar kukan ba saida ya gaji da kanshi ya samu natsuwa kafin ya zame a kasan kitchen din yana maida numfashin gamsuwa,   Shafo wandonshi yayi yaji yayi wet he can believe it ya dago kanshi yaga y'anda ta cure a wurin tana wani irin kuka cankasa kasa,   Muryar ta bata fita wani irin kallo yake mata yarasa y'anda zai fassara ta only kiss ya samu abinda yake nema a week,   Tashi yayi jin k'auri ya kashe gas kafin ya dawo ya zauna dabas a gaban ta ya dora hannun shi a kanta, saurin zabura tayi ta kalle shi idanun ta sunyi ja,   "Allah ya isa shine kawai Abinda zan fada maka yanzu ban yafe maka ba ka cuceni da ka hada mugun bakin ka da nawa jikina mai tsarki ne ka tabani da jikinka na zina, Na tsane ka ban taba tsanar wani a duniya Kamar kai ba wallahi sai anyiwa Matar da zaka Aura kai ma kaji inda dad'i,   " w'anda duk yayi kuskuren taba ta zan iya kashe shi she is belongs to me only me ya furta a hankali,..............   *Matar soja* *BARIKI* _Auren Soja_   _written by FENERH_ Maman Am mar   *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby PROFICIENT WRITERS ASSOCIATION тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09   *UHMM!!! Wai miya sa sis feenat kuke mani hakane?sis aysha alto maza ki jawo mani sarauni da shalele, aunty hanne maza rike mani su ni zan fara*,   *Tirkashi* *Rigi-rigi babban dahuwa, mai karya itacen yaro. In kaji tambari sai sarki, in kaji jiniya sai gwamna. Biki na farar kaza, balbela ba gaiya ba.* Ina kuke? Masoyan *PROFICIENT WRITERS ASSOCIATION.* Kungiyar da Ta tara kwararrun marubuta, masu aiki da basira da hazaƙa.marubuta ne wadan da suka san kan alkalami, yayinda suka karanci matsalalon da duniyarmu ta yanzu ke ciki, basu tsaya a nanba, saida suka zaƙulo maganin matsalalon. kai baki bazai iya baku labari ba, sai dai ku kasance tare da mu, bayan kun antaya shafin mu na Facebook . FACEBOOK: https://mobile.facebook.com/groups/2455147078097572/ *Proficient writers association* *Uhmm lallai!!!, ummu najma ki dena rawan kai,ke nuseey, ina ki ke,wallahi kija da baya, ammiyn khairat, sis khadeeja haydar ku kamo mani su, tirkashi!!! Ashe yaya indabo da yayah sadiq suna neman riga na, bari ku gani*, Ap. Na manta ban fada muku ba masoya. Wannan kungiyar mai haɗin kai, da zaman lafiya, Uwa Uba soyayyar gaskiya da amana, sun shirya tsaf domin kawo muku Audio ɗin littaffan kunyigiyar gaba ɗaya. Bisa Youtube channe namu. https://m.youtube.com/channel/UCa6VZD_0ZlXycCLTT1i-ygQ *Proficient writers association* *RUkayya ikra ya naga kina ta ɗaga hannu ne!?bari kawai!! sia shamsiyya da sa'a datu naga suna gyan gyaɗi, shine zan taɓasu karda abarsu abaya,* *Muna maraba da ku masoyan duk ku antayo, domin, muna alfahari daku ta kuce ta muce,* ~Mu kafta~‍♀️ Alhmdulillah nadawo masoya na Ina Mai farik cikin irin kaunarda kuke nuna min nagode da irin kulawarku agareni fenerh na matukar kaunarku my fans, 15&16 Wani irin kallon tsana take watsamai da idanun ta dake cikeda hawaye ta rike hijabinta dake shirin faduwa daga west dinta,   "Allah ya isa d'an iska kawai ta fita aguje zuwa falo Domin fita daga cikin wannan mugun gidan da take fatan Kada Allah ya nufeta da kuma shigar shi har karshen rayuwarta, Wani irin uban karo suka gabza ita da zuby tayi saurin gyara tsayuwarta Dama cike take da bakin cikin da M. A ya sanyata ciki aikuwa ba bata lokaci ta shake wuyan zuby Domin sauke takaicin akanta, "Shegiya karuwa masu zubarwa da mata aji, saboda irinku maza kema sauran mata kallon duk daya ne halayen mu wallahi kun tabka hasara a rayuwa ta wani irin tureta tareda barin gidan a guje cikin kudurin barin barikin a yau kuma bazata kuma dawo cikin shiba, Zuby kuwa cikin Rudu da takaici ta kasa cewa komai ga zafin shakar da YASMIN tayi mata ga takaicin cin fuskar da MA yake mata Domin tasan da gangan yasa tazo gidan Domin ya wulakanta ta,   Juyawa tayi da nufin wucewa tagan shi A tsaye ya nannade hannu idanun shi a lumshe yana wani irin murmushin da tsawon zamansu bata taba ganin irin shi akan fuskar shi ba,   Cikin fushi ta matso shi "Muhammed takirashi kai tsaye "Wato saboda inga kana rayuwa da wata macen yasa kakirani gidanka KO? "To Kayi kuskure Domin koda akan mace nasameka bazaisa in rabuda kaiba, takarashe maganar hawaye na zubo mata a idanun ta ta matsa gab dashi tareda SHAFA fuskar shi Mai annurin data rasa Ina yasamo asali a yau, "Katuna tsawon shekarun da Muka dauka tare nidakai bazan iya rayuwa dakowane namiji ba bayan kai MA Ina mutuwar sonka kasani kaima nasan kana sona, Wani irin kallo ya watsa mata Mai cikeda ma anoni da Dama amma bai bude baki ya bata Amsa ba Sai ma wucewa da Yayi direct dakinshi ya fada bathroom ya kwabe gajeran wandonshi yana Mai kallon irin ruwan da ya zubar cikin minti kadan to inada yasameta gaba daya? Wani irin tashi yaji tsigar jikinshi nayi dakyar ya watso ruwa ya fito daure da towel Sai tsiyaya yakeyi alamar wanka ya fito, Wani irin kallo zuby kebinshi dashi tareda saurin zabura cikeda masifa ta nufoshi, "M. A Ina gidan nan ka kwanta da wata mace? Bayan nakawo kaina ko kabani kulawar da kasaba bani abaya "MA nicefa zubynka Meye bana yimaka da kakeson fitarda ni daga rayuwarka? Tayi saurin jefarda towel din dake jikinta tareda riko nashi saurin dafe hannun ta Yayi tareda tureta gefe, "Ki Kama kanki ko kiyi waje yanzu, ya fada tareda fadawa kan gadon shi ya kife tareda runtse idanun shi yana mai tunanin lokacin da ya wuce,   Wani irin bakin cikine ya rufeta ganin irin wulakancin da yake shirin yi mata bayan shine ya gayyato ta gidan nashi,   Da yake mayyace matsawa tayi kan gadon tareda kwanciya a bayanshi ta Dora hannun ta ta kasan kirjin shi ta fara shafoshi a hankali,   A lokacin tuna nin shi gaba daya yayi nisa ji yake kamar a lokacin ne yake tareda YASMIN he remember her lips and how they test, Wani irin mika yayi tareda juyowa da karfi tayi saurin hade bakinta da nashi idanun shi na rufe yaji lips dinta a nashi kasan cewar yana cikin shauki yasa shi saurin bata agaji   Wani irin mugun kiss yake bata saidai baiji yanda yaji da farko ba Sam ba test din da yaji dazu ya yi saurin bude idanun shi ya watsa su kanta, Wani irin hankadeta yayi tareda mayarda towel dinshi data kwance batareda yasani ba, wani irin kallon tsana ya ke watsa mata yanajin mugun kyamar hada bakinta da nashi fa tayi wani irin tashin zuciya yaji tuni ya bude mouth wash ya kuskure bakinshi saida ya saita kanshi kafin ya sakarwa kanshi shower ya fito yana mai zuba mata mugayen idanun shi masu girgiza maza,   "Why did you kissed me?? Shine abinda ya fara tanbayarta cike da tsawa, ta taso tana kwarkwasa fuskar ta dauke da farin cikin yau ta d'an d'ana miyan da ya dade yana mata rowar shi, Kokarin shigewa take jikin shi ya watsa ta gefe "kin san banaso why did you do it? Now out before you regret nowing me,   Idanun ta ta watso waje tana Mai tsananin mamakin canjawar shi gaba daya MA ya canja, "This is not you, "me yasa kakeson ka koreni daga cikin rayuwar ka, bayan kasan is impossible in rayu batareda kaiba, please don't purnished me like this muhammed, Wata uwar tsawa ya buga mata "zuby out before I loosed my temper, ba arziki ta hada kayanta ta bar gidan kafin ya mata na jaki don tasan halin shi don yanzu ya mata dukan sojoji bakomai bane,   Tana fita ya datse kofar shi ya kuma fadawa gadon yana mai tuna YASMIN "please baby come to me shine kawai ya fito daga bakin shi He really want her she is the only woman he want right now she is perfect wonderful and amazing, He can do anything to get her in his life,   YASMIN kuwa Tana fita ta saita kanta Kafin tashiga gidan tayi Sa a ba maryam a falon saida ta shige dakin ta wurgarda hijabin ta kafin ta fara hada Kayanta, Tareda kudurin barin barikin baki daya a yanzu Domin ta tsani duk wani Soja ma da mugun halayen shi har mijin yayar tata yau bazata so su hadu ba bare wani d'an iska daban Cikin sauri ta fada ya watsa ruwa tareda yin brush sosai don ta wanke miyanshi da ya gauraya da nata Tana binshi da Allah ya isa yafi Sau d'ari,   Saida ta shirya cikin sauri sannan ta fito tareda leka y'ar uwarta ta ga Tana bacci ita da yaron ta ta a jiye mata letter tayi waje da saurin ta don bama ta fatan Kara koda second ne a cikin barikin   *********************** Mama tayi mamakin ganin YASMIN a wannan lokacin sai dai Tana tanbayar ta dalili tace tanada project ne a school Gobe shiyasa ta dawo, Bata kuma tanbayar taba ta ce tazo ta deba abinci taci, "banajin yunwa mama zan kwanta ne kafin akira sallar magrib, "Aa kinsan kwanciya a irin wannan lokacin batada amfani ki zauna muyi magana, Zama tayi jiki a sanyaye ta zubawa mama ido, "dama babanku ya so insa kidawo kan maganarki da ismail yanaso a gama komai kafin nan da wata daya kya karasa karatun a dakin ki, Wani irin bugawa kirjin ta yayi batasan daliliba kawai taji Sam bata farin ciki da lamarin nan yanzu,   "Kinyi shiru ko akwai matsala ne? Saurin girgiza kanta tayi tareda cewa "aa kawai dai naso sai na kammala karatuna ne kafin ayi maganar Auren "Meye matsalar Yasmin kinfa san halin d'an uwanki ko a gidan wani ne ma shi me iya taimaka miki ne kiyi karatu bare kuma shi Zaki Aura, "Ina tayaki farin ciki YASMIN Domin ni na rike yaron nan nasan nagartar shi zakiji Dadin rayuwa dashi ke kinsani,   Mama ta dade tana mata nasiha tareda nuna mata halaye masu matukar Burgewa gameda ismail, ************ Misalin karfe goma tana kwance a cikin dakin ta a katuwar katifar ta hutadda gadon ka waya takeyi da y'ar uwarta tana bata hakurin irin tafiyar da tayi ba sallama sai tanbayarta takeyi dalilin hakan amma amsar daya ce dalilin project,   Da sallamar shi ya shigo dakin ya nemi gefe daya kan stool din mirrow ya zauna tareda zuba mata ido tane wayar a natse, kallon ta yakeyi kamar ya hadiyeta tana sanye da hijabi amma fuskar ta tayi wani irin fresh takara yimai kyau sosai,   Saida ta gama wayar kafin ta mike zaune ta dukar da kanta Kasa tana mai wasa da wayar tata, "sannu da zuwa ya ismail, saida ya sauke ajiyar zuciya kafin ya iya amsa mata fuskar shi cike da annuri, "Gimbiya sannu kema meyasa baki fadamin Zaki dawo yauba ai Dana zo na daukeki da Kaina, Murmushi tayi kafin tace "shiyasa ai naki fadama banaso ka wahala,. Amma naji Dadin dawowarki gida hankalina ya kwanta don gaba daya a tsorace nake kar sojoji sumin kwace nasan su da son mata bare tawa princess dole wani ya k'yasa, Gabanta ne ya fadi tunowa da abinda ya faru har saida ta daga hannun ta ta shafo lips dinta tana mai tuna yanda ya rika tsotsar su kamar sweet take taji gashin jikinta na mikewa, Maganar ismail ta dawo da ita hayyacinta, "samari nawa kikayi a barrack? Bako daya ta bashi Amsa "ai bana zuwa ko Ina ya ismail kuma ga ka ya zan saurari wani namijin, Yaji Dadin maganar tata sosai ya mike "ki huta zamuyi magana sosai Gobe nasan mama ta fara fada miki ko,? Tasowa tayi tana mai rakashi har saida ta kai gab da gefen part din shi ta tsaya Shima ya juyo tareda zuba mata eyes "baby na matsu ba a daura mana Aure ba Ina bukatar mace a tare dani kuma ban taba sawa raina hakan ba sai ta dalilin ki Ina matukar kaunar ki baby Wallahi in narasaki akwai matsala Babba,   Sun dade yana amayar mata da sirrin zuciyar shi tun tanajin kunya har ta saki jikin ta ta bashi kulawa itama tareda kwantar mai da hankali kafin su rabu,   *********** After a week Tun karfe takwas yau da MA ya fito yake zubawa kofar gidan ido kasan cewar weekend ne, yau kusan sati ko giftawar ta bai gani ba tun ranar da tabar gidan shi bai kuma ganin taba Duk ya fita hayyacin shi ya Kasa natsuwa har a wurin aiki baida walwala gashi bazai iya fadawa Kowa cewa ita kawai yakeson gani ba, Y'an matan shi kuwa ba wadda yake saurara don bai cikin natsuwa bare har yanemi wata mace, Yaran Shima basa ganewa ogan nasu yanzu haka yagama zubawa gidan ido kafin ya koma cikin falon sai faman sintiri yakeyi, Ya dauki waya Sau ba adadi yanaso ya tanbayi Ahmed Amma yakasa to me zaice mishi? Yaron shine fa kar yayi wani tunani akan hakan Yana hakan Emanuel ya shigo tareda Sara mai cikin girma mawa ko iya Amsa mai baiyiba har ya wuce yayi saurin tsayar dashi, Ya dawo cikin hanzari tareda kamewa tsaye kem "yes sir, ware is your friend? "Oh Oga my friend don go back na yerstaday I ask her aunty she tell me say.... "Go ya fada cikin saurin katse labarin jikin shi NA rawa ya mike daga zaunen ya haye sama cikin sauri ya fada bathroom Domin shekawa kanshi ruwa,   Kana nan kaya yasa sunyi matukar karbar shi ya feshe jikinshi da turare tareda daukar makullin motar shi yayi waje cikin hanzari,   Yaranshi na ganin fitowar shi suka nufo cikin hanzari ya daga musu hannu "no need am going a lone ya fada tare da fadawa cikin marcedez benz dinshi kalar army tana sheki ya figeta tareda fita gate din a guje, ***"*********** Tafiya takeyi a hankali a gefen babban titin gwamna road Domin tayi ta jiran mashin ko napep kusan hour guda amma bata samu ba Unguwar bata cika hayaniya ba da wuya kaga giftawar Abin hawa kasan cewar Unguwar ta masu hannu da shuni ce,   Tagaji iya gajiya ga Han nun ta rike da wata katuwar jaka dauke da sakon da ta Amsowa mama, ganin bazata iya doguwar tafiya ba yasa taja ta tsaya tareda fiddo wayar ta, Yaya ismail ta fara nema Kira daya yayi cutting tareda calling her back, "Alhmdulillah ta fada tareda fada mai halin da take ciki jikin shi na rawa yace innalillahi Amaryata jirani Ina zuwa yanzu Ina kusama da Unguwar ai da kinfada min Nazo nakaiki, Katse kiran yayi tana mai jin Dadin y'anda yake matukar ji da ita, Ta ajiye jakar agefe ta tsaya,   Tundaga nesa ya rage speed din da ya kwaso ya zuba mata ido yana fitarda wani irin annurin farin ciki sati daya rabon da ya ganta Amma yau gashi ya ganta batareda ya yi tsammanin ganin ta ba Fakin yayi gab da ita ya fito batareda ya rufe motar ba ya nufo ta............ ️ "Kuyi min afuwa dole sai na daure kafin insaba da typing yanzu kunsan jiki yasaba da zaman banza kuyi manage da wannan love you all my fans, *Matar Soja* [8/30, 2:56 PM] Feenerh Wrtr: PROFICIENT WRITERS ASSOCIATION тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *Tirkashi* *Rigi-rigi babban dahuwa, mai kare itacen yaaron. In kaji tambari sai sarki, in kaji jiniya sai gwamna. Biki na farar kaza, balbela ba gaiya ba.* Ina kuke? Masoyan *PROFICIENT WRITERS ASSOCIATION.* Kungiyar da Ta tara kwararrun marubuta, masu aiki da basira da hazaƙa.marubuta ne wadan da suka san kan alkalami, yayinda suka karanci matsalalon da duniyarmu ta yanzu ke ciki, basu tsaya a nanba, saida suka zaƙulo maganin matsalalon. kai baki bazai iya baku labari ba, sai dai ku kasance tare da mu, bayan kun antaya a cikin wannan link. https://www.facebook.com/groups/2455147078097572/?ref=share Ap. Na manta ban fada muku ba masoya. Wannan kungiyar mai haɗin kai, da zaman lafiya, Uwa Uba soyayyar gaskiya da amana, sun shirya tsaf domin kawo muku Audio ɗin littaffan kunyigiyar gaba ɗaya. Bisa Youtube channe namu. https://m.youtube.com/channel/UCa6VZD_0ZlXycCLTT1i-ygQ *Muna maraba da ku masoyan duk ku antayo, domin, muna alfahari daku* ~Mu kafta~‍♀️ *BARIKI* _Auren Soja_   _written by FENERH_ Maman Ammar *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby   17&18 Wani irin ja da baya YASMIN tayi domin tayi mugun tsorata da ganin shi a irin wannan Unguwar da za a iya sace mutum a gudu, Nan take jikin ta yafara rawa ta fito da idanuwan ta duka waje tana ja baya,   Shikuwa wani irin farin ciki Yaji na ganin ta nan ya fara sauke ajiyar zuciya yana tunkarato, Taku biyu ya riko hannayen ta yana mai kare mata kallo kamar wani mayun wacin Zaki,   Saida ta fada kirjinshi yayi wata wawuyar ajiyar zuciya, kafin ya bude baki ya fara magana, ", baby guduna kikeyi? "Toh ki daina couse koda birnin misra kikaje zan nemoki, kokarin fisge kanta takeyi tareda d'an dukan shi a hankali, "Ka barni banason iskanci ni ba irin Y'an iskan Y'an matan ka bane, "Zaki zama fiye dasu baby tunda raina ya biya akanki kinga kinada laifi daban daban kizo muje mota zanfada miki laifin,   Wasu irin hawaye ne suka zubo mata yau Allah ya hadata da d'an guguwa ba d'an iska bama kadai, Cikin karfi yajata da hannu daya ta tirje ya tsaya cak tareda zuba mata idanu cike da wani irin kallo irin na Y'an duniyar maza,   "Zan daukeki idan baki wuce mun tafiba, sautin kukanta tuni ya fito tafara y'ar fa hannu "don girman Allah ka wuce ka kyaleni yanzu mijina zai zo ya dauke ni ka rufamin asiri,   Wani irin fisgota yayi cikin karfi ya jefata motor kafin ya daga jakar ya jefa baya ya rufe cikin tsananin takaici ya tayar da motar batareda ya ce mata komai ba,   Da gudu yake tukun idanun shi sunyi mugun kadawa kamar wuta saida yayi nisa sosai da Unguwar kafin ya koma gefen titi ya faka, ita kuwa ai ta dade da sallamawa Allah ikonshi yau tana ganin rayuwa,   Juyowa yayi bayan ya dauki lokaci kanshi nakan sitiyarin motar, "tell me yaushe kikayi Aure? Saida ta Kara mannewa da murfin motar kafin tace "ankusa yine ba ayiba,   Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya kalleta cikin wani irin yanayi "zakiyi kuskure baby, karki fara y'arda da Auren wani, "Ko bazan Aureki ba dole ki rayu dani y'anda nakeso Aure baya cikin tsarin rayuwa ta don haka kizo kiyi rayuwa dani shine kawai kwanciyar hankalinki da nawa baki daya, Ai tuni taji tsoran shima da takeyi yafita a cikin zuciyar ta don iskancin nashi ya girmama, ta k'ank'ance idanun ta domin fara zubomai ruwan rashin kunya,     "Kutumar bala'i me ka dauki mace? Wallahi ko a mafarki Kayi tunanin rayuwar BARIKI dani Allah ya isa bare a zahiri, kai mu ya'ya ne NA halas ba haihuwar dadiro ba kuma duk d'an halas bazai taba y'ar da tarbiyar da iyaye na gari suka bashi ba, "Bari kaji ra ayina akan ka da duk wani namiji irinka natsani halayenka tir da bunsurancin ka Allah ya wadaran duk wani namiji mai halaye irin nak.......   "Shhhhhh, ya Dora Han nun shi a kan bakinta yace "breath baby ki numfasa haka mana ya furta yana mai fitarda wani irin mugun murmushi, "Kina yiwa uban yaranki dazaki Haifa a dadiro baki ki Bari karki lalata min Yara, Wani irin kallonta yakeyi tundaga Kasa har sama hijab din yayi mata kyau Amma shi zahirin ta yakeson gani a yanzu,   Tana kan ruwan bala'i ta tsinci hijabinta a Han nun shi ai kuwa a razane ta kurma mai wani irin ihu har saida ya to she kunnen shi, "Baby relaxed Zaki ciremin dodon kunne, wani irin kallo ya fara yi mata mai cike da ma anoni mai dama nan take kalar launin idaniyar shi ta sauya zuwa na bacci, Rigace doguwa roba irin na yayi mai kamar pubu ta kamata tam ga kirjin kamar yayi kuwa saboda tsabar cika da daukar hankali Allah ya hore dukiyar fulani a d'an madai daicin jikinta,   Wani irin yanayi ya tsinci kanshi a ciki Wanda bai tabajin irin shi ba kirjin shi na bugawa da sauri baisan meyasa yakejan haka ba koda hotan ta yakalla sai gaban shi ya fadi,   Karar waya ya dawo dashi daga doguwar tafiyar da yayi a tunanin wannan tauraruwar, Cikin sautin *Alkawarin mu na nan* na umar m shareef Kallon wayar yayi a akan kafar ta yaga my soul Kafin ta dauka tuni ya fisge tana tafara cewa kabani wayata nasan nemana yakeyi karka daga mai hankali,   Picking yayi tareda sakata a handfree, "Kina Ina shine maganar data fara fitowa, Saurin mika hannu tayi "Yaya ismail na na samu Abin hawa na tafi Kayi hakuri mu hadu a gida, "Hmmmm da hankali na yatashi da nazo banganki ba kar amun salalar tsiya a dauke min AMAR..... Kit ya datse kiran tareda bude window ya jefarda wayar ta tarwatse kaca kaca, kafin ya juyo ya fisgota "ki fita hanyar yaron nan idan kina son lafiyar shi Wallahi zan iya illata shi akan ki koda kallonki yayi,   Wani irin murmushin takaici tayi tareda ja baya yau Ina ganin iskanci, "saboda kai waye a wurina da zaka sanya min doka da kuma IkO? "Nine nafi Kowa isa da iko akanki nafi Kowa right akanki I felt like tun tuni kina tare da rayuwa ta na Kasa sukuni saboda ke bansan meke damu na ba Aure baya cikin tsari na haka ajiye mace daya tal ba ra ayina bane tunfarko amma saboda ke inajin zan iya killace ki ke daya zan iya rayuwa dake kekadai,   ("Give me chance) kibani dama I will give you everything idan kuma kin bijire zan gwada karfina don haka zabi ya rage nake,   "Go Ahead ubana Allah ya fika kuma zai kareni daga duk kan sharrin ka yanzu Dan iskancin ka ya rik'a duk karuwan ka sun yima kadan sai ni?   "Bana ra ayin kowace mace sai ke kuma iskancin da kike fada akanki zaifara da wasa nakeyi ba BARIKI ba akanki zanfara BARIKI kisa ido,   "Meye sunan ki na gaskiya? "Ka shafa kaji ta fada tana murguda mai baki harda doguwar tsuka, saidai kafin takai karshe tuni ta tsinto hannun shi a saman kirjinta yana shafa fatar dake waje, wani irin buge mai hannu tayi kafin ta sanya mai kuka, "Allah zai sakamun kuma sai anyiwa naka kaji inda dad'i, runtse idanun shi yayi yanajin wani irin feelings da ya jangwalowa kanshi,   "Baby ki daina yiwa yaranki baki, "Allah ya sauwake Wallahi ko a mafarki nayi ciki akace nakane sai na zubarda shi kafin in farka, "Ni kuma ko a mafarki naga likitan da yamun asarar cikin jikin ki sai na dauke kanshi da bindiga muje zuwa,   "Don darajar iyayenka kabani hijabina intafi gida, ba musu ya mika mata ta ce ka bude min kofar, Tayar da motar kawai yayi "ki fada min gidanku ko in wuce dake gidana daga yau afara zaman dama a matse nake,   Ba musu ta fada mai tana Adduar neman tsari ga wannan mugun bawa a hankali yake driving kamar kar yakai yakeji yanajin D'ad'in moment din wani irin nishadi yakeji,   "Da ma zanje wurin hajiyata intanbaye ta gidan ku kinga Allah naso na naganki cikin sauki batareda bata lokaci ba har Zaki kaini da kanki,   "Zaka gani d'an iska inzan kaika gidan mu, Ganin ya nufi Unguwar Dosa yasa gaban ta ya mugun faduwa kardai yasan gidan nasu? "Ina ne layin naku yake? Wani gida ta nuna mai gaba kadan d'an karami ya faka tareda cewa kije tom sai anjima yayi saurin jan motar ya bar wurin saida taga andauki lokaci tafara takawa rike da jakar ta domin karasa wa gidan su,   Saida taje gab da shiga gidan taji yace "ki kulamin da kanki baby bye, ya fada cike da dariyar mugunta wani irin zabura tayi ya shige da gudu gidan, yau Allah ya hada ta da tsinanne, Juyawa yayi ya nufi inda ya bar motarshi cike da farin ciki ya fada tareda bata wuta ya bar Unguwar duk inda ya bulla ansan wannan wani ne domin motar da kawai yake ciki sheda ce,   *************** Cikin farin ciki ya kwana yau yana juyi a gado yana tuna dramar su da ita wayar shi ya janyo tareda duba lokaci yaga kusan karfe daya na dare gashi Sam bacci ya Kasa daukar shi, A nan ya tuna da barnar da yayi ja fasa mata waya dafe goshin shi yayi "oh god ya furta kafin ya diro Kasa alwala ya yo ya Tada sallar nafila ganin bacci bazai samu ba,   YASMIN ma hakan take takasa bacci tana mai tunanin karonta da M.A Wani irin yam takeji a jikinta tunawa da y'anda lallausan hannun shi ya shafo saman kirjinta ta shafa wurin jitake kamar a lokacin ne yake shafawar, "Kyan d'an maciji zuciya fal zunubi, ta fada tareda runtse idanun ta, ************* Shirye take cikin uniform dinta farare ta rata ya bakar Jakarta ta yayi mai kyau ta fito saida ta leka dakin iyayen nata ta gaida su baban ta ya ce "Auta har kinfito? "Eh tace to ungo kudin motar ki idan kuntashi ya mika Maya 2k tayi godiya tareda fita cikin fargaba, Yaya ismail ta samu zaune a cikin mota yana jiranta, Ta gaishe shi yana fara a ya Amsa "lfy queen of beauty, Ina kika ajiye wayar ki? "ta lalace ne jiya ta samu kanta da boye mai gaskiyar lamarin,   Tundaga kofar gate din shiga makarantar tasu ta hango sojoji birjik ta ko Ina gabanta ya fadi ras tuni jikinta ya fara rawa don ita yanzu duk wani soja ma tsoro yake bata,   "Zaki sauka anan ki karasa kinga kofar gate din masu garin sun rufe sai nadawo daukarki, bata cikin natsuwarta haka ta fita kamar wadda kwai ya fashe mawa ta nufi gate din saida ta wuce ciki hankalinta ya kwanta, M.A ne kwance a bayan motar dake tsakiya tun isowar ta idanun shi NA kanta saida ta shige ya basu umarnin wucewa dama saboda ita kawai ya tsaya a wurin don ya gama binciko tarihin ta kaf yasan rayuwar ta a cikin dabara ya nemi komai a wurin Ahmed batareda ya nuna mai wani Abu ba,   ************** Kusan sati daya kenan Kullum sai ta samu motocin nan a kofar school dinsu kuma ta ankare da ta shige suke wucewa abinsu nan zuciyar ta taba ta d'an iskan nan ke bibiyar ta,   Yau tana dawowa school ta samu mama da maganar Aurenta, "mama baki kuma cewa komai ba akan magana ta da ya ismail? Kallon ta tayi "oh ni zamani maganar Aure kikeyi mama na yau naga lokaci dariya tayi kawai batareda tayi ma mama wani bayani ba , Shigowar baba ne ya katse hirar ta gaidashi Ya Amsa tareda cewa MAMAN Yara bakisan meke faruwa da Unguwar nan ba kwana biyu sojoji sai sintiri suke mana a kofar gida ni Abin ya fara bani tsoro ko suna tunanin akwai barayine a Unguwar?   Tashi kawai tayi tareda fita dakin cike da fargaba da kuma tsoro me MA yake nufi da bibiyar ta irin haka sai kace wata criminal gashi Yaya ismail yayi tafiya bare ta fada Mai gaskiya ta fara tsinkewa da lamarin MA,   Hijabinta tasa ta fita waje tareda zubawa motocin ido, zuge glass din motar yayi ya zuba mata idanu yana lafe kamar wani mara lfy ahankali ya bude motar ya fito ya jinginq a jikin motar,   Idanu ta zuba Mai sanye yake cikin kaki green yayi masifar kyau ba hula akanshi ya sha gyara kan fuskar shi shar da ita ga muscles din nan kamar su yaga hannun rigar su fito, Jikinta na rawa ta karasa wurin shi tana Wai waye cike da tsoron kar baba ya fito ya karasa cikin sauri,   "Baby' ya fada cike da kasala ga yaranshi sai zagaye sukeyi dayan yayi saurin wucewa kofar gidan ya datse "Don girman Allah ka rufamin asiri kabar Unguwar nan ka daina bibiya ta ka taimakeni ka kyaleni karka jefani a matsala,   "Ai ni kin jefani a matsala tunda kinki barina inyi aikina cikin natsuwa ' taurin kanki zaija inyi abinda ko makotanku sai sunji jiki, "Me kakeso? Don Allah nidai kafada ka tafi ta fada tana waige "relaxed kulawarki nakeso ki rika bani kulawa,   "Nayarda please kudaina takurawa Al umma saboda ni kutafi "good for you ya fada tareda sanya hannu cikin motar ya ciro wata Leda a motar ya mika mata yace ga waya kina zuwa gida ki kunna duk ranar da nakira baki dauka ba akwai damuwa don bazakiji da dad'i ba, "Toh tace ya fada motar yana daga mata hannu da gudu suka fada motar da gudu sukabar Unguwar wata irin ajiyar zuciya ta sauke,   Ta fada cikin gidan su cikin Sauri ta fada dakinta ta bude wayar ta cirota sabuwa ce dal akwali akalla zatayi Dari biyu da hamsin iPhone ce ta Yayi,   Ta kunna taga akwai layi tana gama rebooting Kira ya shigo, tasan shine shiyasa ta yi picking   "Hmm kawai ya fada batareda ya ce komai ba kudin shi natafiya na wani lokaci Kafin yace "kin koresu duka baby kinki mayemin gurbinsu duka, Ina rayuwa mara dadi mai kuma wahala, "Meye kika mun? ( I have change am not my self) gaba daya banda natsuwa yaushe zaki dawo barrack? Ki dawo baby idan kina Kusa natsuwa ta zata dawo am (leaving a lonely live) Ina rayuwa nikadai banajin dadi baby,   Magana yakeyi kamar baida laka cikin kwantar da murya, "baby bana iya magana da mace da yawa magana ta da mace daya ce ta gamsar dani, "You are different ke ta daban ce baby kidawo Kusa dani am missing your soup please come and cook for me Abincin ki nakeson ci) nayi kewar miyarki inason kidafa min Abincin ki inci Sirrin zuciya ta kadan ne NA iya fada miki akwai da yawa gashi zanyi tafiya next week kizo kafin intafi don Allah,   Tunda ya fara magana ta yimai uzuri tasan ba laifinshi bane laifin Allurar nan da ake cewa ana yimusu ce taja lallai tashi ma Allurar ta mahaukata ce, Toh ita hauka take zata kai kanta wurin shi Allah ya tsareta da fadawa halaka   Haka yagama sambatu ya Ajiye batareda ya gaji ba ya runtse idanun shi gam don Abinda yakeji yafi karfin feelings kawai abunda da yakeji is morethern feelings yafi karfin sha awa kirjinshi har wani zafi yake mai kamar mai asma Gashi zaiyi tafiya zuwa gambiya sati mai zuwa kuma zai yi wata shida kafin ya dawo.   Ya dade yana Addu ar wannan tafiyar tazo sai gashi tazo a wrong time..........?   *hmm my fans me kuke tunanin zai faru da rayuwar YASMIN da MA da kuma ismail to mudaije zuwa masoyan YASMIN*   *Matar soja* [8/30, 2:56 PM] Feenerh Wrtr: *BARIKI* _Auren Soja_   _written by FENERH_ Maman Ammar *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby   19&20 Kusan kullum sai ya kirata sau ba adadi gashi baida lokacin kanshi da ya samu d'an sarari ita zai kebe ya Kira, Hajiya ma tasan ya canja don yanzu sau da yawa zaije gidan ya Kasa ce mata komai sai dai kwanciya maganar Aure kuwa tama daina wahalarda miyanta da sauran shekarunta, Gefen maganar Auren ta kuwa tana nan baba yace a Bari kawai takarasa tunda saura Y'an watanni ya rage, Sai shirye shirye ismail keyi yana cikin zumudin wannan Auren yauma zuwa yayi tana zaune rike da wayar ta tana chart ya shigo dakin cikin sallama tayi saurin tashi zaune,   Wayar hannun ta ya zubawa ido tare da waro su waje" gimbiya ta kin karo wulakanci baba ya siya miki irin wannan wayar? Saurin girgiza kai tayi tareda saurin kashe zancen "Aunty ce tabani, "OK dama nazo inji size ne nagama siyayya saura iners so number nawa ne gidan ruwan namu? Yafada tareda daga gira hannu tasa tareda rufe fuskarta cike da kunya ta kudundune a katifar, kai maza basuda kunya Wallahi ko kadan harda shi da take ganin kamar ko yatsar mace bazai iya tabawa ba, "Ki fadamin kinsan dai sunkusa zama nawa ko don haka kicire kunya kawai don watarana har a tsakiyar hannu na zasu kwana, "Na bani yau ta fada, mikewa yayi yana dariya a hankali "ki fara sabawa don rayuwar wayewa zamuyi a gidan mu baby na,   "Kituromin a text Ina jira ya fita tareda barmata kamshin shi ta yi Ajiyar zuciya tareda kallon kirjin nata tana tuna lokacin da MA ya shafasu tayi shiru tana tunanin maganganun shi Na jiya,   "Baby zanje wuri mai nisa yanzu bazaki iya zuwa koda sau daya bane inganki? Baby inashan wahala tsawon rayuwata bantaba jin irin Abinda nakeji akanki ba Kowa tanbayata yakeyi lfy ta kalau kuwa?   "Ni nasan banda lfy a jikina ki taimakeni ki bani kulawa koda kalma daya ce mai dad'i guda daya kifada min inji sanyi please   Wayarta ce da tayi Kara tasa ta dawo hankalinta ganin numbar shi ce yasa tayi picking tareda sanya hands free ta Ajiye tana mai kankare kunbarta da nail cuter   Shiru yayi Kamar kullum nadan lokaci kafin ya fara magana, "yaushe ne Zaki fara daga waya ki kirani? Yaushe Zaki fara bude baki kibani Amsar tanbayata,? "Yaushe ne Zaki sama min natsuwar da zuciya ta ke bukata? Jibi zantafi baby please do something kafin mahaifiya ta tarasa ni,   Tsayawa tayi kawai tana nazari kafin ta daga wayar ta cireta a hand free ta fara magana cikin natsuwa, " me kake so da rayuwata? Meye tsakani na dakai? Kai ba saurayina ba ba d'an uwana ba you are nobody to me please free me ka barni in fuskanci masoyina mai burin Aurena mai nufin raya sunna dani bawai mai shirin zaman BARIKI dani ba, Kai ba sona kakeyi ba kawai rayuwar banza kake burin yi dani kuma bazai faruba da ikon Allah aniyarka ta bika, Toh ni ko a tarihi bantaba jin irin rayuwarka ba ba kalmar so ko daya sai mugun nufi a kullum "kai Wallahi nakara tsanar rayuwar ka da duk wani Mai halin BARIKI irin naka,   "Hmmm Meye so? Ya ake agane mutum nason wani? Meye jin dadi A soyayyar bayan Ajiyar da juna dad'i ? Kit ta katse kiran idanun ta na zubar da ruwa tana mai jin wani sabon bakin ciki MA ya gama da rayuwar ta Wallahi sai Allah yasa ka mata gashi ta Kasa fadawa Kowa halinda take ciki,   Ya takura mata duk da tun ranarda ya bata waya bata kuma ganin shiba, number yayarta ta Kira, "Aunty na tafada cikin murna bayan ta daga "Wai YASMIN kin manta dani ko bayan kin gudu kinbarni gashi baban Auwal ya wuce gambiya jibi ogan Shima zai wuce sai sunyi wata shida zasu dawo, Ajiyar zuciya ta sauke haka kawai taji Dadin tafiyar zataso ma kafin ya dawo Adaura mata Aure da ismail sai taga yanda zaiyi, "YASMIN ki dawo don Allah kinga nakusa haihuwa kuma kinga baba bazai taba Bari indawo gidaba ki taimaka kidawo kodan yaronki yana kewarki,   Wani irin tausayin y'ar uwar tata taji nan take ta canja shawarar zuciyar ta na kin komawa BARIKI bayan ga rabin jinin ta a ciki, ***************** Karar wayar ta tayar da ita daga dogon baccin datakeyi mai cikeda mafarkai masu dadi ta Sa hannu ta janyo wayar batareda ta duba ba tayi picking tareda kangawa a kunne ta cikin muryar bacci tace, "Hello, wani irin Ajiyar zuciya ya sauke a hankali cikin natsuwa "hy baby' ya fada cikeda kasala, ba arziki ta bude idonta don jin muryar shi da tayi,   "Baby please say something sweet Gobe fa zantafi ki fadamin kallama mai dad'i da zanrika tunawa da ita,   Shiru tayi mai don tasaba da jin wa innan kalamai daga gareshi basa wani damunta, "um ki fadamin me kikeso inkawo miki kafin intafi, "Banason komai naka nagode, "hmm dole kiso Abinda yake nawa baby kuma kidaina hawa machine natsani mace na hawa machine, "Yanzu nafara hawa kuwa tunda dole inje school kuma Ina ruwanka ba,? "Niko keda ruwa harma da tsaki aciki yazaki rika kwanciya a bayan kowane irin kazami da jikinki mai matukar muhimmanci,   "Zankawo miki mota ki koyi driving, "banaso haka kawai kajamin bala'i wayar nan ma nasha question akanta bare ka kawo wata mota ince wa ya bani? "Kice Muhammed Abdullah ne yabaki wani Mai nacin ki, "bakaji da kyau ba, a wane dalili zai bani mota Meye relation din mu dashi,? "Blood relation inajinki har cikin jini na baby give me chance zanzo infadawa baba sai inkawo miki motar,   "Karufamin Asiri don Allah kabarni ingama lfy da iyayena ni yanzu banason duk wani Abinda zai dagamin hankalin su ta sanadiyata,   "Ni ai hankalina ba akwance yakeba tafiyar nan da zanyi ji nake kamar bazan dawo inganki ba wata shida kamar shekara shida nake hangosu please take care of your self   Zan nemi napep personal ya rika kaiki school please don't say no to this one, sannan ki kiyaye Wallahi ba a sake zantafi inbarki ba zansa tsaro donni ba sakarai bane idan wani namiji ya kusanta ki zaisha wuya I promise don haka ki kiyaye,   Wani irin tsoro taji ya shigeta ita kam ta hadu da rayuwa itada ke murna zai tafi shine zai hada ta da wani tsaro, wayarshi ma tana dauka ne saboda kawai a rabu lfy batason yana zuwa Unguwar su da tawagar shi, "Baby' yakirata cikin kasala tareda yin mika mai karfi har bones dinshi na amsawa "Zanzo inganki kafin in wuce please karki mun musu zanzo gidan ku, "Aa karka zo don Allah katafi tunda muna waya, "I can't inason ganinki please allow me,   "Zanzo idan baki fitoba zan shigo gidan, saurin tashi tayi zaune tareda fara rokonshi da ya rufawa rayuwarta asiri, Gobe zanje school mu hadu a can ka ganni don Allah karkazo nan gidan baba na nan,   "Is OK to kifito da wuri saboda karfe tara jirgin mu zai tashi, shiru kawai tayi don tasan ita Allah ya jarrabeta da ala k'ak'ai a rayuwa,   "Kazo kai kadai karka kwaso yaranka kaga yanda kuke janyo idanun mutane a kanku banaso, "as you wish ya fada tareda katse kiran,   Kwance yake yana maijin bugun zuciyar shi na karuwa ga wani uban feelings dake taso mai kamar Yayi hauka sai mulmula yake a gado,   Bacci ya gagareshi ya mike tareda nufar durowar gadon shi ya ciro magani ya jefa a baki tareda daukar ruwa ya kora ya koma ya kife,   Yana cikin wannan halin Yaji ana shafashi tareda kissing wuyan shi da yatashi duk wata tsiga ta jikinshi ya wani irin juyowa tareda runtse idon shi gam yana mai ayyana Ina ma YASMIN ce tazo,   Jin an Dora baki akan lips dinshi yasa shi saurin bude idanun shi ya zuba mata ido batareda ya motsa ba ya dauke kanshi don kiss idan ba YASMIN ba baya bukata   Zuby ce ta marairaice fuska "haba MA yanzu da Emanuel bai fadamin zaka tafiba da saidai inji lbr ko, "Muhammad Kasan Ina matukar kaunar ka meyasa kake wahalar da zuciya ta,   Kallon hawayen ta kawai yakeyi kafin ya tashi kamar ba akan jikinshi takeba ya juya tareda zuba mata ido,   "Me ya kawoki,? "Nazo muyi sallama ne nakasa daurewa yau ko zaka kasheni bazan tafiba Allah sai kabani natsuwa Kasan munriga munsaba da juna yanzu kakeson ka juyamin baya bazan iya rayuwa dakowane namiji ba sai kai please marry me '   Tafada tana riko hannun shi ya bata wani irin mugun kallo"you are insane nine zan Aureki? Nataba fada miki Ina son Aure? Muntaba Alkawarin Aure dake?   "To me kakeso dani? Bana bukatar komai a wurin ko wace mace please leave me alone, kuka tasa sosai tareda fadawa jikinshi tana lalubarshi,   Gim ya tsaya kamar dutse ta Karachi fitinarta ta mike ta koma gefe tana kuka don jikinshi ko motsawa baiyi ba, "bakada lfy MA kaje kaga doctor   Mikewa kawai Yayi tareda komawa can karshen gadon Yayi kwanciyar shi bai kuma komawa ta kanta ba,   ****************** Cikin Sauri YASMIN ta gama shirin ta ta fito tana rike da Jakarta ta Yayi irin wadda Y'an mata ke son ratayawa yanzu mai doguwar igiya bakomai aciki sai wayarta da ID dinta na school da kuma Y'an canjin ta,   Tsayuwar napep agaban ta ya bata tsoro tayi baya kadan ya leko da kanshi "Hajiya shiga muje umarnin Oga ne, batada zabi ta shiga ya tukata,   Wayarta ta fito da ita tafara dannawa tana mai bude sakonni a watsp bata kuma dago kanta ba saida yace munzo Hajiya, Ta dago kanta taganta bakin tafkeken gate din dake dauke da manyan rubutu a jikin shi, GAMJI tagani, "Yazaka kawoni nan? Maganarta ta kafe lokacin da tayi ido biyu da kyakkyawar fuskarshi yana sanye cikin shigar shi ta kaki yau Como flag ne a jikinshi Yayi matukar yin kyau gayen akwai fitinannen kyau a tare dashi kuma shine sojan da ta taba gani fari sosai kamar baya aikin wahala Abin tsoro atareda shi bai wuce muscles dinshi ba kamar wani roman reigns,   Matso da fuskar shi Yayi gab da ita tareda hure mata idanu tayi saurin dawowa hayyacinta, "Wannan kallon fa karkiga munina baby ya fada yana dariya da gefe daya irinta muiskilayen maza, Hannun ta ya riko tareda cewa ''let go kamar wata magnet haka ta biyo shi ya bude gaban katuwar motar da yazo da ita ya zaunar da ita kafin yazagaya ya shiga,   Facing dinta Yayi sosai ya zuba mata ido kamar zai hadiyeta kare mata kallo yake ta ko Ina ya sauke idanun shi ya gaban hijabinta ya sauke ajiyar zuciya   "Baby kintara komai da nakeso I love your body and your beautiful face bansan y'anda zanfada miki ba, katuwar wayar shi ya janyo tareda saita ta ya fara daukarta Hoto kafin yasa hannu ya janye hijabinta kamar wani mai tsafi batareda ta ankareba, har saida ya cire ya ajiye a kafar shi,   Wani irin zabura tayi tareda zubamai ido ita tarasa dalilin da yanzu Sam take Kasa fada mai mugayen magan ganun ta gashi yau ya mata wani irin mugun kwarjini duk ya cika mata motar Sarkewa idanun su sukayi ta yi saurin sauke nata batareda ta ce mai komai ba don kamar ya daure mata baki yau, "Ni dai kamar bakin nan bashi bane mai tsiwa? Kodai kinbada kaine infasa tafiyar nan baby mu gwangwaje? Dauke kanta tayi gefe ya zubawa sajen dake fuskar ta ido tareda cewa wow domin ta kwantarda shi da gel Yayi wani irin kwanciya mai ban sha awa ga sumar ta tufke ta da katon ribbon ja ta nannade shi kamar kwallo jelar baisan lokacin da hannun shi yakai kantaba ya fara shafa shi tuni lafiyar shi ta motsa, Tayi saurin dafe hannun shi domin kokarin cireshi akanta ya ware idanun shi akanta wa inda suka sauya launi harda wani ruwa ruwa suka tara a ciki, Ya Kara riko hannun ta gam yanajin wani dadi yau ne karon farko da mace ta rike hannun shi haka Yaji wani iri har tsakiyar kanshi hannun ta kamar magic,   Baisan sanda ya fisgota kan cinyar shiba, wata y'ar Kara tasa tareda kokarin sauka tana dukan kirjinshi mai kamar dutse take duka,   "Meye haka Wai kaga shi yasa natsani halayenka banason iskanci, Wani irin ajiyar zuciya kawai yake sauke wa duk da ta cure jikinta wuri daya amma he is feeling the hug he gave her deep down,   Saida Yaji yana shirin sumewa ya saketa ta koma gefe ta dunkule tareda sakin kukan da tarasa dalilin shi, "meyasa kakemun haka kaje wurin Y'an matan ka da suke nema mana saini kakeson kazo ka batamin tarbiya Allah sai ya sakamin, Kanshi ya Dora akan sitiyarin motar na dogon lokaci kafin ya dawo dai dai wayar shi tayi Kara ya yi picking "OK kawai yace ya kalleta, "Am sorry for making you cry ni zan tafi, saka hannu ya ciro wallet dinshi ya ciro ATM guda uku ya zube mata su akan laps dinta "gashi if needed kiyi duk abinda zakiyi dasu zantura miki pin din duka a text   Wani irin kallo tabishi dashi tareda ajiyemai kayan shi "bana bukata inada maiyi min, Kasa cewa komai yayi kawai ya mika mata hijabinta tareda kallon kirjinta for the last time yai ajiyar zuciya tareda fesar da huci mai zafi yaja motar saida ya kaita kofar school din kafin ya bude dash bord ya ciro rafar Y'an dubu dubu ya Ajiye mata guda biyu ganin bazata karba ba ya fisgo Jakarta ya bude tareda sakawa ya ajiye mata, Bude motar yayi ya fita saida ya zagaya ya bude mata ba bata lokaci ta fito ko sauraran shi batayi ba tayi wucewar ta yabi bayanta da kallo har ta bace ya fada mota ya tafi,   ************** Yau kimanin kwana biyu kenan da tafiyar MA tunda ya tafi bai kirata ba kusan duk bayan minti goma saita duba wayar tarasa me yasa ta damu da rashin kiran nashi Gashi yanzu data zauna sai tunanin shi ya fado mata wani iri takeji d'an gane dashi tarasa meke damunta, Mama ce ya shigo dakin ta kalleta "YASMIN Wai meke damunki ne kwana biyu duk bakida walwala gashi sai aukin kwanciya kamar mara lfy, "Ki kitafi y'ar uwarki nata kirana kije kitaimaka kitsaya da ita kinga mahaifinku ya Riga yayi ratsuwa tunfarko bazata dawo mai gidaba ta haihu, Tashi tayi saida ta gyara ko Ina a gidan kafin ta fada wanka ta shirya cikin atanfa mai saukin kudi Riga da sket tayi kyau sosai ta sanya hijabi tareda daukar akwatin da ya shirya Kayanta,   Ismail ne ya shigo gidan cikin shigar alfarma ya karbi jakar ya fita da ita mama ta fito da Wasu kayan data shirya mata ta karba ta ce "ki kaimata zankirata inyi mata bayanin yanda zatayi dasu,   Tunda suka Kama Han ya batace mai komai ba sai shine keta zuba yana bata labarin yanda ya tsara musu gini da kuma tanbayar ra ayinta,   "YASMIN meyake damunki kwanan nan ba yadda kike ba nake ganin ki you are too silent this days "Bakomai ta fada, bata kuma cewa komai har saida ya kaita har kofar gidan ya fitar mata da kayan kafin ya mata sallama batareda ya shiga ba ya wuce don Sauri yakeyi,   Tunda ta fito idanun ta ke kallon kofar gate din gidan nashi yana nan fes kamar koda yaushe sojoji na wurin kamar yana nan aciki, Ji tayi dama ta ganshi yanzu ta kalli saman dai dai wurin da yataba ganin ta da Oga umar wurinda ta lura yafi zama a wurin saboda nan kayan training dinshi suke, Saida ta dauki lokaci cikin tunani kafin ta dauki akwatin ta ta nufi kofar tayi nocking sannan ta dawo ta dauki katuwar jakar kayan da mama tabata ta kawoma Aunty MARYAM,   Maryam tayi Farin ciki sosai da zuwanta saidai taga canji a wurin kanwar tata sosai, duk da haka bata fasa taya ta duk abunda ta sabayi mata ba, ************* Rayuwa nata tafiya yau tayi sati daya a Barrack amma har yanzu bataji daga MA ba tun tanasa ran zai Kira ta har tafara cire rai takai matukar damuwa akan rashin jin wayar shi,   Takira amma layin baya zuwa har kuka takeyi idan ta samu kebewa adaki ita kadai ya tafi ya barta da mugun tabo Wanda tasan shine ajalinta idan tayi wasa MA ya sanya mata mugun guba a zuciya domin ita tasan ta kamu da kaunar wannan bawa Wanda ita tasan shi ba kaunar ta yake ba tunda ya fada mata clearly rayuwar da yake son suyi da ita, Gaskiya Ashe ba laifin matan dake binshi bane yanada qualities da idan ya fara nunawa mace kulawa dole ta manne mai don ya hadu ne karshe gayen,   Tundawowar ta BARIKI bata kuma leka ko waje ba don bata son ganin Kowa MARYAM ta tanbayeta ba adadi meke damunta saidai tace mata bakomai,   Yau kusan karfe goma sha daya na dare tana kwance tana sans ar wayar ta tayi Kara tayi banza da ita domin tasan ismail ne kuma ita yanzu Sam bata son jin muryar shi kwanan nan Saida taji kiran yaki karewa yasa ta fisgo wayar da nufin kashewa taga international call ne mai plus ta samu kanta da daga kiran don har wani rawa jikinta keyi,   "Hmmmm yayi doguwar Ajiyar zuciya jin ta daga mai kiran saida ya d'an dauki lokaci kafin yafara magana, "Baby bakya kewata ko? Nasani ai dama nadameki Addu a kike intafi,   Tunda taji muryar shi gaba daya muryar ta ta fara rawa sai wani irin kuka ne ya zo mata mai zafi, tafara shashsheka, "Subuhannallah baby Meye na kuka please ki daina karki jamun ciwon zuciya a nan,   "Kasa yin shiru tayi ya yi shiru tareda runtse idanun shi yakasa cewa komai saida ta dauki lokaci tana yi kafin tayi shiru, "Hmm am Sory nakasa rike kaina dole saida nakiraki muryar ki nakeson ji kamar inyi hauka please inkiraki video call? Nayi kewarki da yawa,.......... ️ *afuwan hannu na ya gaji ku biyoni domin jin ya zata kaya masoya ismail kuzo jaje YASMIN ta afka komar soja ko ya zata Kasan ce shin rabon waye YASMIN ya zakuyi da baba masoyan MA?*   *Matar soja* [8/30, 2:56 PM] Feenerh Wrtr: PROFICIENT WRITERS ASSOCIATION тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   _written by FENERH_ Maman Ammar *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby   *wow Fans kunyi ruwan comment yanda ya kamata Ina Alfahari daku agaskiya kun faranta min rai sosai da zafafan comment wann ya nunamin kuna biyeda wann littafi nawa 100pcnt godiya dubu agareku masoyan MA da Yasmin* 21&22 Datse kiran yayi batareda ya jira umarnin taba ya kirata kai tsaye, ba bata lokaci ta dauka domin zuciyar ta na mararin ganin kyakkyawar fuskar shi tayi kewar shi fiye da tunanin kanta,   Wata irin doguwar Ajiyar zuciya ta sauke ganin fuskar shi data bayyana ya zuba mata ida sai kare mata kallo yakeyi kamar ya janyota ta wayar yakeji,   Ita kanta tatafi da yawa don ganin tayi yayi mata mugun kyau yakara fresh sati daya kawai da bata ganshi ba, "baby haka kike daman Ashe bana ganin komai' yafada idanun shi kamar suyi aman wuta, Nan tadawo hayyacinta tayi saurin kallon jikinta ta waro ido tareda kife wayar ta dafe kirji shikenan takarawa kananzir fetur dama ya lafiyar kura, Best ce kawai ta mugun kamata pink gashi tamugun fitoda shape din kirjinta da kyau tasaman har ana hango fararen na shanun ta da suka kunburo kamar su fito, Saida taji karar wayar ta tuna da abinda takeyi tayi saurin janyo hijabi tasaka kafin ta juyo fuskar wayar, wani irin huci yaja tareda jan numfashi ya ce, "Why baby please kicire ingani don Allah karkiyi min rowa nariga na gama yawo kin tada abinda bazai taba kwanciya ta dad'i ba please do something kicire hijabin if possible ma harda rigar kicire mun pleas..... Kit ta datse tareda kashe wayar baki daya ta jefar, Ta kife a gadon tana jan numfashi "ya Allah ka yayemin son bawan nan naka kar ya jefani ga halaka, Allah ka rage min kaifin soyayyar shi a zuciya ta kar inyi rauni ya Allah karka nufeni da fadawa halaka, "Astagfirullah tafara nanatawa har saida taji tasamu natsuwa kafin ta wuce ta dauro Alwala ta tada salla domin Addu ar neman sauki,   Shikuwa MA ai yau yayi mugun gani domin yau sai Allah shida lfy wani irin juyi yake akan gadon nashi yana hango irin romon dake kirjin YASMIN "wayyo ta karasa ni, Sai faman rike ciki yakeyi ga wani gumi dake fesomai na wuya dakyar ya tashi ya nemi magani ya watsa ko ruwa bai iya dskko wa ba, Saida ya dauki dogon lokaci kafin ya d'an samu natsuwa ya kuma gwada kiran ta Amma akashe haka ya hakura tareda jin matukar jin haushin kashe mai wayar da tayi,   YASMIN bata kunna wayar taba sai washe gari tana kunnawa kiran ismail ya shigo ta dauka ba bata lokaci "gimbiya nakira jiya busy daga baya kuma naji akashe Ina fatan wayar ba matsala? "Bakomai caji na yayi Kasa shiyasa na kashe nasa caji, "OK idan kina bukatar wata kifada inkawo miki, "aa nagode yasu mama? "Lafiya lau suke, "Kinsan me? "Aa. "Wallahi sai yanzu naji dama baba bai daga Auren mu ba NA k'osa sosai inganki a gidana, Shiru tayi kawai tana sauraran shi ya mugun bata tausayi, Tasan yanason ta fiyeda yadda yaso Aunty maryam don haka dole ta yaki zuciyar ta kodan gudun fadawar d'an uwanta cikin damuwa ta tallafeshi ta kuma cusa soyayyar shi koda ta karfi ne ta cire Wanda ba kaunar ta yakeba saidan Wasu Albarkatu na jikinta,   "YASMIN yakira sunan ta "Na am Yaya, "please Meye kuma na wani Yaya keda zaki zamo matata yakama ta abani wani sunan mai dad'i mana, "wane irin suna ne mai dad'i? "Kice sweetheart ko darling ko my love ko habeebi kidai zaba min inji, dariya ya bata sosai har taji bata tareda duk wata damuwa cikin second kadan yasanyata cikin nishad'i "Yaya ka koyi surutu, "Badole naba tunda ina tareda ke bazaki san irin tanadin da nakewa rayuwar Auren mu bane YASMIN ' wani irin faduwa gaban ta yayi don sai taji Sam bata son yin Auren kuma,   "Bakice komai ba kobakya dokin Auren ne YASMIN? "Inayi Yaya ai lokaci ne "hmm bazan boye mikiba Allah ina cikin wani hali kullum da ciwon ciki nake kwana, ina fada Lafiya kinsani dole inji abinda nakeji yanzu, tanajin y'anda yake mata nishi a kunne yana groaning, Amma ba abinda taji itada ke tareda MA karshen BARIKI ai ita bataga kuma namijin da zai daga mata hankaliba don duk wani d'an iska bayan Muhammad ne,   *********** Wasa wasa ta daina daukar wayar shi koda zai Kira Sau d'ari a rana ko yayi fushi zai kuma gwadawa a haka aka share kwanaki,   Duk ya firgice don ma jarumini ba Wanda zai gane yanada damuwa har Ahmed dasuke tare har yanzu baisan tsakanin shi da Yasmin ba,   Yakai kololuwar karshen hakuri yau ya tura mata text _rashin daukar wayata ba Abinda zai rage akan kuduri na koda bana nan Wallahi zantura gidanku baba yasan komai Abinda zanyi bazai taba yimiki dad'i ba don haka be careful_ Ya tura mata lokacin tana zaune da Aunty maryam ta ji karar shigowar msg ta kalli fuskar wayar da kamar karta daga Amma tasamu zuciyar ta da bude sakon, Tsaki tayi bayan ta gama karantawa tana mai ayyana ba abinda zai iyayi, "Lafiya kike tsaki sis? "Bakomai Aunty, "nifa bangane miki bane Yasmin naga tun zuwanki kinki ko fita waje saikace bake ba nasan ko Emanuel baisan kina nan ba, "banason surutun shine Aunty kinsan shi da gulma, hhhh dariya tayi "kodai nasan ku ai duk daya keda shi to ai Oga baya gari gulmar me zai kawo miki? Koda yake ance budurwar shi kusan kullum saitazo gidan watarana har kwana take a ciki,   Wani irin takaici da kuma mugun kishine ya rufeta tasamu kanta da jin zafin Abin sosai saboda jaraba har da bai gari yana basu damar shiga gidansu, samun kanta kawai tayi da shigewa cikin dakin ta ta kwanta tareda runtse idanun ta Wasu irin hawaye masu zafi nabin kuncin ta "Allah ka yaye min son wannan bawa zuciyata bakiyimin adalciba da zakisa inso wannan irin mutum, karar wayarta tasa ta mika hannu ta dauka batareda ta duba ba,   Jin muryar shi yasa ta bude idanu, cikin natsuwa yafara magana yau bai tsaya jan Ajiba, "inkika kuskura kika Ajiyemin waya billahillazi zaki ganni a 9ja idan nakuma Kira kika ki dagawa Wallahi zan bata miki rai, ki tsaya ki saurareni kawai azabtarwar ta isheni karki samin hawan jini, Bude bakinta tayi tafara zazzaga mai ruwan bala'i "me zaka fadamin Wai kai wane irin namiji ne baka gari amma karuwai nayima zarya agida "oh who no ko kana zuwa Kayi ka koma ban saniba, Tunda ko yanzu gashi kana kirarin zaka zo idan nayi kuskure Wallahi bantaba ganin mutum irinka ba ana cewa iskanci na BARIKI ai kaine ma barikin don iskancin ka yafi na Kowa don kaine jagora,   "Kingama koda saura? Shiru tayi kawai kafin yafara magana" su waye agidan nawa? Ya akayi kikasan da mace? Ina ruwanki da su? Koda ina gari zanyi abinda nakeso, "Bantaba bin kowace y'a mace ba tamun wulakanci kuma inci gaba da binta saike wace yarinya ma ta isa inbita Sau biyu Wallahi bata a Nigeria amma ke kullum ina nacin ki kina min wulakanci ban fasa ba, "So kike inkori masu son bani hutu da natsuwa in tare a gindinki kawai inci gaba da shan wahala, duk macen da kika gani Sau daya nake neman ta itake bibiyata sannan zuby da kike gani a gidana munyi kusan shekara bakwai is imposible murabu da ita koda kuwa kin bani kulawa bare har yanzu yanga kike famar yimun saboda kinga na mutu akan ki,   Wani irin kuka ne ya kufce mata mai ciwo yanzu wannan ne zuciyar ta keso? Shiru yayi yana mai jin zafin kukan nata har cikin ruhin shi "please stop crying karki hanani natsuwa Meye Abin kuka anan nafada miki sirrin zuciya ta ne bana karya bare infara akanki,   Katse kiran tayi saboda takaici ta manta da kashedin shi, tana kuka Mai shiga zuciya, kuma kiranta yayi, saida ya Kira Sau biyu kafin ta daga, "You are testing my patience baby nafada miki idan ina magana don't cut my call zakisha mamaki nafada miki, Rage murya yayi yafara magana "me yasaki kuka? Kinsan rashin dagamin waya kamar kina samun wuta a zuciya ne tun ranarda naganki da best baby kika Kara tafiya da tunani da natsuwata naji araina dole in mallake ki baby kinada kayan hutawa sosai "ahh ya fada yana mika mai karfi, "kinsan inason mace mai nonuwa ga naki kuma full chest kamar ballon baby sunada laushi ko nine zansa suyi laushi are still strong?   Karuwa kukan ta yakeyi don tarasa nayi gayen nan yanada digiri a harkar BARIKI gaskiya, "Um baby bari inbarki sai anjima zamuyi video call please kisa bra kawai, bye, ya kashe wayar tabi wayar da kallo tarasa ma mezatayi,   Tunawa tayi da wata kawarta Amira da ya dade tana bata labarin tsakanin ta da surayinta dole ma ta nemi shawarar wani wannan karon dole tanemi mafita kafin lokaci ya kure mata, Number Amira ta nema saida ta dauka tasa ihun murna "bakida kirki kawata sai inyita kiranki kiki dauka yau dai kinkirani da kanki, "Hmm ya kwana biyu? Wallahi sai Alheri kinsan ina barrack tareda my love yanzu su baba sunga ba sarki sai Allah sunyi mana Aure kar kwabarsu tayi ruwa, "Shiyasa kikaga na kyaleki Amira iyaye ba Abin wasa bane yazaki biyewa namiji da baida tabbas ki nemi bijire musu? "Ki bari YASMIN na nemi yafiyarsu kuma Wallahi ko da can da kike ganin kamar ina kinjin maganar ku giyar soce ke jana Amma kibari zanzo har Unguwar ku zamuyi magana   *********** Bayan kwana biyu Aunty maryam ta haihu a asibitin NDA dake barikin ta samu baby girl murna wurin su Yasmin ba a magana nan Y'an Uwa suka fara sintirin barka har zuwa ranar suna yarinya taci sunan NANA Aisha Iyayen su suntaka rawar gani harma da ismail ranarda kayan uban gayya ya iso kuwa ai ba a magana don kayan sun basu tsoro harda YASMIN akwatin ta daban gana baby gana Auwal da kuma mai jego, Yasmin tayi matukar mamakin irin tsadar kayan dake cikin akwatunan don nata ma yafi na mai jegon, Aunty maryam saida takirashi tana mai godiya, "ba aiki na bane Oga ne yadauki wannan nauyin madam kinsan irin Alkhairin shi agaremu Sosai kuwa Allah yasaka mai da Alkhairi mungode Allah ya tsareku, Bata fadawa Yasmin ba kawai tayi shiru don tasan zaisha tsinuwa ne kawai kuma bazata taba sawa ba, ************** Akwance take bayan ta kammala Aikin gidan ta na hutawa wayarta tayi Kara tasan mai kiran ta daga tareda sawa akunne, "hello my beauty ya kike? Ya tanbayeta "lfy kawai tace "ya baby? Kalau take,   "Hmm baby kinason Yara? "Waye bayason Yara "nidai da banaso Amma tunda muka hadu nakeson inga nabaki ciki kihaifamin baby inason inga cikina a jikin ki inga kina bawa yarona wa innan no non "wow zanrike mai dayan idan ya zubo inlashe mai da halshena, "Saboda kazanta? Ta fada batareda tasan maganar ta fitoba kuma batasan lokacin da maganar shi ta shigeta ba har tayi tasiri ba, "Kazanta baby nonon nakine kazanta ai ko Abinda yafi ruwan no non ki ne zan iya shanyewa ke nifa ko ruwan...... Don Allah Wai kai Kasan kunya kuwa? "Meye kunya? Ai bamu hada hanya ba da ita ke kika Santa baby idan ina tare dake nifa bansan komai ba sai Abinda yafito daga bakina, Wayar ta sauke gefe saida ya gama ya kashe batareda taji karshen maganar isksncin nashi ba,   Sannu bata hana zuwa gashi yau YASMIN ta kammala karatun ta Wanda maganar Aurenta ta Kara matsowa gefe daya kuwa MA na dokin dawowar shi gida don saura wata daya ya diro kasar,   Ismail sai rawar kafa yakeyi akan Auren shidai yau ma yakirata tana kwance "Matar zanzo indaukeki karshen satin nan saboda mu fara shirya event din da zamuyi friends dina dunata shirya mana party, Ajiyar zuciya kawai ta sauke don tana cikin damuwa zataso Auren ta ya kasance kafin dawowar MA don tana cikin mugun fargaba kodazu ya fada mata "Baby ki yimin girki ranar da zandawo girkinki kawai zanci idan nadiro nasan bazaki kiyimun ba gashi yanzu ismail yanaso ta koma gida kafin isowar MA yazatayi...... ️ Kufada mata my fans I don't no   *Matar Soja* [8/30, 2:56 PM] Feenerh Wrtr: PROFICIENT WRITERS ASSOCIATION тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   _written by FENERH_ Maman Ammar *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby *wannan shafin nakune BENEFICIAL WRITERS GRP kunayi inajin dad'i Allah dai ya biya comment dinku na farantamin* *Abdullahi zainab* *Aesh* *Ummi zaria* *Mrs faruq* *ina godiya Allah yabar kauna* 23&24 Kwanakin kaf cikin fargaba YASMIN take duk ta rame sai haske da takarayi ga kuma wani irin fresh datakeyi domin gyara da Aunty maryam ke musu ita kanta maryam din ta goge ga cikar jego da tayi tana murnar tarbar Oga Ahmed, Ga y'ar ta tayi wayau sosai tayi bulbul da ita gwanin sha'awa, yanzu ma zaune suke ta mikawa YASMIN wata roba cike da danbun naman kaza mai had'in magani, Yatsine fuska tayi kafin takarba tajuya robar "Wai don Allah meyasa kuke bani wannan Abin ne yanzu? "Kibari kya tanbayi Yaya ismail bani ba watara na mu na nan zakizo nema, "Gaskiya banason dure duren nan kalli wannan hadin mai kamar madara Sam banason shi har wani tsiyaya yake sani kuma kalli kirjina sai cikowa suke karayi nidai bazan kuma shaba, "Kedai wawuyace Wallahi YASMIN kinsan sirrin gyaran nan kuwa? Bakya ganin y'anda baban Auwal har yanzu yake likemun ke har Gobe ina alfahari da mama na domin gyaran da takemun yasa mijina baya hangen wata macen ki duba koda yake soja duk inda yake zuciyar shi na tareda ni, Bansan rayuwar shi abayaba Amma ni nasan koda ace da can yanemi mace to yanzu bazaiyi ba don ya d'an d'ani irin baiwa ta Yasmin ki gyara kanki ki kwaci y'ancin ki a gidan Aure, Shiru tayi tana mai ayyana dama A ce MA zata Aura da tasan sai tafi kowace mace Sa a da Farin ciki, saidai kash' ko da ba ismail tasan bazai taba Auren taba don yafada mata shi baida tsarin Aure a rayuwar shi, Maganar maryam ta dawo da ita" ki shirya kije gida ki karbo min tsumi mama tace ta dafamin ki kawo muci gaba da sha, "kidai sha ni bazan shaba Allah, ke kika sani ina ruwana, Zantafi inkwana sai jibi zan dawo "aa ki karbomin kidawo please kinga jibin Zasu dawo fa inaso inkara tsumuwa kinsan mazan mu sunkwaso yunwa, "tab kyaga yunwa bari ki kuma gwarne, tafada tana rugawa da gudu ciki domin shiryawa ta tafi gida, "Zaki sani y'ar rainin hankali ai Matar so ke gwarne, "Matar wahala dai ta bata Amsa daga ciki Allah yasa duk shekara ki dura ciki don Yaya ismail ma dagani sai yayi jaraba, Shiru tayi kawai tayi tareda tuno shugaban jarababbun ta Wato MA ta, ************* Koda ta isa gida saida ta kwanta taci barcinta sosai kafin ta ci Abincin mama mai dad'i tayi wanka tasaka wata doguwar riga armless robace ta kamata sosai sannan ta dora kimono akanta tasaka west belt mai kyau ta ciro Farin gyale ta yane kanta tayi matukar yin kyau batayi wani make up ba ta nufi dakin mama suna zaune yau harda baba da Auwal sai wasa yakeyi, Ta gaishesu cikin ladabi tareda daukar yaronta, "Dakai zantafi ko? "Aa Aunty zanje ba, suka Sa musu dariya "kinga yaci tuwo mai dad'i baya bukatar jagwal gwalonku mamana baba ya fada cikin nishadi, kuma ai wayau ne ta dauke ki ai dole tabar mana shi mugani muji dad'i gida kamar kango ba yara, Inji mama "ki dauki sakon yana cikin daki a Leda kuma dai kinsan dole kidawo cikin satin nan ko don saura sati daya kinsani akwai shirye shirye itama maryam zankirata ta sallamoki kawai Gobe kidawo tunda mijinta zaidawo, maga Wanda zata kuma gani idan kinyi Aure,   "Kibarsu lokaci ne basuda Wasu abokan shawara sune kawai muka haifa kinga gwara su shaku ko sayi zumunci irin namu da d'an uwana, Saida suka d'an taba hira kafin tafi, ***** Tun isowar ta taga sojoji birjik a kofar gidan nashi saida gaban ta ya fad'i ganin y'anda suke clean up ko ina sai gyarawa akeyi, ga sabon penti da ya Kara haska kofar gidan, Ta shigewar ta ciki ta samu Aunty maryam tana faman soye Soyen tarbar Oga "kai sannu Aunty na har kinfara aiki? "Badoleba ai tunda kikaga su Oga MA sundawo yanzu saura su baban Auwal gwara inkimtsa komai, wani irin tsoro ne ya shigeta tareda dafe chest tace "yadawo? Kallonta tayi cikeda mamaki "eh Meye matsalar ki kuma da dawowar shi? Saita kanta tayi kawai batareda ta iya cewa komai ba ta hadiye wani abu, " ke kuma daga zuwa karbo sako sai inji shiru tunfa safe gashi yanzu karfe biyar, "Wallahi bacci na nasha ganin ba sallah nakeyiba saida na koshi natashi nan Aikin ki kadai baya barina bacci, "sorry my sis ke kadai nakeda shiyasa kinga dole kitaimake ni, Daki ta wuce tareda janyo wayar ta don Sam ta manta bata fita da itaba wajen miss call ashirin tasamu nashi sai kuma text guda daya,   Sakon ta bude _call me back idan kindawo_ Jikinta sai rawa yakeyi tarasa Abinyi Allah yagani tanason ganin shi sosai saidai batajin zata iya kiranshi ga wani mugun tsoro dake dawainiya da ita, Tashiga uku da rigimar wannan sojan ta ina zata fara, taso tasamu Amira suyi shawara Amma takasa zuwa bare ta nemi mafita, Karar wayarta yasa tayi firgigit ta kalli tsohuwar numbarshi ce ke kiranta duk da batayi seving ba tasan number shikenan ya dawo na boni yau,   Saida ya Kira Sau biyu kafin ta dauka jikinta narawa takara cikin fushi yafara magana, "ki cigaba da yin Abinda kikaga dama ba laifinki bane kinji amma karki damu zanyi maganinki tunda nadawo Ina jaji ki nemamin Abinda zanci kafin in iso nan da thirty minute "yanzu don Allah ta ina zan shirya ma Abinci bayan Kasan ba Wanda yasan tsakanin mu Wai ya kakeson jefani a damuwa ne,? "I don't care matsalar kice idan kinso kifadawa Kowa munatare you are my property zanzo hakan kiyi ihu duk bariki Kowa yasani bandamu ba hakan ma dad'i zanji ke ni yanzu na shirya Kowa yasan ke tawace nikadai bazan taba sherring dinka da kowane namiji ba, kibar wannan maganar kawai sai na iso zamu karasa we have All night for our self, idanu ta zaro cike da tsoro, "All night? Kutt Kasa motsi tayi don batasan ma ta ina zata fara ba kwance d'aurin da tayiwa sumar ta tayi ta baje shi domin iska yashiga don wani zafi takeji yana shigarta,   Har akayi magrib bata samu mafita ba haka ta mike ta fita falon Aunty tasameta tana bawa NANA nono tace "ina yin salla zankwanta yau nagaji kyaban labarin film din mu Gobe, "Tom kawai ta iya cewa don tunanin ta yayi mugun nisa, Dakin ta koma ta yi wanka tareda kimtsa kanta saboda tana mugun rushing idan tana period ta mayarda rigar ta tareda feshe jikinta da turare don tana son yin Amfani da turare a irin wannan yanayin,   Wayar ta ta dauka ganin miscall din ismail ta kirashi " matana ina kika shiga ne nayita Kira? "Sory Yaya wanka nashiga, "Ahh my wife damunyi Aure tare zamu rikayi kina cudani ina cudaki ba wani kunya a lokacin kinzama ni Nazama ke, Shiru kawai tayi tana sauraran shi "baby Gobe zanzo indauke ki inason zuwa Abuja kafin ranar kamu akwai wani uzuri da zai kaini kuma inada magana dake saidai mun hadu goben,   Yana Ajiye wayar kiran MA ya shigo ta dauka kawai domin gwara ma ta rage nuna mai tsoro kar ya ga damanta da yawa, "Ki bude min falon zan shigo, ya fada tareda katse kiran kitt, ta d'askare a zaune kamar wadda ruwa ya cinye ta saida tayi suman wucin gadi kafin ta dawo cikin Sauri tayi dialing number shi, "Ina jira ko inballa kofarne? Ya fada cike da hasala, "please katafi Wallahi Gobe zanyi maka duk Abincin da kakeso don Allah ka rufamin asiri ka wuce,   "Wallahi bazaki cuceni ba kifito yanzu ko inyi Abinda zakiyi kuka da kanki, a firgice ta mike tareda bude kofar a hankali ta fita saida ba Kowa a harabar wajen sai haske da ya hasken security light ko ina,   "Kana ina tafada domin dama wayar na kunne "ina cikin gidana ki Kara so, ta kalli kanta d'an karamin mayafinta ne kawai ta warware tareda nufar hanyar gudun idon jama'a don tasan ana ganin ta za ace itama kalar Y'an iskan Y'an matan shi ne,   Ko kallon masu gadin nashi batayi ba zuciyar ta na bugawa ta shiga falon da ke bude daman, tun fitowar ta yake kallonta ta sama saida ta iso kofar gidan yafara sakkowa, koda ta shigo yana dai dai step yana sanye da singlet na Como flag da wandon tree quarter Shima irin rigar ya Kara murdewa ga ga Farin shi na sheki Kamar ba soja ba, Wani saje ya ajiye a fuska wannan karon Kasan cewar sunje peace keeping suna iya barin shi tun shigowar ta ya zabga mata idanu yana karema halittar jikinta kallo tundaga sama Har Kasa,   Takara cika ta sama duk da fuskar ta ta fada wani irin shaukinta ya shigeshi yafara sakkowa a natse nan ta sauke wayar a kunnen ta ta zuba mai idanun ta masu kyau da kuma daukar hankali   Saida yazo gab da ita idanunshi sunyi wani irin sauyawa ba bata lokaci ya bata zazzafan hug,   Tayi Zuru kirjinta Kamar yayi tsalle ya fito tsabar rawar da jikinta keyi, "wow baby kinkara kyau Wallahi Alhmdulillah Dana dawo Lafiya na sameki kwace jikinta tayi don ba wani riko yayi mata ba taja baya kirjinta na sama da Kasa tsabar tsoron shi,   "Don Allah kabarni in wuce kar aunty tagane bana nan dare nayi saida safe ta juya cikin Sauri,   Tunda ta fara magana yayi suman tsaye domin maganar ta kawai kokarin dauke mai numfashi takeyi ga lips dinta masu she kin lip gloss yana Kara mai shaukin ta, Taku biyu yayi ya fisgota zuwa kan kirjinshi ya samu tarbar randar ruwan dakyau har wani daukewar numfashi ya samu najin wannan dukiyar a tsakiyar katon kirjinshi, Hannun ta tasa masu laushi da santsi Kamar na baby ta dafe muscles dinshi da niyar tureshi taji Kamar dutse ta rike ga wani shock da taji tundaga tafin kafar ta har tsakiyar kanta,   Dai dai kunnen ta ya Dora bakinshi "baki isa ba baby yaxaki zo ba wani barka da zuwa ba tarba mai dad'i kawai kizo kimun kwalele ki wuce Ashe na zama sakarai kenan da zaki nunamin wa innan kayan kuma kijuya ba wani tayi ina baki isa ba,   Ya dagota tareda zubawa dukiyar fulaninta ido Kamar ya cinyesu yakeji don sunyi mugun fitowa a rigar saboda robace har yana ganin shacin breziyar da bata gama rufesu ba, tuni idanun shi sun canja, Ganin yana shirin Dora hannun shi akai yasa tayi saurin komawa cikin kirjinshi ta kankame shi "don Allah kadaina karka tabani, tafada, Rungumar da ta bashi tayi mugun shigarshi fiyeda wadda yayi mata a farko don dai yana jarumine da tuni ya zube dasu runtse idanun shi yayi ya dafa kafadar ta, "To ki sakeni kar inyi aika aika yanzu muje kibani abinda zanci am hungry, Kuka tasa don Allah kabari sai Gobe zanyi yanzufa kalli ago go karfe goma fa, "Oho ke Wallahi sai kinbani abinci naci ko kiban dafaffe ko inci d'anyen dake jikinki yanzu don haka zabi yarage nake muje, Batada zabi haka tayi gaba yabiyota abaya yana karewa shape dinta kallo gaba daya duk wata lfy ta jikinshi yau ta gama motsawa ya dunkule hannu tareda kallon wandon shi dayayi mugun kunbura Wai ma don ya kamashi ne data lura da Shi, harbawar da jikinshi keyi shikanshi tsoro yake bashi bai taba jin irin haka ba,   Aiki takeyi shikuwa yana tafama da kanshi ga wani irin burgeshi da tayi yanda take Aikin a natse Kamar Matar gidan saida ya dade daga nesa kafin kamshin yasa shi matsawa kusa da ita, "Ahhh baby me kike dafamin yafada tareda dafa kafadar ta ta ture hannun shi tareda wanke albasar ta zuba "noodle ce don tafi Sauri kaga dare nayi, tafasa kwai ta hada su citta da tafarnuwa harda albasa ta zuba domin kashe karni tafara soyawa kafin indomin ya dahu, Wani irin Farin ciki yakeji ganin shi tareda ita a gida daya gaskiya zaiso su kasance a haka har abada yanajin ta har cikin naman jikinshi, Gama daya kuzarinshi ya kare ganinta dayakeyi yanzu zuciyar shi na d'ad'a narkewa da kaunar kasancewa da ita a cikin gidan shi, yayi nisa cikin tunani ta yi mai magana "nagama zantafi,   Matsota yakeyi cikin wani irin yanayi tafara ja da baya har ta mannu da sink din kitchen din ya matsa gab da ita, wani irin numfashi yaja kafin ya fesar akan fuskar ta, "Please don't leave me I want you in my life, ki zauna dani karki Barni ganin ki kawai yanzu ya daukemin duk wata damuwa banaso kiyi nisa dani stay with me,   Wani iri taji a zuciyar ta domin sakon nashi ya isa inda ya kamata dama zuciya mai bege tuni idanunta yaciko, Kasan bazai taba yuwuwa ba zama saida Aure, "Then marry me please marry me wani kallo tayi mishi gashi ya cika. Ko ina ba ako hangota sai ma ya d'an rankwafa kadan suke daidai da ita, Mamaki ya cikata yau MA ke zancen Aure a tsakanin su shine ke rokon ta Aureshi? Kodai mafarki takeyi ba gaskiya bane, jin bakinshi da tayi akan nata ya dawo da ita daga mafarkin ta, Kokarin fisge kanta takeyi takasa dole ta tsaya don Kamar dutse haka jikin shi yake ya sanya hannu ya tallafo keyarta ya samu damar samun tongue dinta da kyau ya mai wani mugun kamu tareda yin wata y'ar karar dad'i saida yaji zai fadi ya zame da ita Kasan tile's din kitchen din tayi saurin komawa gefe tana tuna y'anda ta tsine mai a karon farko saidai yau ba haka bane tausayin shi taji y'anda yake dafe kanshi tareda rike mara yana goga kanshi a durowar kitchen din da Alama yana cikin jin zafin cikin sosai,   Mikewa tayi da niyyar fita fallon, ya Kira sunan ta karon farko "YASMIN karki tafi kitsaya please ' muyi magana, saida ya d'an nutsu kafin ya tashi ya matso gab da ita tareda gyara mata sumarta da ta zubo gefen fuskar ta ya gyara mata zaman gyalen kafin ya riko hannun ta "Am ready to get married, "Wallahi baka isa ba MA indai ina raye dole ka aure ni ba kuma wata macen da ta isa ta rabeka idan ko tayi kuskuren yin hakan zan salwantar da ita, Maganar zuby ce ya dawo dasu, wani irin kishi ne ya rufewa YASMIN ido tayi saurin tsayawa gaban shi tareda kallon zuby cike da tsohuwar tsiwarta data motsa,   Ta riko hannayen shi gam "amma ke anyi jaka Wallahi tunkiya Aladiya mai bin mazan mutane kawai Sau nawa nake miki kashedi akan mijina kifita a idona kifita hanyar mijina Inba hakaba zan sabautaki, baki sanni bane haryanzu, "Wannan nawa ne don haka kifita hanyata ta, wani irin kallo yake aika mata ga Farin ciki da ya mamaye mai zuciya "wow kalmar mijina abakinta is something else a wurin shi yaji kalmar sosai har cikin kanshi, ga bakinta mai tafiya dashi tana motsashi cike da tsiwa, Zuby ce tayi sauri zata rikoshi Yasmin ta shige kirjinshi tareda rungume shi gam tayi saurin daga kanta tayi tsalle ta d'ane jikinshi Kamar wata Yar tsana yanda Kasan mutum ya hau ice ta hade bakinta da nashi gam saida ya gyara tsayuwa domin shock din da yaji har kan babban yatsar kafar shi,   Tuni ya fara bata wani zazzafan kiss tana tayashi batareda tasan ta iya hakan ba y'ar karamar hauka MA yayi a cikin d'an k'ankanin lokaci, Ran zuby inyayi dubu ya baci tayi kukan kura tareda kokarin cafko YASMIN daga jikinshi yayi saurin maida ita gefe tareda kallon idan zuby dake zubarda hawaye, "Uban me yakawo ki gidana by this time? "Oh haka ma zaka fada min ai dole kafada min kasamu y'ar jaririyar yarinyar da ko kosawa kirjinta baiyi ba kana lalubewa ai Wallahi Kayi faduwar tasa MA Wai me zaka samu a nan,? Gyara tsayuwa yayi tareda Kara rungumeta a jikinshi, "ni ma da bansamu Amsar tanbayar ba sai yanzu "eh nasamu Abinda bansamu ba a wurinki kuma bakida shi kuma bazaki taba samu ba a wurina. Ki sani this girl is different from others kinsaba yimun hauka akan bebs dina ina kyaleki wannan karma ki gwada Inba hakaba Wallahi zansa a sab'a miki kamannin da ba karenda zai kalleki,   Kuka tasa kai cin rai "yanzu don cin fuska Sau nawa ka taba rungume ni da kanka bare har takai ga kiss kalli yanda kake kissing dinta koni baka taba yimun haka ba..... Out before kiga y'anda zanyi sex da ita yanzu,   Ya buga mata tsawa jiki NA rawa ta juya tana kuka da karfi ta fita gidan, tana ganin ta fita ta fisge jikinta ta fita da niyyar barin gidan yayi saurin binta tareda riketa, "Meye haka baby ? Juyowa tayi cikin fada" tafiya zanyi mezanyi maka ka dawo da karuwar ka kawai kuci gaba dama sans ar kace idan kaso ma zaka iya kwana da goma a rana I don't care, Nima Aure zanyi don haka kaje kaci gaba da harkar da ka saba ranar Friday zan zama Matar wani.......... ️   *nayi nan baruwana Fans baza ayi agabana ba mu hadu a next page masoyan Asali Aisha dahiru ina jiran ki nasan kina bani wuta love you baby* [8/30, 2:56 PM] Feenerh Wrtr: PROFICIENT WRITERS ASSOCIATION тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   _written by FENERH_ Maman Ammar *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby *nakune my grps BARIKI Auren soja️ da kuma BARIKI Auren soja 2 ina Alfahari daku masoyan Asali* Kunada yawa my fans bazan iya fado sunayenku ba Amma ina Alfahari daku bakidaya kuci gaba da gashi, 25&26 "Aurena zanyi don haka kaje kaci gaba da bin Y'an iskan matan daka saba bi, Wani irin kallo yake aika mata mai cikeda ma anoni kafin yayi wata irin dariya ya matsa gab da ita "you are dreaming (mafarki kikeyi baby ko) narkewa tayi tareda gyara tsayuwar ta "am serious Aurena ranar Friday kuma ai Kasan da labarin tunfarko daman kawai damuna kakeson yi, Wani irin fisgota yayi tareda hade bakinsu, kawai jintayi rigarta tayi Kasa domin rabata biyu yayi ya jefar a gefe, wani irin mazari jikinta ya dauka tafara kokarin neman ceto saidai ina yayi nisa domin kafin tayi wani yunkuri ya cirata ya nufi kujerar dake falon ya shinfideta, Wani irin zabura tayi zata tashi yabita ya danne tareda sakar mata nauyi, ya zubawa kyakkyawar fuskar ta ido tareda d'an ja baya kadan ya danne hannayen ta duka biyu don karta samu damar motsawa, Wasu irin hawaye ne masu ciwo suka fara zubo mata, yau Allah yakawota hannun wannan d'an barikin, Kallo yake karewa halittar fuskarta har zuwa kirjinta daya danne yadan dago kadan domin samun damar kallon Abinda yafi komai kauna a jikinta, Ta fara mai kuka mai sauti" Wallahi natsaneka natsani rayuwar ka banson inkuma haduwa dakai ko a hanya wace irin rayuwace wannan,? Bai masan tanayiba wani iri yakeji tundaga marar shi har cikin kwakwal war kanshi tuni jinin shi ka Kara gudu ganin irin wa innan kaya duk da suna cikin bra zuciyar shi Kamar tayi tsalle gaba daya yayi confused yarasa me ma zaiyi ko yarage Abinda yakeji nan take ya fara sambatu, "Ahhhh babyyyy ya furta dakyar "please ke tawace karki Auri wani Wallahi ba Wanda zanbarwa ke ni na cancanci wannan harka ba wani banza canba, "I love your body I love your everything I want to marry you be my wife baby zaki iya daukata nonuwanki Zasu cika tafin hannu na ina son su baby ki mallaka min you have the must beautiful breast Wallahi,   Cikin dimuwa da rashin sanin mai ma zaiyi yasamu sauki yayi saurin Dora bakinshi a saman fatar breast dinta, wata irin mika tayi tareda sanya mai ihu don taji lips dinshi har cikin kanta ta sanya kafarta garin shure shure ta zunguro hanyar Abujan shi, ai kuwa tuni ya mance kanshi da waye uwarshi ya sanya bakinshi ya janye bra din ai tuni ya nemi sumewa domin bayyanar kan gidan ruwanta da yagani a zahiri ai gaba daya notukan kanshi suka Kara loosing Kuka takeyi mai karfi jin yanda yake sarrafa kirjinta da bakinshi Kamar ya samu na uwar shi ga jikinshi sai wani irin vibrating yakeyi tsabar tsumuwar da yayi,   A hankali jikinshi yafara saki saboda irin kukan datake yi yana ratsashi har cikin jinin shi yakejin kukan, cikin saurin kwace kanta tareda curewa wuri guda ta kudundune, shikuwa mirginawa yayi Kasa yana gurnani kafin yasamu natsuwar da ya so ta kasance a cikin HQ tar ta, Ya dade a kwance yana maida numfashi kafin ya juyo ya zuba mata idanu cike da wani irin shauki mara misali, "I can't let you go baby you are mine,   Ya furta yana Ajiyar zuciya kafin ya tashi zaune ya matso wurinda take cure sai kuka take tana Ajiyar zuciya muryar ta har ta dishe, Zama yayi tareda d'an rikota ta buge mai hannu yayi dariya kadan "baby saikace nayi wani Abu irin wannan kuka haka kice ranar da duk na ratsaki akwai aiki, ki shirya kuwa domin kwadayina na shekaru akanki zai kare don haka ki shirya daukar gwarzon namiji, Mrs muhammed Abdullah ya furta yana shafo kanta cikin tattali da jinta Kamar ya lasheta yakeji, Kallon wandon shi yayi yayi dariya tareda cewa "baby kalli irin abinda kika tatso tun yanzu hmm kice ranar da na shiga ciki akwai show Babba,   Kukan nan ya isa ko inyi mai gaba daya itadai kuka kawai takeyi "Wato haka kake wa Yaran jama a KO? Yau gashi ka gwada akaina nagani a she banga komai ba a cikin iskancin da nake gani ba sai yau daka nuna min, "Hmm me kika gani ai banyi komai dake ba baby "amma kisan wani Abu kece macen farko danake romancing da kaina "noo I can't waste my saliver couse nasan bazaki fahimceni ba yanzu, Ki tashi muyi wanka kitafi gida, ko zamu kwana ne don ni bangaji dakeba "um Gobe tsarabarki zata iso baby dole ma inkara miki da wata kyautar don irin wannan kayan naki da nagani sunfi karfin kyauta kadan,   Kukanta take karayi takara dunkulewa bata ma kaunar kallon fuskar shi, Kara shigewa yayi jikinta "baby ya Kira can kasan makoshin shi cike da wani irin tattali hade da lallashi,   "Please stop this crying yana taba min zuciya sosai you have no I dear kukan na kona min rai bai kamata kina kuka ba farin ciki kawai nakeson gani A fuskar ki, mace ce ke mai daraja a wurina bayan mahaifiya ta kece mace ta biyu mai mahimmanci a Rayuwa ta,   Dagowa tayi tareda zuba mai idanunta da sukayi ja saboda kuka, "da inada daraja da baka nemi yimun fyade ba, da baka nemi yin rayuwar BARIKI dani ba, banda darajar da kake fada MUHM'D don ba kaunata kakeyi ba kawai kana son ka more Albarkar dake jikina ne,   Juyo da ita yayi da sauri ya kankame ta a kirjinshi duk da tana a curen ta kudun dune kirjinta wuri gudu, bai fasa yi mata rikon kwai ba, "So baby? Wane irin so? Meye so? Yanzu duk wannan Abinda dake tsakanin mu ba so bane? Baby you are mistaken, sone mai zafi na dade da sanin kece macen da nakeso a lokacin da nake gambiya idan ina tuna ninki har zazzabi rufeni yakeyi kece kadai macen da nakeji har cikin ruhi da kashi na,   Ki daina zancen soyayya please bata bakine tsayawa bayani, sannan sha awarki eh ina son jikin ki baby sosai ma kuwa saboda ina son ki dole in so ki inyi sha awar komai naki, Shiru yayi tareda fesar da iska mai zafi domin tasa shi yin dogon bayanin da bai taba iya yiwa wata macen ba, YASMIN wani irin farin ciki taji tareda sakin jikinta ta bashi wata irin runguma tareda sanya wani sabon kuka ga koshi ga kwanan yunwa,   Wanda take mafarkin yasota gashi yau ya bayyana mata irin son da yake mata Amma kash is too late to cry sun makaro yaza ayi suyi Aure ta ina Zasu fara yanzu,?   Jin y'anda ta rungume shi yasa shi sauke Ajiyar zuciya tareda yin wani irin kyakkyawan murmushi, Kamar zata shige cikin jikin shi takeji tsabar jin dad'i ta manta laifin shi gaba daya farin ciki ya mantar da ita cewar daga ita sai tree quarter irin na mata baki don ya dade da fisge bra dinta, Don haka jikinshi da nata da ba riga tuni sun dade da gauraya sun haifar da wani irin yanayi na kauna tareda tsantasr shaukin junan su,   Jin irin nishin da ya fara fitar wa yasa tayi kokarin raba jikin nasu bai da kuzarin riketa don haka binta kawai yakeyi da kallo ta sanya hannayen ta ta rungume kirjinta dasu,   Hannu yasa yana son ya cire hannun saidai taki ta kwabe fuska zata mai kuka "ka daina mana, "Baby please har yanzu bangansu yanda nakeso ba ki tashi tsaye ingani mana, ko tabawa fa baki bari nayi ba kawai na lasa sune da lips dina,   "Ahhh they test sweet baby, kukan shagwaba tasamai nidai ka tashi kamiko min rigata intafi gida, Dariya yasa ya mike tareda janyo yagaggiyar rigar ya nufi sama yana layi Kamar Wanda yasha giya ya sakko da towel ya mika mata "ki daura muje kiyi wanka saiki saka kaya, Daura wa tayi duk da iyakar shi cinya ta mike tareda dafewa Kamar zai kwance, ta kalli wurinda ta tashi gaba daya ya baci da jinin ta don tanajin irin rushing din da takeyi lokacinda yake bata wuta, A she har ambaliya tayi, innalillahi, wata irin kunya taji ta rufeta Kamar ta nutse Kasa Al adarta yau wani kato zai gani na shiga uku,   Murmushi yayi domin ya dade da ankarewa Kuma yasan bata cikin tsarki tun karon farkon da ya danneta yaji pad a jikinta, Yasan dalilin yin rushing dinta ya matso tareda dafeta, relaxed baby nine naja wannan Abin da kinada tsarki ruwan dad'i ne Zasu zubo haka ba jiniba, Muje ki yi wanka kinga bazaki tafi a haka ba, batada zabi dole ta bishi saman ya hada mata ruwa mai zafi tareda fitowa ya sakko kasan da kanshi ya sanya vacuum cleaner ya goge kujerar tas yana murmushi mai cike da farin ciki, Koda ya koma har ta fito tana tsaye, cikin walldrp ya bude tareda ciro mata jallabiyar shi ya mika mata ta karba ta sanya cikin sauri tareda janye towel din ta ajiyemai,   Yana tsaye ya jingina da kofa sai kallon ta yakeyi Kamar ya hadiyeta ya Kara so ciki' yakamata kidaina boyemin komai baby kin hana ni kallon ki yanda nakeso me yasa?   "Nidai zantafi kaga kusan sha biyu, riko ta yayi suka sakko bayan ya saka y'ar Riga, "muje inraka ki kafin indawo inyi wanka, Karamin gyalenta ta yafa tareda daukar wayarta yana biye da ita Kamar ya riketa a gidan yakeji, har kofar gidan ya rakata tashige cikin sauri ta kulle kofar sannan ya wuce, saida ta leka dakin Aunty taga tana baccin ta hankali kwance, sannan ta wuce dakinta saida ta Kara kitmtsa kanta ta cire rigar shi mai she gen kamshin jikinshi Kamar yana wurin ta sunsuna tareda lumshe ido ta ninke ta Ajiye a kayanta, Katifa ta haye tareda janyo wayarta ta Dora saman kirjinta ta runtse idanun ta tana tuno Abinda ya faru moment ago "MA karshen Y'an iska Wallahi bata taba ganin iskanci irin nashi ba, Wani irin yamm taji tsigar jikin ta na tashi da ta tuno da yanda yake lasar kirjinta Kamar wata Zuma kai yau ta hadu da namijin Zuma, Shima MA haka ya kasance bayan yayi wanka ya Kara dumama Abincin da ta dafamai ya zsuna yaci sosai badon yunwaba saidon hannun da ya girka shi saida ya wanke baki kafin ya jefa sweet mai tsada da kamshi ya haye gado wayar shi ya janyo ya duba time, Runtse idanu yayi yanajin Kamar yaje ya dawo da ita murmushi yake na farinciki da Kuma shauki, Kasa daurewa yayi ya Kira layinta,   Ba bata lokaci ta daga, "hmm yace na dogon lokaci ya Kasa cewa komai sai fitar numfashin ta kawai yake saurara, "Baby am speechless bansan mezan fada ba, kingama da zuciya ta kintafi da natsuwa ta I can't sleep today kitayani hira kozan samu natsuwa, Narkewa takarayi akan filo tareda kwanciya lub ta rike wayar gam Kamar shine, "ina ganin komai baby Kamar indawo da hannun ago go baya nakeji, "Ki soni don Allah bazan iya hakuri da rashin kiba ke rabin jikina ce ki soni baby please kisoni, ya mai maita yafi cikin kwando, tayi Ajiyar zuciya tareda sharce hawaye masu zafi, "Kadaina maganar so Aure zan..... "Please kidaina zancen nan karki samun ciwon zuciya yanzu Aure Hmm in my foot Wallahi ba wannan limamin a kaduna da zai daura Aurenki da wani babu shi, ko abani ke ko indauke ki muyi rayuwar da kowa bazaiji dadinta ba ke tawa ce koma waye ya cire idon shi akan matata,   "D'an uwana ne yanada ikon Aurar dani ga koma waye bare shi karan kanshi ne zai.... Stop YASMIN banason ji karkisa inyi Abinda banyi niyya ba,   Saida safe kawai yace tareda katse kiran zuciyar shi na zafi, Wato YASMIN d'an uwanki kikeso har kike iya fada min Baki damu da halinda zuciya ta ke ciki ba, ko Y'an biyu ne ku sai ya bar minke baby, ya furta tareda yin jifa da wayar shi ya dafe kai, A ranar Kasa bacci yayi har saida Asuba tayi ya tashi yayi salla kafin yayi wanka yafita wurin da yake motsa jiki, Ko kiranta baiyiba yau ya shirya motocin shi suka iso ya wuce bakin aiki cike da haiba da kwajini ga kaki na mugun karbar shi dole maza su girgiza idan ya fito *************** Karfe goma YASMIN ta hada kayan ta domin ismail zai zo ya kaita gida duk ta damu da rashin kiranta da baiyi ba ga shi baxata iya kiranshi ba itama haka har ismail yazo suka wuce, saida suka kai kofar gidan su kafin ya fara yimata magana don yau komai bai ce mata ba tunda suka fito, "Yasmin Akwai matsala fa, ta kalle shi " mai yafaru? Ki shiga baba na ma na nan yazo, zakiji koma Meye, Saidai kisani ina sonki sosai YASMIN, kanta ya d'aure haka ta fita jikinta yayi sanyi ta shiga gidan shi ya kwashe mata kayan ta ya shiga dasu,   Muryar baba Zango tafara ji yanata ruwan fada domin shi yafi baban su zafi, "Yaya bai isaba mu zai mayar mutanen banza? "Mamuda babu ruwanka yarodai ya fadi ra ayinshi don haka dole mubi don iya biyayya yayi mana, "Yaya Wallahi kai ke biye mai don haka babu ruwana bada miyau naba, "Dama ai bamusa miyanka ba nidai don kana uban Yasmin ne nafada maka karkaji daga baya, Gaishe su tayi bayan tayi sallama ta Kuma ji duk sharhin su Amma bata kamo bakin zaren ba, Ta gaida baban Zango yanda suke kiran kanin mahaifin nasu, "Mama na kin iso? Ya maryamar da yarinyar ta, ? Lfy lau baba yasu innan Zango? Duk suna Lafiya mama na ismail ya shigo baba ya kirashi, "Kaje ku gama magana a tsakanin ku Gobe insha Allahu zamu kammala komai kaji karka damu, Dakin ta yasameta har ta cire hijabin jikinta zani ne single da Riga play tayi kyau sosai duk da ba make up tayi matukar haskawa, Zama yayi tareda zuba mata ido "Fatima ya Kira real sunan ta yau tasan akwai magana, um ta zauna tareda zuba mai idanun ta tana sauraren shi, "Kiyi hakuri da Abinda zanfada miki, yaja numfashi ya fara magana, " lokacin da narasa maryam mun hadu da wata yarinya a wurin Aikin mu gaskiya bazan boye miki ba naso Zainab sosai kafin mahaifin ta ya yi mata miji ya Auradda ita na dauki dangana a lokacin na Kuma y'arda da kaddara nasan Allah da ya hana ni Auren maryam da Zainab shi zai yaye mun soyayyar su cikin zuciya ta, Cikin satin da ya wuce kwatsam na samu labarin a she sabodani taki yarda Sam tayi zaman Auren ta har mijin ya sauwake mata, ina wurin aiki ta sameni da kuka sosai akan idan ban Aure ta ba zata kashe kanta, Maganar gaskiya YASMIN ina son Zainab Kuma nayi mata Alkawarin Aure, ina sonku duka don haka na fadawa baba zan hadaku baki daya ina fatan zaki bani Goyon baya kanwata,?   Tunda yafara maganar ta zuba Mai idanu tareda yimai wani irin mugun kallon Kama raina min wayau, "Yaya kenan to ni na hakura kaje ka Aureta ba laifi Wallahi na yafe ka tafi kawai, wani irin kallon ta yayi "karkiyi mun haka YASMIN na kwallafa rai akanki don Allah karkisa in zaba tsakanin ku bazan iya barin kowacce ba a cikin ku, "Wallahi sai ka Barni don bazan y'arda ka hadani da wata ba tun yanzu ni Yasmin kishiya a rana daya ina Wallahi kaje kawai na hakura, Jiyo maganar su baba ne yasa sukayo waje, da sauri, mama ma tafito rike da ludayi a hannu jin jiniya ta cika ko ina a Unguwar baba ya sharce gumi ya kalli kanin shi,   Mamuda ina ganin barayin da akace suna Unguwar nan da gaskiya ne watannin baya sojoji Kamar yaki kullum cikin Unguwar nan kaga yau ma sundawo Allah ya jishe mu Alkhairi,......... ️ *ai ina ganin tawagar su maman kids ne sukazo artabu ni nayi nan ba ruwana fan's love you All'* *Matar soja* [8/30, 2:56 PM] Feenerh Wrtr: PROFICIENT WRITERS ASSOCIATION тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09   *BARIKI* _Auren Soja_     _written by FENERH_ Maman Ammar *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby   *NA sadaukar da wannan shafin gareku my people kungiya mai tarin Albarka da dumbin hadin kai proficient writer's ina Alfahari daku Allah yakara hada kanmu Allah ya baku lfy mutane na Nabeela sarauniya tareda MAMAN Mamy SHALELEN proficient* *Ammyn khyarat* *Rukayyat Ikra* *khadeja Auta* *baba sadeq* *nusee y'ar Amana* *Ummu najma* *Aisha Alto* *Tareda kai bawan zage zagi Yusuf Indabo* *jinjina agareku baki daya Allah ya kiyaye ku da ga sharrin mahassada ya Kara muku zakin hannu da kaifin kwakwal wa* 27&28 Wani irin trumbling cikinta yayi saboda tsabar tsorata ta zaro idanun ta waje tareda dafe kirji, "nashiga uku ta fada a fili duk suka zuba mata ido' "Meye najin tsoro YASMIN bayan gani anan, ismail yafada ta zabga mai wani irin kallon bakasan me kakeyi ba ya nufi hanyar waje a rude domin tabbatar wa idanun ta,   Take mata baya su baba sukayi domin suma duk suna son ganin meke faruwa a wajen, baba da y'ar butar shi ya fita a hannu ta Alwala, Kusan suman tsaye tayi domin motocine sunkai kusan goma a jere sai katuwar hummer dake tsakiya duk kalar Army sauran duka hilux ne, Tunfitowar ta ya hangota tareda yin Ajiyar zuciya yana kare mata kallo tayi mai masifar kyau da shigar native wear din saidai ranshi yabaci data fito ba hijabi ga kirjinta sun kunburo sosai don Abinda yafara kallo kenan Ajikinta, Kallon irin Yaran da yakwaso yayi yabasu umarnin komawa cikin motocin su don duk sunfito sungama zagaye wurin gaba daya da bindigogi,   Takowa yafarayi cikin takun girma da Kuma haiba lokacinda su baba ke tsaya suna kallon ina wa innan mala I kun duniyar zasuje? baban Zango kam kanshi kawai ya leko daga waje,   Ta Riga ta gama sumewa da tsoro jin kawai tayi anrungume ta tareda yin Ajiyar zuciya, Saurin dawowa tayi daga doguwar sumar tsayen da tayi ta yi saurin ja baya tareda sanya kukan rashin mafita musamman data kalli gefen da baba ke tsaye ga butar hannun shi ta fadi duk ta tsiyaye sai ismail da idanun shi suka juya tsabar kishin ganin wani kato rungume da Matar. Da zai Aura,   Kara matsota yayi kamar zai shige jikinta ga wani kallo da yake mata kamar zai lashe ta tsabar so "baby meyasa kika wuce baki fada min ba? "Nifa da nayi fushine Kuma zuciyata taki y'arda da hakan ina bakin aiki naji bazan iya hakurin rashin kiba dole na koma gida nasamu Wai kinyo nan shiyasa na biyoki, "baby I can't indure nakasa daurewa indai akanki ne zan iya yin komai baby I can do anything bcous of you,   Ai YASMIN tashin hankalinda ta shiga bai misaltuwa yau tashiga uku da baba yau MA ya gama kasheta yau ta gama yawo,   Ai tuni su baba sunkoma cikin gida har ismail ma sun barsu a wurin Sam tarasa madafa sai kukan da ya Kara kufce mata ta kalleshi hawaye share share ta ce "meyasa baka tunanin Abinda zaije ya dawo meyasa kake Abu ba tunani me yasa baka Abu cikin hankali? Bata fuska yayi tareda zuba mata ido "oh nine bana tunani? Naji idan akanki ne banda tunanin komai Kuma zan nuna miki banida tunani yanzu, Kofar gidan ya nufa kai tsaye ya kutsa kai tareda sallama mama na nan rike da ludayinta tana sonjin labari ko wa ya Kasa cewa komai baba ne ya janyo kujerar roba zai zauna yaji sallama hade da kutso kai ciki ba wani bata lokaci, ai duka sun tsorata tuni baba ya mike tareda matsawa jiki na rawa baban Zango ne ya Amsa cikin rawar jiki tareda mika mai kujera, "Bismillahi d'an nan zauna, Dukawa yayi har kasa ya gaishe su tareda cire hula cikin bangirma ya fara kwasar gaisuwa mama tuni ta shige ciki Kanta ya daure sosai yau me suke gani haka. Meye hadin su da wannan murdeden katon? "Baba kuyi hakuri don Allah na shigo kai tsaye bayan nasan hakan bai dace ba, Amma idan kunduba ta wani gefen ba wani Abu bane don nine surukin ku, Baban zango yace "toto Amadu ne? Baba yace aa bashi bane bari muji dai ko waye shi? "Alhmdulillah baba nine keson YASMIN mundade sosai da ita taki bani damar zuwa nan gidan ingabatar da kaina akan cewar kun zabamata miji batason ta bata muku rai taki bani hadin kai Amma Wallahi baba ku yarda dani YASMIN ni take so batason zabin ku kawai biyayya zatayi badon zuciyarta nasoba, Yasmin data rabe gefe guda tuni ta Kara sautin kukanta tareda fara magana "baba Wallahi ni sharri zai mun ni banason shi kawai so yake ya hadani daku, Wani irin d'aci yaji a cikin zuciyar shi yanzu shi YASMIN zatace bataso kai tsaye? Ranshi yakai kololuwar baci ya mike tareda mikawa baba hannu "baba ni zantafi ina bakin aiki ne jiya na shigo kasar zanje tarbar rundunar da na wakilta a jaji, Duka hannu suka bashi cike da girma mawa don sun san wanna mutum daga gani yataki wata tsiya ko a gidan soja, Banda ismail da ya hade fuska tareda dauke kai cike da kunar zuciya, kusa da ita ya matsa tareda yimata kallon zaki biya bashi ya fita ya barta da fargabar Abinda zai biyo baya,   Ba Wanda ya iya cewa komai saida sukaji karar jiniyar tafiyarsu baba ya zauna tareda sharce gumin da ta tsatsafo mai kamar ya shiga gidan brodi, Baban Zango ma malum malum dinshi ya gyara tareda kallon YASMIN "zo nan mama na, ya fada cikin natsuwa, jiki na rawa ta matso tareda tsugun nawa tana jiran hukunci, "Saude' baba ya kirata, ta fito tareda janyo kujerar mata ta zauna "malam Wai meke faruwa ne naganku kamar gidan mutuwa Nifa bangane ba? "Toh ai nima saudatu bangane komai ba sai wadda tayi jagorar komai tayi mana bayani' wake nan? "Yarki mana waye in banda YASMIN, "Yaya mubi a hankali muji komai a natse don ni koda yaron nan ke magana bangane komai ba, "toh mamuda idan banbi a hankali ba garaje zanyi? "Yo ko zafi nayi ina zai kaini kana ganin y'anda ya zagaye mana unguwa kamar masu laifi kaduba ma kota har a katanga suna leko mu irin wannan bala I har ina? "Mama na Meye wanna ina kikeso ki jefa mu shikuma wanna don girman Allah ina kika tsinto shi? Abarikin? Ku Kuma haka Zaku kare a jajubo mana masifa ita maryam ta makale tace sai soja kema ji me kika kwaso, "Mamuda daga gani wannan yaron bazaiyi mutunci ba, don haka ka dauketa kawai ku wuce zango idan andaura Aure Sa dawo da mijinta 'Yaya ai wanna ba shawara mai kyau bace ai ko birnin sin zamuje banjin wannan yaro bazai biyomu ba Kuma ai nida natafi da ita ni kwabata zatayi ruwa, "Kai samaila dama kanada zainabu sai ka hakura kawai da mama na, "Aa mamuda banson Abinda kakeyi meyasa kakeson rabashi da y'ar uwar shi? Tashi kawai baban Zango yayi ya saba malum malum tareda gyara zaman hula" toh nidai nafada muku inkuma dai nine waliyin Yasmin to ban daura mata Aure da kowa sai in wanna sojan yazo yace ya fasa zancen Auren ta don haka ni nayi gida Saude Allah bamu Alkhairi, Ya wuce kawai batareda karawa waigowa ba, baba zuba mata ido kawai yayi kafin yace "tashi ki wuce ai ke kanki kinzama Abin tsoro Fatima Kuma nasan komai da sanin maryam zamu gauraya da ita,   Ciki ta wuce tarasa me ke mata dad'i tarasa madafa tarasa ina zata tsoma ranta tana hango bacin randa ya tafi dashi ya mugun tsaya mata a rai, ***************** Bayan ya tashi aiki ya nufi gidan su dama Hajiya tasan da zuwan shi don haka ta shirya mai dish Kala Kala da kanta ta jera mai a dadduma ya iso da tawagar shi kamar gwamna,   Saida ya koshi ya fara bata hakurin rashin zuwan shi da wuri, "aa bakomai nasan aiki ne ya rikeka, riko hannun ta yayi cikin damuwa, "Akwai magana kenan yau don nasan ka tun kana yaro daka rikeni hakan akwai babbar magana, "eh mama akwai, ina cikin damuwa , narasa mafita bansan yazanyi ba,?   "Tell me what to do kaina ya kulle, "kayimin bayani badai matsalar wurin aiki bace ko? "Akan yarinyar da nakeso ne, ya fara yimata bayanin komai akan YASMIN, Amma banda zancen Auren ta ya boye wannan,   Hamdala tafarayi kafin tace kai nagodewa Allah yau kaine ke zancen Aure? Lallai wannan yarinya ta ciri tuta Ashe soyayya ta da ita akwai Abinda Allah yaboye, Kai nayi farin ciki sosai baba na Allah yasa rabonka ce, ya Amsa da Amen, yaushe zakuje nema min Auren ta? "Banson garaje Ai gobe zankira kannin mahaifinka sai muyi magana inyaso sai mu tsara komai, "Don Allah kar ya wuce jibi zuwan su 'ya ciro ATM ya mika mata gashi asiya komai da ake bukatar kaiwa akwai kudi sosai a ciki zasukai 2milion idan basu isa ba kifadamin inturo muku Wasu, Sakin baki kawai Hajiya tayi tareda mamakin d'an nata yau ba mafarki takeyi ba kuwa? Muhammad ke son Aure kuma cikin sauri haka? Lallai mahakurci mawadaci   Allah ya ma wannan yarinya Albarka ita kam koda Asiri YASMIN tayima MA tana farin ciki da hakan kuma sai takara mata kudi takaiwa malamin,   Ma kuwa a gidan ya yi wanka ya shirya domin yanada daki na musamman, ya sallami yaranshi kafin ya fito cikin shigar manyan kaya shadda ce fara kar ya murza hula kamar wani sabon Ango ya fito yana zabga kamshi fadin haduwar da yayi bata bakine, Waya ya dauka yakira tareda bada umarni kai tsaye, "Mu hadu a Unguwar Dosa da wannan motar harma da kayan cikin duka,   Ya fita Hajiya nakara godewa Allah da Yau take ganin irin wannan farin ciki, *************** Yasmin dai yau a daki ta wuni bayan tafiyar ismail , ya gama yi mata bori ko kallon shi batayi ba kuma tasan da bai bullo da zancen Auren Zainab ba bazata taba yimai hakan ba,   Yama raina mata hankali Wallahi kuma ta shirya ko baba zai Yanka ta bazata taba y'arda da Auren shi ba, Baba kuwa yakasa cewa komai ya zubawa sarautar Allah ido yaga ta ina wannan rikici zai kare? Karfe takwas na dare YASMIN ta samu tsalki ta sheko wanka tareda yin Alwala ta shiga dakinta ta shirya kanta tsab cikin wata rigar baccin ta guntuwa dai dai guiwa tareda daura zani ta Dora hijabi tareda tada salla,   Tana sallamewa baba ya kirata falon su ' ta zauna kamar wadda tayiwa sarki karya gefe guda tareda dukar da kanta, "Mama na kimun bayani ina sauraren ki " me kikeso ki fadamin? Kema bazaki Auri d'an uwanki ba kike nufi? Dake da y'ar uwarki kun gama watsa min tsarina baki daya ko,   "Haba malam yakamata ka barwa Allah wannan lamari ita maryam da kake magana Ina zamukai wa innan rabon kana ganin cikin shekara biyu Yara biyu ai sai mu yarda da yin ubangiji,   "Haka ne saudatu yanzu kina so ki fadamin bansan Allah keyin komai ba kome? "Toto yanzu nasan komai ma da sanin ki sukeyi tunda ba danginki bane shiyasa kike zuge ya'yan ki su ki Auren shi ko? "Haba malam ya zaka fadi haka bayan kasan irin y'anda na reni ismail da hannu na kamar ni na haifeshi bai dace wannan kalma tafito daga bakinka ba, Toh kusani keda Yasmin indai nine mahaifin ta to bazata taba Auren wannan yaron mara tarbiya ba, ya mike fuu ya fita, YASMIN tashiga tashin hankali najin yau saboda ita iyayen ta na misayar yawu, abinda bata taba jiba tsawon rayuwar su, Kuka taji ya kwace mata mama ta kalleta,   "Toh Allah ya biyaku ya'yan Albarka Wato dai kullum sai kunja mun magana idan zancen Auren ku yataso haka y'ar uwarki tayi kema gashi Abu yazo gab shine kika bullo da naki iya she gen, "Kuyi kokari Kuyi Auren ku inda kukeso ni kuma sai ku kashe min nawa kunji nagode muku, itama maryam yanzu zankirata inji don nasan da sanin ta komai ya faru, Kukan tane ya Kara sauti tareda girgiza kai cikin Kuka" mama don Allah kiyi hakuri Wallahi ni ban turoshi ba kuma Aunty batasan komai akai ba, ni wallahi na yarda da Auren ya'yan karkuyi fada akaina don Allah, . "Tashi kije ni nagama magana kuma, tashi tayi kamar wadda kwai yafashe mata ta nufi dakinta, Baba na fita yaci karo da motoci sababbi dal a kofar gidan daya fara sai kuma ja y'ar Kara ma mai shegen kyau kirar Volvo sabuwar fitowa ya tsaya cak tareda makakin ko suwaye a ciki,   Fitowa MA yayi daga cikin farar ga kayan jikin shi farare yayi mugun haduwa ga kwarjini da haiba da ya cika ko Ina, baba bai gane shiba saida ya matso tareda mika Mai hannu, "Salamu alaikum baba barka da dare' baba ya Amsa cikeda ganin girman yaron yace wa kake nema yaro? "YASMIN nine dazu nazo da safe "toto nagane soja ko? "Eh baba sunana Muhammad Abdullah, to Sannu muhammadu bismillah shigo,   Tana kwance ta Dora wayar ta saman kirjinta tana tunanin rashin kiranta da yayi yau kardai fushi yakeyi da ita? Kamshin jikinshi tajiyo tun shigowar shi taji domin turaren nada mugun kamshin da da mutum ya doso zakasan mutum na zuwa,   Wani irin faduwa gabanta yayi kardai shine ya dawo? Tashiga uku, kuwa MA zai jefa ta a damuwa,   Kiran baba yasa tayi saurin zabura cikin tsoro batareda ta tsaya daukar hijabi ba ta fito ta gyara sumar ta ta nannade ta sai zanin da ta Dora a kugunta saman rigar baccin ta mai guntun hannu Mai dauke da hoton frozen a jiki,   Kirjin nan na MA ya fito da kyau gwanin burgewa saida tasawo kanta wajen ta ganshi cikinta ya Kara d'urar ruwa, Idanu ta zuba mishi cikeda tsoro gashi wannan ne karon farko data fara ganin shi cikin shigar manyan kaya yayi mata kyau sosai kamar Ango,   "Kije ki fito mana da kujera kintsaya kina kallon mutum kamar zaki cinyeshi, saida taji kunya tareda shigewa dakin mama tafito da kujerun roba guda biyu ta ajiye jikinta narawa ta koma daki cikin sauri,   Tunda tafito ya zuba mata ido kamar ya cinyeta yakeji tayi mugun yimai kyau gashi kanta ba dankwali yaga y'anda sirrin sumar ta yafito Wani iri yakeji kamar ya bita cikin dakin ya turmushe ta yakeji,....... ️   *hmm fan's yau hakuri zakuyi dani wallahi nayi typing ya goge tas by mistake don haka Kuyi manage gobe zan wanke muku zuciya da yardar Allah*   *Matar soja* [8/30, 2:56 PM] Feenerh Wrtr: *BARIKI* _Auren Soja_   _written by FENERH_ Maman Ammar *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby   *Ina son ku ina kaunar ki kuna faranta min ina matukar jinjina muku Allah yakara dankon zumunci yakaro kauna my real fan's AISHA BABAYO, HUSSY ALI MAMAN ABDULLAH UMMI ZARIA, MOMYN KIDS, MOM HUSNAH,* _WA INDA MA BANKIRA BA ZAKUJINI A NEXT PAGE, AP NAYI TUYA NA MANCE DA ALBASA AISHA DAHIRU UWAR GAYYA MAJI D'ADIN M. A JINJINAR BANGIRMA UWAR DAKIN YASMIN ALLAH YABAR KAUNA DA AMANA_   29&30 Yaudai taga Rayuwa, kirjin ta har wani irin tsalle yakeyi kamar zaifito tsabar tsoro "MA zai kasheta kwanan ta bai kare ba,   "Bari inkira mahaifiyar ta ku gaisa, baba ya fada tareda mikewa ya shiga dakin mama, wayar shi ya janyo tareda tura mata text _kifito kefa nazo gani kin wani shige ciki kinbarni da yunwar idanu_   Saurin dubawa tayi tareda cewa "naboni yau, kasa motsi tayi ta koma lafewa a katifar ya kuma turo mata wani _wallahi zan shigo ciki kuma sai nayi Abinda nakeso zanfito inbarki da kunya kinsan ni bansan Abinda ya dace ba_   Zabura tayi ta mike cikin sauri ta saka hijabin ta tareda fitowa, wani irin kallo yake binta dashi tundaga sama Har kasa ya matse fuska "me kike boyemin?   Marai raice fuska tayi tareda matsowa kadan" don Allah me kazoyi? "Bansani ba kicire hijabin sai inbaki Amsa, "Don Allah muh'd ka rufamin Asiri ka bari inji da tashin hankalin da ka jefani, "banajinki saikin cire wannan hijab din sai muyi maganar,   Cikin sauri ta koma dakin domin jiyo maganar su baba Zasu fito, gyara zaman shi yayi da kyau ya zubawa fuskar mama ido cike da farin cikin ganin inda YASMIN din shi ta gado kyau da fari, Ya zame kasa tareda cire hula cikin bada girma irin na soja "mama barka da dare, ta Amsa cikin farin ciki da natsuwa bayan ta d'an zauna kan karamar kujera "ya aiki,? Yace Alhmdulillah, "to Allah ya tsare ku ya kuma kare ku, Amen Amen nagode mama, Yaji dadin Addu ar ta har cikin zuciyar shi ga Matar nada kwarjini da kamala ga tsafta don tunda ya shigo gidan karan farko yasan Matar gidan nada matukar tsafa don sumintin tsakar gidansu tsab Abu zai fadi ka dauka ka jefa a baki, Saida suka gama gaisawa ta mike tareda cewa" kaga Yasmin din? "Aa ya fada cikin sauri "mama tagan ni Amma taki fitowa kuma tasan saboda ita nazo, mama don Allah kiyi mata magana tana wahalar dani bayan itama fa tana sona sosai, Wata irin kunya ce ta rufe mama naganin y'anda yake mata magana kamar wani Kara min yaro, shikuma harga Allah jinta yake kamar hajiyar shi, Ya koma kan kujera ya zauna da kyau tareda dukar da kanshi kadan ya kalli baba yasan baba baya ra ayin shi sarai don yasan yanda Akayi akan Auren maryam don haka yasa shi nuna iko kota karfin mulki sai Anbashi Yasmin sunyi Aure su sami jikokin sunnah ko kuma su tarbi jikokin soyayya, "Toh Nima bari inshiga ciki sai tafito Kuyi magana, baba yayi magana, "eh dama baba inaso infada maka jibi iyaye na zasuzo nan sukawo kudin gaisuwa,   Tsit baba yayi na d'an lokaci kafin yace "tom muhammadu nidai banine mad'aurin Auren Fatima ba Amma gobe zan Kira kanin nawa infada mai sai kuyi maganar komai a tsakanin ku, Kara dukowa yayi kadan yayi godiya kafin ya koma mazaunin shi, shigewa sukayi ciki tareda barin shi a wurin bayan baba ya kwala wa Yasmin Kira ' kuryar daki suka shige domin su tattauna magana atsakanin su, Alokacin ya mike zuruf ya nufi kofar dakin nata cikin hanzari, Dai dai tana canja kayan jikinta domin rufawa kanta a siri domin tasan bazata iya fita da kayan jikinta batareda hijabi ba kuma a tsakar gidansu,   Riga da sket ne ta fito dashi na material ja domin canjawa, bata taba tunanin MA zai shigo cikin dakin ba shiyasa ta tube daga ita sai pant da bra ta saka sket din ko guiwar ta baikai ba ya shigo, Da yake tabawa kofar baya yasa yaja ya tokare tareda nannade hannun shi a kirjinshi,   Wani irin trumbling marar shi tayi naganin ta a tsaye sanye da pant da bra farare duk da bata juyoba he can see ha awesome hips dai dai jikinta masu daukar hankali ga bombom dinta wow, Ai tana zuge sket din ta janyo rigar yayi wuf ya karasa kusa da ita tareda rungume ta ta baya ya Dora hannayen shi akan westdinta tareda sauko da kanshi daidai wuyanta ya Dora mata kiss a wuyan,   Lamarin MA yadai na bata mamaki saidai tsoro don haka koda taji hannun mutum tasan shine, cikin tsoro tayi saurin juyowa bayan ya sauke mata hot kiss a wuya, Tama manta da ba Riga a jikinta ta zuba Mai ido jikinta NA rawa tareda dafe bakinta da hannu cikin rasa mafita, "Wai meyasa kakemun hakane? Don Allah kafita kajirani ina zuwa please kaje waje karsu mama su fito suganka muh'd ka rufa min Asiri don darajar iyayenka,   Aikin banza domin shi yayi nisa tunda ya Dora idanun shi akan boosty boob dinta ya rikice idanun shi suka juya Kala yayi wani irin kalar tausayi tareda kokarin rikota taja baya da sauri tareda kare kirjinta da rigar, cikin tsoron Abinda tasan zai iya yi, Baya baya yakoma ya fada kan katuwar katifar tata mai cike da kamshin ta mai dadin gaske ya runtse idanun shi tareda kokarin natsa kanshi,   Gaskiya yau yayi namijin kokari DA bai yi striping dinta a cikin gidansu ba don ta mugun kunnashi sosai d'auriya iya d'auriya yau yayi, Ganin y'anda ya runtse idanun shi yasa ta yi saurin saka rigar tareda janyo d'an karamin mayafin ta ta yafa ta matsa kadan kusa dashi' katashi mutafi don Allah karsu mama sufita inshiga uku,   Bude idanun shi yayi tareda zuba mata su cikeda shaukin zazzafar soyayyar ta "love you baby more and more, ya fada cikin kwantar da murya kafin yabi dakin nata da kallo, Bayan katifar sai walldrp mai kofa biyu da mirror dinta dake dauke da turaruka da kayan shafa gefe data akwatunan tane guda shida pink masu kyau domin su ba talakawa bane don duk Wanda keda maganin lalurar yau da gobe ya wuce talaka, don Albashin baba ya ishesu suji dad'i har ma suyiwa Y'an Uwa Alheri,   Kan bangon dakin ya sauke idanun shi dake dauke da hotunan su Kala Kala ita da maryam tundaga na kuruciya har zuwa yanzu,   Murmushi yayi mai kyau ganin wani hoto nata tana sanye da kayan ta na nurse tayi masifar kyau, yatashi tsaye tareda kakkafe shaddar shi data fara squzing ya nufi wurin tareda ciro hoton ya rungume yasaka hannu ya ciro wani datake sanye da wata doguwar Riga pink kamar babie kanta da crown daga gani na wani occasion ne,   Kallon shi kawai takeyi, ga kamshin shi yacika dakin nata tab ya matso gab da ita" tank's for this beautiful pictures muje inbaki tsarabarki tana waje,   Bai jira komai ba ya fita tabi bayanshi cikin sauri domin ganin ko ba Wanda ya fito, tayi Ajiyar zuciya har suka kai kofar gidan bakowa, Yana rungume da hotunan kamar kwai saida ya bude gaban motar ya ajiyesu kafin ya dawo wurinta, Baki Yasmin ta saki wurin kallon motar da tagani y'ar karama tayi mugun yi mata kyau tana sheki duk da dare ne akwai d'an hasken wutar nefa a Unguwar kota ina, Matsowa yayi tareda sanya hannun shi cikin pocket din Aljihun shi ya d'an rankwafo ta fuskar ta kadan "hope you like it? Idan kuma batayi ba a canjo miki' Wani irin kallon shi tayi cikin tsoro, " me kake nufi? "Motarki ce akwai tsarabarki ma a ciki ya bude motar tareda bude bayan boot din ya Wasu irin akwatuna ne guda uku Kala daban daban manya duka girma daya blue red da kuma purple ya fito dasu kamar bakomai a ciki ya dauki biyu ya shiga dasu cikin tsakar gidan kafin yadawo ya dauki dayar ya shiga da ita, Takasa cewa komai saida ya dawo yace "zomuyi magana kai tsaye ya riko hannun ta suka shiga gaban motar, Juyowa yayi dakyau ya dafe kumatun shi ya zuba mata ido "baby nasan kinfi karfin wannan y'ar kyautar Amma kiyi hakuri zamuje kasuwa insiya miki komai ya d'anka mata key din motar a tafin hannun ta,   Gaba daya tarasa nayi ita yanzu ta ina zata fara tasan kotace mai bazata karba ba Aikin banza zatayi don ta lura dashi mutum ne mai ra ayin rikyau idan yayi niyyar Abu ba Wanda ya isa ya hana shi, don haka kallo kawai take binshi dashi, Saida ya bata key din ne tayi saurin girgiza kai" aa nidai ka bar ni banason mota ta ina zanshiga da wannan key din incewa su baba me? Bayan kayan da kashiga dasu nidai don Allah kabari ingama dasu Lafiya, "Hhhh yayi dariya sannan yace "tom idan bakyaso sai ki yi sadaka nidai nakawo kuma bazan koma dasu ba don kiji, Matsowa yayi tareda riko hannun ta ya kashe mata ido, "baby kinfa dauki alhakina yau, kiri kiri Kinyi min kwalelen Abin kallo na inaji ina ganin su kin hana ni morewa, "Tun fa shekaran jiya rabon da in rage ruwan Marana kinga yau Kim in wani Abu Inba hakaba yau bazan iya bacci ba, Kallon nariga nasaba da halinka kawai takemai kafin tayi magana, "wannan ne soyayyar taka da kake fadar kanamun? "Sosai baby da banasonki da na danne ki wallahi na rabaki da wannan y'anar dakike yanga da ita tuntuni, "dama kasaba yiwa yaran mutane ' "Point of correction, yaran dake ra ayi dai ko yanzu zuby najirana a gidana zanje ta ragemin wannan ruwan dole yau sai sun zuba zan iya bacci ya fada tareda shafo marar shi, Cikin takaici ta bude motar ta fita, yana kiranta ta shige abinta Allah yagani tana tareda aiki don KO Auren MA tayi to sai tasamu hawan jini domin shi mutum ne mai yin Abinda yaga dama ba Wanda ya isa ya hanashi, Fitowa yayi tareda rufe mata motar ya shigo gidan bai koma takanta ba ya ajiye key din akan akwatunan ganin karfe goma harda rabi yasa ya wuce gidan shi, ********************** Tundosowar shi kofar gate din ya ga motar zuby a wurin ya matse fuska kafin ya shiga cikin gidan, tundaga falon yaci karo da Emanuel, Yafara yimai ruwan bala'i akan yadawo zai fara barin mai gida kamar gidan karuwai ko, ya fara bashi hakuri jiki na rawa "Oga sory sir I no go do one again, ys fada yana sarawa kamar koda yaushe,   Dakin dake kasan falon ya nufa tareda kullewa gam da key ya fada kan katon gadon ya kife tareda runtse idanun yana tuno Abincin zuciyar shi Yasmin, Kasa daurewa yayi ya kirata, lokacin tana kwance cike da kishin Kila yana can wurin karuwan nashi har Wasu hawaye takeyi na bakin ciki taga Kiran shi,   Ba jan Aji ta dauka domin tanason tasan halin da yake ciki, "babyyyyyy ya furta yana nishi "ad'aura min Aure zuwa jibi kar inkara lalacewa, I can't sleep Marana babyyy, ya fada cike da bukatuwa tareda sauke mata huci mai zafi a kunne, Ajiyar zuciya kawai ta sauke tareda fara magana, "kana ina ne yanzu? "Ina gida na a BARIKI, "kaida waye agidan? "Nida zuby ne tana sama ni kuma ina kasa nazo nasame ta agidan,   Wani kululu ne ya tokareta yanzu don iskancin MA yake fada mata shida wata ne a gidan? Tsaki taja mai karfi, ya dago da kanshi daga kwancen "baby ina fatan tsakin ba nawa bane? Banza tayi mai "Hmm you must pay that, ya katse Kiran, minti biyu ya kuma kiranta again "karki kuma yi koda badani kike ba banaso zan shigo gidan da safe injira baban mu da zai mana Aure,   Ajiyar zuciya tayi tareda rike wayar gam a kunne. "No matter how he is she love him to the extend da bata taba iya fushi dashi tana jin son MA kamar fitar numfashin ta,   "Baby barci kikeji? "Aa tace cikin sauri tareda Kara rungume wayar kamar shi ta rungume "kaifa bacci kakeji? "Aini idan ina tareda ke banajin bacci baby banki mukai safe ba ahaka,   Tuni ta baje idanun ta bude ido tarai domin zataso su kwana tana jin shi kar yaje wurin zuby don jitake ina ma tana barikin yau sai takoreta a gidan, ko yanzu jitake kamar tace ya koreta Amma ita a wa?   Haka suka kusan kwana yana zuba mata sambatu har karfe hudun Asuba kafin ya katse "baby bari inje inyi wanka inyi salla kafin akira asuba kinsani zubarda ruwa jin numfashin ki kawai "baby kema kinajin me nakeji kema kin yi yo yo? Kit ta katse Kiran tana dariyar halin muh'd , shidai baruwan shi saidai inbaiyi niyayyar magana ba duk abinda yafito abakin shi sai ya fada,   Saida tayi Alwala tafara nafila tareda yin Adduar neman zabin Alkhairi a rayuwar ta kafin akira salla tayi ta d'an karanta qur ani kadan tarufe ta haye katifa domin biyan bashi don yau gaskiya saidai mama tayi mata hakuri, Aikin gidan nan saita tashi,   Saidai karfe shida baba ya doki kofar ta ta zabura ta mike idanun ta cike da bacci ta fito waje tana hada Han ya, idanun ta a waje ganin baba ya zubawa akwatuna ido, mama na gefe rike da carbi,   "Fatima wa innan kayan fa ga mota nagani awaje tun jiya ga kuma makulli a anan? Bakin ta na rawa tafara in ina" baba shi ya kawo min Wai tsaraba,   "Harda mota? Inji baba cikin karaji, Amma y'ar nan me kikeso kimayar dani ne karamin mutum? Aurenki saura kwana uku ki karbi kayan wani kato haka akeyi me kika bashi zai miki irin wannan kyauta haka harda motar da har in mutu kudin Albashina bazasu taba siyan rabin taba,   Kuka tafarayi najin maganar baba, mama tace "malam kabi a hankali idan mamuda yazo sai asan nayi KO ka bashi hakuri kawai yadai na zuwa, Kallon ta yayi da kyau "lallai Saude to bari mamuda yazo muji shi zaisan nayi tunda shine uban yarinya, "aa ai kai zakayi wani Abu akai kafin shi yazo saika jamai layi, "Anki aja layin kifita idona saudatu inkinaso mu shirya kema ai uwarta ce kija mai layin kuma ki binciki y'ar ki sarai nidai nafada miki kuma itama maryam ina nan yau ina jiranta,   Ya wuce ciki fuuu, mama ta kalleta "saiki kwashe kayan kishigo dasu ciki ai kin kyauta, jikinta na rawa ta Sa hannu ta ja daya dakyar take janta ta shiga da ita tana mamakin yanda taga ya dagasu kamar empty Ashe uban nauyi garesu, Baccin da bata koma ba kenan ta fara Aikin gida saida ta shirya break takai dakin tajera a falon su mama tasame su suna dramar da ta kun no gidan yanzu na zancen MA, baba yasa ta bude akwatunan duka kayane English wears da takalma masu tsada sai zannuwa masu tsada da jakun kuna da sarkoki harda gwal da passion masu aji ga inter wears dai dai size dinta kusan kowane dozen yakai biyar, Idanun ta awaje lallai MA d'an iskan ciki da waje ne na bugawa a calendar, baba yakasa magana ya kalleta kwashe kikai dakin ki ai nakine tarkacen, Haka ta kuma kwashe su baba ya karbi makullin motar yace bari mamuda yazo zanbashi ya mayar mai da ita, "hmm kawai mama tace,   Karfe goma ismail ya iso da jerin saitin akwatunan shi har saiti biyu na yayi ya shigo dasu tsakar gidan da taimakon Abokin shi suka baje su a wurin kafin ya leka falon mama yace tazo tagani in akwai Abinda baiyi ba ya karo natane Dana zainab,   Mama kallon kayan kawai tayi tana tunanin gwaramar dazata biyo baya tasa Albarka tareda cewa "Allah dai ya muku zabin Alkhairi ismail in Yasmin rabonka ce Allah yasa ayi damu in kuma ba rabonka bace Allah yabaka dangana,.......... ️ Kujira sabon post zuwa dare mutane na insha Allah, *lamarin nan yafi karfi na my fan's kuyi Addu ar sauki don akwai gwarama nake gani gaba akwai kura*   *Matar Soja* [8/30, 2:56 PM] Feenerh Wrtr: PROFICIENT WRITERS ASSOCIATION тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   _written by FENERH_ Maman Ammar *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby 31&32 Yasmin na daki tana maida bacci batasan ma me yakeyi ba a tsakar gidan, karfe sha daya baban zango ya iso Shima, ya tarar da kayan a nan, Bayan sun gama gaisawa da mama ya zauna takawo mai Abin kari yanaci yana kallon kayan saida yayi kat ya fara tanbayar yayan shi, "Saude ina Yaya? "Malam ya fita yanzu zai dawo baiyi nisa ba, "wa innan kayan zainabu ne ko? "Eh da na Yasmin, "waya kawosu? Yafada cike da rainin hankali, "na ismail ne, "Wato duk maganar da mukayi dashi baiji ba KO?   "Mahmud Kayi mai Addu ar zabin Allah kawai kubi komai Ahankali, "to nidai Yaya yakirani akan maganar soja kuma nidai Saude inkinga ba ayiba to bana numfashi,   Ko kuma shi yace bayaso ai ni tunda ismail yakawo maganar Auren Zainabu naji hadin yafita araina banason Auren shi da mama na nafison tayi Auren hutawa ba gidan kishiya ba,   Dariya mama tayi "Au shiyasa Kuka kasa Aure kaida malam? "Ai kune Kuka hanamu keda hinde "aa karkuyi mana sharri baruwan mu mukan, Rahar su suka taba kafin dawowar baba suka zauna domin neman mafita "ai ni Yaya inada mafita don gobe su liman zasuzo mu Amshi kayan Aure shi yaje can yakai ma zainabu wa innan duk mun yafe,   "Mamuda kana Abu kamar mace wallahi nidai ismail zanbawa Aure "to mu zuba muga uban ya' Sallamar MA ce ta tsayar dasu ya shigo cikin haiba sanye da kakin nashi green kanshi ba hula yayi matukar fitowa kayan na mugun Amsar shi, Suka gaisa mama ta kawo wata kujera ya zauna, baban zango yace "Saude karo mana kosan idan akwai da kokon, ta ce to ta shiga kitchen tareda hado wa kan tray cikin jug mai kyau ta dakko kular kosan hade da cup da kuma robar sugar ta Ajiye musu tareda komawa daki, Domin basu wuri su tattauna, Baban Zango ya ce "suriki na bismillah ga Abin karya wa ko bazaka iya cin Abincin mu ba,? "Noo baba ai inason gargajiya sosai ya dauki karamin kofi ya tsiyaya kokon tareda Sa sugar kadan domin ciwon shi, Yasaki jiki dasu sosai yanasha yana zuba musu hira har baba dake d'ari d'ari yasaki jiki baban zango daman shi akwai son shafta, saida yaci sosai don kosan Yamai dad'i yayi hamdala daman dokin ganin Yasmin bai Sa ya tsaya karya waba daga office kawai ya gudo, gashi baiji ko motsinta ba Anya ma tana gidan,?   "Toh muhammadu kake ko? Inji baban Zango yace "Alhmdulillah naji dadin da kakeson jinin mu kuma Kayi mutunci daka zo kai tsaye ka same mu kuma indai nine mad'aurin Auren mama na to nabaka gobe muna jiran zuwan manya, Saidai kuma wani hanzari ba gudu ba kasan da zancen Aurenta da Dan uwanta to yanzu dai yasamu wata kaga iyaye mata muke jira yanzu sukai akwati in Allah yakai mu jibi a daura Aure, Toh yanzu dai naku maganar Auren sai manyanka sunzo sai muga kamar wata nawa zamu sa, yayi saurin kallon baban dake magana "A gaskiya inaso a daura da namu jibin ni basai kun tsaya wani shi shiri ba tunda dama a shirye kuke da Auren don haka don Allah Karku daga a barshi a hakan, Baba kallon shi kawai yakeyi y'anda ya ke rokon a daura mai Aure jibi sai kace y'ar tsana ko kuma mara Gata, Baban zango yace "ka bar magana sai su manyanka sunzo wannan tsakanin mune zamu tsara komai, Shiru kawai baba yayi yana ganin zamani agabansu yaro yazo yana zaben ranar Auren shi, MA shiru kawai yayi bai gamsu da wani zancen daga Aure ba, don bazai haifarda da Mai idoba don gaskiya hakurin shi yakai bango,   Kamar a mafarki Yasmin take jiyo maganar shi atsakar gidan tareda kamshin shi mai rikitarwa duk da haryanzu katifar ta na kamshin jikinshi Amma Wanda takeji tasan fresh ne, ta zabura tareda lekawa ta window shine da gaske tana mam akin y'anda ya zage sai hira sukeyi kamar sundade da sanin juna gashi harda kofin koko a gaban shi lallai MA baida ta I do, Kamar yasan tana kallon shi yakalli dai dai window sukayi ido biyu ya kashe mata ido tareda bata wani shegen murmushi, tayi saurin sakin labulen ta koma tana dafe kirji kawai tagama sallama wa MA,   Wayar shi ya danna ya tura mata sako _"kifito ko intashi inshigo kinsan zan iya_ Ai ba wasting time ta sako guntun hijabi akan kayan doguwar rigar dake jikinta kana kallon ta kasan bacci ta tashi, Tafito kamar mara gaskiya ta gaida su baba batareda ta kalleshi ba baban Zango yace "Aa mama na dama kina ciki a she? "Eh baba bacci nakeyi, "to y'ar Albarka kwashe kayan nan ki shiga dasu mungama,   Tunda ta fito ya zarga mata na mujiya tareda yin Ajiyar zuciya yana jin wani irin nishadi Allah yasa su baba su yarda su mallaka mai wannan halitta ko zai samu natsuwa shidai gaskiya ya mutu kan kaunar Yasmin,   Kasa fitowa tayi daga kitchen din tarasa Abinyi idanun shi sunyi mata kaifi sosai, jin yana musu sallama yasa tayi Ajiyar zuciya tareda hamdala, Saidai yana fita ya dsnna mata Kira ta daga ba bata lokaci yace "ki fito inganki ina waje, Zuru tayi Rashin mafita yasa ta fito sum sum ta fice, a jikin motar shi ya dogare tareda zubawa kofar gidan ido, Tsayawa tayi daga nesa ta kasa cewa komai, "good morning madam Muhammad Abdullah, murmushi tayi mai kayatar wa kafin ta Gaishe shi yace ki motso ko inzo indauke ki, Karasowa tayi cikin takunta mai ban sha awa "wow masha Allah yafada yana kallon ta kamar ya rungumota yakeji, "Baby Hajiya tayi farin ciki sosai da maganar Auren nan Hajiya ta na sonki sosai, "Nima ina kaunar ta sosai tunfarko ta nuna tana kaunata don haka Nima dole insota, wani irin dad'i yaji har cikin zuciyar shi yace hmm "Maison Uwa ya so d'an ta, Kallon shi tayi kafin tace "ai dole ne kodan Alharkar Uwa a so d'an, zaro ido yayi "yanzu ke bakya sona sai don Albarkar Hajiya? "Ina sonk... Tayi saurin rufe bakinta ya yi dariya sosai "no need baby nasani kina sona ko baki fada ba and I love you too much baby, Kisa baki a mana Aure jibi kar in baki ciki a gida don nakusa aika aika Wallahi, Wai meyasa bakajin kunya ne? "Wane yarene kunya kuma? Ya fada tareda rike kuma tunshi tace nidai banajin wannan yaren,   Isowar Aunty maryam tareda mijin ta yasa Yasmin ta shige gida da gudu cike da kunya tabar shi, Ahmad na fitowa ya Sara ma ogan shi cikin girma mawa, "Oga a she nan kazo? "Eh ina nan baby ta hana ni zuwa aiki, dariya kawai Ahmad yayi domin shikan shi baisan komai ba saida maryam tafada mai jiya, bayan baba ya kirata ya wanke ta tas, Gaida maryam yayi cikin bata girma $Sannu Auntyn mu kunya ta rufeta domin tunda take bata taba haduwa da ogan mijin nata face to face ba sai yau, Lallai dole mata surika rububin shi gashi duk iskancin da suke fada nashi yau yadawo yana son kanwar ta,   Shigewa tayi tabarsu rike da y'ar ta a hannu da sallama ta shiga cike kuma da farin ciki domin tunda tabar gidan bata kuma zuwa ba saboda baba sai yau da rikicin na Yasmin ya taso,   Dakin maman ta tashiga cikeda farin ciki mama ma tayi murnar ganin ta ta karbi NANA Aisha "mama ina d'an rigimar ki ko baya damun ki? "Aa ba ruwan shi sunfita da malam yanzu,   Bayan ta natsa sungama d'an zantawa da mama sannan ta mike domin samun Yasmin, Tana shiga dakin ta ce "toh kingama gudun munafuka? Wallahi Yasmin kin gama binne ni da raina a ce muna tare dake ki kasa fada min komai kinja baba ya warwareni jiya Banji ba bangani ba? Dariya kawai tayi tasan ba gaskiya, zama tayi gefen ta domin jin labari, "yaushe aka kulla? Ina BARIKI Bansani ba wai yaushe kukayi wannan sabon Yasmin?   "Gaskiya kin shammace ni ace muna tare ko Alama bangani ba ina tsine mai da kikeyi? Yaushe kema Yama zuciyar ki Gini? "Kai Aunty wa innan tanbayoyi haka,?   "Dole kice tanbayoyi bayan kin gama min boyo Ashe shiyasa ya so ya kulle min miji lokacin da kuke soyayya da Oga umar Ashe kishine yasa yake ma baban Auwal warning oh kice ba abanza ba umar ya fita hanyar ki Oga na ciki,   "Hmm Yasmin to be sincere nayi farin ciki sosai wallahi ki daina maganar mata mafi yawan maza yanzu suna bin matan waje Wanda ya bayyana nashi ne kawai ake gani, bare Oga MA kowa yasan mafi yawan su suke kawo kansu, "Yasmin koda yana bi ke zaki gyara Abinki, nayi farin ciki A ce kanwata zata Auri Oga MA da ko wace mace ke burin samu, naji Wai har zaki fara murza sitiyari,? Dariya Yasmin tayi kuma sai bataji dadin boyewa y'ar uwarta ta datayi ba tun farko gashi yanzu taji farin ciki. "Aunty kiyi hakuri Wallahi ni kunya naji bayan na gama zagin shi kuma infito infada miki Wai muna soyayya kuma gaskiya da farko banaso...... Ta bata labarin komai maryam ta rike baki lallai kin ciri tuta saboda ke zai fita layin gauro, saidai Yaya ismail fa ta ake ciki? Nan ma ta mata bayani sun dade suna hira a tsakanin su saida baban Auwal yashigo suka gaisa da mama ya fara sarawa Yasmin cikin tsokana,   "Toh kanwata haka labari ya juya lallai kin zama Babba dole mubiki mu dangwali arziki dariya sukasa gaba daya, maryam ta kawo musu tsarabar dawowar mijinta harda Yasmin bayan ta bata tace "ai ke mezakiyi da kaya masu Arha bayan kina Matar Oga to be,   Sun wuni cikin farin ciki kafin ta tafi ranar Oga MA bai samu kanshi ba har dare sosai kafin ya kirata a waya, Zuby kuwa iya naci tayi Amma bataga ko keyar shiba koda ta tashi ranar har ya shirya ya fuce bakin Aikin shi, amma tana nan don jaraba,   Washe gari gidan mama ya fara cika da mutane domin bikin ismail da Zainab don baban Zango ya buda mai wuta sosai dole ya hakura da zancen Yasmin badon yasoba, Kuma a yaune Zasu tarbi bakin MA Wato iyayen shi masu nema mai Aure, Aunty maryam tazo da wuri suka shirya musu kayan tarba su snack tareda kaji dakwala tarbar girma dai suka shirya,   Karfe goma baki suka iso falon baba aka bude musu ta waje Wanda dama don baki ya tanade shi yau angyare tas yana kamshi,   Mayan mutane ne kana ganin irin motocin da suka shigo Unguwar kasan MA ya gaji Arziki gaba da baya, baban Zango da baba da Abokin mahaifin su limamin Zango dattijon Arziki suka tarbesu cikin girma, Maryam ta shigo musu da kayan motsa baki cikin harkar girma kuma sun yaba da inda MA yazo neman Aure, sungabatar da kayan nema irin su giro sweet katan katan dasu biscuit da dai sauran kaya hade da dubu d'ari na gaisuwar iyaye,   Baba liman yace ina Abin yayi yawa kudin gaisuwa ai ba sadaqi bane, sukace Sam Abarshi haka bama haka yaron ya so ba kawai sun ragene don Albarkar Aure kawai suke nema ba riya ba,   Baban Zango yace to Allah yasa Albarka, suka nemi Alfarmar daurin Aure a gobe inyaso tarewa a jira lokacin da duk suka shirya,   Baba baiso hakan ba Amma baida ta cewa don kanin shi tuni ya Aminci da zancen tareda baba liman suka sa Albarka a nan take suka ajiye dubu d'ari biyar na sadaki,   Suka rabu cikin mutunci tareda farin ciki..... Kyawon Alkawari cikawa shiyasa nayi muku amma da ba haka ba   Kudai biyoni zuwa jibi my fans‍♀️ *Matar soja* [8/30, 2:56 PM] Feenerh Wrtr: PROFICIENT WRITERS ASSOCIATION тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   _written by FENERH_ Maman Ammar *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby *Wannan nakine my Aunty Hajiya Sa'adatu Allah yaraya mana Ummu kulthum ya Albarkaji Rayuwarta Heart you wlh irin so na jini*   33&34   Fadin farin cikin MA bata bakine don da labarin za a daura mai Aure gobe yazo yana office kanin baban shi ya Kira ya shaida mai, sujada yayi tareda godiya ga ubangiji yanzu gobe za a daura Mai Aure da Yasmin? Alhmdulillah yake ta mai mai tawa,     Inter come ya danna tareda kiran Ahmed yana shigowa kafin duk ya saramai yayi saurin rungume shi kam tareda cemai "nagode Ahmad sanadin ka nasamu farin cikin Rayuwa, ya sakeshi tareda riko hannun shi,   "Karka damu zankula da Yasmin bazan taba wulakanta ta ba ina son ta sosai Ahmad sorry for not comfesing my love earlier to you wallahi komai ya faru a lokacin da nikaina ban shirya ba, "oh my god ya fada tareda dafe kanshi cikin so much excitement "gobe zata zama tawa zan mallake ta zata zama mallaki na karkashin iko na, she is going to be my queen my princess,   Mamaki ya cika Ahmad sosai don shi bai taba tunanin MA zai taba son wata ya' mace ba saigashi yau yanayi wa Yasmin so mai zafi da har zaka iya gani a idanun shi,   Ranar yaranshi sunsha kyauta don saida ya rabawa duk Wanda ke office din dubu Ashirin Ashirin Ahmad kuwa transfer kawai Yamai na one million yace ya Kara Yama iyali hidima,   Arziki kashi ta sanadin Matar Auren shi yasamu ci gaba lallai dole yakara rike maryam gam domin ita din Alkhairi ce a rayuwar shi,   Ranar barin office kawai yayi ya nufi gidan Hajiya, itama taga sambatu ranar Wanda ita tafi kowa farin ciki, "baba na kana son Yasmin sosai na ga Alama duk ka firgice haka, saidai magana daya bazata tare ba gobe sai An shirya,   Tuni ya gimtse fuska "haba wane irin shiri kuma? Mu kammu muna bukatar lokaci a hado mata lefe kamar kowace mace y'ar Gata karka manta yayyinka mata sunci burin Aurenka jiya nakirasu duk nafada musu, Halima zataje Dubai dama nace zanyi mata transfer ta hado mana lefe a can,   Ajiyar zuciya kawai yayi duk da baiso haka ba Amma Shima zaiso a san zaiyi Aure dole a shirya grand wedding Duk da yaso su tare goben Amma no problem andai daura ai tazama tashi to ai ba damuwa,   Yasmin dai Abin yazo mata a bazata Auren ta da MA gobe? Kutumar uba lallai ta kade har buzunta, duk da tana son shi Amma bata shirya Auren shi ba yanzu taso sai ta gyara kayanta kafin ta shiga don tasan akwai matsala da Y'an matan shi musamman zuby,   Tana cikin tunani ya kirata ta kalli wayar takasa dauka domin jikinta yayi mugun sanyi saida ya Kira kusan Sau uku kafin ta yi karfin halin dauka,   "Hmm AMARYA ta yanga ake mun? Kibari har a daura gobe kinga bakin ma sai nasiya zaki bude kimun magana, "Wai baby gobe za abani ke baki daya zaki zama tawa komai naki zai zama mallaki na "wallahi daga gobe duk Abinda nace ina so kiyi kawai Inba haka ba kisha tsinuwar mala iku,   Ai tasani kuma sai y'anda Allah yayi da ita yanzu tunda za adaura musu Aure da sarkin naci, Saidai baby Wai bazamu tare ba sai an gama shiri hmm zaki tare da tsohon ciki kuwa baby don wallahi ki shirya bazan y'arda ba gobe I must loose my virginity on you,   "Ko ba virginity ba shine zai wani Kira kanshi virgin bayan ya gama lalibe Y'an mata, wani daci taji a zuciyar ta data tuna da kalubalen da ke jiranta, "Baby yakirata domin yaji tayi shiru, ta Amsa a hankali ya ce "yau inaso inzo Amma bazan samu zuwa ba saboda shirin daurin Aure akwai a lot of things da zanyi dole zanyi inviting a bokai na da kuma my god father, the you no burutai na sona like his son Nima I respect him like my on father, Saidai muntare you will no a lot about me, ya katse kiran badon yagama fadar duk Abinda yakeso ba,   Jikinta yayi mugun sanyi sosai, wayarta ta dauka ta kira Amira nan take fada mata komai, Ai wani ihu da tayi saida Yasmin ta to she kunne "Meye haka saikace wata yarinya, "wallahi Yasmin nayi farin ciki Oga Muhammad zaki Aura? Kinsan waye shi kuwa wane mataki ya taka? Mazajen mu duk a karkashin shi suke fa shine shugaban battalion guda, kwanan nan suka dawo daga kasar waje kinsan irin kudin da mazajen mu suka kwaso kuwa? Bare shi Oga kwata kwata, Yasmin kin haye wallahi kin more,   Amira kenan bakya tausayamin da Y'an matan shi? Sunci kutumar ubansu kece Matar gida wallahi kishiga ki shinfida iko duk tsinanniyar da ta tako ki hada ta da kuratan sojojin kofar gidan shi sumiki waje da ita, Dariya Yasmin tayi sosai jin Amira ta zage sai d'ura musu zaki take "ke jirani ma gani nan zuwa dole inzo Ayi dani wannan Abin arziki ai dole inshigo daga ciki Nima ko nasamu nawa, *************** Kafin shabiyu gida yayi makil da mutanen zango Y'an Uwa ne makil kana gani kaga yan dangi Mama hindatu maman ismail dai tace ita tazo domin y'ar ta don tana zuwa ta kulle daki ta fara dirka mata kayan harka tareda dilke ta da wata irin dilka irin tasu ta gargajiya mai hadi da lallae, Aunty maryam itama tace ina sai anyi mata ganin. nan da nan yasmin takara ja ga Amira ma itama tuni ta baje tace dole ayi da ita,   Sunkulle kansu sai hira sukeyi manya nata Dora tukwanen miya da girke girken daurin Aure gobe, Mama kuwa ai batada natsuwa Auren Yasmin gobe ga NA ismail duk da yayi fushi dasu sosai ko gidan yaki y'ar da ya shigo,   Biki fa ya kankama gefen MA oda kawai suka bada a wani lafiyayyan hotel na Abincin daurin Aure Ahmad yaron Oga kai yayi zafi, kowa mamaki yakeyi Wai Oga MA zaiyi Aure har cikin barikin sunji Abin a bazata,   Duk da daurin Aure kawai za ayi gobe event sai Anshirya Amma kudi ake kashewa Abinki da masu Abun tunda kudi ke komai don haka a wuni guda komai An kammala,   Bai samu kanshi ba sai karfe goma ya shigo gidan shi, zuby ya tarar tayi kuka har taba uku lada tana zaune a falon ga Emanuel agefen ta yana matsar ido tareda bata hakuri,   Wani irin tsawa ya buga mai ya tashi da gudu ya bar falon ta taso idanun ta sun kunbura saboda kuka, Zama yayi tareda Dora kafa daya kan daya ya yi mata wani irin mugun kallo tareda shirya Rashin mutunci, "Lafiya kike mun kuka a gida? "Abinda zaka mun kenan MA yanzu wata zaka Aura kabarni? Don Allah me na Gaza yimaka dazaka yimun irin wannan wulakanci bayan ka gama lalata min Rayuwa,   "Kin gama? Ya tanbayeta, tayi shiru "let go ya fada tareda nufar dakin shi ta biyo shi jiki na rawa ta, tube rigar jikin shi yayi tareda wandon ya rage daga shi sai boxer yace full your cloth, ba bata lokaci jiki na rawa ta fara cire matsatsun kayan jikinta, Saida ta cire har pant ta Yar ya kalli kirjin ta da kyau da suka rankwafa bakyan gani tareda sauke idanun shi ta kasanta yace ki kwanta ina son ganinki da kyau ne yau, Shegiya tuni ta baje mai kafafu ya kalla tareda watsa mata mugun kallo yana daga tsayen get up 'ya bata umarni ta mike don mugun tsoronshi takeyi, Kayanta ya jefa mata yace ta mayar. Tayi saurin nufarshi ya dakatar da ita ki sa kayanki nace, Mayarwa tayi ya zauna tareda fara magana' kifadamin who is your first man? Waye kika farawa budewa kafafun ki? Tafara in ina "kamar ya? "Waye yafara bude ki? Nifa bangane KO me kake nufi ba, "ok bari inyi miki dalla dalla,   "Kinsan ke ba virgin bace? Sannan nasan duk mazan da kikebi, kinsan dalilin da yasa ban taba ratsaki ba? Banason kazanta bazan taba cin gonarda wani yayi no ma ba look at your chest kamar na tsohuwa zuby in Aureki ince na Auri wa? Da farko na dauka kinada kamun kai but am mistaken nasan duk Rayuwar da kikayi a UK ya janyo wayar shi tareda bude mata pics harma da nude video dinta da maza, "I no you in and out, so bazan koreki ba if you like stay Matar gidan nan idan tazo zakuyi dai dai ita ba karuwa bace kamar ke Amma inkina takamar rawar kaine kinsanta Zaku hadu,   Goge fuskar ta tayi tareda kallon shi cikeda takaici, "naji MA yau nice karuwa saboda wata can "aaaaaaa karkice wata Matar so na Matar kwarai Matar da zan Aura gobe, "Zatazo tasamu sauran mata domin ni nasan koda baka taba sex dani ba kasan Wasu matan don dariya kawai yayi, "eh kece bazan hada jiki dake ba saboda ke shaddar kasuwa ce, "Ya isa MA zantafi Amma kasani ina sonka rabuwa dakai bazan taba yiba kome zaka kirani ka kira I don't care, ta fita fuu, Dariya yayi sosai "zaki hadu da my mata kidawo y'ar iska, ya tashi tareda fadawa bathroom yayi wanka tareda kwanciya ya janyo waya don kiran Yasmin yajita akashe, Yazata kashe mai waya bayan tundazu baiji taba, kasa bacci yayi ya mike tareda jero nafil fili da Addu o i na neman Albarkar Auren shi, Yasmin dai ranar gidan wata makociyar su suka kwana kawar Aunty maryam ce tareda Y'an Uwan su Y'an mata dasukazo daga zango hira suka kwana yi ana raha kana ganin su kasan sun waye domin matan zango badai ilimi ba da wayewa, shiyasa ta kashe wayarta don kar ya hanata hira da Y'an uwanta, Maryam ma dole Oga Ahmad ya barta kwana Amira dai tace sai da safe zata dawo, Gefen Hajiyar MA kuwa gida ya cika da nasu dangi ka yayyin shi da yaransu Y'an mata makil kowa na murnar Auren Muhammed, **************** Da safe ya aiko Ahmed da katuwar akwatin kayan da Yasmin zata saka na ranar Aunty maryam yakira ta shiga dashi gidan da suke suka bude Kala shida ne Y'an ubansu kayane da kana gani kasan dukiya ta koka English wax da kuma Holland sai tsadaddun code less da kuma dry less takalma deziners da pos dinsu Kala shida suma, Sai ihu Y'an mata ke zubawa suna wannan angon d'an gaske ne gaskiya kowacce naso ta gan shi,   Mai gyara suka kira tazo ta mata gyaran kai ta zuba mata make up atanfa tafara sakawa aka mata dauri da dankwalin ga dinkunan kamar Angwada ta, Maryam tace ni nabada measurements dinki jiyafa Ashe kayan na yaune, tab kudi kare zance dubi har an dinko, Fadar kyan datayi bata bakine Abinki da asalin kyau, Y'an mata suka fara rangada guda Amira ta iso itama aka farayi da ita, Ango kuwa yau ba a magana tun safe ya wuce malali a gida ya shirya cikin babbar Riga gezner fara kal taji dinkin sarauta kamar wani sarki ya Dora hula ga bakin takalmi ga Agogon Gucci mai tsada Abinka da fari har wani daukar ido yakeyi ya fito yayyin shi suka fara yimai tsiya "gaskiya Amaryar nan tayi sa ar miji irin wannan sankacecen namiji haka, Dariya yayi sosai yace Hajiya kifada musu itama kyakkyawa ce nine nayi dace "barsu baba ai basuganta bane da Zasu sani, *************** Karfe biyu Al Umma suka shaida daurin Auren Fatima da Muhammad sai kuma ismail da zainab a babban masallacin sultan bello dake tsakiyar Kaduna,   Tarone da ya tara manya a ciki harda gwamna mai ci ga sarkin zazzau da ya wakilci uban gidan nashi Wato burutai da baisamu zuwa ba dole su baban zango suka kauce mai martaba ya bada Auren yasmin ga kanin baban shi,   Manya fa sun hallara gaba daya sojoji sunyi wa wurin zobe kowa yasan wani kusa ne ke Aure yau y'anda aka datse titin ta ko ina, Inkaga bakin Ango abin ba a magana ismail dai ba yabo ba fallasa don yasan yasmin tamai nisa sai ma dayaga convoy na sojoji yasan ai ta wuce da tsarin shi harma da ajin shi dole ya baje ya bawa Ango hannu don yashafi ta baraki, Sai rabon kudi manya keyi a wurin Shima Ango na barar wa maroka har saida baban zango yaja kanin baban shi gefe yace suyi mai magana karya karar da kudin shi don maroka basuda hankali, Dariya kawai yayi mutumin yace kabarshi malam mamuda ai yatara kuma farin ciki yakeyi,   Baba madai yau farin cikin shi a bayyane yake sai gaisawa yakeyi da mutane a yau yasan matsayin da y'ar shi ta taka don ganin irin manyan da sukazo kawai yasa yaji jikin shi yayi mugun sanyi yayi nadamar jayayyar da yayi akan Auren maryam don yau Auren ta ya kulla Alkhairi Babba, Nan ya Kara godewa Allah da ya bashi ya'ya biyu rak masu Albarka,   MA fadawa mota kawai yayi yabada umarnin akaishi wurin Matar tashi Ahmad yayi dariya "Oga ai bazaka samu ganin taba ko dazu gidan ba sauki bare Yanzu, Muje dai ya fada yana dokin ganin Yasmin a matsayin Matar shi yau, farin cikin dake fuskar shi baya faduwa, Kofar gidan ma makil yake da mutane kowa saida yazubawa convoy din idanu ganin irin motocin da suka jero ga hilux cike da sojoji bai fitoba yace "Ahmad ka kiramin ita har yanzu wayar ta a kashe take, Maryam yakira yace don Allah sufito da AMARYA suna waje da Angon, ta fada musu tuni suka fara canja mata kaya zuwa wani code less sky blue yana daukar ido kamar readymade suka murza mata head tareda wankan turare harda su humra masu kamshi tayi kyau fiyeda farkon ta saka takalmi golden da pos dinshi irin na Amare rigar saida ta d'an rike saboda saukar da tayi,   Y'an matan suka fitowa baki daya kowacce ta dauki Ado maryam ma ta y'arda NANA wurin mama hindatu tuni ta murzawa baban Auwal ado mai daukar hankali,   Fitowar su yasa gaba daya kallo ya koma kansu ya tuni masu hotuna suka fara daukar AMARYA da kawayenta, Oga MA kuwa yana cikin motar mai tinted ya hango fitowar ta tuni ya sauke glass din ta hanyar danna wani Abu a jikin motar, ya zuba mata ido kamar ya Ruga ya sungumota yakeji yanzu Matar shi ce wannan wow" Alhmdulillah ya furta ganin masu hoto sun hanashi ganin ta ya bude motar tareda jefo kafar shi waje cikin isa yatako tareda matsowa kusa dasu, Y'an mata tuni sun zuba mai ido suna kasha Allah Amira ma yau taga Oga MA ido da ido ba lbr ba, Yasmin kuwa saida kirjinta ya buga ganin y'anda yakara kyau ga kwarjini wani kishi taji ganin Y'an mata suna kallon mata miji,   Yana matsowa ya rungume ta tareda dukawa kadan ya daga ta, tuni sukasa shewa tareda ihu irin na Y'an mata, ya yi saurin sauke ta ya rike hannun ta batareda ya damu ba yace muje, Maryam yau taga Rashin kunya agabanta ko a jikinshi ta ja mijinta sukabar wurin shi kuwa ko a kwalar rigar shi Masu hoto kuwa ai sai kashe Kala Y'an mata sai Adduar samun danshin yasmin sukeyi,   Motar ya bude mata tashiga Shima ya zagaya ya shige, ........... ️   ‍♀️‍♀️‍♀️‍♀️‍♀️ Aisha dahiru banda leke ta glass ba Abinda zaki gani   *Matar Soja* [8/31, 8:53 PM] Asli Smasher : PROFICIENT WRITERS ASSOCIATION тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   _written by FENERH_ Maman Ammar *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby 35&36 Suna shiga ciki ya ma driver a lamar su tafi kawai, ta waro idanun ta waje cike da tsoro "ina zamu tafi? Shiru kawai yayi mata tareda sanya wayar shida ke ringing a kunne, "Yaya Halima ki budemin side dina ta back yard ina zuwa yanzu, "Wane irin bude side Baban Hajiya Baki na jiranka kazo direct cikin gida "su waye suke jirana? Y'an Uwa mana kana tanbayata, Yaya kice musu ankirani aiki please zanzo da my wife don't tell Hajiya please,   "Wace Matar ta fada da sauri tana barin cikin mutane tareda nufar side din nashi dake gidan, baban Hajiya kanada hankali kuwa? Ka bari ta tare yanzu daga daura Aure yau ka dakko musu ya' me zaka yi mata,? "Bari dai in iso zakiga me zanyi nidai find food for me "don Allah ka komar musu da yarinya karka fara yin haka, kit ya kashe kiran, ya zuba mata ido ganin tana juya kai" don Allah ka tsaya karka tafi dani haba wane irin rashin kunya ne haka?   Dage gira daya yayi tareda mata kallon banajin yaren ya mata banza, kiran Ahmed yayi yabashi umarnin su wuce kawai driver ya kaishi gida, Daga NDA suka rabu driver Kawai ya wuce dashi malali, su kuwa su Amira Baki sake sukabi motocin da kallo daga daura Aure yau ya tafi da AMARYA? Lallai wannan Angon akwai aiki,   Aunty maryam suka fadawa tace suyi shiru kawai tasan mezata fada kafin su dawo, Ahmad takira ta tanbayeshi KO BARIKI suka tafi, yace eh amma Oga yayi malali, Ajiyar zuciya tayi tace tom, tasan dole yadawo da ita saidai tana Addu ar Allah yasa yadawo da ita da wuri,   Bai koma kanta ba yana kallon y'anda ta daure fuska tayi kicin kicin da fuska tareda turo bakinta mai kyau yayi murmushi tareda shafa goshin shi,   "Duk wayon AMARYA sai ansha manta ya fada a hankali tajishi sarai, tayi mai dif, suna zuwa Mai gadi ya wawake mai gate driver yashiga da ita, dai dai part din driver ya Ajiye motar,   Yaya Halima ta fito domin ganin da gaske yakeyi KO wasa don tasan ba ataba yiba bare a fara ta kansu, Baki ta saki ganin ya fito tareda zagaya wa dayan side din ya bude mata" fito yace taki motsawa hannu yasa ya janyota tareda dagata cak in a bridal style,   Yaba driver umarnin ya tafi karma a san ya dawo, "Baban Hajiya da gaske dauko ta Kayi da tsakar rana? "Toh sai me ba a shaida bane? Kunya ta mugun rufe Yasmin ganin fuskar y'ar uwarshi dakana gani kasan jinin su daya, don suna mugun Kama ga hasken su daya Ta sunne kanta cikin kirjinshi cike da kunya "please ka Ajiyeni tafada idanun ta na cikowa takasa dago ido, "yi hakuri Fatima nasan balaifin ki bane nasan rashin kunyar baban Hajiya sarai, wallahi ka mayar da ita kafin Inturo maka su Yaya Hauwa su tugeka, "noo my sister nasan ke ce zaki rufamin Asiri please ki ce bandawo ba kawai, Ya wuce ya barta Baki a sake ta dafe kai na boni kar ya illata musu ya' don tana hango yarintaka a tare da ita gashi kuma tsohon tuzuru, Komawarta tayi ciki cike da mamakin halin kanin nata,   Suna shiga tafkeken falon ya sauke ta tareda kulle kofar ya shige ciki Abinshi tareda cire malum malum din ya Ajiye akan kujerar tareda cire links yana wani irin murmushi,   Saida ya rage dagashi sai singlet da rigar shaddar ya dawo kusa da ita' "Baby wannan fushin fa? Dama ta cika tuni tafara zazzaga mai masifa, "Don Allah wane irin Abin kunya ne wannan daga daurin Aure ka dakko ni inkoma gida ince musu me in kallesu da wane ido,   "Alright Ashe kinfa iya masifa? Ok to bazama ki koma ba sai ki huta da jin kunyar basu ganki ba bare kiji kunya, nidai saika mayar dani, "umarni ne ko roko? Ya fada, Matsowa yayi tareda bata hug "ok ya isa kizo ki yi Abinda yakawoki the earlier the better inkin sallame ni in mayarda ke da wuri inkin ki kuma mukwana a nan kinsan KO a rigata,   Kokarin cire hannun shi takeyi a kugunta yaki tareda ture head dinta tareda daga ta cak ya nufi cikin katon bedroom din dake falon mai dauke da tafkeken gado hade da waldrop da komai a hade, Tsakiyar shi ya Ajiye ta kafin ya cire wandon shaddar ya haye, Baya taja da sauri tareda kokarin samai kuka, "don Allah kabari MUHM'D , "lala sunana har yau kike fada? Bari inyi Abinda zaisa ki daina adresing dina da suna na,   Kuka tafara sosai ya tsaya ganin y'anda ta kwabe fuska ga make up din dake fuskar ta ya zubawa red lips dinta ido ganin yanda take sharbe kuka, Dariya yayi sosai "baby Sory nine KO "ka mayarda ni gida mana tom" ok ya isa ya fada tareda matsawa gab da ita ya riko kumatun ta,   "I love you kinsan da haka ko? Ban taba tunanin Aure ba saida na hadu dake yau gashi Alhmdulillah kin zama matata today you are Mrs Muhammad Abdullah for ever insha Allah, Yasmin ina cikin farin cikin da bansan da wa zan yi shearing ba saida ke din da Allah ya bani, I want to spend this moment with my on wife please support me make me more happier, don't be angry zafin soyayyar ki ke sakani yin Abubuwan nan yasmin ina miki sonda bana tunanin wani namiji nama matar shi irin shi ba, Today you are my wife today is the most happiest day in my life, Kallon shi tayi cikin tsan tsar soyayyar shi tareda dora hannun ta a fuskar shi da yayi shave kadan ta shafa ya riko yatsunta da sukasha jan lalle yayi kyau, yayi kissing, "Tell me how you are feeling baby? Sakin jikinta tayi kadan ganin y'anda yake mata confessing soyayyar shi gareta tuni taji she can do anything to make this handsome guy din nata happy as he wish,   Tunawa tayi da hirar su da Aunty maryam jiya darake fada mata yanda zata nunawa mijinta soyayya da tattali, Ki nuna mai kema kin iya kin tanadi saninki a gidan Auranki ne Ki karki rika yimai garda ma ki sakar mai jikin ki y'anda yakeso karkibi Al Ada wallahi ko gobe. Yace yana bukata kibashi mijinki ne, inkin hana kuma kisha tsinuwar mala iku,   Kara sakin jikinta tayi ya kwanta akan laps dinta tareda riko hannun ta ya nufi kasan shi dashi tareda runtse idanun shi domin yanason jin dadin santsin hannun nata a jikin shi,   Taso ta kwace amma ta kyale shi domin bashi kulawar da ya kamata don tanaso ta faranta mai, da kanta takarasa da hannun ta domin tanaji a littafan Hausa y'anda hannun mace ke haukata namiji idan ta taba mai hanyar Abujan shi,   Wata irin y'ar karamar Kara yasaki domin jin laushin hannun ta a tsakiyar shi da y'anda ta Kama mai kamar wata kwararriya, Duk da da boxer a jikinshi yaji touching din har cikin tsakar kanshi saida ya zabura ya yi wurgi da boxer din ya fuskanceta da kyau jikinshi na rawa, "Touch me like that again baby I feel it hold me again am yours you are mine please do it karkiji kunya ba kunya a tsakanin mu, Hannu yasa ya zuge. Mata rigar tareda sauke rigar ta kafadar ta, wani iri yakaraji ganin y'anda milk factory dinta ya bayyana a cikin bra dinta mai kyau kamar net tuni ya kwantar da ita tareda tsugunawa ya janye bra din batareda ya cire hook din ba, "Wow subuhanallah shine ya furta cikin sarkewar miyau ganin yanda suke kallon shi kamar su tsokane mai idanu ya ce "baby sun Kara kyau sun Kara girma baby ina son su sosai,   Hannaye biyu ya dora a but ya fara mitsika su kamar yasamu toy, tuni ya sauka akan layin mtn ya hau glo jin touching din shi takeyi sosai har cikin tsakar kanta tuni ya mantar da ita inda take ta fara mayar mai da martanin wasan don bazata iya kauda kaiba dole ta nema makanta sauki, don mugun romance yake bata tako ina da hannu da kuma bakinshi, Wani irin sheshshekar kuka yakeyi batasan lokacinda ta cafko gidan gwamnatin ba ai tuni ya hau international network yafisge pant din jikinta cikin karfi har saida tasa Kara, Tuni ta dawo hayyacinta ganin y'anda yake kokarin kutsa kanshi takarfi gashi kirar shi tubarkallah ai sai tafara neman ceto,. Ina ya rude kawai hanya yake nema ta karfi ya ware kafar ya na nema Abu ya gagara, "baby open please open yaketa mai maitawa Amma Abu yaki, Yasha wuya iya wuya itama ya wahalar da ita Amma ya gagara haka ya koma gefe yana maida numfashi, kallon ta yayi "baby why you are too tight? Banza tamai ta kife tareda godiya don tasan da ya ratsata yau sai taji jiki kuma da wuya taje gida ba a gane ba, Wani irin zugi kasanta ke mata ga kuma kirjinta dasukasha matsa tanajin yanda suke mata,   Tashi yayi yana hada hanya ya nufi bathroom batareda ya ko maida boxer dinshi ba ta kalli shape dinshi ita kanta tasan ta Auri namijin Zuma ga zaki ga harbi,   Saida ya hada musu ruwa ya fito tareda tsayawa "baby taso muyi wanka, Kara kudun dunewa tayi domin batason ganin shi tsirara ga sanda a tsaye, "Kayi kafito ni basai nayi wanka ba, takowa kawai yayi ya dagota cak ya manne jikinta da nashi da ba kaya tuni ya Kara kunnuwa ya juya da ita, Cikin bath tub din ya Ajiyeta tareda shiga instead of suyi wanka yafara wani irin mugun wasa da kirjinta dayan hannun shi na yawo ta inda yake neman hanya,   Yatsan shi ya tura a hankali yaji hanyar Abude "baby akwai hanya fa kikaki bari inshiga ❓ itadai wani irin zafi taji na shigar yatsan nashi jikinta, tariko hannun shi, "Noo allow me ya fada kasan makoshi, sundade a ruwan yana bata zafafan wasanni kafin ya d'an samu natsuwa yayi musu wanka yana mai Kara lalube Abinda yafiso sunyi mata mugun tsami Amma don jaraba yaki barin su,   Da Alwala suka fito ta gege jikinta da towel tareda tsane kanta da daya yace "bari insa akawo miki hijabi muyi salla ko' Yaya Halima ya kira yace takawo mai hijabi, Dakanta tazo da ta kwankwasa kofar yana budewa ta zabga mai harara tace bani hanya inga y'ar mutane don Allah, "Me zakigani Yaya? Bansani ba nidai kauce, shiga tayi direct har cikin dakin ta sameta kwance ta rufe kanta da abin rufa, don tanajin zuwansu ta shige don mugun kunya takeji,   Yanzu zatace sunyi wani Abu koda basuyiba gaskiya MA yakaita ga karshen kunya, "Fatima' takira sunan ta dariya yasa "Yaya wallahi ba komai ai banyi ba yafada yana turo Baki tareda matsowa kusa da ita "yaya bayan nakasa shiga duk wahalar na, "Innalillahi wallahi bakada kunya baban Hajiya Allah ya shiryeka ni natafi ga kaya nan nakawo mata ta canja cikin lepen da muka fara hadawa a nan, kaja ko fuskar kanwar tawa ma ban gani ba saboda muguwar zalamar ka tunta kuruciya ta zarce ta fada tana mita tayi tafiyar ta, Taji dadin y'anda bai samu ya shigan ba da yakar y'ar mutane kuma tayi farin cikin samun natsatsiyar mata da kanin nata yayi,   Kusa da ita ya matsa yana dariya ai saiki tashi ta tafi, ta tashi tana tura Baki jakar kayan ya janyo ya fito mata da su doguwar rigar shadda ce galila y'ar gaske irin dinkin Mali din nan yaji design da kuma stones dai dai ita yace ya kenan ba iner wears? Pant dinta ta dauka ta mayar ta zura rigar tuni ya kama kanshi don yasan inhar bai fasa kallon taba yau Zasu iya kwana a nan yana lalube ta,   Salla sukayi tare ya bude frij din dake dakin yafito mata da yourghout mai kauri kisha nasan kina bukatar ta ya furta yana daga mata gira,   "Nidai ka maryada ni gida kaga karfe kusan biyar fa, kayan Abincin da yagani ya janyo ya bude kula daya pepper chicken ne yana tururi sai daya yaga tuwon shinkafa ga miyar ugu tayi kyau dauke da namomi yace "wow my Aunty I love you yana son Y'an Uwan nashi kamar yadda suke son shi, "Come and eat ya fada yana mika mata hannu, "na koshi ni kamayar dani gida, "ok zamu kwana a nan kuwa in har bakiciba, Zama tayi dole a gefen shi ya bude musu oya bismillah spoon ta dauka ta bude tuwon daya ta zuba miya a gefe da kanshi ya Dora mata naman kazar a gefe, Ta fara tsakura a hankali tanaci don gaskiya tana mugun jin yunwa saidai tuwo ba Abincin ta bane, naman ta fara ci don ita kamar kura take fagen nama, duk da tanajin kunyar ci a gaban shi saida ta cinye Wanda ya samata, Kallon ta kawai yakeyi cikeda admiration din ta komai nata burgeshi yakeyi "so madam batason tuwo? Hmm ga ni ina so ya kenan? Shiru kawai tayi "ki Kara gashi nan ni banason nama kazar turawa nafison na gargajiya su nake siya a gida na, "Tab zaka fara siyan wa innan kuwa ni inaso tafada batareda tasan maganar zata fitoba, dariya yasanya "ok madam ko sa kikeso dole insiya, "Matar Muhammad Abdullah ai saidai kibawa wani baby, dad'i takeji idan yakira ta da matar shi, Abincin shi yaci sosai kafin ya dauki wayar shi yakira driver yace yazo yamayar da madam dinshi gida,   Dankwalin shaddar ta daura tareda yafa farin gyale akai duk da ba bra bai nuna ba saboda irin kirar kirjinta mai kyau a tsaye suke kamar Zasu cire idon masu kallon su,   Driver na zuwa yakira shi Oga I come, ta mike tareda saka takalmin ta sai pos dinta data dauka ta fito yana biye da ita har yanzu yana cikin jallabiyar da yayi sallah,   Saida yabawa driver umarni suka fita ya koma yana murmushi baiki ace yau zata tare ba, saida ya koma daki ya shirya cikin sabuwar shadda sky blue sabuwa dal fited yayi kyau sosai, Ya baza kamshi kafin ya nufi cikin gidan a falon Har zuwa tsakar gidan dauke yake da mutane kasan cewar gini ne mai girma mata sai guda suke mai Ango sai yanzu? Yanata famar blushing kamar maijin kunya da gaske bayan yanzu ya gama lalube Amaryar, sai tsiya ake mai ya shige inda yakejin muryar yan Uwan shi, Babbar yayar su Hauwa tafara magana "Amma baban Hajiya wallahi Allah ya shiryeka sai nemanka ake tuntuni kaki kazo miss call nawa nayi maka Halima ma takiraka, SALMA ma takiraka shiru, Shiru Aunty Halima tayi don tasan komai ya kalleta yayi dariya, "Aunty Hauwa ki tanbayi Yaya Halima tasan ina gidan nan,   Wani kallo take watsa mai "au haka zamuyi ni narufa maka Asiri ni zaka tona min? Dariya ya kyalkyale da ita tareda zama kusa da ita ya rungumeta Sory my Yaya " ba wani ni karka goga min iskanci badai niba akwai wata rana ai,   "Kudai kuka sani har yanzu kuka hadu sai kuntaba kuyi fada ku shirya, "Yaya kiji fa me yake fada Wai nasan yana nan kinsan me yayi? "Tsaya Yaya yafada "nazo da matata ne kawai fa to shine me, ? "Idanu suka zaro "wace Matar? suka hada Baki ita da SALMA, "Kuna tanbayar shi ne toh bari ni infada muku nan tabasu labarin komai yana dariyar yanda suketa famar jinjina Abin, yace " Saikace nayi wani Abu? Fitowar Hajiya ya sa sukayi shiru tace meke faruwa kuka samin Auta gaba? "Ai Hajiya gaki ga Autanki nan munbar miki,   Abinka da Y'an Uwa wayayyu tuni suka bunne a tsakanin su, a cikin Y'an uwanshi ya karasa hirar shi har zuwa magrib shi baida Abokai sai na wurin aiki kawai,   Gidan shi ya wuce bayan sungama shirya yanda Zasu hada komai yakamata **************** Driver na sauke Yasmin ya fito tareda bude mata tafito cikin kunya gidan makotan da suka kwana ta koma tayi sa a duk suna ciki har Amira, Ihu suka samata tareda tsokanar ta "Ya naga tafiyarki dai dai?, lallai salihine angon nan tunda ya dauki zankadediyar AMARYA kamarki yadawo dake kuma garau lallai mun jinjina mai, Amira tace "kai kutsaya ina kayan dakikaje dasu? Hannun ta takai saman kanta taji da d'an shi tasa ihun tsokana, "kai kuce ansha love Abin harda wanka, Ganin idan ta tsaya kunya zasuyita mata tsiya yasa ta baje tareda basu Amsa" toh sa idawa ina ruwanku Dan nayi niyya nadawo ma Zaku wani samun hakwara da gayyar miyau kuna batamin rai yanzu zankira shi yazo mukoma,   Shewa sukasa harda tafawar su, Amira tace "ai ni zanma rakaki wallahi dasafe nazo da gudun mawar ruwan zafi,   Shigowar Aunty maryam tace "oh yau ina ganin Rayuwa sai yanzu yasmin har nagaji da karya, kizo mushiga mama hindatu sai nemanki takeyi za ayi miki dilka kuma,   Zaro idanu tayi jin za a gurji jikinta bayan Wanda jikin yasha matsa duk yamata tsami ga kirjinta ma zafi yake mata tana jin yanda niple dinta ke mata zuki, Haka batada zabi sukaje ana gurzarta tana matse ido, sai karfe tara tayi wanka tareda yin sallar da ake binta gidan yarage Baki ne kawai najiki kowa ya koma gidan shi daga ita sai cousin's dinta da suka baje suna cin Abinci, wayar ta tayi Kara tasan waye don haka ta haye katifa tareda ce musu, "Surutun ku yayi yawa kuyi shiru zanyi waya da mijina, "toh masu miji munji adaibi a hankali wannan miji naki sai ya hade ki har baya gashi gabjeje ga muscles kamar d'an danbe ai kin boni yasmin,   Picking tayi tareda yin sallama, ya yi dariya kadan "madam MA ya ne? "Lfy saidai kasa inajin zafi sosai ya fada cikin shagwaba kuma a hankali don ko wa inda ke dakin basajin me take fada, Koni Banji komai ba Aisha dahiru mai kunnen jin gulma ta fadamin   "Meke miki zafi? Yafada cikin jin nishadi yau tasaki jiki har tana fadamai damuwar ta, "kirjina mana da kuma... Dariya yayi sosai kafin yashafa kai yanajin dadin moment din "Baby ai banyi komai ba Amma don worry nayi searching yanda zanyi gobe inshiga a internet don haka get ready, Zaro ido tayi "aa nidai da zafi ga kirjina suna zugi sunyi ja fa nidai aa kabarni ko na tare karka mun don Allah you are too huge, Dariya yayi sosai tab baby ai ko dazu don bansamu hanya bane shiyasa nabarki if not ba Wanda zai hanani ninkaya, "Wai bakajin kunya ne? "Aa ba a haifeni ba lokacin da akayi kunya, Bari inkira ki video call inga breast din yanda suke zafi, "Aa nidai akwai ma mutane, katse wa yayi saida yakira ta dauka yace tell them to leave you Alone, "cikin salon tsokana tace "Mijina nason privacy don haka kubamu wuri, ai ca suka yi mata shikuwa yajita dakyau yaji wani irin dad'i yau tana kiranshi mijinta,   Saida ta juya musa wayar ya ce kuyi hakuri zata nunamin Abune kunga bazata iya agabanku ba kunga kayana ne nikadai ban yarda wani ya kalla ba, Sum sum suka fice a dakin don MA ya girmi tunanin su. Dole su gudu yace oya fool your shirt ingani, Da gangan ta kwabe tareda haska maisu da kyau, ya zuba musu ido ji yake kamar ya cabko su yace "oh my god baby wallahi kindaga min hankali gaskiya dole inzo intaba su yanzu if not I can sleep "please karka zo don Allah nidai kabari karfe kusan goma fa....... ️   *Matar Soja* [9/2, 8:45 PM] Asli Smasher : PROFICIENT WRITERS ASSOCIATION тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   _written by FENERH_ Maman Ammar *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby   *Domin ku takwarorin juna AISHA Dahiru Allah ya baki lfy ya kuma Kara tsaremin ke da duk kan musulmi daga duk kan kaddara, Tareda ke my sis AISHA Alto marubuciya mai yayi ina kaunar ki fisabilillahi kaunarki agareni ta musamman ce Allah yakara mana d'an kon kauna* 37&38 Cikin minti talatin ya iso ya kirata a waya, tana kwance tana Addu ar Allah yasa kar yazo ga Y'an uwanta Sun sata gaba suna tsigeta Wai ta lalace, Ya kira wayar ta tana dagawa yace "come out, Wayar tabi da kallo cike da mamakin halin shi, Hijabi kawai ta dora akan kayan baccin ta fito, Motar ta nufa tareda Adduar kar baba su fito suganta, yana hango ta ya bude murfin motar tana isowa ta tsaya ta waje, "please me yasa kazo, "come on kishigo ko infito ni,   Shiga tayi tareda rufe kofar ko gama zama batayi ba ya fisgota zuwa jikinshi cikin sauri ya fisge hijabin tareda daga rigar ta dama bata saka bra ba tabarsu susha iska akan matsa da tsotsar da suka sha,   Jin hannun shi akai yasa tayi wata irin Y'ar Kara mar Karar da ta Kara tsuma shi, don ji yayi kamar ta Kara mai tsumi, ita kuwa zafi taji don ba rikon wasa ya musu ba,   Kwantar da ita yayi kan laps dinshi ya kwanto tareda fara Aikin tsotsar Abin son shi tana matse ido don zafi takeji sosai akan niple dinta, tanajin yanda jikin shi ke rawa kamar mazari,   Ga Abu na tokarin ta ta bayanta tasan ko Meye, tanajin yanda take Harbin iska, dakyar ya barta, ya koma jikin kujera yana numfashi, "Please let go our home baby natada wa kaina damuwa wallahi I want to go in kibari muje gidan mu, ssurin tashi tayi tare da mayarda hijabinta tana dafe kirjinta dake mata zugi, Tana hauka ne zata bishi ya kashe ta baiyi ba ma ta sha wuya bare yayi tab ita zataso kar ma su tare da wuri sai nan da wata shida ko shekara,   Riko hannun ta yayi "kinaji na baby? "Eh ni bazanje ba, wani irin kallon ki tausaya min yayi mata, tareda riko hannun ta ya dora a jikin shi, "zafi takemun sosai please,   Cire hannun ta tayi tareda cewa "nidai katafi dare nayi don Allah, "ok kawai ya fada tareda bude mata motar ta fita, yana binta da kallo ko magana baya iya yi shikadai yasan halin da yake ciki,   Saida yasamu y'ar natsuwa yatafi, ita kuwa tana shiga tafada katifar ta domin duk sauran sunyi bacci,   Ranar kasa bacci yayi yasha magani Amma a banza saida yayi daya sanin taba ta dayaje yayi yatadowa kanshi kwadayi a banza, Ganin zai halaka dole ya dauro Alwala ya tada salla, Domin nemawa kanshi sauki, saidai baya kaiwa ko ina take war warewa haka ya kwana juyi cikin wahala, tareda kudirin wallahi dole ma a bashi matar shi da sauri if not yayi aika aika,         Yasmin dai baccin ta tasha hankali kwance, da safe bai kirata ba saida yaje office, lokacin baki duk sun wuce gida yarage daga su sai su baba da mama hindatu don sunce sai ta tare Zasu koma,   Ina labarin Ango ismail ya tare Abin shi tareda kwantar da hankali akan matar shi Zainabu don yariga yasan wutsiyar rakumi tayi nesa da kasa,yasmin tafi karfin shi,   MA kuwa yau da takaici ya dawo daga office domin ana bukatar su a Abuja sunada meeting da shugaban kasa dama sauran manyan sojoji baki daya dake kowane sashe na Nigeria kuma taron zai daukesu kusan sati,   Yana isowa gidan shi ya zauna shiru tareda dafe goshi yasan Akwai damuwa idan har yaje taron nan haka dama Yasmin ta tare ne da da ita zai tafi tunda kowa da hotel din shi daban,   "Ina bazai yuwuba gaskiya ya fada tareda dukan kujera, wayar shi ya dauka ya kirata, Tana dauka yace "ki shirya na je school din naku Wai dole saikinje da kanki don haka zanturo driver yanzu ya kaiki, Ya katse kiran batareda yajira Amsarta ba mikewa yayi cike da jin dadin yasamowa kanshi mafita,   Ita kuwa kasa motsawa tayi don Sam jikinta bai bataba wane irin school karfe biyu yanzu? Saida driver ya iso ya kuma kiranta "kifita driver na waje yana jiranki, Tashi tayi jikinta a sanyaye ta shiga falon su mama tareda fada musu zataje school yanzu " kinfadawa mijinki? Inji mama hindatu, "eh shine ya kirani ma har ya turo driver, "Toh ai saikiyi maza kishirya karki tsayar dashi, tom tace tareda komawa dakinta dama tayi wanka komai bata shafa ba, Ta zauna ta murtsuke jikinta da mayukanta masu kamshi da hadin culaccar ta mai mugun kamshi y'ar saudiya da Aunty maryam ta bata, Cikin kayan da yakawo mata shekaran jiya nafitar biki ta dakko wata Atanfar diamond mai blue da fari Riga da sket tayi mugun kyau ta hada da farin mayafi da farin plat shoe da jaka ta feshe jikinta da turaruka masu taushin kamshi cikin wa inda yakawo mata daga gambiya,   Daurin kanta kuwa ya zauna kana hango sumarta ta kasan yanda take sheki, ta fita tareda sallamar su mama, Tafito as Mrs Muhammad Abdullah a yau kana gani kaga matar manya, Yanda take taku cikin rausaya da natsuwa kadai ya isa ya birkita namiji, Driver da yake sanye da kaki saida ya Sara mata tareda bude mata motar ta shiga ya ja, jin kanta take wani iri yau it ace a matsayi irin wannan? Matar MA itake Auren Soja lallai yau ta Y'ar da bawa bai isa ya bawa kanshi Abinda yasoba sai Abinda ya zaba mishi, it ace mai cewa bazata taba Auren Soja ba saboda halayen MA at last kuma shi da kanshi ne yazamo mijin Auren ta Allah mai iko, Bata ankaraba saida suka kai bakin wawakeken get din na NDA taji gabanta ya mugun fadi, tasan umarnin Oga kwata kwata, ne, Sukansu sojojin wurin saida suka Sara mata kafin ya wuce tayi saurin daukar wayarta domin kiran shi yana sama yana yana daga karfen shi yaga kiranta dariya kawai yayi yaki dagawa har ta tsinke, Jin tsayuwar motar yasa ya Kara yin murmushi ya tareda Ajiye karfen da yake dagawa kamar yana daga Kara, ya tashi daga shi sai guntun wando ya dauki karamin towel yana goge jikinshi, Kallon ta yakeyi yanda fuskar ta ta canja daga gani kasan ranta ya baci, yayi y'ar karamar dariya, "Sory madam I can't help it, Kallon kofar gidan tayi tareda juyawa cikin sauri ta nufi gidan Aunty maryam, duk yana kallon ta, Aunty maryam naciki tana kwasar soyayya ta kwalo sallama don ta shirya ba inda zataje, Saidai yagaji ya kyaleta, maye kawai, Maryam ta fito cikeda mamakin ganinta "mezangani haka AMARYA "me kikazo yi? Bakinta ta turo tana fada mata, dariya tasa "aiki yaganni Yasmin yaci Ace yanzu kinsan wakike Aure don haka nidai kitashi kitafi gidan mijinki kinzo haka kawai ina farantawa nawa mijin kin katseni, Kije ko ki zauna gadina har ingama mijina zaiyi tafiya inaso inbashi harda reserve, baki tasaki tana mamakin Aunty maryam, Tako wucewar ta tabarta nan Karar wayar ta yasa ta dauka, "inshigo ne indauke ki? Tasan sarai zai iya don haka ba choice dole ta mike jikinta ya mugun sanyi gaskiya tsoro takeji,   Kar yace zai yi wani Abu da ita don haka taketa gudun zuwa gidan, Inba ma iskancin MA ba yayi hakuri sutare mana,   A kofar gidan tasameshi yayi wanka yana sanyeda singlet na Army da mahadin su tree quarter ya yi mata mugun kyau ya zuba mata ido kamar ya lasheta tsabar kyanda tayimai, "Baby guduna kikeyi? Yafada tareda matsowa kusa da ita ya rungumota ta gefe, mata masu leke kuwa tuni baki yacika da gulma, Baiko san anayiba ya wuce da ita, duk sojojin tasowa sukayi suna Sara mata ko kai bata daga ba don ita a tsorace take sosai, falon ta zubawa ido like Always very neet kan kujera suka zauna ya shige jikinta kamar wani mayen karfe, tareda kwalawa Emanuel kira,   Ya fito da gudu kawai ya saki baki ganin yasmin rungume a jikin Oga, shidai yasan Oga yayi Aure a haukarshi zuby ce ya Aura don baisan Abinda ke faruwa da relation din ogan nashi ba,   "My friend ya fada cike da mamakin ganinta ya karaso da niyar riko hannun ta, MA ya buga mai tsawa, "you are mad ema are you going to touch my wife? "Your wife? My friend ' ya zaro ido cikeda mamaki da kuma murna don sunyi mugun matching da juna, "wow congratulations my friend now you are not my friend you are my madam, ya fada cikeda wautar shi yanajin dad'i sosai yanzu dama itace Oga ya Aura "chineke me, Sai mamaki yakeyi, MA yace in ya gama yatafi sai gobe yadawo, ya mikamai kudi masu kari yayita godiya, itadai ba baka sai ido batada tacewa barawo a hannun mata,   Tashi yayi ya riko hannun ta" let go inside, kafada ta makale mai idanun ta suka ciko da kwalla" Wai ni yaushe zaka daina min haka ne? "Sai ranarda na mutu, ya fada kai tsaye, tareda komawa ya tsuguna a gabanta tareda dafa cinyoyinta ya zame gyalen jikinta tareda ture d'an kwalin yana bata wani irin deep look, "Sorry Am going to travel tomorrow I can't travel like that kiyi hakuri baby kibani hakki na wallahi inashan wahala please just once give me this chance please, Rike mai hannu tayi tareda girgiza kai "please no kabari don Allah nidai Wallahi tsoro nakeji "kitaimaka ke matata ce ko kina so inci gaba da bin nawaje bayan inada ke, Turo baki tayi cikeda kishi "zakasa inyi kisan kai ko zsnkashe macen da duk tazo kusa dakai yanzu, dariya yayi tareda janyota tafado jikinshi, I love it when you show your jealousy baby ina jindadi idan kika saki jiki tare dani, Kara lafewa tayi ta dora hannun ta saman kirjin shi yaji wani irin shock a hankali yanayin shi yafara sauya wa ya zura hannun shi cikin rigarta ya fara lalubota "am hungry baby but I can't eat anything now sai kinbani Abincin jikin ki nakoshi ina matukar yunwar shi,   Sungumar ta yayi ya nufi dakin da ya kawatashi a gidan na musamman ba wadda ta taba shigar shi sai shi kadai yaji lafiyayyan gado dauke da zanin gado mai mugun kyau dakin dai yafi kowane daki na gidan haduwa,   Zaunar da ita yayi tareda cire rigar jikinshi yarage daga shi sai tree quarter ya tsuguna a gaban ta, ya saka hannu ta bayanta jikinta yayi sanyi don tana hango tsantsar fitina a idanun shi Wanda ya gauraya da zallar kaunarta, She can see that in his eyes, batasan lokacin da ya gama cire mata rigar har bra ba tayi nisa cikin tunani, saida ya kwantar da ita, tareda kwantawa gefen ta cikin natsuwa, he want to be gentle bayason ya wahalar da ita da yawa,   Hannu ya dora a kirjinta cikin natsuwa ya suka sauke a jiyar zuciya atare juyowa tayi ta fuskance shi ganin yanda yake shafata a hankali kamar yana shafa kwai, ta tuno da maganar Amira "karki tsaya ma na miji kamar gunki idan yana nemanki ki bashi taimako shi zaisa duk inda yaje kina cikin zuciyar shi, Tanason ta Kara mallamar MA itaka dai Tanason ya manta da duk wata macen da yayi tarayya da da ita A baya don haka ba bata lokaci ta dora hannun ta akan kirjinshi mai fadi cike kuma da suma mai ban sha awa ta fara shafashi tareda matsawa jikin shi sosai ta dora bakinta dai dai lips dinshi batareda ta yi mai komaiba, ya cafka da sauri don ta kunno shi tunda ta sa hannun ta a kirjin shi,   Tuni yasa zafi yafara bata hot kiss tareda lalubar ta cikin zafin shi, tuni ta fara jin tsoro don ya rikice sosai wani irin mugun rawa jikin shi yakeyi,   Cikin sauri ya zabura ya tashi ya janyo wani cream ya kwabe wandon shi yana layi kamar zai fadi ga Hajiya Babba na halbin iska ya koma gadon ya tube sket dinta dayai saura tareda zare pant din ya haye gadon, ya matso cream din ya bude kafarta ya shafa mata a kasan tana jin kunyar yanda yake leketa, Ya shafawa kanshi tareda jefar da robar ya haye tareda manneta gam a jikinshi bakinta ya kuma kamawa cikin sauri yake aika mata Wasu sababbin sakonni,   Kafafuna najawo don bazan iya ganin mai zai faruba don yanda Oga MA yau yayin nan nasan saifa yashiga, Kofar nafara jawowa a hankali na nufi falo tareda zabga tagumi ina matsar ido, Tausayi take bani don duk mace tasan zafin wannan ranar farkon,   Ihunta yasani saurin zabura namike wani irin ihu ta Kara zubawa kai taba zuciyar mai sauraro wani irin sanyi jikina yayi shikenan ya aikata, Kukanta duk ya karade gidan da ace gidan ba girma to har ma kota zasujiyo ihun nata, Saida aka dauki kusan minti talatin kafin inji kukan ya tsagaita, can na kumajin sabon ihu, dagudu na nufi dakin don bazan yarda ya la anta y'ar mutane ba, Iya jikata tayi don ba Aikin wasa yakeyiba haka yake har zuciyar shi bayaji baya gani ina hango yanda jini ke malalowa ta kasan ta, Wasu irin hawaye yake fitarwa Wanda bansan dalilin suba saida yaji y'ar gamsuwa ya kwanta a jikinta, kafin ya cigaba da gashi,   Gaba daya yanzu bata iya kuka ta sad'akar tabarwa Allah, ci hudu yayi kwarara kafin ya rungumota zuwa jikinshi kamar zata gudu yana bata kiss masu zafi hawaye na Ambaliya, shesheka takeyi tareda Ajiyar zuciyar wahala ko yatsar ta bata iya motsawa jitake kamar ma duk ya rugurguza mata kasusuwa jiki,   Saida ya ji ya samu numfashin shi ya dai daita ya sassauta mata rikon ya tashi yanajij yanda marar shi ta saki wani irin dad'i yakeji har cikin jikinshi bai taba jin Abinda yakeji ba a yau tsawon rayuwar shi,, "Yasmin ta gama da rayuwar shi takaishi wata nahiya ta daban ta shayar dashi ruwan koramu masu dad'i gaskiya yayi wauta a she da baiyi Aure da wuriba Ashe Aure ni imomi gareshi ga samun gamsuwa tunda ko a romance din ma yafi jin dad'i da matar shi, Yagodewa Allah da ya mallaka mai wannan precious gift din, kallon ta kawai yakeyi cike da wata irin sabuwar kaunarta bai koshiba Allah yagani sabon kwadayinta kawai yake karaji hardai yanzu ya tsoma yaji abinda ke ciki,   "I love you my wife ya fada tareda nufar bathroom ya hada musu ruwa kafin ya fito. Zama yayi gefen gadon ya dafa ta" Sory baby muje muyi wanka, Kuka tasamai sabo, tuni hankalin shi yatashi ya haye gadon tareda rungumo ta "haba farin cikina yazaki yi kuka bayan kinbani farin ciki, banason zubawar hawayenki komai naki mai tsada ne Fatima ke ta daban ce a cikin mata, bansan yanda zanfada miki yanda nakeji ba, "Ina sonki matata I love you more and more you deserve to be happy not sad "nine ya kamata inyita kukan dad'i bake ba, Kuka ta Kara sakamai don mugun haushi yake bata yanzu mugu kawai mara tausayi, "oh my god baby wallahi zaki tada min hankali da kukan ki KO kinaso inkara yi miki kuka ne?   Jin kukan nakaruwa yasa ya daga ta cak ta sa Kara don jin kasan ta take kamar ciwo "kasaukeni zafi " ta fada jikinta narawa, bai direta ba sai cikin bath tub din, Ta kwalla wata uwar Kara tareda rikoshi tamau, "Sory baby nine ko duka ta kaimai "wallahi ka cireni mugu kawai Allah ya isa Azzalumi sai Allah yasaka mun kuma sai ka sakeni banason Aur.....   Saurin hade bakin su yayi jiki na rawa tuni tayi tsit saida yaji tayi shiru ya cire bakinshi tareda tallabota cikin yanayi mai ban tausayi yace "don't think like that again baby banason zancen kiyi nisa dani ma bare rabuwa dake kamar zancire ruhina daga jikina ne Wallahi I can't spend even one second witout you by my side I can't,   Bazaki koma ko ina ba we are going to Abuja to gether "ba inda zanje ka mayarda ni gida, Shiru yayi kawai tareda taba ruwan yaji yayi sanyi ya cirota ya kuma tara wani ya maida ita ciki taji dadin ruwan sosai don har ta rage jin zugin, Fita yayi cikin sauri ya yaye bedsheets din ya dawo ciki tareda jefa shi cikin washing machine ya kunna ya koma tareda cire towel din jikinshi ya shiga cikin bath tub din ya saki ruwan tareda kunna musu hands shower ya fara wanketa tana ture shi a haka ya cudeta cikin dauriya Don ya kuma daukar charging,   Dakin ya dawo da ita ya shinfideta tareda goge mata jiki da towel ya daura mata wani tareda fita cikin sauri ya dawo dauke da plate cike da farfesun kayan ciki sai fresh milk, Yana fita ta gwada tashi saidai ina bata iya tsayawa da kafafun ta dole ta koma ta kwanta, tana matsar ido, karasowa yayi tareda janyo wani d'an karamin stool ya Ajiye tareda dagota ya zaunar da ita cikin taray raya ya fara bata farfesun dakyar ta bude baki ya saka mata, Tasha sosai kafin ya zuba fresh milk din ya ballo mata pain killer ya bata ta sha don wani irin mugun zazzafi takeji yana kokarin rufeta,   Kwantawa tayi ya zuba mata idanu yana mata kallon kingama yi Arayuwa yasmin ya zama speechless akanta yau yarasa kallama guda daya da zai fada mata,........ ️   *Matar Soja* [9/4, 10:19 PM] Asli Smasher : PROFICIENT WRITERS ASSOCIATION тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   _written by FENERH_ Maman Ammar *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby _*Addu'a ta agareki mai girma ce my queen Nabeela Allah ya baki lfy mai dorewa Allah ya yayewa duk kan musulmi cutukan dake damun su ina miki fatan Alkhairi Arayuwa sarauniya Allah ya rabaki da duk wani mugu mai son ganin bayanki,*_   39&40 Saida yaga tayi bacci ya shirya cikin sauri ya fita domin yanason zuwa gida wurin hajiyar shi, saida yaje har kofar gidan su Aunty maryam ya kwankwasa,   Ahmad ne da kanshi ya fito yayi mugun mamakin ganin ogan yau a kofar gidan shi, cikin sauri ya saramai "ya ce ina Aunty na? "Tana ciki sir bismillah bai taba tunanin zai shiga ba saiko ya shige har falon ya zauna, cikin sauri tareda mamaki ya wuce kiran maryam din,   Yau Oga MA a cikin gidan shi fitowa tayi sanye da hijabi ta gaida shi nana na rungume a hannun baban ta Auwal yazama d'an gidan mama,   Mika hannu yayi batareda kyama ko wani nuna girma ba ya karbi nana sai tsallae takeyi dama Tana miko hannu, wani son yarinyar yaji har cikin zuciyar shi saboda ta dibo yanayi da yasmin farinta da idanu har ma d'an karamin lips dinta, "wow she look like my baby, yafada cikin ko in kula,   "Am please Aunty zanje malali don Allah baby na bacci zata iya bukatar taimakon ki idan tatashi please I need your help bazan dawo ba sai dare kar ayi magrib tana kwance,   Ya fada yana mikewa tareda zaro bandir na kudi guda biyu ya Ajiye ma nana gashi asiya mata sweet Ahmad let go, Ya fada yana fita cikin hanzari, biyoshi yayi cikin jin dad'i suka jero tareda ogan nashi kamar friends suka fito sai kallon su akeyi mutane na mamakin Oga MA a gidan yaron shi ko yayi mugun laifine? Don da yawa basu san waye ya Aura ba,   Maryam dai baki sake tabisu da kallo baby ba lfy kuma tana bacci? Me MA ke nufi bazai mayar da ita bane kome? Tab yau baba zaiyi grumbling   Kulle gidan ta tayi ta nufi katon gidan yau a karon farko ta shiga, falon tsayawa tayi domin kallon yanda dukiya tayi kuka a cikin falon tangamemen TV kawai abin kallo ne bare furniture's din "Masha Allah Ashe kallo na cikin gidan MA tab, rasa ina zata nufa tayi, Ganin kofa ta hannun daman ta ta nufa tareda turawa takoyi sa a ta hangota dunkule a bargo tana baccin wuya,   Dakin take bi da kallo hmm "yasmin kinsami duniya lallai ke ya dabance Autar baba, tafada tana murmushi mai cike da Alfahari da gidan kanwar tata,   Zama tayi akan kujerar dake dakin guda daya mai kyau, saida taga za a kira salla ta matsa kusa da ita "yasmin kitashi haka magrib tayi, dakyar ta bude kunburarrun idanun ta, ta kalli Aunty maryam Ai sai kuka, "ke Meye haka kuma daga tashinki sai kisamin kuka? "Aunty bayana kafafuna kaina kirjina wallahi bazan iya tashi inyi tafiya ba, nikikaini gidan ki banason shi ki mayarda ni gida wallahi mugune kalli yadda ya yagani Allah ki duba min karkashi na Aunty ya ciremin komai na wurin, Dariya Aunty tasa sosai "eh lallai yasmin daga farawa irin wannan raki haka me akayi da maza, "ai yarinya ki girgije kawai ki bada kaya ki Amshi kaya,   Ganin takiyin shiru yasa tafara lallashin ta dakyar ta iya mikewa bata ko iya hade kafafun ta takuma hada mata ruwa mai zafi ta shiga saida tayi mata kusan sau uku taji dama dama ta dauro Alwala suka fito ta shinfida mata dadduma tareda bata hijabin ta tayi salla ta nemi kitchen domin nema mata koda tea ne Ta samu akwai komai ga store shake da nau in Abinci Kala Kala Wasu kuloli ta bude taga kajine soyayyu Anyi pepper chicken dasu ta zuba a plate don tasan kanwar tata da naman kaza ta debi farfesun kayan ciki itama ta fito musu dashi Nana nagefe tanata wasan ta, tana idarwa ta mika hannu tareda cewa "come my baby ta rungume ta, maryam ta Ajiye mata nata a gaban ta ta zauna itama tafara sha tana tanbayar ta, "Yasmin yanzu yaza ayi ki koma gida a haka? Kinga yanda kike tafiya da kika mike, wallahi kina zuwa sai Anganeki, yanzu ya zamuyi,? Hawaye tafara zubowa Aunty bayan yace bazan koma ba wai nazo kenan nidai don Allah mutafi kafin yadawo please, "Aa niba yayar banza bace haka kawai sai in kwashe ki mutafi ni nakawoki? "Ai mijinki ne yasmin kuma koma Meye zaiyi saidai Ace baida kunya kuma yafi ai da yaje waje ya nema,   "Toh ni da wane idon zankalli su mama? "Kifa murje kawai kinji suma ai bazasu miki fada ba don yafisu iko dake yanzu, Komawa tayi ta kawo mata doguwar riga a cikin sababbin kayanta ta saka tareda d'an karamin gyalen ta yafa akanta, ************* Y'an Uwan shi yasamu duk suna shirin tafiya gobe " yau wa baban Hajiya yanzu muke maganar zuwa gidan naka don gobe kowa zata koma gidan ta, Munaso muga yanda za a tsara ma gidan, sosa keya yayi cike da jin nishad'i yace "no ai zata tsara Abinta dakanta tunda tana ciki, "Mene? Eh tana nan gwara da bakuje ba gaskiya da kun kwafsa, "lallai baban Hajiya wallahi bakada kunya ko kadan yanzu dakko y'ar mutane Kayi bata tare ba kuma ba biki Al Ada ce ko addini? Ca suka yimai har hajiya tasa baki akan baiyi dai dai ba shidai shiru kawai yayi Saida sukayi shiru, "yanzu so kuke inje ina shan wahala bayan inada mata, "To da can dakaki yin Auren fa? "Lokaci ne baiyi ba Allah keep Yasmin for me sai yanzu na hadu da matar Aure na, "Yaya Aure akwai dad'i wallahi jina nake complete yanzu gaskiya na yarda da ake cewa inbakayi Aure ba baka cika namiji ba, Mikewa yayi zuruf" Yaya bari intafi na barta batada Lafiya don haka zamuyi magana a waya gobe Abuja zamuje meeting kayan Akwatin zantura miki kudin ta Account dinki,   Yaya hauwa tace "lallai ka mayarda mu matsiyata kenan da saika bada kudi mu hado ma kaya, Autan namu guda daya zaiyi Aure ai kaine ka bata mana tsari da sai Ansan muna Aurar da gudan kanin a kaduna,   Don haka kaje saika dawo zaka tarar da kayan, "godiya yayi ya fita duk hankalin shi nakan Yasmin Hajiya farin ciki fal zuciyar ta burinta ya cika tilon d'an yayi Aure, duk da bataji dadin dakko Yasmin da yace yayi ba, Ya fito Ahmad ne ya jasu yace "muje Unguwar dosa infada ma su baba muna tare da Yasmin, dariya Ahmad yayi, "ai Oga na dauka zamu koma mu dakko ta ne? Sai mu yarda ita, "Nop ina AI duk wata Al ada abarta I can't take it gobe ma tare zamuje Abuja da ita, zaka iya tafiya da madam kaima saboda inmun fita suna tare bazataji loneliness ba,   Ahmad yaji dad'i don yanason ya tafi wuri da matar shi Amma ba hali yau gashi zaije da ita Albarkacin matar Oga,   Baba suka samu suna Alwalar isha a kofar gidan, fitowa sukayi suka gaisa tareda mika musu hannu cikin jin daddin ganin surukan nasu, buta suka mika musu sukayi Alwala tare suka karasa cikin masallacin da ba nisa da gidan saida suka idar suka dawo cikin falon baba, , "ya fara sosa kai "dama baba nazo in dauki kayan Yasmin ne zamuje Abuja tare gobe inada meeting zanyi kusan sati acan, baban zango yace "Masha Allah to Allah yakara tsare Ku bari sai Ayiwa Yasmin din magana ta shirya, don basu san bata gidan ba su,   "Ai muna tare dazu nasa aka kaita gidana. ya fada hankalin shi kwance ba wata kunya don shi Sam baiga rashin dacewar hakan ba, "Baba yace ikon Allah to ba komai Ku isa Ku yi magana da matan sai subaku kayan ko, yako mike ya shige shidai Ahmad kunya kamar ya nutse bashi yayi ba Amma yafi shan kunya, Don haka ma ya kasa shiga cikin gidan don ya lura Oga ko a kwalar shi, Maganar gaskiya nefa MA basu hada hanya da kunya ba,   Baba ya fara ruwan fada "kagani ko mamuda saboda gadara ya dauke y'ar ba izini na kuma don rashin kunya yazo daukar mata kaya koda yake laifin ta ne ita tabishi,   Al adar bikin ma bazata bari ai mata ba ta kai kanta dakin miji to tayi wa kanta Y'an kudina sun huta "aa Yaya ina ruwanka mutum da matar shi nifa wallahi ina son yaron don shi kaifi daya ne kana ganin shi ko a fagen aiki a tsaye yake shiyasa Allah yakaishi babban matsayi cikin kana nun shekaru, ai mu haihuwar ya'ya tayi mana rana don mun ga mutanen da ma saidai da mugan su a hoto ko a TV, Kaduba Yaya har gaisawa nayi hannu da hannu dashi kaga yard..., ya isa hirar tunda kai Goyon bayan surukin ka kakeyi, "to wai Yaya meyasa baka fadamai ra ayinka ba saida ya tafi?   Da sallama yashiga cikin gidan suna zaune a tsakar gidan saman tabarma "Maraba suka cemai mama hindatu ta mike da kanta takawo mai kujera ya zauna, "Daga gani dai wannan suruki na ne ta fada cikeda fara, a mama tace "eh shine, "tokai dana ina y'ar tawa take tunda rana shiru bata ba labarin ta, dariya yayi kadan tareda dukar da kanshi " ai muna tare yanzu haka nakaita BARIKI tana tareda Aunty maryam, Nazo daukar mata kaya ne dama bari inga Wanda zata bukata gobe Abuja zamuje, yafada tareda mikewa batareda ya jira izini ba ya fada dakin nata, Duk sakin baki sukayi sukabishi da kallo "zamani inji mama Allah yakawomu yau muna ganin BARIKI mama hindatu kuwa cewa tayi" ke barsu suyi lokacin sune namu ya wuce, Amma ita yasmin ta biyewa namiji takai kanta ba wata daraja? "Aa darajar ta na jikinta Yaya Saude ai mutuncin mace budurcin ta kuma ni na yarda da yayan mu da izinin Allah ba bora a zuri ar mu,   Yana shiga ya bi dakin da kallo, akwatunan ta ya kalla tareda janyo su ya dakko guda daya ya bude wa inda ya kawo mata daga waje ya zabo mata kananan kaya masu kyau dasu iners ya zuba tareda duk wani Abu dayaga zaiyi mata Amfani ya zuba ya dauki akwatin yafita saida ya dire musu bandir daddaya na dubu dubu sannan ya mike ya fita, Mama hindatu tabishi tace mai "bari inbaka sako ka kaima maryam, kayan gyaran jikin yasmin ne, sai sukarasa da kansu, Karba yayi tareda godiya ya tafi bayan ya direma su baba nasu kudin mai tsoka ya fada mota ya tafi wurin Abincin ruhin shi,   Wani irin lumshe ido yakeyi tareda murmushi mai kayatar wa ya matsu bai ganshi kusa da itaba wani irin tashi yaji tsigar jikinshi nayi da yatuno da moment donsu na dazu,. "She is Amazing in and out ya fada a zuci ya baisan ta fitoba, Ahmed yayi Dari ya "Oga Aure yayi dad'i yana sambatu, Tunani MA yakeyi dama mutum nazuwa duniyar sama yadawo bai saniba, don dai shi yau yasmin har sama ta bakwai ta leka dashi, saida suka tsaya ya siya mata Wasu kaji a NDA gate kashi biyu ya siya kafin su wuce gidan, Suna tsayawa yace Ahmed ya shigo ai madam na ciki, Ya biyoshi da ledodin kajin suka samesu a falon zaune suna kallo tareda hira a tsakanin su, tanajin shigowar shi ta matse fuska tareda janyo gyalenta ta rufe fuskarta ganin harda Ahmad suka shigo, Yafara tsokanar ta "Aa kaga madam yau ni kike rufewa ido, ai dole gidan da kike zuwa leke yau yazama naki da duk wani daukar maganar da kikayi a nan gidan Ashe kanki kikema yaki bansani ba, Aunty maryam ta yi dariya "kaji ka baban Auwal kai ma da tsokana, shidai MA yana shigowa wurin ta ya nufo tareda zama a hannun kujerar datake kai ya duko yana leka fuskar ta, "My madam ya akayi? Ya jikin ki ya kikeji yanzu? Banza tayi dashi tareda aika mai harara ta kasan gyalen, itadai maryam mikewa kawai tayi ta saba y'ar ta ta fita mijinta yabi bayanta, Leda biyu yace su tafi dashi bayan yayiwa Aunty maryam godiya suna fita ya rufe falon, Yadawo jiki narawa ya zauna a gefen ta, "please open your eyes ta dunkule tareda nade jikinta bata kaunar ta kalli ma idanun shi, "Ok bari inkara swimming a kogin dad'in kya bude min fuskar ki ingani, tayi saurin bude wa tana turo mai baki tareda yin narai narai da idon ta tana shirin yin kuka, Saurin rungume ta yayi tareda runtse idanun shi gam "karkiyi kuka my happiness bazan juri ganin zubar hawayen ki ba bayan kinbani farin ciki, yasmin narasa wace irin kyauta zanbaki a matsayin kyauta a Fadin duniyar nan in zan mallaka miki duk Abinda na tara a duniyar nan bazan iya biyanki farin cikin dakika shayar dani ba,   "You make my day kin farantamin fiyeda tuna ninki, a hankali zaki fahimci soyayya ta agareki kin gama da zuciyata harma da gangar jikina, ni nazama bawanki yasmin kingama mallaka ta sai yanda kikayi dani,   Sambatu yake ta sake mata kafin ya saketa yace ta tashi su shiga ciki, kintashi tayi, yayi ta rokonta "please baby banason intakura miki "to karka tabani zantashi kuma banason kazo kusa dani again,   "Impossible yasmin kina kokarin raba gangar jiki da ruhi bazai taba yuwuwa ba innayi miki wannan Alkawarin zan cutar da zuciya ta,   "Amma I promise bazan kusanceki ba yau, Ajiyar zuciya tayi domin tasan inhar yace zai kuma kusantar ta tabbas sai ta dangana da Asibiti,   Tashi tayi a hankali tafara takawa yabi bayanta da kallo yanda yake motsawa tuni ya fara dana sanin yimata mugun Alkawari, Suna shiga tafara yimai darun ya mayar da ita gida kawai, yace ki kalli time to 10 baby ai Abuja zamuje gobe namaje gida na dakko miki kaya Idanu ta zaro cikeda mamakin halin shi, yanzu ka dauki kafarka kaje har gidan mu ka kwaso min kaya? "Wallahi ka gaba bani kunya a Rayuwa wai kai me yasa kake mun haka yanzu yazanyi da kunyar iyaye na? Laifina Zasu gani gashi bazan iya komawa gida a haka ba don nasan tsab Zasu gane Abinda ya faru dubi yanda ko Ajiye kafafuna bana iyayi da kyau nidai nayi dana sanin soyayya irin taka gaskiya, matsowa yayi jikinta tareda kallon ta cikin yanayin tausayi da kwantar da murya, "Sory baby haka mijinki yake ni bana iya kwana kwana banson karya bazan iya cutar da zuciyata ba ina bukatar ki I want you bazan iya hakuri ba bayan nasan ke halali nace, kuma yanzu na d'an dani zumarki bazan taba iya nisa dakeba, Wallahi ko malami kikabawa kudi kika mallakeni haka zan iya Kara miki ki kaimai kinbiyani yasmin ina sonki ina sonki ina sonki.. Ya fada cikin wani irin salo mai tsuma zuciya tuni ta natsu tareda sakin jikinta ta zuba mai idanu, Tashi yayi ya fita Ledar kazar ya dauko ya shiga kitchen ya dakko plate da kuma cup ya hado da hollandia yourgout , ya Ajiye mata yace ta sakko ga kazar Amarcinta ya fada yana daga mata gira,   Tura baki tayi tace "ni nakoshi naci Abinci kuma kazar da saida aka gama cin zalin mutum sannan za awani kawomai kaza daga baya ta fada tareda kwanciya Abinta, dariya yasa sosai Sory my wife zanbiya har Abinda yafi kaza karki damu,   Dakyar ya lallaba ta tashi taci kadan tace ta koshi kafin ta koma gadon, saida ya kammala shirin shi tsab ya haye gadon ya kwanta nesa da ita yana kallon ta, Ji yake kamar ya matsa ya shige jikinta Amma yasan bazata yarda ba don haka ya zuba mata idanu har saida tayi bacci sannan ya matsa jikinta a hankali, Ya shige kamar mayen karfe, ya shafo fuskar ta tareda dora mata kiss a goshi, yau shine a gadon shi da matar shi ta sunna ba karuwa ba, Wani irin farin ciki yake ji, motsawa tayi kadan ta juya tareda rungume hannun shi zuwa kirjinta daba bra, duk a cikin bacci, "Ahh yafada a hankali yana hura mata iska a kunne "baby kin tsokanoni wallahi yafada yana mika a jikinta, gashi yanajin laushin kirjinta a hannun shi tuni ya saki layin ya fara lalubarta "Sory baby I can't I can't please open your eyes I want more, Yafara fada a hankali Amma ina tayi nisa domin domin maganin da tasha akwai na bacci kuma yanada mugun karfi,   Jiyota yayi jikin shi narawa ya hade bakinsu yafara bata zafi, saida yayi nasarar cire mata komai ya yafara kokarin kutsa kai ta farko, Cikin bacci tafara jin zafi na d'an ratsa kirjinta da kuma kasanta ta bude idon ta a hankali ganin yanda yake kokarin shigarta yasa tayi saurin tureshi ta tashi tareda janyo zanin gadon ta dunkule tasa mai kuka,   Tashi yayi jiki na mazari idanun shi sun mugun kadawa saboda tsabar kaduwa, ya matso jikinta "yi hakuri my wife nakasa hakuri ne kitaimaka min in samu relief a jikin ki nariga nasa rai inban samu ba zan iya rasa Lafiya ta da daren nan please baby,   "Ni wallahi aa kasheni zakayi bazan yarda ba haka kawai nidai bazan yarda ba har yanzu zafi nakeji ta fada tana kuka sosai, "ok ya isa ki kwanta daina kuka ya fada cikin bantausayi,   Haka takoma tayi kwanciyar ta shikuwa tashi yayi yashiga bathroom ya sakarwa kanshi ruwan sanyi, yadan ji sauki kadan kafin ya dawo saman sofa ya kwanta tareda zuba mata idanu har yasamu bacci ya daukeshi,     Karfe biyar ya tashi tareda tashinta tana tashi saida tayi wanka tareda gasa kanta taji saukin wurin sosai yanzu tafito da Alwalar ta tasamu yana nafila itama ta tayarda tata saida suka idar ya fita domin motsa jiki, ita kuwa gado ta koma, sai karfe bakwai ya shigo cikin sauri yayi wanka kafin ya shirya cikin sabon kaki yayi masifar kyau ya zura but kalar kayan yafito a MA dinshi, Kafin ya tashe ta bude idanu tayi cikeda bacci, yana daura ago go ya ce "kitashi ki shirya ana jiran mu, "ina zamuje? "Kin manta kenan? Toh kitashi Abuja zamuje su Aunty maryam sun shirya, da ita za aje? Tafada cikin jin dadi "eh madam, yafada tareda murmushin jin dadin ganin farin cikin ta,   Tashi tayi ta kuma watsa ruwa ta fito shiryawa tayi cikin doguwar rigar Atanfar da ya Ajiye mata dinkin ya yi mata kyau sosai tasaka sarka da ago go mai tsada Shima ya shigo tana daure sumarta, tsayawa yayi tareda zuba mata idanu cike da so tayi matukar yimai kyau "natural beauty yace,   Ta saka takalmi ta ce" ina waya ta yace tana moto muje ko, shi ya daukar mata jakar ta suka fita, cikin burgewa suka jero, suna kawowa kofar fita yace "wait, ya dora mata gyalen saman kanta tareda rungumota zuwa jikinshi, "Ana ganin mun Ajiyata dole in boye kayana banason wani yaganin mun kayan dad'i na, Shiru tayi mai suka fito taga motocin nashi birjik aka fara saramasu kafin driver ya bude musu mota su shiga, "banga Aunty ba? Ta fada tana waige, "relaxed tana motar gaba itada Ahmad,   Suka dau hanya yana kwakume da kayarshi, wani irin nishadi yakeji traveling with his wife,......... ️ *JUMU'AT KAREEM TO ALL MUSLIM IN THE WORLD MAY ALLAH SHOWER HIS ENDLESS BLEESING UPON US AMEEN JUMU'AT MUFEEDA* "Sory jiya na d'an yi blaguro ne nafita wani uzuri bansamu zubo muku typing ba kuyimin Afuwa uzurorin nada yawa kuyi manage da wannan,   *Matar Soja* [9/7, 3:00 PM] Asli Smasher : PROFICIENT WRITERS ASSOCIATION тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 https://www.facebook.com/groups/2455147078097572/?ref=share     BARIKI Auren Soja Written by FENERH Dedicated to Fiddousi mainasara 41&42 Tunda suka dauki hanyar Abuja tana manne ajikinshi baccin ta takeyi hankali kwance wani irin nishadi yakeji sosai a cikin zuciyar shi mara misaltuwa har suka isa cikin garin inda convoy dinshi suka faka a bakin katon hotel din dayayi fice a babban birnin na Abuja Wato Sheraton hotel Suna sauke su a masaukin su suka tafi Abin da yakawo su, Wanka sukayi tareda bajewa suka ci Abinda aka kawo musu tareda hira a tsakanin su cikin farin ciki maryam tafito mata da kayan gyaran jikin yasmin ta kalleta " Aunty gaskiya nagaji da shaye shayen nan Kibarni haka, "lallai bakida hankali Yasmin kinsan me kikeyi kuwa? Gyara shine mace kigyara ciki ki gyara waje shine kika cika mace bawai ki gyara waje ciki lami, cikin natsuwa tareda fahimtar da ita tareda Kara mata dabarori masu Amfani yanda zataja mijinta ta Kara mai soyayyar ta a cikin zuciyar shi,   Sai karfe goma suka rabu Yasmin takoma nasu masaukin da ke sama danasu maryam wanka tayi tareda shafe jikinta da turaruka masu kamshi da kuma mayukan ta masu Kara gyara mata fata dakuma sa laushin jiki ta gyara sumar ta ta d'an Kama shi da band wata sexy nightie mai shegen kyau da ja ana hango komai na jikinta batasa komai ba sai pant din ta Dan siriri rigar nada gidan bra sunfito shar gwanin sha awa da daukar hankali, tafito tayi kyau sosai ta kalli mirror din dake dakin taga yanda tayi mugun fitowa tasan yau sai Allah idan yaganta haka Amma yazatayi dole ta Kara kokari wajen kawar da idanun mijin nata akan matan banza,   Har kusan Karfe goma shabiyu kafin suka dawo hotel din lokacin har ta gaji bacci ya dauketa akan kujera wayar datake dannawa har tafadi kasa rigarta ta yaye daga kasa pant din ta a bayyane a waje ga fararen kafafunta masu sheki dasukasha gyara sun Kara haskawa, yana bude kofar da katin shi da ita yafara cin karo, jingina yayi kawai ya rungume hannun shi yana sauke mata kallo tundaga yatsan kafarta har zuwa laps dinta kafin ya dire saman na shan un ta da suka fito ga dayan har yana ganin bakin kan tasama yaja wani huci cikin mutuwar jiki da wata uwar kasala da ta rufe shi lokaci daya "oh Allah yafara godiya da Allah yaba shi Yasmin duk wata gajiya da yakeji tuni yaje ta baje kawai so yake yaji shi cikin lafiyayyan jikinta, takawa yafara yi cikin natsuwa ya isa kusa da ita tareda tsugunawa ya daga wayar tareda zubawa kafafun ta ido, cikin natsuwa ya daga hannun shi ya fara shafa su cikin wani irin salo yana lumshe idanun shi kafin ya dire hannun shi zuwa daidai shatin pant dinta ya shafo tareda Kara yaye rigar zuwa sama baki daya, Bakinshi ya sauke saman pant din nata yayi kissing nadan lokaci tareda kamshin dake fita daga wurin tuni yaji ya rikice don wata irin humra Aunty maryam tabata tace ta kasance kullum tana Amfani da ita a a kasan matse matsin ta domin mafi yawan cin maza nakai bakinsu kasan matan su, Abin yabata mamaki yaza ayi namiji yasa bakin shi a wannan wurin? "amsar Aunty maryam ta bata mamaki "Au ke bazaki iya sucking mijinki ba kenan? Zaro idanu tayi a lokacin jin wai mace ta tsotsi wannan Abar yark "" Allah ya kiyaye, "eh lallai Yasmin za ayi baki kuwa karki Dage,   Cikin baccin takeji sauyin yanayi tafara mika domin wani irin tsotso yake bawa cibiiyar ta tareda shafe ko ina na jikinta daga zaunen tuni yayi fatali da boot dinshi har ma kakin jikinshi, wanka yake bukata Amma cin karo da wannan kayan dadin bazai bari yayi wankan ba sai ya sauke damuwar shi hankali yake tafiyar da ita kamar wani barawo ya daga rigar ta sama ya yi wani irin gurnani ganin sun bayyana a fili ya yi saurin dora lips dinshi a daya tareda Kama daya cikin zakuwa yana tsugunnen guiwar shi a kasa jikinshi har rawa yakeyi a hankali ta fara bude idanun jin hakoran shi akan boosty boob din ta don har wani ciazawa yakeyi a hankali Zare idanun ta tayi ganin yanda yake sarrafata kamar zai tsinke mata kirjin saurin tashi tayi tareda kwace jikinta tana murje ido ya zauna dabas akasa yana jan numfashi don takatse mai jin dad'i fisgota yayitareda fincike rigar kasan capet din ya kuma kwantar da ita yakasa bude baki ma yayi magana kallon shi kawai takeyi ganin yanda yake sarrafata yasa taji tausayinshi ta sakemai jikinta sosai domin tana jin dadin. Wasan nashi sosai, ya ware kafarta ya fincike d'an kamfen tareda kuma sauke kanshi domin kuma shakar kamshin dake fisgar shi a wurin tuni jikinta yafara rawa kardai zaiyi Abinda Aunty maryam tafada mata dazu, Ai kuwa wani irin ihu ta saki domin jin wani irin salo da bata taba jin irinshiba wani irin tsotsar yakeyi ka mar yasamu sweet ture kanshi takeyi tana rokonshi "please kabari zan mutu taketa fada tareda kokarin janye jikinta tana ture kanshi saidai ina yaki bata dama rike cinyoyinta yayi gam, tanajin yanda take bulbulowa Amma yaki cire bakinshi a wurin saida ya sa tayi lakwas kafin ya barta ya sudeta tas kafin ya koma saman kirjinta yafara basu wuta, saida tafara rokon yabarta ya girgiza kai, "Kibarni kawai yake iya fada duk ya rikice, saida ya matseta gam har kashinta nakara kafin ya koma ya zube yana kallon ta cikin wani irin so da yake mata, tareda shafo sumar kanta, "love you more and more wife, Saida yadan daidaita ya sunkuceta suka je wanka tare sukayi ya kuma sunkuto ta ya fito da ita da kanshi ya goge mata jikin ta ya zura jallabiya ya fita tashi tayi tareda kwashe kayan shi dayayi fatali dasu tana dariya" lallai ma Wato shi haka yake baruwan shi idan yaso Abu sai yayi wani irin mikewa tsigar jikin ta tayi tunawa da irin Abinda yayi mata yanzu wani irin Sonshi ne ke kara huda mata jiki salon shi na daban ne gaskiya tuni taji kuma ranta yafara baci tunawa da kila shiyasa mata ke makale mai tunda ya iya haukata mace a gado da romance kawai, she feel very jealous data tuna, a tsaye yake yana kallonta tareda nazarin yanda take fara a tareda kuma sauya war fuskar ta zuwa sadness, Hankali ya Ajiye ledodin manya da yadakko a mota ya rungume ta ta baya a hankali tareda zare towel din jikinta, tayi saurin shigewa jikinshi, "me ya baki farin ciki daga farko kuma daga baya kuma fuskar ki ta sauya zuwa bakin ciki, kinsan banason ganin sadness a idanun ki, ? I want you to be happy All the time kifadamin duk Abinda kikeso I will do it for you baby, ba bata lokaci ta fadamai abinda yake damunta, "Suma haka kake musu? " me nake musu? Kuma suwaye? " Y'an matan ka, ta fada kai tsaye, " menake musu yafada cikin wani irin jin dadin ganin kishin shi a idanun ta "dukan kirjin shi tayi cikan shagwaba "ban saniba tana juyawa tareda juya mai kugu " Ahhhhhh baby yafada tareda saurin fisgota "please kidaina juyamin su haka zaki sa in kwana akanki yau Allah, come and tell me your problem, banza tayi dashi tareda janyo towel zata daura ya fisge "Allah kika rufemin zanyi miki Allah ya isa Kibarni in kalli Abuna. Yafada yana bata wani irin kallo tareda lumshe idanu kamar suyi Aman sparm Kara juya mai tayi tareda sa sauri ta haye gadon ya fisge numfashi tareda binta cikin sassarfa ya cire jallabiyar ya cillar kasa dama towel ne a ciki ya fada jikinta "zaki kasheni baby idan kuna juyamin nafada miki tuni yafara murzata tana nidai banaso ina bakinta ya Kama, tayi saurin kawarda nata "why baby me yafaru? "Kabani Amsar tanbayata, "oh come on letter not now, ta tashi kawai yayi saurin riko hannun ta "Sory baby karki yi fushi dani kinsan yanda nake don haka kiyi hakuri da duk Abinda yafaru a baya lokacin bakya cikin rayuwata ki fuskanci future, Kwantar da ita yayi tareda kissing bakinta saudaya, "wannan ne baki na farko da nafara tsotsa believe me ya kuma tsotsa kadan tareda kuma sauke kanshi kasanta ya bata wani irin soft kiss tareda dawowa "kasanki ne nafara d'an danawa And it test sweet kisa aranki ke kadaice nake kwadayin saduwa dake ina son komai naki baby yafada tareda shafo kirjinta dake tsaye, Tuni taji ranta yayi fari tafara bashi hadin kai tareda shigewa ta manne mai gam, hannun ta ya janyo ya dora Akan jikinshi "hold it tight baby takice ke kadai kece kadai matar da zakiji zakin ta don haka kibani dama in moreki yanda nakeso, aikuwa nan tayi Amfani da shawaran Aunty maryam ta zake tana bashi wasa ta fitar hankali tuni ya rikice mata tareda Alkawura Kala Kala, a daren ya moreta kamar yanda yakeso tsbashi hadin kai sosai duk da taji jiki, saida suka kuma yin wanka ya janyo ledodin da yashigo dasu ya bude wata mai dauke da tanbarin exclusive jewelry ya fito da wata dankareriyar sarkar daham katuwa wadda kana gani kudi yayi magana ya matso tareda mika mata case din "wannan gift dinki ne na Auren mu na first night zaizo idan mun isa kd Tayi matukar godiya tareda jin dadin kyautsr tashi ya bata kiss a kuma tunta dake fitarda murmushi mai burgewa "I want to see this on your face All the time baby you look more pretty when you smile, "oya muyi bacci inada aiki early morning so zankara da safe kafin infita aiki, yafada yana daga mata gira,. Kwanciya sukayi cikin farin ciki bayan ya nuna mata sauran kayan Gayun da ya suyo mata, Da safe Saida ya Ajiye musu kudi mai tsoka yace driver na nan zai kaisu shopping idan sun shirya, ai kuwa ranar sunsha yawo a garin na Abuja sunyi siyayya sosai sunyiwa yaran su sunji dadin wannan tafiyar sosai, bayan sundawo ne Aunty maryam tace "yasmin mama na gaisheki tace bakya ko kiranta da baba, "wallahi Aunty inason jin muryar su Amma ta ina zanfara kiransu bayan MA ya gama dani, " hhhhhh murjewa zakiyi ai ki fuske mai afkuwa ta auku,   Haka suka shafe sati dayan nan cikeda farin ciki yasmin ta zama y'ar hannu suna kwasar soyayyar su kullum kara manne mata yakeyi tana daurewa sosai ganin ta bashi hakkin shi yadda yakeso ta murje tayi wani irin cikar Amarci takara fresh kullum suna karkashin a c ga cima mai kyau ga kulawar gwarzon mazajen su, sai Ana gobe Zasu koma suna kwance sungama murzar juna ya janyota hannun shi akan kirjinta tace " mine kabarsu haka fa sungaji kaga har girma suka kara, "Ahh aini din banawasa bane hannu na ya kunbura su ai Kibarni in more kayana nawa ne, "Ai idan munkoma kd zangudu gida sai Anyi biki zandawo, saurin tashi zaune yayi tareda matse fuska "baby don't try that please karki Barni ko na dare dayane bazan iya numfashi ba nariga nasaba da dumin jikin ki karki tafi ko ina ki kwana sai tare dani, "ok tafada tana dariya tareda janyo shi "bazan tafiba nima bazan iya nisa da kaiba zumata, rungume ta yayi yana jin dad'i,   Washe gari suka kamo hanyarsu tadawo bayan ya kammala Abinda yakaishi suna kwakume da juna hannun shi a cikin rigarta yana sans ar sai shagwaba take zuba mai sun hakimce a bayan katuwar jeep din da ake daukar shi ac na bugasu, sun isa lfy su Aunty maryam suka shige nasu gidan bayan sun gama magana a tsakanin su matan BARIKI sun zuba musu ido suna kallon su cike da mamakin ganin su Maman Auwal tareda Oga a jeren motocin shi, Tundaga falon ta saki baki domin an canja komai na falon daga purple da bari zuwa blue da fari tsarin yayi kyau sosai ba acewa komai yayi dariya tareda rungume ta ta baya "baby yayi miki gidan? "Wallahi yayi sosai ya burgeni, "tank god tunda kin yaba yafada tareda riko hannun ta suka nufi ciki" muje Kiga cikin, Da jin dad'i ta bishi saidai suna shiga farin cikin ya ya tsaya cak domin ganin wata katuwa kwance akan gadon da yake ikirarin tazo tagani ta baje tana bacci, Kallon shi tayi tareda bashi kallo mai cikeda tanbayoyi Shima fuskar shi ta sauya yakasa cewa komai, "wacece wannan MUHM'D? Ita kumafa wacece ita har cikin bedroom dinka? Tafada hawaye na zubo mata masu d'aci kafin yabata Amsa ta bude idanubta tareda sakkowa cikeda yanga da karairaya, "oh my MA you are back wel.... Yayi saurin tureta "what the hell are you doing in my house impact who give you the right? Yafada cikin karaji, tafara karkada jiki cikeda karuwanci "or relaxed dear my baby gave me the right that your baby in my tomy wani irin kallon yasmin yakeyi dake ja baya tana girgiza kai tareda hawaye masu zafi, ta fita aguje, Matsawa yayi batareda ya iya bintaba don yasan bazata wuce gidan Aunty maryam ba gwara yafara cin uwar wanna karuwar kafin ya koma kanta, "ke Dan ubanki me kikace "baby my baby what baby how? Tell me yafada yana matsota jikin ta tuni yafara rawa ta fara ja baya sorry please ba laifina bane, "no karki fara confess tunyanzu sai naci ubanki tukuna zakiyi bayanin, "no please I will tell you everything please don't beat me, Emanuel ya kwalawa kira ya zo aguje don baisan da zuwan ogan ba ya Sara mai cikeda tsoro musamman ganin wadda ke cikin dakin "heee I tink I tell you to go Oga no day so you no go you come enter Oga.... "Keep quit my friend, yafada cikin tsawa don hankalinshi yayi mugun tashi ganin tashin hankalin Yasmin, wurga mai belt din yayi tareda komawa gefe ya ce idan baiganta a sume ba sai shi ya koreshi a aiki, Ai tuni Emanuel mugu ya zage ya hada mata jini harda majina kafin ya kwasheta ya watsata a waje don ba belt ba har da kafa da hannu ya saka mata don datayi mai sanadin aiki gwara shi yayi Ajalinta, ya dawo yace daga yau yadaina zuwa gidan shi baya bukatar shi tunda bai iya tsaremai gida, yana kuka yana rokonshi ya ce yafita kawai , yabarshi da bala inda ya janyomai , Yasmin nafita Jakarta kawai ya fisga ta fice da gudu ko Aunty maryam bata nema ba ta tari mashin tace ya kaita bakin titi, tana sauka ta zaro dubu daya tabashi ko canji bata nema ba ta tare wani ta haye, yanata godiya, tace Unguwar dosa batareda tunanin komai ba ta manta yanda tabar gidan ma.........   *Afuwan my fans hannu na naciwo typing ba kullum zanrika yiba kuyi hakuri* [9/9, 6:47 PM] Asli Smasher : *BARIKI* Auren Soja   Written by FENERH *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby *This one's special for you my father 80k Allah ya karo din bin jama a da kuma hakuri dasu jinjinar bangirma tsoho mai rankarfe*   43&44 MA na gama korar Emanuel ya fito cikin sauri tareda nufar kofar gidan Aunty maryam nocking yayi Ahmad da ko zama baoyiba ya fito, ganin ogan nashi a birkice ya fara tanbayar akwai matsala ne? "First tell me ina matata? "Ai bata shigo ba, dafe kanshi yayi cikeda jin matsanan cin haushi ya naushi iska, tareda kallon Ahmad " look ka yi ma good for noting din yaran nan da ka Ajiyemin a kofar gida da basuda Amfani am taking this bull sheet for years wallahi if something happens to my wife I want spare them yazasu rika barin ko wace shegiya cikin gidana koda can ai sai wadda nayi ra ayi bare yanzu da bana bukatar ko wace karuwa Wallahi duk shegiyarda nagani Ariyar gidana sunan ta gawa, Ya juya fuu batareda Ahmad ya ce tak ba, saida ya wuce yasamu sojojin Shima ya nuna nashi girman ta wurin basu warning, kafin ya koma cikin gidan yana fadawa maryam, "Amma dai Yasmin akwai wawuya wallahi Meye na wani tafiya don iskanci a haka zatayi nata Rayuwar Auren, "ki kirata first kiji dalili don Oga ihu kawai ya saukemin ban gane me yafaru ba, MA falon shi ya koma kamar yayi ihu saboda takaici "why baby why zaki tafi just for small issue,, "ga wayarta ya kira taki dagawa wani irin jifa yayi da wayar tareda dagargajewa lokaci daya ya haye saman shi saida ya canja kaya kafin ya fita kotakan driver bai bi ba ya fada motar ya fisgeta, Kofar gida mashin ya Ajiye ta tabiyashi tareda fadawa gidan ba tareda tunanin komai ba, saidai tana shiga taci karo da baba da y'ar butar shi zaiyi Alwala, tuni ta dawo hayyacin ta tareda natsa kanta kadan " waye haka kamar mamana? " ni ni c ce baba ta fada cike da jarumta da kuma rawar baki " yanzu nake cewa azo a kai miki motar ki gidanki tunda kinkai kanki, shiru tayi takasa cewa komai jikinta na rawa mama ta fito itama ta zuba mata ido " aa kaga Amaren zamani daga ina haka da yamman nan? Matsawa ciki tayi jikinta yayi mugun sanyi ta gaida su tareda shigewa dakin mama ta zauna, " malam lfy kuwa wannan yarinya? "Aa kalau take jedai kiji bakya ganin yanda ta murje tayi wani bulbul cikin sati guda Inba lfy ai a jeme zaki ganta, dakin mama tashiga baba ya fita masallaci Abinshi, itama bata koma kanta ba saida tayi sallar kafin tace kije kiyi salla ko bakyayi ne? Ita kadai tasan irin kishin dake cin zuciyar ta kanta wani irin ciwo yake mata kamar ya tsage, a haka ta mike cikeda tangadi ta fita, saida ta shiga tsohon dakin su tayi salla tareda canja kayan jikinta ta dawo dakin mama, Zama tayi tareda dafe kanta tana hango wata katuwa wai da cikin mijin ta bayan ya fada mata bai taba sex da wata ba to ina aka samu ciki,? Cikin hikima mama tafara yimata tanbaya domin tana hango tsantsar damuwa a idon nata, "ya me yafaru daga dawowar ku kidawo gida? "Bakomai dama wayau ya mun yasa aka kaini gidan shi, ," yanzu me kika dawoyi? "Haba mama nima ina son nima akaini kamar kowace mace mai daraja wallahi bazan koma ba sai Anyimin biki nima kuma ankaini kamar kowacce AMARYA   "Hmmm yaro ho to yanzu kikasan da hakan ko akwai matsala ne tsakanin ku? "Bakomai ni inaso don Allah mama ki taimakeni ko yazo ku hana inkoma sai anyi bikin don Allah kodan mutunci na, "Yasmin kifada min menene matsalar? "Kifadamin ko kinada Wanda zaki fadawa sama dani? "Aa tace "to kifadamin ni uwace nasan mafita, badon taso ba ta fadawa mama komai tareda bata d'an labarin MA kadan, "Hmm Wanda yasai rariya yasan zata zubda ruwa Amma bakomai zamu gyara shi karki sake ki kuma guduwa daga gidan ki idan kin koma saboda wata karuwa ki tsaya ki kwaci yancin mijin ki wata kila sharri ne kawai saboda jin haushin bai Aure suba "Don haka kidage ki kwato mijinki daga kadan garun BARIKI, ta danji sanyi sosai zantawar da tayi da mahaifiyar ta har ta rage jin damuwar Abin A ranta, sai maganar sharri da mama tace what if sharri ne? Dafe goshin ta tayi koma Meye bazata koma ba sai ta saita shi yanda ko gobe bazai yi wani gangancin ba, Baba yadawo mama ta fara yimai maganar mijin ta ne yace ta dawo har Ayi bikin tukuna don haka kusa rana, "Wallahi wannan yaron saudatu sai A hankali yanzu sai bayan sun kwashe sati daya shine zai dawomin da y'ar wai wani biki, "to ai dole hakuri zakuyi ayi hakan bambami Kala Kala baba yayi kafin yayi shiru mama ko tak bata cemai ba yayi ya gama Yasmin kuwa KO mawa tayi dakinta dama tanajin fadan baba, wayar shi ya ciro ya kira baban zango " mamuda surikin ka Wallahi baida mutunci yafara fada mai komai kafin baban zango Yace "to Yaya yanzu ya kakeson Ayi? "Ya kuwa za Ayi nidai banida isassun kudi yanzu na wani biki " tom zanzo mu ga yanda zamuyi,.   MA na fitowa da nufin zuwa gidan nasu aka kirashi office baida zabi dole ya tafi, saidai bacin ranshi ya kara karuwa jin wai zai kwashe rundunar shi zuwa birnin gwari nan da kwana biyu signal ya fito saboda barayin da suka addafi garin, gaba daya ya fita hayya cinshi tafiya daga dawowa kuma ga matsalar datafi kowacce damun shi yanzu yasmin, don haka malali kawai ya wuce ya samu hajiya, bai iya boye boye ba ya fada mata mai ya faru tareda bayyana mata komai na Rayuwar shi ta BARIKI, "yayi kyau ai yanzu gwara da ta tafi kuma bari kaji karka sake ka koma gidan su har sai Anyi mata biki kamar kowacce y'ar Gata don haka bana sonjin wani Abu daga gareka idan ka ga dama ka koma kaci gaba da bin karuwan kuma wallahi in har maganar cikin nan tana nan kuma naka ne baba na bazan yafe maka ba babu shege a zuri ar mu don haka bazaka gurbata min tawa zuri ar ba shiyasa kakiyin Aure tun tuni a she har gida kake kawosu ko, . Ranar yayi nadamar Rayuwar BARIKI don bacin ran mahaifiyar shi kawai ya isheshi ishara bare aje kan Yasmin da tariga tasani bazai iya second daya batareda ita ba shine take neman ta daga mai hankali gashi hajiyar shi ta yimai gargadi, dole yaje yaganta ko zai iya bacci yau,   A kofar gidan ya faka tareda yin sallama kai tsaye lokacin suna zaune a falon mama suna hira tareda cin danbun naman da mama tayi Mai shegen dad'i na. Kaza yayi sallama a tsakar gidan, tana jin muryar shi ta matse fuska tareda gyara zama dakyau don ta kara daga mai hankali, Baba ne ya fita tareda bashi kujera suka zauna gaishe shi yayi cikin girma ma wa, mama ma tafito suka gaisa ta koma cikin falon gaba daya hankalin shi na wurin son ganin ta don yasan tana gidan   Kwanciyar ta ma tayi a falon tareda runtse idanun ta tanajin muryar shi Tanason kallon kyakkyawar fuskar shi Amma Tanason ta nuna mai ita ba kamar sauran mata bace tanaso ta nuna mai ita Mai mutunci ce kuma y'ar gidan mutunci yanda nan gaba dole zai tsare mata mutuncin gidan ta na Aure, kasa har kusan Karfe goma ya yi musu sallama zai tafi a gidan yaci Abinci sukaje har massalaci tareda baba Amma bai sata a idoba mama saida taji tausayin yanda duk yayi sanyi gaba daya baya tareda walwalar shi kamar yanda ta lura dashi akoda yaushe, Son ta yakeson yi ita kawai yakeson gani he is missing he want to kiss her swwt lips hug her impact he really need his wife yariga yasaba da jikinta bazai iya daurewa ba, har ya fita ya kuma dawowa "mama don Allah yasmin fa tunda nazo banganta ba, "ai bacci takeyi tundazu ko intaso tane? "Aa yace badon yaso hakan ba ya tafi cikeda damuwa tun a hanya ya gwada kiranta kota bude wayar yaci sa a wayar na bude ta hau wtsp Aunty maryam na mata magana tafada mata kudurin ta ta goyi bayanta itama bayan ta mata fadan rashin zuwa gidan nata ta fada mata, "Aunty nasan bazaki Barni intafi ba shiyasa kawai kuma raina ya 'b'aci yanzu inda gaske ne cikin nashi takeda shi ya zanyi? "Ba gaskiya bane baban Auwal yayi bincike yagano cewar ba gaskiya bane zuby ce ta aiko ta don ta bata zamanku kuma tayi nasara don haka ki shirya next time kiyi maganin Abin karki bari su sami nasara akanki anzo mishi da cikin karya bakisan dame za azomishi wani karon ba kuma,   Ganin kiran shi da ya shigo tace "Aunty yana kirana, "kidauka ni bari inje wurin nawa mijin, picking tayi bayan ya katse ya kuma kira tayi Mai shiru "Ajiyar zuciya ya sauke tareda cewa "baby meyasa zaki nemi bani horo mai tsanani,? Kinsan bazan iya dauka ba shine kike son bani wahala why zaki gujeni a lokacin da nafi bukatar ki? Kinsan jikina yasaba da naki why zaki tafi Kibarni akan Abinda ni nasan sharri ne maniyyina bai taba ratsa mutuncin kowace mace ba sai ke don't you understand your husband is a virgin like you, kece kika bareni nima a Leda baby believe me,   Shiru tayi Mai batareda ta bashi Amsa ba "Fatima please gobe da safe zanzo inganki don Allah kifito inganki kafin inje aiki ni yau bansan yazanyi bacci ba ma batareda keba, inada tafiya jibi zuwa birnin gwari ki bari gobe inganki, please " saikazo tafada tareda kashe kiran, yasamu y'ar natsuwa da yaji sautin ta karasa gidan shi a ranar bai iya runtsawq ba sai juyi kawai yakeyi "zuby ta cuceshi ta hana mai farin cikin shi na dare daya da yafi na dare dubu tsawo a gurin shi,   Itama Yasmin haka ta kwana juyi don tasaba da jin hannun shi akoda yaushe cikin jikinta yana ya mutsata a sati dayan nan tasaba dashi ya mugun yiwa jikinta illa ya mata mugun sabo, tuni tafara mishi tana juyi tunowa da irin dad in da yake jiyar da ita MA namiji ne da ake kirada namijin Zuma ya iya tafiyarda Rayuwar mace a ko ina dare da rana dole mata su makale mishi yanada qualities da yawa da sukadai sun isa su ruda mace basai anje gado ba,   Kusan Karfe biyu ya kirata tayi zurfi cikin tunanin shi taji karar wayar shi dauka tayi ba bata lokaci ta saka a kunnen ta cikin yin kasa da murya tace "lfy bakayi bacci ba? "Tanbaya ta kikeyi baby? Ke me yahanaki bacci? Kin jamun damuwa baby bazan boye miki ba meyasa zaki bani irin wannan wahalar? I can't sleep today meyasa zaki nisanceni bayan kinsan jikina yasaba da naki hannu na suna kwadayin taba nonuwanki baby miyauna na missing naki why zaki wahalar dani "mika tayi a hankali domin saida tsigar jikinta ya tashi magan ganunshi suntaba ta ya iya rudata da kalaman shi, Mika yayi Shima "baby kinsa kaya yau? "Um tace kawai don yagama kasheta da dirty talk dinshi "wane iri kikasa? "Zani kawai na daura zafi nakeji, ta tafada cikeda fisgo magana "kidaina daura Zani akan kirji karki zubarmin dasu, "Ahhh baby jibi zanyi tafiya gashi hajiya ta hana ni dawo dake wai sai Anyi biki kuma jibi zamuje birnin gwari yanzu sai nadawo za ayi bikin mu kitare kenan? "Gsky zan wahala da yawa kuma hajiya ta yi fushi da sai na daukeki mungudu Allah, "Ina zaka kaini? Can zamuje tare " tab wurin barayin? "Ba muna tareba noting will happen mijin ki nq nan , har saida Asuba tayi sukayi sallama domin yin salla tareda fada mata zai zo ta fadawa mama zaisha kokon ta da kosai, tace tom, taji dad in yanda hajiya ta saka baki a lamarin da yanzu ya sungumeta ya gudu again,   Karfe goma tayiwa baban zango a gidan domin tattauna biki "to yanzu me za a siya Saude? Ya tanbayi mama "Aa ai maganar kuce ko ka nemi hindatu itace uwar ya, to nidai. ga kudin nan asan nayi yarinya dai dole mufitar da ita kunya, baba ya zubawa tulin kudin da ya juyesu cikin gari yayi zafi ya zaro idanu "ina kasamu kudi mamuda? "Ai jiya muna gama magana dakai na kira dillalai mukayi cinikin filayen nan da na wurin gwaggon mu da kuma na wurinka muka kammala komai tunda safe kudi suka shigo hannu na don haka musan nayi ayi a wuce wurin,   "Amma dai mamuda kagama dani ni nafada maka inason sayarda filina filin da zaiyi miliyan uku kasayar kuma namu na wurin gwaggon mu da yayi miliyan da rabi nawa kasayarda su duka? Yanzu kai yazaka dauki gadon mu nidakai kasa a kasuwa su sauran yarafa ga ismail gasu hajara duk suna cikin gadon mu sai a kashe su akan mutum guda, "Yaya nidai na siyar kuma filinka tsakani da Allah nawa ka sayeshi? Lokacin can"dubu Dari biyar da hamsin' " to ka godewa Allah ansiya miliyan daya kaci ribar hudu da biyar sai na wurin gwaggon mu Dari tara kaga nawa kenan, kace fa bakada kudi me kakeson muyi munada kadara basai tamana rana ba, don haka gado da kujeru Y'an yayi nake so a sakawa y'ata, mama daki ta shiga tana dariyar wa innan Y'an Uwa biyu da kullum dramar su bata karewa tana mutunta mamuda kodan zumuncin shi da fadar gaskiya yi yake da zuciya daya ba algus a zuciyar bawan Allah, su biyu kadai Amma sunada fahimtar junan su,   Yasmin ma tanajin su tayi dariya tareda kara kaunar kanin mahaifin nata nan ya kara jin kunyar rashin Auren jinin shi da basuyi ba ga matar shi ma dai dai da halinshi itakam sai godiya, ita ta fito sanye cikin doguwar Riga baka mai stone tana sheki ta yafa karamin gyalenta ta tsuguna tareda gaishe da baban zango yace 'Allah ya miki Albarka mamana ina soja? Dukar da kanta kawai tayi takasa Amsawa saboda kunya, ta hado mai kari don tasan idan yazo gidan to sai ya ci Karin mama yake tafiya,   Karfe goma sha daya MA ya iso tareda Ahmed suka shigo wannan karon suka zauna a kaci gaba da hirar Rayuwa kafin suyi maganar da ta kawo baban " to yanzu mudai mun shirya zuwa sati mai zuwa sai ayi bikin tarewar ko me kuka ce? "Eh gaskiya naso da yau ta koma ne don zanyi tafiya gobe, yafada musu kuma bazasu dawoba sai karshen wata,, baba yace to in haka ne sai a bari idan kadawo sai Ayi bikin ta tare zsifi cikin natsuwa, ba haka yasoba gsky Amma yazaiyi hajiya ko yau saida ta gargadeshi da zancen tsaurin idon nan na rashin kunya, dole ya hakura tareda fada musu za akawo lefe jibi,   Wayar shi ya ciro tareda tura mata text "baby kina ina? Ta bashi Amsa da "dakina kawai, ya mike yana sosa keya ya nufi kofar dakin "Ahmad kamar ya nutse kasa gaskiya Oga karshen rashin kunya ne, shikuwa gaskiya ya matsu ya ganta he can't take it anymore, ta mugun firgita jin sallamar shi a kofar dakin ta zabura cikeda tsoro "na shiga uku wani irin kallo yake kare mata tundaga kasa har sama cikeda kewar ganin ta na kwana daya ya nufeta cikin sauri kafin tace wani Abu ya rungume ta tareda hade bakinsu wuri daya ya kuma tura hannun shi ta saman kirjinta,   "Ahh yaja mugun numfashi tareda wani irin gurnanin fitina "babyyyy yaja sunan bayan ya cire bakinshi da a nata "ya zanyi am in need very badly touch me and feel my body is getting hotter, am going tomorrow gashi wai tarewarki sai nadawo bazan iyaba baby Allah I can't, tausayinshi taji duk da irin shigoma matan da yayi ta raba jikinsu tareda ciro hannun shi a jikinta tace "me yasa ka shigo? "You are my wife now I have the right, shiru tayi tareda cewa "bari inkawo ma breakfast din ko Kayi? "No bring it, to kafito waje mana, "no ki kalli jikina inna fita su baba zasu gani yafada tareda nuna mata wandonshi tayi saurin fita tana jinjina Rayuwar MA,   Baba shiru kawai yayi daga baya ma mikewa yayi yace "muje ko mamuda muga baba liman don dole mu nemi shawarr shi, don bayason ganin wata rashin kunyar sukabar Ahmed dake rikeda yaron shi yana mishi wasa don ya gujesu yazama Dan gidan mama, daga karshe ma fitar su sukayi ya sakashi a mota yace muje insiya maka sweet, Zubewa MA yayi akan katifar ta tareda sauke gurnani yana danne marar shi cikeda tsananin feelings ina he can't bazai yarda ba gaskiya, Koda ta fito duk sun fice mama dama baccin ta takoma yi batama san shigowar su ba, saida ta kawomai komai yana kife yana jin marar shi ta mugun daurewa saida ta Ajiye tayi Mai magana "gashi nakawo, juyowa yayi idanun shi gaba daya sun kankance ya kalleta cikeda fitina "ina Ahmad? Baya nan yafita, ta bashi Amsa "su baba fa? Suma bangansu ba, "mama bata gidan ne? "Bacci takeyi tundazu, good ya fada tareda mikewa yana hada hanya ta zuba mai ido tareda binshi da kallon me zaiyi, ganin ya garkame mata kofa yasa ta zaro idanun ta "Meye haka kakeyi Meye na kulle min kofa? Idan wani yayi tunanin wani Abu mike... Maganar ta kafewa tayi ganin yayi wurgi da kayan jikinshi tareda barin guntun wando kawai yana nufota yakeyin komai cikin zafi zafi,   "Ki daina min taibayoyi kawai kimatso kiji dani Aike kikaja koma Meye don haka wallahi kisan nayi,......     Na boni wannan shawar Ummu jidda ce don na lura itama uwar dakin MA ce don haka nayi nan,   *Matar Soja* [9/10, 9:26 PM] Asli Smasher : *BARIKI* _Auren Soja_   Written by FENERH   *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby   *Addu a agareku tareda dumbin godiya zuwa ga fan's din BARIKI Auren Soja ina matukar jinjinawq kokarin ku na bani goyon baya ta hanyar zafafan Addu oin ku ina matukar godiya Allah ya karo kauna mai yawa masoya*   45&46 Ja da baya tayi tareda fitoda kyawawan idanun ta "please mana MUHM'D Meye haka don girman Allah a gidan mu kake shirin jamun wani Abin kunyar bayan Wanda Kayi a baya? Fisgota yayi cikin karfi "come on my friend karki bata min lokaci harsu baba su dawo, wurgata kawai yayi kan katifar batareda ya bata damar kuma furta komai ba ya hade bakin su tuni na gudu nabar dakin ganin da gaske yi zaiyi a cikin gidan surukai,     Saida ya murjeta na minti talatin kafin ya barta ya koma gefe yana maida numfashi tareda riko hannun ta cike da gamsuwa ya bata kiss itadai kallon shi tayi tareda cewa "tunda Kayi son ranka ka tashi kamayar da kayan ka kafita don Allah kafin mama ko su baba sudawo, "munyi son ranmu dai baby kema fa kinaso banason gulma kitashi muje muyi wanka kafin intafi, zabura tayi tana mai wani irin kallo "in wasa kakeyi kadaina please katashi don Allah, "kinsan dai banason zama da najasa ko kaje gida Kayi wanka nidai katashi ta mike tareda janyo zanin gadon ta domin rufe jikinta ya fisge tareda zubawa kirjinta ido "kinsan banason kina min boyon kayana ko Meye na rufe min jikin ki bayan har ciki na shiga nayi iyo,   Itadai kokarin take taga yatashi kafin yakaita ga kunya kayan shi ta mikamai ya tashi zaune tareda zuba ma jikinshi da ya baci da sparm ido, ya yatsine fuska, "kizo ki goge min wannan Abin baby, yafada yana mata wani irin salon kallo, batada da zabi don haka towel dinta ta janyo tareda gogemai yana runtse idanun shi "Allah ban koshiba baby zan dawo da dare in kara kafin in tafi gobe, Kinga zanyi kewarki fa sosai zanyi sati kafin inshigo ko sati biyu, idan nadawo zaki tare gidana so you have to be ready baby kinsan waye mijinki me yasa zaki daga hankalin ki akan wata y'ar iska no matter what kece matata kece na Aura su bakya ganin bakin ciki suke miki, and so what idan Kinga wata da ciki tace nawa ne baki yarda da mijinkiba baby that's why, "any way nasan dama kallon d'an iska mai kwaso mata kike min ko yes inada Y'an mata Kala Kala Wasu ni keneman su Wasu suke nema na and don't blame me for that kaddara tace hakan but believe in me duk Abinda nayi baya I want repeat it again insha Allah, Amma inaso kizama strong woman be like a soldier wife ki zama jaruma yanda nasanki now you are weak because of my love, yafada yana janyota dakyau zuwa jikinshi, Zaki fara koyan mota fa na sa ayi miki booking a driving school don haka zan Ajiye miki driver da zai rika kaiki banason matana a motar haya, "wait a minutes a me kika dawo gida jiya? Yafada tareda zuba mata ido cike da tuhuma, "mashin ta fada kai tsaye, ya bata rai tareda mata mugun kallon da bai taba yimata shiba, "matana a bayan wani kato how dare you yanzu haka kika hau bayan wani kazaki kirjinki na gogar. bayan shi kina matsayin matata, impact let me make it clear to you daga yau idan zaki fita idan baki iya mota ba ki jira duk inda driver yake yazo in ba hakaba Allah bazan yafe miki ba, ya fada cike da kishi tareda rufewar idanu ya zura kayanshi ya fita, Bayan shi tabi da kallo tareda yin dariya ya mugun bata dariya waishi kishi, saurin zura katon hijabi tayi tareda fita ta hada ruwan wanka cikin sauri ta tsalkake jikinta ta fito tana mai fitarda wani irin Annuri a fuskar ta "I love that shameless man, ta yi sa a har ya fita mama bata tashiba cikin sauri ta fara kokarin shirya musu lunch,   Shi kuwa yana fita ya haduda Ahmad ya dawo yace yaje ya kaishi gida yayi wanka kafin su koma office, kallon mamaki Ahmad yabishi dashi kallo ba halin tanbaya lallai in har Abinda yake tunani yafaru to Oga karshe ne a duniyanci, tare ya tafi da d'an shi Shima domin gwara Shima ya dana rashin kunyar don yana bukatar d'an shi a kusa dashi, saidai mama ta shafa taji shiru,   Maryam tayi mamakin ganin shi da Auwal din tace dakko shi Kayi? "Gashi kingani zahiri gaskiya baka kyauta ba sun gama shakuwa dashi zaka rabosu da shi, "ah ai gwara ni da Oga, "me yayi ogan? Kema kinsan halin shi yanzufa wanka yace min zaiyi bayan bai dade dayiba muka fita, yagama bata labarin komai tayi dariya "shine dai dai da yasmin din, yaron ta mikawa hannu tuni yasa mata kuka shi a mayarda shi mama, "To nima inada yarinya ta ka mayar musu da d'an su baya bukatar mu,   ************* Mama na tashi ta fara tanbayar Auwal "Yasmin ina yarona? ", ai sunfita da babanshi kila ya dauke kayanshi, "hmm Allah ya kyauta zamani muna fama da surukai, dariya yasmin tayi ta reda cewa a zuciyar ta rashin kunya ya wuce namu ai Ahmad yasan kunya, Bacci ta kwanta bayan ta kammala komai sai karfe biyu ta tashi a makare ta yi wanka tayi sallah tafito jin hayaniyar mutane a gidan nasu,   Su mama hindatu ne da Wasu Y'an uwansu na zango sukazo domin karbar kayan Auren nata da batasan da zancen ba tana isowa ta dukar da kanta cikeda jin kunya ta gaidasu mama hindatu tafara yimata tsiya ", kaga Amaryar zamani lefe bayan ta kai kanta to bari mujira muga Amaryar da za ayi biki da ciki, "kai hinde wani irin ciki kuma? Daya daga cikin su ta fada, "to zakuce na fada muku muje zuwa irin wannan kyalli da takeyi ai daga gani na kusa samun wani jika, "saikace wasan yara yaushe akayi Abin bare har ciki ya samu, ? "Nabar zancen yaya Saude, shiru kawai tayi musu tana jin suna zancen su itada ta kusa ganin ma Al adarrta suke zancen ciki yaushe nema suka fara saduwar da Har za a hango mata ciki, MA bai samu kanshi ba a yau saboda shirin tafiyar su tunda ya koma office suke kaida kawowa naganin sojojin shi sun shirya sosai domin tunkarar mugayen barayin, Y'an Uwan shi ma koda suka kirashi zasu kai kayan motoci kawai ya bada yace aje a kaisu gidan, Kamar shine ke shigowa Unguwar motocine guda goma a jere guda biyu sababbi wa inda aka zubo kayan Aciki sauran kuwa Y'an Uwan shi ne tareda escorts din shi dake take mai baya,   Kasan cewar falon baba yafi girma nan suka bude musu aka gyara Aunty maryam ma tazo suma sun hadu harda Zainab din ismail tazo domin tarbar kayan yasmin Y'an Uwa sun shirya musu tarba irin ta Al Ada, mama hindatu uwar gayya tuni ta mike tareda musu tarbar girma su Aunty Halima dukan su sukazo kawo lefen na kanin nasu guda daya tal, sunyi matukar yabawa da tarbar girman da suka gani daga gidan na su yasmin, Umarni Babba yaya ta bada aka fara shigo da akwatuna, sojojin ne suka rika jido su ana jera su a tsakiyar falon tuni tsoro ya rufe su ganin Anshigo da saiti shida kuma ana kokarin shigo da na bakwai ai tuni mama hindatu da Wasu tsoffi suka fara rangada guda suna shewa "Allah mai iko ya' tayi goshi tubarkallah, saida su yaya Halima suka fitoda key na sabbin motoci guda biyu suka Ajiye masu bayan manyan gana most go guda uku na kayan sa lalle, Ai su mama tuni sun rasa ta cewa sai kallo kayan ma sun rasa Wanda zasu bude sai karamar kit guda daya da su yaya Halima suka mikawa mama hindatu "ku adana wa innan gold dinta ne a ciki, ai tuni mama hindatu ta karbe tace sosai kuwa kodan mutane wannan basai annu nasu ba gaskiya, ga motocin ta can a waje za a wuce mata dasu gidanta idan kungani, ai guda kamar zasu cire kunnen mutane a ranar, saboda farin ciki ganin kayan, "Ina Amaryar tamu take ne? Suka tanbaya, "ai ta gudu tunda ta gano kan zancen, "dariya sukayi saikace a kauye Aida ta tsaya munga matar Autan hajiya, bayan ma mara kunyar ya gama dauketa saida ga baya yace wani biki Ai baban hajiya sai a hankali ba ruwan shi da kunya sai kunyi hakuri da surukin ku, "aa kubarshi zamanin sune watarana sai labari, Sun yi hira sosai kafin sutashi tafiya cikeda kayan soye soye na Y'an kawo lefe manyan robobi da kuma carton carton na drinks dai dai karfin su sukayita godiya batareda sun raina musu ba kudi dai suka ki karba sukace basai sun basuba wallahi Allah dai ya karo musu d'an kon zumunci tareda zaman Lafiya a tsakanin ma auratan,   Bayan sun tafi su mama suka baje kayan abin ba a cewa komai ko lefen Zara sai haka don kayan ciki kawai sai sun girgiza mutum bare gwalagwalan da aka zubo, fada bata bakine ai, su baba kam kasa cewa komai sukayi, mama hindatu ce tace a fadawa mijin kawai ya kwashe kayan ya kai gidan ta yafi gudun mutane ko Barayi tunda anriga ansan tayi aure basai An tsaya kiran mutane suzo ganin kaya ba Baban zango yace "haka ne har motocin ma ai zasu kawo mana Barayi BMW ce fa daya kuma crv4 ce ina zamu Ajiye su anan a biyo dare don haka zan jira zuwan shi sai ya kwashe su, baba dai cewa yayi kaya sunyi yawa anyi riya "baruwan ka yaya matar shi ce duk Abinda yayi mata yanzu bamuda ta cewa don kowa ya shaida sun tara tunda ya dauketa na tsawon sati guda, "tabbas kuwa kilama da rabo, inji mama hindatu,   Ita kanta Yasmin ta tsorata da irin dukiyar da aka kawo mata wai lefe takasa cewa komai tasan MA na matukar sonta kodan irin rawar kafar da yake nunawa akanta ya isa ta gamsu 100% yana mata so mai tsanani da ace ya Aureta domin manufa ne da yanzu da yasamu Abinda yakeso da tuni ya barta kamar sauran mata , wani irin kaunar shi taji ta kara ratsa ko ina na jikinta ta koma dakinta ta kwanta tareda rufe idanun ta "me zata yimai domin farantamai itama? Me zata yiwa MA yasan cewa tana mai so kila fiyeda ma Wanda yake mata, gaba daya tunanin shi ya shigeta bataji shigowar Aunty maryam ba saida ta dafata ta tashi zaune tareda rungume Aunty maryam tasa mata kuka, "Ikon Allah Meye na kuka kuma keda zaki yi farin ciki yasmin, "Wallahi you are very lucky samun miji irin Oga MA sai an tona kinga motocin ki kuwa yanzufa motocin ki uku yasmin ko sarkokin ki kawai sun isa su sai gidan mu uku Amma duka ke Kadai ba Abinda zanfada miki Yasmin sai dai ki kara hakuri tareda yimai biyayya akan duk Abinda bai kauce hanya ba "Aunty nasani wallahi me zanyi mai infarantamai rai yau Aunty? "Zokiji ta fada mata tana mai mata rada a kunne ido ta dago tareda zaro ido Aunty su mama fa,? "Ki share kawai baby kije gobe fa zai tafi, shiru tayi kawai kafin ta zabura ta ciro wata Riga da wando damammu rigar ta na dauke da rubutu mai kyalli an rubuta lucky me da manyan harafi rigar ta kamata sosai fara sai kuma wandonta pencil baki yana sheki ta cikin shi golden wajen kuma net ne baki ya hadu sosai duk cikin siyayyar da sukayo A Abuja ne data tanada domin yimai Ado, ta gyara kanta dakyau tareda feshe jikinta da turaruka masu mugun kamshi Aunty maryam ta fito da wani Abu ta bata ungo ki matsa da sauri miski ne mai hadi zaki bani lbr idan kin dawo,   Matsawa tayi ba musu dontayi kudurin farantamai rai a yau koda zata mutu kuwa sai ta nuna mai tana Sonshi itama a yau tayi wanka da turaruka Kala Kala tayi light make up tareda saka hijabi mai gyale tasaka plat shoe da jakarshi mai kyau Aunty maryam ta ci wow sis kinganki kuwa matar M.G MUHM'D Abdullah kinfito as matar officer dinki, tace muje intake miki kafin su mama su gane zaki fita, "idan suntanbayeki ina inafa? "Zance kina gidan kawata har yanzu baki dawoba ai ba Wanda yaga shigowarki bayan sunfita ta d'an tsaya tayi shiru, "Aunty ya hana ni hawa mashin fa, waya fada miki mashin zaki hau, ganin yaya ismail a gefe yasa maryam ta karasa tareda gaidashi tace Gata nan yaya, dama ta gama tsara komai yazo yana tsokanar ta "Amaryar general muje inkaiki ranki ya dade tunda ankwala ni da Kasa,   Kunya taji sosai ganin ya manta komai har yana shirin taimakon ta wajen farantawa gwarzon mijin nata bazata manta dashi ba a Rayuwa, shiga tayi Saida suka fara tafiya ta fito da wayarta ta kirashi, ringing daya ya daga, "my only wife, yafada cikin gajiya, "kana ina ne? "Office Amma yanzu zanje gida inyi wanko dole inzo inganki kafin intafi gobe Me zandafa maka? Tafada kai tsaye, "Anything from my wife zanji dadin shi yunwa nakeji gashi na gaji baby tunda nabar wurinki wanka kawai nayi na koma aiki haryanzu gashi ina kai, Ok saikazo ta fada tareda katse kiran, saida ya ismail ya Ajiyeta tareda tsokanar ta ya wuce Abinshi, Kofar gidan ta nufa cikin natsuwa sojan dake kofar gate din cikin sauri ya bude mata tareda Sara mata don yaganeta itace matar ogan, don yanzu basa yarda kowa yashiga saida izinin mai gida wannan kuwa basu isa su hanata ba su jawa kansu,   Gidan tsab yake ba wani datti ko ina fes yake ta kalli katon hoton shi dake katon bangon yana sanye da kaki kanshi ba hula yayi matukar kyau a hoton ma, ta cire hijabinta cikin sauri ta haye dakin shi dake sama domin bata kaunar shiga dakin da ta ga katuwar banzan nan a ciki ajiye wayarta tayi tareda Jakarta akan gadon ta sakko kicin din tasamu akwai komai ta bude freezer ta ciro naman sa ta wanke ta zuba A wuta tareda hada mai spices tareda Yanka Albasa ta watsa saida ya dauki lokaci kafin ta janyo robobin dake dauke da su daddawa dakakkiya mai citta da kayan kamshi, Lafiyayyar miyar kuka ta hada mai cikin lokaci kadan tareda tuwon semo yatuku da kyau ba gudaji kodaya yayi d'anko,   A Leda ta zuba mai tareda zubawa a warmers din dake kitchen din nashi tabar miyar akan gas, tana goge wurin ya dawo lokacin har ta feshe kitchen din da kamshin turaren air freshener , tundaga falon yafara jin kamshi Amma saboda ya gaji yakasa tsayawa domin yasan bakowa agidan may be yunwar da yake ji ne, yasa yakejin kamshi, sama ya haura domin yin wanka yana shiga yaci karo da jakar mace hade da hijabi tuni ranshi ya baci ya sakko cikeda fushi domin cin uwar koma wacece, dai dai zata fito daga kitchen din suka gabza karo yayi saurin tarota tareda zuba mata idanu cikeda tsantsar farin ciki, "baby is that you? "Wow yafada tareda rungume ta cikin murna kamar zai ballata,   Dariya tayi "karka shafi zufa kabarni inyi wanka first am All yours, "really my queen wow, yau kin farantamin rai baby wannan irin surprise wallahi kingama biyana baby, daukarta yayi cak sai saman ya direta tayi saurin sa hannu tafara cire mai rigar cikeda jin kunyar shi ya wani kafeta da ido yana kare ma shigarta kallo, "inason wannan shigar baby komai nawa ya fito, "zanrika yimaka irin shi idan kana so, " da gaske baby? Sosai kuwa tafada tareda shafo fuskar shi, "I love you my hubby so much tank you for everything tafada tareda kara rungume shi, wani irin dadi yaji "why are you thanking me you deserve morethern that my wife kingama bani farin ciki a Rayuwa baby the Amazing first night and this surprise am very happy am lucky to have you as my wife,   Dad'i taji tareda bashi kiss a kumatunshi bayan tayi Dage kadan don tsawon shi ta dariya ya mata "My short wife dukan kirjin shi tayi kadan cikin tsokana yace "Aouch baby it Hurt me, "oh sorry my dear tafada cikin wani irin salon da yakara shagalar dashi wurin kallon ta, muje Kayi wankan your food is ready, "tank you lovely wife, but in one condition, "what? "Muyi tare, "yes sir your anything for you, Gaba daya ta gama bashi mamaki ta juya tareda cire rigarta ta Y'ar a kasa tareda kuma zame wandon jikinta ya zuba mata idanun ta da suka shanye don tsabar jarabarshi data motsa ya zubawa hips dinta ido yaga yanda suka kara tudu kirjinta suna wani kyallin cika tuni ya zauce ya fice a hayyacin shi wajen kallon ta, saida ta kwabe komai ta zubar sannan ta juyo tareda taku tana girgiza mai kirjin cikin salon zautar dashi ta matso kadan tareda shafo fuskar shi ya yi suman tsaye ta juya tana juyamai bayanta tace " muje honey yamma nayi..........         *Matar Soja* [9/13, 8:40 PM] Asli Smasher : *BARIKI* _Auren Soja_   Written by FENERH   *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby   *Daga marubuciya* HARAMTACCIYAR SOYAYYA AUREN SOJA KUSKURE NA YA'YAN GATA NOW BARIKI TYPING........   47&48 Binta kawai yayi kamar wani sakarai tareda jin ko ina na jikinshi na sakewa tareda ruruwa da wutar sha awar ta, bakin kofar bathroom din ya dogare yakasa matsawa nan da can ya zuba ma bayanta ido ko kiftawa baya iyayi saida ta shiga bath tub ta bude mai hannu Alamar yazo, yana hada hanya ya karaso ba bata lokaci ya shiga tareda shigewa cikin jikinta yayi wata irin wawuyar Ajiyar zuciya jin fatar jikinta mai santsi datake karbar gyara ta hadu da jikin shi ga kirjin nan dasuke haukata shi suna tokareshi ai ba bata lokaci ya zame tareda cafkesu tuni ya fara bata wuta tana kara tallabo mai yanda zaiji dadin moreta yanda yakeso, Itama tana yamutsa shi a hankali take shafo kirjinshi mai haukata mata har zuwa marar shi kafin ta karasa gidan gwamnatin shi, Wani irin gurnani ya yi tareda Sakin wata irin shashsheka ya kara manne mata, saida suka murji juna sosai a cikin ruwan kafin suyi wanka, jiyake kamar ya mayar da ita cikin jikinshi ya boyeta tsabar yanda yakejin soyayyar ta na karuwa cikin jinin shi, dakko ta yayi cak ya fito da ita tana makale a kirjin shi ta lafe, yana Ajiyeta a gefen ta kara makale shi taki Sakin wuyan shi, " baby ba inda zanje kawai zan rufe gidan ne banason azo adame mu, sannan ta sakeshi ya fita daure da towel, ta mike ta nufi mirror, hand drayer ta jona tareda baje sumarta tafara busarwa,   Saida ya rufe kofar shigowar kafin ya wuce kitchen din, warmers din ya bude ya yayi murmushi tareda bude tukunyar miyar yasa spoon ya dibo kuka soup din ya sha yana runtse idanun shi saboda test din dadin da ya ratsa mai kwanya, "my wife, yafada cikeda jin dad'i kafin ya rufe ya nufi frij ya dakko musu holandia milk ya hado da cup ya koma saman yana jin yunwa ga kuma best food dinshi Amma bazai iya tsayawa cinshiba bayan ga Abincin da yafi komai dad'i na jiranshi a sama, samun ta yayi tana kokarin dunkule sumar kan nata yayi saurin karasawa bayan ya Ajiye milk din, "nooo karki dunkule min kibarshi haka nafison shi haka inason inji hannu na na yawo a ciki impact idan kintare zanrika kaiki saloon da kaina ko indauki wadda zata rika miki gyaran shi kullum in biyata a wata ina son suma baby ga naki wow baby am the luckiest man ever to have a wife like you kin hada komai da nakeso,   Juyowa tayi tareda dora hannun ta a saman wuyanshi ta sakaloshi tareda Sakin mai murmushi mai kyau tace "nice nayi dace da samun miji one in town, kirjin shi ta shafa har zuwa kan round and small niple dinshi, yayi wani irin mika tareda dora kan shi a kafadar ta "Asshh baby idan kina mun haka zakija koda yaushe inrika danne ki fa, "so Am ready for my husband anytime he needs me, zaro ido yayi tareda zubawa fuskar ta ido, "a you sure? Baby bazan gaji dake ba fa kawai ina tausaya miki ne banason incika takuraki da yawa karki gujeni Amma inkin bani kanki batareda gajiyawa ba kingama da MUHM'D Abdullah sai yanda kikayi dani, yafada cikin kidima don hannun ta yaki tsayuwa wuri daya sai zautashi takeyi bai taba jin dadin hannun wata mace ajikin shi ba kamar nata, magic hand, Nidai nace bawani magic halas kenan ba yanda za ayi ka hada dadin halas da kuma haram Wanda kanayi zuciyar ka na jin tsoro wannan kuwa halalinka ne ko wani yaganka ba komai   A wannan yammaci Yasmin ta kara siye Oga MA da sabbabin salonta da batasan tana dasu ba wani irin manne mata yake karayi kamar wani chewing gum ranar har Wasu hawaye ya rika zubar mata bayan lamura sun lafa, "please baby karki taba barina zan mutu idan narasa ki a rayuwata, zan iya hadiyar zuciya in mutu idan naganki da wani namiji koda magana kika yimai, baby ina kishinki sosai kishi mai tsanani banason wani ya ratsamin zumar da nikadai nakeson shanta, "pray for me in dawo Lafiya muci gaba da Rayuwar mu cikin jin dadi, ina so indawo mu Kasan ce koda yaushe muna tare banason inyi nisa dake, ina son aiki na but today I felt like resigning imbar Aikin saboda ke am scared for the first time am weak,   "You are a soldier wife ki zama jaruma so that idan yaran mu sunzo suma su zama jarumai, saurin tashi yayi tareda yaye Abin rufar ya shafo marar ta "baby ina son inga yarana inason inganki da ciki please kibani babban farin cikin da nake jira yanzu, tashi tayi ta shige jikinshi tareda dora lips dinta a bakinshi ta d'an tsotsa kadan kafin ta cire ta zubamai ido yanda yake kan lashe bakin kamar Wanda yasha Zuma ko sweet "Zuma na ni takace bazan iya Rayuwa da ko wane namiji ba nasaba da kai ka Riga Kayi training dina nasaba da mijina mara kunya I can't be with anyone ba wani namiji da zai bani farin cikin da nake samu daga gareka kaine ruhina ina sonka Muhammad so mai girma I tink na fara sonka tundaga ranar farko danafara ganin ka shiyasa nakejin tsanar ganin kowace mace a kusa da kai ko gidan ka, ko lokacin da kafara kissing dina bawai haushin hakan najiba haushin ganin zuby ne a cikin gidan nan ya bata min rai ina da kishin da yafi naka bazan iya jure ganin ko wace shegiya kusa dakai ba Allah zan iya kisan kai akan ka wata rana, Bakinta yayi saurin kamawa ya tsotsa sosai kafin ya saki cikeda jin dadi, "oh ana sona dama akayita garani ai bansani ba meyasa kike jamun Aji kika wahalar dani kikasani kullum cikin tunani kullum banda sukuni I na hango irin ta asar da zanyi idan aka hanani ke wallahi zan daukeki ba Wanda zai kuma ganin ki, Kinsan har gini nayi miki na musamman yanzu furniture's kawai zasu kawo daga Dubai a zuba gidan na Unguwar rimi, sai nadawo zamuje muyi hutun Amarcin mu a can, "wane Amarci bayan ka shanye romon tun bamu tareba, "waya fada miki ni ko rabin spoon har yanzu ban shaba,   Jin kiran sallar magrib yadawo dasu daga duniyar soyayyar dasuka Lula ta diro cikin sauri, "Zuma bari inyi sauri ba asan fa na fitoba nabar Aunty maryam da jirana, sakko wa yayi Shima yana zubawa kirjinta dake rawa saboda yanda take motsa jikinta, ya matso tareda shafosu, tafiya zakiyi kibarni? Ya fada kamar wani jariri, "Sory honey idan kadawo zamu kasance tare har Abada, sunkutar ta yayi "sai mun kuma wanka kafin muyi salla sai in mayarda ke,   Wanka sukayi ta mayarda kayanta ta saka hijabin ya zubawa jikinta ido tareda kankance ido "haka dama kika fito kuma har wannan gayen ya kawoki ya ganki a haka? "Me nayi? "Kinga yanda kikayi kyau da shigar ga komai ana gani gaskiya nidai gobe zaki fara zuwa koyon moto banason kije ko nan da can da driver kije da kanki idan kin iya kuma banyarda da yawo ba, "ok mijin, tafada tana dariya, ya bata fuska "Am serious niba sakaran miji bane ki boyemin kanki ki kulamin kanki ki tsaremin kanki nabaki Amanar kanki please baby,   "Karka damu ai bazaka dade ba zaka dawo muyi Rayuwar mu tare insha Allah, "pray for me yafada tareda shafo fuskar ta tare sukayi salla ta kawo mai Abin cin yaci sosai itadai fresh milk kawai ta iya sha hankalinta na gida Saida yayi brush ita kuma ta wanke kayan da tabata kafin ta fito ya shirya cikin kanan kaya yay I matukar kyau yana zabga kamshi suka fito shiya bude mata ta shiga kafin ya rufe ya zagayo ya tayar da motar gaba daya jikin shi yayi sanyi bayason ya mayarda ita saiso su kwana tare Amma yasan bazata soba baya son ya bata mata rai don ta faran ta mishi, Har suka isa kofar gidan bai iya ce mata komai ba saidai yana driving cikin kwarewa yana d'an waigota a hankali yana kallon ta ita ma dai hakan ne a wurin ta har ya tsaya ta bude motar zata fito ya rikota gam "sauri kikeyi kin gaji dani ko? "Aa banason A gane naje wurin Kane za aga rashin kunya ta "inaso kizama kalar mijinki ki cire kunya idan har ba Aikin sabo zakiyi ba, you are my wife don haka ba wani kunya tsakanin mu koda anganmu ba komai, Shiru yayi nadan lokaci kafin ya ce "um hope kayan da suka kawo sunyi miki? "Sosai har sunyi yawa ma fa baba yayi fada moto biyu fa kuma ka karo, "uhm ni banida lokacin hawa motocina sai na soja ko na siya bana hawa kinga yanzu inada iyali sai insiya musu Kala Kala su hau idan kinga wata ma kina so just tell me sai akawo miki,   "Dashboard ya bude ya ciro ATM ya saka mata a hannun ta "kirika sa mai a moto gobe za akawo miki kayan Amfanin da kike bukata naci if anything needed just used this and buy ya fada tareda janyo wata ledar a bayan motar "I forget to gave you this, ya mika mata ledar na siya mana waya iri daya idan kin shiga ciki kisaka sim a ciki nayi mata caji cire kwalin wayar tayi ta zuba mai ido wayar da tagani a TV tana burgeta galaxy 20 20, rungume shi tayi tareda godiya, "meye haka don nayima mata na Abu take mun godiya? "Uhm ita matar Ajiya tabawa mijin da bazata gode mai ba? "That's my duty my wife to make you happy banason matata ta rasa komai koda kudina zasu kare kuwa,   "Allah yakara budi, ta fada, Amen wifey, bazan samu shigowa ba but zamuyi waya idan nakoma gida kisa sim din zanje wurin hajiya idan nadawo zamuyi waya, tace "tom kafin ta juya zata fita, ya kuma fisgota bakinsu ya hade nadan lokaci kafin ya saketa yana fesarda numfashi "Sory na zama mayenki bana koshi dake yanzu haka inajin kamar in koma irin dazu you are sweet baby, dariya tayi ta bude motar tana daga mai hannu, yace "wait, daukar ATM din yayi da ta barmai that means bazata dauka ba, "saida ya matsa kusa da ita ya d'an ka mata a hannun ta "yanzu ba da bane ke matata ce you have right over my everything don haka feel free kiyi Amfani da komai nawa, "naga ba Abinda zanyi da kudine what if na kwashe maka kudin ka duka ina fa kashe kudi? Ta fada cikeda tsokana, dariya yayi "oh zaki iya cinye kudin ciki ok "I will see that my current Account hhhh yayi baby idan kika cinye duka inaso inga kinyi kiba kuwa kafin indawo,   Saida ta shige gidan yabi bayanta da kallo kafin ya fada motar ya tafi cikeda jin kewar rabuwa da ita ta mugun lasa mai Zuma mai zaki ta tafi ta barshi da tand'e baki, koda ta shiga gidan gaban ta ya fadi ganin yanda suke baje a tsakar gidan sunata hira, yasa ta dukar da kanta gani ba Aunty maryam da Alama itama ta kama kanta, "yanzu don iskanci yanzu kike dawowa gida Yasmin? Mama ta fara fada "yawon da bakiyi da bakida Aure ba shi zaki tsiri yi yanzu da igiyar Aurenki yanzu da mijin ki yazo nemanki fa me zamuce mai? Ajiyar zuciya ta sauke jin ba agano taba, mama hindatu tace "ya isa yaya Saude tunda gyara taje yi kuma maryam ta fada miki gidan kawarta ne meye na fada,   Hakuri kawai ta bayar ta shige dakin ta saida ta tube kayan jikinta tasa rigar bacci mara hannu Mai silbi batareda ta sa komai ba don zafi takeji, ta dora zani tareda sako hijabi ta fito, gefen mama hindatu ta zauna tace "mama meye akwai yunwa nakeji sosai, "akwai shinkafa da miya kuma tuwo miyar taushe, ya mutsa fuska tayi bataji Abinda take son ciba kitchen din ta wuce ta samu fulawa ta kwaba ta soya wainar fulawa da taji su tarugu da Albasa ta dakko yajin tafarnuwar mama ta zuba ta dakko plate din ta wuce dakinta ta ajiye ta koma dakin mama ta dakko zobo mai sanyi da yaji Abarba dasu cucumber ta koma dakinta ta, saida ta hada wayar da ya kawo mata ta kunna, kamar jira yake kuwa taji ringing, ganin video call ne yake kiranta yasa ta dauka tana dariya tareda janyo plate dinta, Zuba mata ido yayi kawai bai iya cewa komai ba yana kwance akan gadon shi, "yau na kurma zamuyi? "Eh idan har baki cire min hijabin jikin kiba, "oh shine matsalar Oga? ai umarni kawai zaka bayar in aikata, ta kwabe tareda cire zanin ma ya zuba ma kirjin ta ido, wainar ta ta fara ci tana runtse idanun ta saboda dad'i ya mayarda idon shi fuskarta "meye haka kikeci? "Wainar fulawa "shine Abincin ki? "Shi nake sha awar ci kawai, Hmm kawai ya iya cewa yayi shiru "kidaina cin any how food gwara ma naman kazar naki zansa aka wo miki kirika ci, wai ma me kikafi so a Abinci? "Ummmm indomie spaghetti macaroni and,... "Wait sune Abincin kayan basir noo ki rika cin Abinci mai Lafiya bawai kiyita fama da starch ba shiyasa marar ki a shafe a haka zaki dauki ciki? Any way I love it, Saida tasha zobon ta yana kallon ta komai tayi burgeshi take karayi komai nata Abin sone a wurin shi, tace ya jirata ta dawo zatayi brush ta na zuwa, ok kawai yace ta Ajiye batareda tayi cut off ba ta fita tayi brush saboda garlic din da taci ta kuskure bakinta da mouth wash sannan ta dawo bayan takai kayan kitchen, duk sun shige daki sun kwanta, ta rufe nata dakin ta haye gadon tace "Sory nadawo sweet ta bude mai kanshin fruit tace open your mouth, ya bude yana kallon ta ta jefa Abakinta, "zaki biya bashi baby idan nadawo you must pay for that sai na tsotsi sweet abakin ki tunda kika samun rai da Ina kusa harda lips din ma zan cinye, naso mu kwana tare yau baby amma bazamuyi bacci ba zamuyi hira for the last time, "no not last saikace bazamu rika yin waya ba kuma ai bazaku dadeba, "eh zamuyi wata daya zuwa biyu Amma bazan yarda ba nan da one month ina bukatar ki a cikin gidana don haka choose ina kikeson zama barracks ko gidanki? "Duk inda kake bukata nan zamu zauna Oga, "to zaki zauna Unguwar rimi idan nadawo gaba daya mu koma BARIKI tare, "Yes sir ta fada tana dariya, kallon ta kawai yakeyi "wannan kallon fa Oga? "Na so ne da kuma sha awa, ya juya tareda haska mata jikin shi "kinga fa tun dazu haka nike indai zanganki bata taba ha kura ta kwanta "dazu fa ta koshi kusan fa sau uku fa, "uhm kedin ce ai kamar Zuma kike zubawa da madara a ciki baby, yafada yana mika, "kin kama kin rufe min su a Riga ma kibude min ingani please nida kayana, har zata bude ta tuna karon farkon su data cire mai , "aa karka kasa bacci kace zakazo gidan mu da daren nan, "no I want I just want to see ne kawai please, Zame rigar tayi ya zuba musu ido "baby suna responding fa kinga yanda suke kara girma kuwa hannu na akwai magic gaskiya, shagwabe mai fuska tayi "to ai ma zafi sukemin ba ka musu da wasa fa ta taba kan kadan kaga nan zafi yakemun sosai dazufa har cizona Kayi, ido ya zaro "kai baby sharri zaki mun yau ya zan ciji Abin dadi na idan naji mai ciwofa na jawa kaina, "kasani ne ai baka hayyacin ka, "kai baby sai kace wani Wanda ya suma? "Eh mana harfa kyautar yaya Halima kamun dazu da Aunty salma, dariya yayi harda rike ciki "baby sharri? Dama haka kike, kallon kyawawan hakoran shi tayi gayen karshen kyau ne karajin shi take sosai a cikin jinin ta batasan lokacin da ta fara fada mai dada d'an Addu oi ba, "Allah ya kare mun kai mijina yadawo min dakai Lafiya in faran tamaka har karshen Rayuwar mu Allah yabani yara masu kama da baban su, Dadin Addu ar yaji har cikin zuciyar shi "Amen my wife Allah yabani masu kama dake dai kinfini kyau baby, "zagina zakayi kuma ka kalle ka fa Zuma na, "me yasa kike kirana Zuma? "Because you are the sweetest thing ever happened to me ina Alfahari dakai farin ciki na, "Alhamdulillah ko mutuwa nayi yau zan mutu as happy man magan ganun ki yau suna tsuma zuciya ta baby kibarni haka karki hanani yin aiki na a natse fa,   Haka wa innan masoya suka raba dare suna farantawa zuciyoyin su kafin ya umarceta da tashi domin gudanar da salla ta neman kariya da biyan bukata, saida aka kira sallar Asuba tayi salla ta koma bacci, shikuwa training ya taba kafin ya fitoda manyan Jakun kunan shi guda biyu falo ya fito cikin kakin shi ya dora hula tareda cire karamar pistol din shi ya makala a gefen kafar shi yafito a sojan shi karfe bakwai motocin shi suka jera Ahmad ne ya fito mai da kayan shi suka zuba a bayan motar har an bude mai zai shiga ya kalli Ahmad "Aunty na nan? "Eh tana ciki ya wuce tareda tsayawa Ahmad ne ya bashi izinin shiga, dai dai ta fito domin tafiya gida itama don bata shirya zama ita kadai ba miji a gari ba, batayi mamakin ganin shi ba, suka gaisa batareda ya zauna ba ya ciro envelope ya mika mata "na gode Aunty don Allah ki kulamin da baby na barmiki Amanarta, Abin ya bata dariya wai baby sai kace wata babyn roba,   To kawai tareda godiya ya juya ya fita Ahmad ya daga mata hannu ya tafi Shima, suka kama hanyar su ta birnin gwari sai muyi musu Addu ar kariya daga duk kan sharri, Yasmin kuwaSaida Aunty maryam ta isa gidan ta tashe ta "ke kina nan kina bacci mijin ki ya kama yana faman tunanin ki bayan ya gama danka min Amanar ki, murje idanun ta tayi sannan ta tashi zaune "wallahi Aunty jiya banyi bacci ba muna waya, "kaji masoya bari inga meye aka bani ta fito da envelope din ta bude idanun ta ta zaro ganin mikakkun kudi Y'an dubu dubu sunkai hundred tace "kaga kyautar manya yasmin "kingode ai, wayar ta tagani ta waro ido "kaga matan manya komai a wurin ku ake fara gani, Kai Aunty , to kitashi nakira kawata y'ar sokoton nan zatazo zamu fara gyara kafin mazan mu su dawo nasan kudi ba matsalar mu bace tunda munada matar Oga MA sosai kuwa ina nan a kusa ta fada tareda fita da sauri domin yin wanka, Su mama suka fara mata tsiya "kaga manya idonki kenan? Gaishesu tayi sannan ta wuce domin yin wanka,   Baban zango dai ya baje kudin shi wajen zabowa yasmin best furniture's na yayi masu matukar kyau da tsada ko y'ar wani Babba sai haka su mama ma sun kwaso mata kayan kitchen masu kyau na yayi siyayya dai sunyi Masha Allah ita kuwa ta Dage wajen gyaran kanta domin burge mijin nata idan yadawo, Tunda ya tafi bai samu natsuwa ba yana matukar kewarta Amma ba halin kira suna cikin hadari domin kowa yasan hadarin dake tattare da kauyen, ita kanta tana kewar shi sosai,   ********** Two weeks Idan ka kalli yanda ta murje ta kara cika don batada matsalar komai sai ta rashin mijin nata domin tana tareda y'ar uwarta koda yaushe ga familyn ta masu matukar jida ita domin baba ma yasan haihuwa nada rana don shi kanshi ta dauke mai lalurori da yawa ga kayan Abincin da ake kawo musu duk bayan sati daya, hannun ta ya fara fadawa a tukin da take zuwa mota daya kawai ta Ajiye a gidan sauran baba yasa ankwashe an mayarda su BARIKI gudun Barayi KO sa idon mutane,   Yau ta dawo da wuri daga driving school tana zaune a gefen Aunty maryam tace "Waini Aunty kina damuwa kuwa? "Dame fa? Bakyajin labarin baban Auwal naga kuma ko q jikin ki, "Lafiya lau suke yanayin aiki ne madam MA welcome to the Army work madam, "hmm gaskiya matan soja fa na hakuri , "jarumai ne idan bakida hakuri sai ki jefa kanki a halaka wallahi don haka Wasu ke karuwan ci da Auren su, Allah ya kyauta, "Aunty d'an malele nake jin ci wallahi, wani irin kallo tayi mata ke banfa gane ba kinga Al adarki kuwa? "Fesar da ruwan data fara kurba tayi tareda dafe kirjin ta tace "wallahi kusan kwana goma kenan da wucewar Al adata kanbu, ta fada tana waro idanun ta waje,   Dariya Aunty ta tuntsire dashi "meye haka? "Ciki na shiga uku wannan ai Abun kunya zanyi ciki ban tareba wayyo Allah na, "banson shirme nidama kallon ki kawai nake kinga yanda kika cika kirjin ki yayi full ga hips dinki ya kara budewa fuskar ki har wani sheki takeyi in anyi magana kice wai gyara ne don haka k8daina shan hadin nan saboda gudun matsala, itadai tana tunanin kar a gano tasha kunya, dafe kanta tayi kawai tayi shiru MA ya gama da ita shi yanacan Abinshi,   Ai fa kunsan sharrin Abin kamar karta Ankare da cikin ai kuwa ta fara kananan laulayi don ma gidan nasu sukadai ne sai Aunty maryam da mama, cikin sati daya kullum sai ta kyelaya Amai da safe yauma tana kwance a katifar ta tana jin yanda zuciyar ta ke tashi takasa fita don tasan mama na wajen, ganin zata gala baita dole ta fito da gudu tundaga kofar dakin ta fara kelaya amai mama ta tsaya kawai tana kallon ta, saida ta gama tace to zoki wanke bakin ki maryam gyara wurin, idan kuma kungama boye boyen ku kya rakata Asibiti taga likita ai, Ko akwai d'an da kuka haifa a gidan nan ne ban sani ba waye yaro a nan dazaku raina mai hankali, ai sai ki yi rainon ciki a gida kya tare da d'an ki, "kunya dai ta shata ranar haka ta koma dakinta Aunty maryam tayi tsit saida mama ta gama sannan tace "bayan sun kwashe sati daya a Abuja mama dole kisa ran hakan ai, "to yayan zamani, jan bakinta tayi ta shiga cikin dakin nasu domin ganin halin da yasmin ke ciki,   Saida suka kwashe sati uku a kauyen kafin yasamu lokaci ga rashin network a daren ranar ya fadawa Ahmed ya shirya zasu shiga kaduna gobe ya yi kewar matar shi sosai ga shi tunda yazo bai suyi waya ba don haka he will surprised her, bana bukatar escorts mukadai zamuje, yace ok sir, A daren yasmin zazzabi yasa ta gaba sosai don haka tunda safe suka nufi Asibiti wani private hospital suka bata kulawa sosai bayan sun yi mata scarning kafin subata gado domin tana bukatar ruwa saboda rashin karfin jikinta da kuma Aman datake tayi, ........   "Afuwan my fans nima jikin sai a hankali ina lallabawa ne yau ciwo gobe lfy bansani ba ko ciwon tare mukeyi da yasmin *Matar Soja* [9/15, 8:14 PM] Asli Smasher : Follow this link to join my WhatsApp group: don Allah duk wadda take cikin grp dina kartayi joining wann ina rokon ku, https://chat.whatsapp.com/KurmEtaqVGVByLrCjiVwZF *BARIKI* _Auren Soja_   Written by FENERH   *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby 49&50 Sun iso garin na kaduna lfy direct Unguwar dosa yace Ahmad ya wuce dasu Don ya mugun matsuwa ya ganta kewar ta yakeyi kamar hauka don baida yanda zaiyi ne yasa ya dauki satuka bai ji koda muryarta ba ya wahala sosai ji yake kamar yayi tsuntsu ya ganshi a jikinta, saidai yataki rashin sa a suna isowa suka tarar basa gidan mama ta fada musu sunje Asibiti, cikin kidima yake tanbayar ta waye ba lfy? "Yasmin din ce ta kwana biyu tana jin jikin shiyasa yau nace su tafi Asibiti, wani iri yaji a cikin zuciyar shi kamar yayi kuka yace "mama meke damun baby? Wane Asibiti sukaje kuma? Kunyace ta rufe mama wai baby, Taji dadin ruwan da suka samata don taji karfin jikinta sosai sun bata magun guna tareda shawarori kafin su dawo, driver ne ya tukasu don bazata iya driving ba, sun dawo gida suka samu bakuwar mota a kofar gidan nasu, Aunty maryam tace "yasmin ko su baban Auwal ne suka zo? Wani irin dadi taji tareda Addu ar Allah yasa sune don tana cikin damuwar rashin jin muryar shi sosai cikin rawar jiki ta nufi cikin gidan Aunty maryam ta dauko mata magun gunan tareda takardar scarning dinta, ta shigo dai dai yana famar tanbayar wane Asibiti sukaje,   Sallamarta ya dawo da hankalin shi gareta, wata uwar Ajiyar zuciya ya sauke tareda zuba mata ido cikeda tausayi don ya hango y'ar ramar da tayi saidai ta kara kyau sosai duk da ba make up a fuskar ta, ba bata lokaci ya taso cikin sauri tareda riko kafadunta ya zuba mata ido "baby meke faruwa meke damunki don Allah kinga likitan? Takasa cewa komai sai kallon kwayar idon shi takeyi duk ya rude mama dai shigewa kawai tayi don gudun ganin Abin kunya don ta lura ko makobtaka MA baiyi da kunya ba, yama manta da cewar tana wurin ga kuma Ahmad dake rungume da yaron shi a gefe maryam jan kayan ta tayi ganin Sam su Yasmin sun manta da mutane a wurin ko ince MA, falon baba ta bude mai suka shige Abinsu, bayan ta Ajiye musu magun gunan tace "idan kun gama kallon soyayyar love birds ga result din da magun gunan ta wuce, yasmin kadai taji ta shi ya Riga ya gama rudewa da kallon ta Abu biyu ya daga mai hankali, na farko ciwon nata nabiyu cikarda yakara ganin kirjinta yakarayi gaba daya yasa baima san me yakeyi ba saida tace "ka kori mutane ai sai mu zauna ga kujera,   Waigawa yayi tareda kallon ta "akan me zan zauna A nan muje cikin dakin ki indan latsa ki kadan wallahi a matse nake nayi kewan zumar ki baby nayi full dayawa, dagata yayi cak suka shiga cikin dakin nata saida ya Ajiyeta ya yaye katon gyalen ta ya tsuguna a gaban katifar ya zubawa ko ina najikinta ido, "baby meke damun ki? Bakida Lafiya but ki kalli nan dinki sunkara cika, yafada tareda dora hannun shi saman kirjin ta, bata fuska tayi bakai bane kaja mun ciwon, zaro ido yayi "saboda rashin jina kike ciwo baby ai nafiki damuwa sosai kullum bana iya bacci, "nidai zanci Abinci yunwa nakeji ban karyaba, "ok ko zamu tafi gidan mu ne? "Aa nidai bazanje ba sai muntare baki daya, dafe kanshi yayi " yazakiyi da damuwata tom bayan saboda ke nazo, Kayi hakuri, "hakuri meye kuma hakuri ai bansan wane yare bane haka? "Nikaga banda lfy kuma Anbani magani ance sai naci Abinci zan sha gashi ka hanani, "noo ina magun gunan da kuma Abincin,? "Aunty maryam zata bani, wayar Ahmad ya kira yana dauka yace "ina Aunty please tazo, tom kawai yace ya kife wayar tareda zama gefen ta kafadar su na gugar na juna ya dora hannun shi saman kirjin ta yafara shafawa yana lumshe idanun shi, tayi saurin turewa "Aunty fa na zuwa, "so ita kikasan me sukeyi? Sallamar Aunty maryam yasa ta yi saurin matsawa daga kusa dashi shigowa tayi da jakar Yasmin tareda kuma magun gunan da suka bari a waje Sannu da zuwa tayi mai tareda kallon yasmin "wato kinga miji kin manta da maganar likita ko? "Aa Aunty ai shiyasa na kira kizo tace yunwa takeji Abata Abinci, "to nidai zanje inji da mijina yanzu Aikin ka ne nayi nawa ga result din da kuka bari da kuma scarning, "ciwon har yakai Ayi scarning meke damun matana haka Aunty? Mikamai takardar tayi ya bude,   Wata irin zabura yayi tareda mikewa tsaye ya zubawa Yasmin ido "what? Ciki' ya fada tareda zama yana kara janyota jikin shi "tell me baby ciki gareki? Duk ya rude ya gigice "ciki Aunty ciki takeda shi cikina? Am going to be a father,,? Tasan zaiyi farin ciki Amma bata tama tunanin farin cikin shi zai kai har haka ba, ya manta da Aunty maryam tuni ya rungume ta tareda Dora hannun shi a marar ta cikin kidima "Tnk you baby tank you tank you Wasu irin hawayen farin ciki ya ke fitarwa ya zabura cikin rashin Abinyi ya saka hannun shi cikin wandon shi ya zaro duk kudin ciki ya zubewa Aunty maryam a kasa Aunty kiyi manage zan kuma ganin ki idan na natsu,   Aunty Abin ya mugun burgeta irin wannan farin ciki sai kace akan shi aka fara haihuwa, zama yayi tareda rungume ta gam "baby me zakici? Kici Abinci baby na ya yi kiba "oh zaki wahala inya yi girma sosai wurin fita please me zaki ci tell me Aunty kibata Abinci don Allah karta yi aiki ko kadan karta wahala, to Abu yazo wurin masuyi fa, inji Aunty, wayar shi ya ciro yafara shedawa hajiya, "mama na Yasmin nada ciki zaki samu jikan da kike ta Addu ar samu a wurina mama zan zama baba, "to sarkin Y'an rashin kunya ina fatan ba gaban surukan naka kake tabargaza ba? Sosa keya yayi tareda kallon Aunty maryam yace "Aunty maryam ce kawai hajiya, to tunda ciki yasamu sai ta tare karta haihu a gidan su KO kuma ta dawo gidana sashen ka da zama, "zanzo muyi maganar yanzu,   Ajiye wayar yayi bayan ya gama kiran sauran Y'an Uwan shi suna mai tsiya, hajiya dai tafi kowa farin ciki d'an baban ta Alhmdulillah Allah ya kawoshi lfy, Aunty dai kama kafarta tayi ta fice tareda mijinta, suka nufi gidan su don Oga yace shifa yau yana gefen Yasmin zasuyi raino, mama dai ta rufawa kanta Asiri ta yi zamanta dakinta Amma bata tsira ba ya bita tareda sallama ta fito yace "mama baby ciki takeda shi zan zama baba don Allah mama ki kulamin da ita zanje inga hajiya indawo bataci Abinci ba gashi Aunty maryam ta tafi barracks da Ahmad nace mutafi tare taki yarda muje mama kisa mata ido karta yi aiki,   Ikon Allah mai karfi na bara, yau tana ganin ruwan rashin ta ido Allah dai yasa malam baya gida da Yau zatasha mitar surukinta baida kunya duk da yau ta shaida haka ya gama sanbatun shi ya fita bayan ya koma ya gama bata warning, "karki wahalar min da baby please ki jira bazan dade ba zandawo me kikeso inkawo miki? Shiru tayi kawai don ya gama bata kunya don tanajin yanda yake sakin layi gaban mama, saida ya bude shaffen cikinta ya bata kiss tareda cewa "baby yaushe zai girma cikinki yai kato? Itadai ya isheta wallahi ranta ma ya fara baci don ita yama daina damuwa da ita tun ba aje ko ina ba soyayyar ta koma kan cikin da ko kosawa baiyi ba, daure fuskar ta tayi tamau ya zauna "come on baby please karki sa damuwa ki cutar min da ciki please, "katafi don Allah kaina zaiyi ciwo tafada cikeda kufula, "ok ok sorry bari inje sai nadawo ya tashi ya fita, Dawowa yayi "aramin key din motarki Ahmad ya tafi da tawa, Nuna mai Jakarta tayi ya bude tareda yin dariya ganin agwaluma a ciki, "mai ciki an fara kwalama, tayi mai banza ya dauka ya tafi cikeda wani irin farin ciki gaba daya ya manta da wata Abu wai sha awa farin cikin da yake ciki tuni ya mantar da shi wannan shafin, Gidan su ya wuce kawai, a can suka gama tattauna komai kafin ya dawo bayan hajiya ta bashi sakon danbun naman kaza mai yawa da kuma soyayyun kajin ya kawo ma Yasmin din, saida ya biya bakin dogo ya jido mata su lemo dasu kankana da duk kayan da yasan zasu kara mata kuzari da lafiyar jiki ya iso da kaya Niki Niki,   Lokacin baba ya dawo ya fara tanbayar ina Auwal yau baiyi mai Oyoyo ba, "ai yabi uban shi suntafi BARIKI, baba yayi dariya "to sun shigo kenan? Don yasan dole tare zasu zo da uban gayyar, ina ita yasmin din take? "Tana ciki inaga bacci takeyi tunda an hanata motsi saboda kar d'an so ya wahala, "bangane ba wane irin Dan so ina d'an yake? "Au kai fa bakasan zaka samu jikaba tom ciki take dashi kuma tun muna gani da idanun mu ka bashi matar shi su tare bazan iya shirgin rashin kunya ba, "tofa ciki to bari yazo ya kwasheta su tafi tunda haka suka zabi nasu Auren ya kasance gashi mamuda ya kama ya kashe mata kudi kamar ita kadai ce ya, "ya kuma rage tsakanin ku yanzu, suna maganar ya iso,   Cikin girma suka gaisa da baba ya mai fatan Alkhairi tareda Addu ar Allah ya kara tsaresu yace Amen, "Amm tom sai ku shirya tarewa zuwa jibi zan kira uwarta suzo sai a gyara mata gidan ta ko, "ai baba ba wani Abu da za a saka a gidan na gama sa komai kuma gidana zamu zauna saina dawo zamu zauna tare a BARIKI Amma yanzu Unguwar rimi zamu tare, "yanda duk kuka tsara Abinku ba damuwa matarka ce Amma maganar kaya ku nemi inda za a zubasu baza a yi hasarar dukiya ba tunda anriga anyi hasarar dukiya an siya, toh baba mungode Allah ya kara girma da Arziki, Amen yace tareda yimai fatan Alkhairi a Rayuwar su da kuma rokon Allah yakara karesu,     Baccin ta taci sosai ta koshi bayan taci d'an waken da mama ta jefa mata da yaji cucumber da kayan miya harda dafaffen kwai taci sosai tasha magani shiyasa ta more idonta ga Kasan zuciyar ta tana farin cikin ganin farin cikin zuciyar ta mijin ta Abin Alfaharin ta, wani Annuri fuskarta ke fitarwa, jin ana shafa cikinta harzuwa saman kirjin ta ta bude idonta a hankali ta sauke akan kyakkyawar fuskar shi, "Sory for waking you up ina gaisawa da lovely daughter na ne "Kasan mace ma zan haifa kenan? "Insha Allah zaki haifamin baby girl mai kama dake baby da suma irin taki, tashi tayi tareda zuba mai ido "wai Zuma ta ko kewata bakayi kana zuwa ta cikin ka kakeyi ko, ta fada tana tura baki cikin shagwaba, "oh no ni na isa baby wallahi ke Kinsan ina sonki fiyeda komai a duniyar nan kuma wannan cikin yafada yana dora hannun shi saman cikinta bansan yanda zankwatan tamiki yanda nakejiba, wallahi bazan so ko guda ya sauka akanshi ba I love you so much dole inso duk abinda yafito a jikin ki,   "Saboda farin cikin samun wannan babyn ko Abinda ya kawoni banyi ba don banason in wahalar dashi, harara ta balla mai "oh duk saboda babyn ka harda jarabar ta ragu? Kai naji dadi kuwa Allah yasa har sai na haihu, "what? Hmm jibi zaki tare baby don haka ba wani sauri da zanyi duk da ina matse farin cikin da kika bani ya rage min komai, shiru kawai tayi ta zuba mai ido don ta lura ya zauce akan wannan d'an tayin cikin, "baby gobe zamuje muyi wa baby shopping ko? "Wai me yasa kadawo ne ba yanzu katafi ba, ai Inba bani iyali na akayiba yanzu kika fara gani na a nan gidan, shigewa yayi jikinta tareda cusa hannun shi ta Kasan rigarta ya fara lalubarta a hankali, ta riko hannayen shi "meye haka zaka wahalarda baby fa, "oh come on ba wani Abu zanyi ba just play kwantar da ita yayi tareda hade bakinsu wuri daya yafara bata wani irin salon da bazata taba iya kawarda kanta. Ba, Jindadin Abin takeyi sosai kamar karya cire lips dinshi a bakinta jin test dinsu takeyi sosai sai kara rikoshi takeyi tana kara haukata shi, ganin yana kokarin janyewa daga jikinta yasa jikinta na rawa ta tashi tareda maida kofar ta rufe gam tadawo ta fara cire kayan jikinta don mugun bukatar Abin takeyi tarasa dalilin hakan zuba mata ido yayi cikeda mamakin ta don bata taba nunsmai tana bukatar Abun ba sai yau saidai shi yayita kwakwa, fadomai tayi yayi saurin rikota "oh baby kibi a hankali mana cikina karki mun asara, ko jinshi batayi ta dora hannun ta saman wandonshi saida yayi y'ar kara ta balle belt din tareda sanya hannu ta bude rigar jikinshi yana taimaka mata tuni ta zautar dashi baijin zai iya barin wannan garabasa ta wuceshi   Tuni ya fita zakewa suka fara tumurmusa juna cikeda kewar juna da sukayi, karar wayarshi ya dawo dashi daga duniyar tsotse tsotsen da yatafi dakyar yake iya bude idanun shi ya daga wayar saida ya gama sauraren su kafin ya mike ya ware idanun shi oh my god ya fada da kyar sannan ya Ajiye wayar , dakyar ya bude bakin shi "baby zanje office am sorry I will be back for you get ready for me in the night kintayar min da kwadayi ga shi sunkira ni a wurin aiki, cikin sauri ya mayarda kayan shi ya tsuguna tareda manna mata kiss take care of my baby, ya fita da Sauri tabi bayanshi da kallo, Tashi tayi tana murmushi tareda jin soyayyar shi na da da karuwa koda yaushe cikin zuciyar ta shi na daban ne a cikin maza tana son Muhammad Abdullah so mai tsanani tanajin kishin shi gani take har gobe mata nabi mata miji, Baisamu dawowa ba saidai kiranta yayi yabata hakuri saboda soja baida hutu koda yaushe yana bakin Aikin shi, duk da yazo ya huta ne amma bazai taba hutun ba sai ranarda yayi ritaya, Da safe su mama hindatu da Aunty maryam da kuma wasu Y'an Uwan mama suka zo domin rakata gidan mijinta baba yace ba wani taro da za ayi ta bari idan ta haihu sai ayi taron tunda ga ciki nan, saidai uban gayya tuni ya shirya kwarya kwaryar liyafa a officers mess domin Abokan Aikin shi yace maza zalla ne kawai zasu hada barbecue domin tayashi murnar Aure da kuma samun karuwa, Cikin sirri yasa aka kwashe kayan da akayiwa yasmin yace akaiwa Aunty maryam mama kawai ta sani da mama hindatu don gudun fadan baba, itadai Aunty maryam tayi farin ciki sosai domin ko a Aurenta bata samu wannan dama ba, kayan kitchen dinta ma da suka kai mata ajiyewa akayi domin ba abinda ba a zuba a yafjeken gidan da suka kira da Aljannar duniya nera tayi kuka gidane d'an karere ga katon garden da yaji kayan marmari Kala Kala gefen shi da sweeming pool mai burgewa, furniture's din kuwa set ne na royal Italians masu shegen kyau masu ruwan Zuma da fari gida dai Masha Allah , tuni sunkai mata kayanta gidan harma da motocin hawan ta,   Washe gari karfe biyu baba yasa ta shirya da kanshi ya dauketa domin yimata rakiya dakin mijin nata domin ya nemi Alfarmar yanason tazo da wuri akwai party da aka hada mai, Tasha nasihohi masu karya zuciya da shiga jiki daga gefen mama harma su baban da suka zaunarda ita, su mama sun mata Nasiha mai Amfani sosai saida tayi kuka Aunty tace sai sun hadu a BARIKI yanzu ta zama matar manya gidan ta shigasaida izini saboda sojojin dake kofar gate dinta, zuciyar ta ta karye sosai ganin da gaske shikenan yau zata koma gidan Muhammad gaba daya,   Hawaye ta share tareda yin shiru, komai nata yazo daban da na mutane Aure ba shiri tarewa da ciki kuma ba taro, ba kuma mai rakata, haka suka isa gidan nata tafkeke, shi kanshi baba ya tsorata da ganin irin wannan katon gidan yanzu a nan y'ar shi zata zauna, Allah mai iko da kuma girma , bude musu katon gate din sojojin sukayi baba ya shiga da motarshi suka fito wata dattijuwa ce ta fito tana musu Maraba da isowa tayi musu jagora saida ta sadasu da falon tace. "Sannu da zuwa uwar gida Sannu da zuwa gidan ki Allah ya kade fitina, fitowar su Aunty Halima dukan su suka fara mata Maraba da Amaryar baban hajiya yaudai zamu ganki ko, dukarda kanta tayi tareda kara janyo hijabin ta, har kasa suka duka suka kara gaida baba tareda godiya ya Dan ka musu Amanar ta tareda sa Albarka ya tafi, sunata mai godiya, Kamar ta riko shi takeji tana ganin ya fita tasa kuka shikenan itama An sallame ta daga yau tabar gidan su, su Aunty suka ce tayi hakuri ta tashi ga mai make up tana jira za aje partyn yanzu bata da zabi haka ta mike suka Nuna mata wani daki ta shiga saida aka hada mata ruwa tayi wanka tareda yin Alwala ta fito saida tayi LA asar sannan ta zauna aka fara tsantsara mata make up, Wane irin party MA ke shiryawa tana da ciki meye na wani taro itadai batasoba gaskiya gashi tun shekaran jiya da yazo bata bata kuma ganin shiba saidai waya a gurguje, Wani farin less suka bata Riga da zani na buba suka daura mata zani a saman rigar tareda daura mata wani head mai golden yana sheki suka Ajiye mata poss da takalmi mai tsini sai a shoken kalar head dinta tayi kyau fiyeda tunani, suka rika Masha Allah baban hajiya ya iya zabe gaskiya tubarkallah sai kunya take ji yanda suke kod'ata, Kiranshi sukayi akan sun shiryata, yace motoci nanan a waje su fito harda su zasu iya zuwa don yaga Y'an gayyar sodi ma da ba gayyace suba duk sun shirya zuwa kwasar gara, domin na hango Aisha dahiru da katuwar Jakarta tareda Ummu jidda da ta kwashi katon no respect gudun raini a hankali nafara ankarewa gaba daya ma BARIKI fan's sun cika gidan harda su hussy Ali gasu maryam dina andauki wanka nace to nima dole in dauki nawa Gayun muje kwasar gara........     Mu cigaba da hakuri da juna my fans muna nan zuwa inda mukeson mu isa da ikon Allah komai yayi farko zaiyi karshe,     *Matar Soja* [9/16, 10:05 PM] Asli Smasher : (¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯) тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   Written by FENERH   *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby   51&52 Motocine guda shida aka ajiye musu sababbi dal suna sheki ta tsakiyar tasha Adon balloon kana gani Kasan motar AMARYA ce ta fito tareda su Aunty Halima driver ne ya bude mata ta shiga suka shiga sauran motocin, BARIKI suka nufa basu tsaya ko ina ba sai 2 batallion officers mess, tundaga titin farko zakasan an kawata wurin sosai ga sojoji tundaga farko baka ganin karshen su kowane sanyeda ceremonial dress sunyi matukar haska wurin ga fulawowi da aka watsa saman red carpet suna tsayawa aka bude mata tafito wasu Y'an mata ne suka jero suna paret sanye da ceremonial dress na mata mai sket su goma, suka sata a tsakiyarsu gaba daya tafara rudewa don bata taba tunanin haka taron zai Kasan ceba, ko ina shi uban gayyar yake oho? Fushi ma takeyi dashi tunda rabon da ta sanya shi a ido tun ranarda yazo aka kirashi saidai yakirata yaji lafiyar babyn shi ya kashe that's means ta tashi aiki ita tunda yasamu ciki a jikinta tana haihuwa kuma shikenan,   Hango shi tayi yana takowa cikin nashi ceremonial dress din da yaji stars da igiyoyi dauke kuma da aninan shi da zasu Nuna maka he is the boss wata sandar girma ce a hannun shi yana dogarawa yayi masifar kyau tundaga nesa suka zubawa juna idanu yana mai jin farin cikin ganin ta gashi ta fito kamar wata tauraruwa karasowa yayi, ta dauke kanta tareda hade rai ya na zuwa ya rungume ta batareda ya damu da mutanen dake wurin ba ya dora hannun shi a marar ta "ya baby na? Rage murya tayi a hankali tareda cewa "ni nazama hoto ai yanzu wallahi a matsa inyi flushing din shi inga tsiya, "what me kikace? Tayi mai banza ya matse fuska sosai ya riko hannun ta suka shiga ana take musu baya ga masu hotuna tuni sun fara Aikin su,   A she kallo na ciki don Fadin kawatuwar wurin kawai zai cinye fejin yau saidai BARIKI fan's zasu baku labarin haduwar wurin ba Abinda ya burgeta irin ganin y'ar uwarta datayi a wurin ga yaronta da ke cikin nashi ceremonial dress din na yara harma da hula yayi kyau da y'ar karamar pistol ta wasa a soke a Aljihun shi, wurin zaman su suka nufa batareda ya kuma ce mata komai ba don yaji mai tafada, ga Army bands sai sakin kida sukeyi da kuma busa wurin ya tara manyan sojoji da matayen su Abokan Aikin shi gefe daya matan NAOWAS ne wato NIGERIA ARMY OFFICER'S WIFE ASSOCIATION ne suncian anko mai dauke da tanbarin gauraka Abin ba a cewa komai Abin ya mugun kawatar da ita su Aunty Halima ma gefe guda aka ware musu man yan yayyi Aunty maryam ta jone cikin su, aka fara gudanar da taro party ne mai Aji ba wani hayaniya harka ce ta girma sai masu raba drinks da kayan motsa baki keta kai da kawowa snacks ne da su namomi Kala Kala kawai kake gani, tuni na hango Ummu jidda na boye kularda ta yo guzuri don zuba rice sai yakasan ce bikin ba na rice bane, Wani cikin manyan sojojin ne ya mike tareda gabatar da taron ta hanyar taya Abokin Aikin su murnar Aure tareda fatan Allah yabada zaman Lafiya gefe daya suka gabatar dashi a matsayin jarumin soja mai hazaka da gaskiya akan Aikin shi sun yaba mai sosai a irin kokarin da yakeyi akan Aikin shi, tareda bashi A word a kan nasarar da yake samu a operation din da aka turashi, yanda suke yabai tareda saramai lokacin da ya karbi a word trophy din ya mugun burgeta ga wani paret da ake bugamai tun tasowar shi a yau ta kara sanin waye take Aure taji takarason shi ko ba a fada ba tasan mijin nata jarumi ne, Saida ya karbi trophy din ya karbi speaker tareda godiya cikin halshen turancin shi mai tsada, kafin ya juya wurin Y'an Uwan shi ya kara musu godiya akan irin soyayya da goyon bayan da suke nuna mai kafin ya juya kan yasmin data hakimce ta zubawa tsadadden mijin nata ido, Ya tako zuwa gaban yasmin data zuba mai ido yafara zubo mata kalamai batareda ya damu da duniya na kallon shi ba "you are my happiness you are my world, yaci gaba da koro mata kalamai cikin harshen na nasara, samun ki a rayuwata shine babban farin ciki yasmin Kasan cewar ki a inuwar gidana shine muradin Rayuwa ta kece kika cikamin burin Rayuwa you thank you for being my wife tank you for giving me the best happiness in the world that's my unborn child in your belly please take care of my baby I love you now and I will continue loving you, Mika mata hannu yayi ta taso tareda zagayowa ya ajiye sandar hannun shi tareda cire hular kanshi yasa guiwar shi a kasa saida ya manna mata kiss ya tommy dinta kafin ya saka hannu ya ciro wani karamin akwati mai dauke da wani diamond ring ya riko yatsar ta ya saka mata tareda bata kiss a hannun ba Abinda ke tashi sai ihun sojoji da shewar mata dayawa mata wasu sun mugun bugesu wasu kuwa wutar kishi ke ruruwa musu don sun san mijin Yasmin yafi nasu, tasowa yayi tareda zagayeta ya hade fuskar su ya tsotsi hawayen da yaga duna zubo mata na farin ciki kafin ya sauke bakin shi kan lips dinta yabata wani irin romantic kiss ga kidan da aka saki na D banj na baby don't make me fall in love kidan na kara kawata romantic moment din gaba daya kowa ya mike a hole din ana musu tafi, saida yayi kissing dinta na minti biyar kafin ya riko hannun ta bayan ya mayarda hular kanshi ya karbi pos dinta ya rike suka matsa gaban wani katon table da aka kawatashi da wani jan kalle, wata soja woman ta bude shi saiga wani katon cake mai dauke da hoton su ita dashi Abin ya mugun kayatuwa saida aka zagayesu kafin Abasu umarnin yankawa bayan ansaki wakar sojoji na this is the way I wanted to be,   Ya sanya spoon ya saka a bakin shi kafin ya nufi bakinta ta bude suka cinye tare ya tsiyayo ruwan champagne ya bata kadan gaba daya zuciyar ta tashi ta farayi don Sam batason cin cake din saboda zakin shi Sam batason Abu mai sugar yanzu, , Allah Allah take su tashi a wannan taron ga kidan dake tashi yana hawa kanta ya lura da yanayin ta don haka ya sa ayi sauri a tashi yanzu madam is exhausted, ya rikota suka dawo mazaunin su Aunty maryam ta taso ganin kanwar tata ta gaji ta tsaya kusa da ita "Lafiya madam MA, "Aunty Amai nakeji wallahi, fito mata da tom tom tayi tace ta jefa a baki zata rage jin tashin zuciyar, hakan tayi saidai a matukar takure take gaskiya, Gift ake ta Ajiye musu a katon table din dake gaban su wasu ma harda baby set suke kawo musu wasu kuwa envelope masu kauri kai a dai haka wannan taro ya tashi cikin farin ciki duk Wanda zai fita sai anbashi jaka mai dauke da atanfar Ango da AMARYA da kuma agogon bango ba Wanda bai samu ba harda Y'an gayyar sodi ma don Ummi zaria bayan Anbata da farko komawa ta kumayi don neman kari, Saidai muce Alhmdulillah Allah ya kade fitina,   Suna shiga mota ya biyota Shima ya shigo ya rungumota sosai zuwa jikinshi " Sory madam bari muje gida ki huta ko, shigewa tayi jikin shi sosai tareda shakar kamshin shi har Allah yasa suka isa gidan nasu Lafiya yaso su tsaya BARIKI taki domin tana dokin zama cikin katon gidan nata da ya hadu da kayatuwa, Daukar ta yayi cak batareda ya damu da masu gadin ba ya shige da ita cikin gidan saida ya kaita cikin wani tafkeken dakin baccin su ya Ajiyeta yafara rage mata kayan jikinta da kanshi , Ruwan wanka ya fara hada mata ta shiga batareda ya bitaba don ba karamin dauriya yayi ba wajen kyaleta batareda ya jagwal gwalata ba yasan ta gaji idan ya bita bathroom akwai matsala, don haka ya barta saida ta fito ya shiga Shima,   Shafe jikinta tayi da mayuka masu shegen kamshi da gyara fata tanayi tana karewa lafiyayyan dakin da kallo tasan ta gama sa a a Rayuwar ta samun miji one in town daula irin wannan dole ta godewa Allah tana nan zaune ya fito tareda matsowa gaban mirror din ya rankwafo tareda dora lips dinshi a saman wuyanta, "why are you thanking Mrs Muhammad? And what are you tinking? "Am thinking of my husband, tafada kai tsaye domin faran tamai kamar yadda yake kokarin bata farin ciki, daga ta yayi ya zauna tareda dorata saman laps dinshi, "fadamin Abinda mijinki yayi da kike tunanin shi? "Yayi min komai a duniyar nan ya bani duk wani farin ciki, magan ganun da ma fadamin dazu sunfi komai sanya ni cikin farin ciki ka nuna ma duniya cewar nidin mace ce mai sa a Ina jin kaina kamar wata sarauniya, "you are my queen I can shout out and tell the world I love my wife so much zan iya miki komai a duniyar nan idan baifi karfina ba Ina son ki yasmin I have change because of you kin nunamin ni imar dake cikin Aure tundaga ranar da na Aureki nake jina as complete man da ni kaina nakanyi tunani inada komai inada mata Kala Kala Amma I always think that something is missing, "yes gani nazo yanzu you are complete dama ni kake jira, yeah jirana ya kare dama am waiting for my woman to arrive, yafada yana janye towel dinta zuwa west, ya dora bakinta shi akan boosty boob dinta yafara bata wani irin salo tuni tafara turo mai su sosai tareda dafe kanshi takara taimaka mai wajen wasa da sumar kirjin shi, Ganin zaman wurin na kokarin gagar ta yasa ya sunkuceta zuwa katon gadon sukaci gaba da ya mutsa juna, sunyi matukar kewar junan su don haka kowane kokarin farantawa d'an Uwan shi rai yake ta ko wane fage gama daya sun gama lulawa duniyar maji dadi yasmin ta mugun zama y'ar hannu shi kanshi yaji dadin moment din fiyeda ko wane lokaci gashi batayi mai complain ta gajiba duk da yana yi yana tausayawa babyn shi, saidai yaga Alamar hajiya yasmin ta zama oganniya a wannan fagen,   Saida suka natsa tafara mai shagwabar marar ta, ya zabura tareda shafa mata marar a hankali tareda zuba mata idanu yana bata wani irin salon kallo, irin kallon kingama yi a Rayuwa, saida suka kuma yin wanka tare suna likeda juna kafin ya bude walldrp ya fito mata da wasu English wears Riga da wando masu hannun shimi wandon ya kama jikinta komai nata ya fito shagala yayi wurin kallon ta ya ce " wow baby naso mu zagaya gidan nan ki ga ko ina gashi bazan iya bari kifita a haka ba bari inkawo mana Abincin a nan muci nasan baby na najin yunwa ko, Fita yayi bayan ya zura jallabiyar shi ya nufi kitchen din da ya zuba mata masu yimata hidima harda wata tsohuwa da Y'an mata guda biyu sai shirya dishes sukeyi yace su kawo ma madam Abinci yanzu kafin ya koma dakin, ya sameta zaune tana cin pop corn mai madara data samu a dakin, zaro ido yayi "meye kikeci haka? Karfa ki zukewa yarona jini bakomai zaki rika ciba, zama yayi a gefen ta tareda rungumota sosai, kafin ta bashi Amsa budurwar ta yi sallama tareda shigowa ta Ajiye musu a bincin akan d'an karamin table din dake dakin, wani irin kallo yasmin kebin budurwar dashi tana sanye cikin damammun kaya Riga da sket na atanfa ga uban atarch har gadon baya domin kanta wani mayafi ne mai shara shara, tana tafe tana faman rangwada da motsa jiki, duk da tana nan kamar maburgi Abin ya bata haushi sosai,   Saida ta gama salon ta face "Sannu madam, sir komai yayi ready ta juya tana fita tana karairaya shi kuwa ko kallo bata ishe shiba baima san tanayi ba yana danna wayar shi saida ta fita yace "madam ga Abinci, mugun tsaki taja tareda tashi daga gefen shi tayi saurin komawa kan kujera tana girgiza kafarta cikeda kishi wato budurwa zai kawo mata cikin gida da sunan mai aiki tazo tana daba mata Abinci tana kokarin nuna tsiraicin ta don ta jawo hankalin shi gareta, tasowa yayi cikeda mamakin ta me ya faru bayan yanzu yanzun nan suna cikin farin ciki, dafa ta yayi tareda cewa "what is wrong madam? ", oh baka saniba ko wacece wannan? Dariya yayi "baby wacece kuwa bayan y'ar Aikin ki, "wannan da takejin kamar ta ciro kirjinta ta dorama a tafin hannun itace zaka kira da y'ar aiki, wallahi bana bukata I can cook for my house ko na fada maka ni ban iya girki bane ko bazan iya yima Abinci ba zaka kawomin Y'an matan ka cikin gida wallahi sai sunbar min gida bana bukatar su, Ta fada tareda mikewa saidai tana tashi jiri yafara kwasar ta ta koma ta zauna, gaba daya ya sarawa Aikin hankalin ta Yau, saurin zama yayi kusa da ita "kingani ko kishi zaija ki mun asarar baby na come on relaxed mana madam irin wannan kishi haka, buge hannun shi tayi yayi saurin tsugunawa a gaban ta, "listing bansan waye suke aiki a nan ba hajiya tasa aka nemo su KO fuskar su ni ban sani ba idan bakya bukatar su zaki iya sallamar su dama saboda su taimaka miki nace akawo su kuma in banda Abinki yasmin me zanyi da wata house help please am not that kind man da ke neman ko wace irin mace and believe me idan har zanyi wani Abu zan fada miki yakamata kisani bana boyo kuma bazan taba miki karyaba, I wanted to tell you something a bout zuby.... Saurin daga mai hannu tayi "please nasani tunfarko kafada min cewar bazaka iya rabuwa da itaba, to wallahi kasani nima bazan yarda da tarayyar ku ba kuma na shirya cin uban ko wace shegiya cikin gidan nan dama barikin baki daya kuma kana tafiya zan koma can inga tsinanniyar da ta isa ta kuma takomin gida, ta fada cikeda masifa tareda mikewa ta kwashi tray din Abincin tayi waje, dariya Abin yabashi sosai "my jealously wife,   Tana shiga kitchen din ta samesu su biyu suna hira a tsakanin su ba tsohuwar basu maga shigowar ta ba, dayar data kai musu Abinci kebawa dayar labari "ladi bakiga yanda naga gayen nan ba dagashi sai singlet da short wow wallahi gayen yakai karshen haduwa a gaskiya zan iya yin komai domin samun gayen nan a bed irin su akwai lasting a gado ga kyau ga kwarjini ga.... Watsar da tray din da tayi ya dawo dasu cikeda tsoro suka zuba mata ido tareda fara kame kame, "Wallahi yanzu right away right at this moment I want you All out of my house before I open my eyes Inba haka ba zan illata ya' shegu matsiyata masu bin mazajen mutane ankawo ku ku nemi Abinci kuzo kuna neman bin mazajen mutane to kuyi gaba ba gidan Fatima ba, cikin rawar jiki suka fice da gudu ta bisu da harara, a tsaye yake yana kare mata kallo yana fitarda wani irin murmushi na farin ciki kafin ya karasa shiga ciki ji kawai tayi ya rungume ta ta baya "my madam Karfa kija wata rana a daureni inkin daki ya'yan jama a saboda kishi irin wannan kishi haka madam, tureshi tayi tafara kokarin dafa musu Abinci shaf shaf ya haye kan durowar kitchen din yana kallon yanda take komai cikin korewa, Tsohuwar ce ta shigo cikin rawar jiki tafara tanbayar ta "hajiya ina fatan bamuyi kuskure ba naga ankori sauran yaran don Allah nidai Karku koreni ina neman Abinda zan rufawa yarana asiri inada marayu, juyowa yasmin tayi cikin sauri "aa baba baza akoreki ba kuma zaki tayani wanke wanke da kuma dafawa masu gadi Abinci idan Oga nanan ni zanrika dafawa da kaina Amma wa incan bana bukatar su na sallamesu a gidana, "to nagode hajiya Allah yakaro Arziki, ta fita yasmin ta ci gaba da Aikin ta wani irin burheshi yaji tana karayi gashi ta nuna cewar ita din matar shi ce mai kishin shi that's the best thing ever, cous cous ta hada musu da yaji kayan lambu tareda bushashen kifi ta hada musu lemon kwakwa saida ta gama hada komai ya sakko tareda daukar kayan Abincin yana mai kallon fuskar ta data hade tamau,   A katon falon ya Ajiye musu a tsakiyar carpet ta biyo shi rikeda plate da kanta ta zuba musu bayan ta kira matar tace ta dauki sauran idan zata tafi don bata kwana a gidan, janyota yayi zuwa tsakiyar kafafun shi yace "that's enough madam banason kina fushi akan abinda baida wani fa ida let us be happy for ever kinsani ina bakin aiki ne nabarshi na zo saboda ke kawai I have only two days to go back don haka banason wani Abu ya gitta mana na bacin rai, sakin fuskar ta tayi ita kanta ta rasa dalilin jin bacin ran nata sosai, sakin jikinta tayi yafara feeding dinta yana ba kanshi Shima saida suka cinye tas ya tsiyayo musu lemon kwakawr yakai mata bakin ta ta kawar da mai don ta mugun koshi batason ta kara wani Abu duk da Aman nata bakoda yaushe take yinshiba sai taci Abinda bai kwanta mata ba, Shidai yasha sosai saida suka kammala suka kwashe komai suka kai kitchen kafin suyi sallar magrib data kawo jiki, tayi matukar gajiya bacci kawai take sonyi, wayar ta ta janyo domin kiran Auntyn ta, taga miss call dinta har uku, ta kirata back, "Yasmin yaushe zaki dawo gidan ki na BARIKI you have to live here nan ne wurin Aikin mijin ki hakura zakiyi da Rayuwar wannan gidan ki dawo nan kodan kare mutuncin gidan Aurenki tareda kore duk wasu kadan garun dake neman bata miki ruwa........   "That is fact kowace matar soja tanada kalubale a Rayuwar ta ta BARIKI ko sharrin matan banza ko kuma sharrin shaye shaye duk macen da Allah ya kare mata mijinta a BARIKI ta godewa Allah duk da a kowace Rayuwar Aure ba matan soja kawai ba KO civilian din akwai kalubalen don haka Allah yabamu ikon cinye jarabawo yin mu baki daya,   *Matar Soja* [9/18, 6:30 PM] Asli Smasher : (¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯) тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   Written by FENERH   *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby 53&54 Shiru tayi tareda kallon shi, kafin tace meyake faruwa ne Aunty wani Abu ya faru ne? "Aa kawai ki dawo nan da zama zaifi miki nidai Abinda zanfada miki kenan, kashe wayar tayi kawai tarasa meke faruwa da yasa Aunty maryam tace ta dawo BARIKI, matsota yayi sosai tareda dora hannun shi saman kirjin ta dake tsokale mai ido, "ya akayine matar MA? "Meyake faruwa ne a gidan ka na BARIKI? Tafada tareda cire hannun shi a jikinta , d'an matsawa tayi kadan tana mai kallon tuhuma, "oh come on baby kidaina rigimar nan haka mana kece fa matata kibarsu da da shirmen su I will handle them in my way I just want you to believe me, wai what is going on? Kafada min, "Tundazu naso inmiki magana akan zuby baki bani chance ba tun ranarda nadawo aka kirani tana son ta batamin suna a wurin aiki na last ta turomin wata da sunan tanada cikina this time A round ta dakko ciki da kanta ta dawo gidana bayan ta yi report a office din mu cewar tana dauke da ciki na nakuma koreta yanzu an bani umarnin dole in kula da ita har ta haihu, "but the truth is ba cikina bane bantaba Tarawa da kowace mace ba turmi da tabarya ni nasan ina tsayawa suyi romancing dina domin insamu relief saboda sha awar dake mun yawa Amma bantaba kusantar zina ba impact kyamar tsoma jikina nake a jikin kowace kazama, kece mace ta farko da nafara jin feelings irin haka a tareda ni tundaga ranarda na dora idanu akan ki naji a jikina you are the one for me , Yasmin ke kadai ce mace ta farko a Rayuwa ta and you are the last insha Allah, inkin lura tun ranarda na dawo ban samu kaina ba Abin ya dameni sosai ba komai nake tsoro ba sai banason Abinda zai daga miki hankali zuby ta bullo ta inda banda yanda zanyi da ita Amma nabata dama har zuwa lokacin da zata haihu muyi DNA test a lokacin zan mata nawa wulakancin, Ajiyar zuciya ta sauke tareda shigewa jikinshi to yazatayi da kaddarar ta haka ta sameshi bata isa ta canja mai Rayuwar da yariga yayita Abaya ba dole zata taimaka ma mijinta har ya fita daga kaidin matan BARIKI, "oh baby nagode da kika fahimceni dama ina tsoron Abinda zaifaru ne nakasa miki bayani tunfarko am afraid of loosing you in my life, zame kayan jikinta yafarayi tayi saurin riko hannayen shi, ya bata fuska kamar yaro "why now? "Dazu fa munyi kuma kaga ana kiran sallah " yeah I no muje muyi sallah yau ba bacci sai kinbiya bashi Kinsan ni mayen ki ne bazan taba gajiya da keba, A daren sai da taso guduwa domin ganin tayi ya kara like mata daya huta zai nemi kari saida tasa mishi kuka tareda pretending marar ta na ciwo ya sarara mata, washe gari basu tashiba sai karfe goma suka tashi tunda sukayi sallar Asuba kawai suka shige bargo, ita tafara tashi ta hada musu simple breakfast tareda taimakon baba jummai mai tayata aiki saida ta kammala ta nufo dakin nasu tayi wanka tareda gyara kanta ya zuba ado cikin Riga da zani na atanfa tayi matukar yin kyau saida ta feshe jikinta da kamshi kafin ta matsa kan gadon. Ta zubawa kyakkyawar fuskar shi ido ta yi murmushi tareda shafo saman kirjinshi mai daukar hankali da tafiya da hankalin mata, bai bude idanun shi ba ya Dora hannun shi a kan nata kafin ya bude idon shi ya sauke a kanta, kara ware idanun shi yayi ganin yanda tayi kyau sosai ya shafo marar ta tareda maida idon shi kan kirjinta dake kunbure har yana hango tsagun su ta sama, ya finciko ta ta fada kanshi, "a bani breakfast madam tunda antashe ni, "Good morning tafada tana kara lafewa kan kirjin shi, "how are you? "Fine, muje Kayi wankan your break fast is ready, "noo ba wannan nake magana ba Abincin cikin zani nake magana bana kitchen ba, ido ta zaro "haba mana kusan kwana fa mukayi fa muna Abu daya, "uhm ai kece kike ja Kinsan bazan iya jin dumin jikin ki in hakuraba gashi kinzo early morning kinkuma tayar min da hankali don haka kiji dani idan kinaso intashi mu karya, so take ta zama jaruma ta fagen bashi goyon baya a duk lokacinda ya nemeta don haka tashi kawai tayi tareda zuge zip din rigarta saida takaishi karshe kafin ta tashi tsaye, gaba daya ya zuba mata na mujiya ya matsu bata bude mai Abin kaunar shi ba, cikeda tsokana tafara sauke rigar daga sama tana jamai rai, duk ya k'agu ji yake kamar ya fisgota, saida ta cire dama batasa bra ba saboda Sam batason sawa yanzu saboda kirjinta sai ya rika yimata zafi,   Saida ta cire ta juyomai su tareda Dan juyawa saida suka motsa sannan ta daga rigar zata mayar ta juya tana shirin gudu, saika tashi Kayi wankan zanbaka kasha Inba... Tsit tayi jin hannayen shi duka biyu akan su ya musu wani irin salon kamunda saida ta hadiye sauran maganar ta tuni kasala ta rufeta gashi ya manna mata jikinshi tanajin yanda yake sukarta ta baya, "kinaso ki karasa ni ne zaki jamun rai ki gudu to baki isa ba, dagata yayi cak ya maidata gadon sannan Shima ya haye tareda maida bargo ya rufesu ruf saida ya kuma gurzarta kamar ba gobe kafin ya sarara mata ya koma gefe yana lallashin ta "sorry baby gobe zantafi zanyi kewarki sosai, wancan karon nikadai nasan irin wahalar da nasha don wurin ba kyaune da bazan iya tafiya inbarki ba a nan, Juyowa tayi tareda rungume shi, "yanzu ma bazamu kuma yin waya ba sai kadawo? "Noo nasa an kara service a wurin kullum zamuyi waya yanzu ai bazan iya zama Banji muryarki ba sai jini na ya hau gashi inaso inrikajin lafiyar baby na, Ok tashi muyi wanka yunwa nakeji, sauka yayi bakomai a jikinshi ya dagata cak sai bathroom bajewa yayi ya bubbude a tub din yace ita zatamai wanka, haka tafara wankeshi yana lumshe ido tareda yawo da hannun shi a ko ina najikinta, dakyar tasamu tayi escape suka gama wankan haka suka fito yana layi domin jinshi yake kamar ma baiyi komai ba Amma yasan inyace zai kara zai cutarda babyn shi,   A dakin ta kawo musu komai suka karya sannan ta shirya cikin wata shigar na purple code less mara nauyi Riga da sket ya zauna cif a jikinta ta murza dauri Shima ya fito cikin farin yadi mai shara shara kana hango farar singlet din shi yayi kyau yana baza kamshi, yace ta dakko gyalenta zasuje malali sugaida hajiya, cikin farin ciki ta ce tom tareda ciro farin mayafi da gyale harma da jaka, ta kara fesa jikinta da turare yana tsaye ya zuba mata idanu, wani farin ciki yakeji domin yasan yayi sa ar mata ga kyau ga kuma nasaba don ta cika mace ciki da waje, Rikota yayi suka fito ta sallami baba jummai tace sai sundawo cikin sabuwar motar lefen ta daya fara suka shiga yace yau ke zaki tuka mu ina gefe,, tace tom muje, ta murza key ya zuba mata ido kamar ya cinye ta, ta fita a gate din suka dauki titi " kaifa zaka rika nuna min hanya bansan ta ina zamu bi ba, gyara zama yayi ya zuba mata ido tareda janye gyalen daga kafadar ta ya mayarda hannun shi wurin da yakeso, "ina tuki nefa karka sa in watsar da mu a titi Kasan ba wani iyawa nayi kamar kaiba, "uhm sai mu tafi tare mu duka Kici gaba da tukin ki kawai kibarni inyi wasa da kayana, haka yaketa motsata yana lumshe ido har suka isa Lafiya tareda taimakon shi, katon gate din sojoin suka bude mata ta kunna kai tuni suka fara saramai ya wani hade gira bayan ya gama lalibeta a cikin mota matsowa yayi kusa da ita, "Baby hajiya zata gane kin gama more mata yaro a mota kinga yanda nakoma, yafada yana mai manna mata jikinshi a gefen ta, ido ta zaro "baka gajiya ne wai kai,? "Indai da gidan dadi ne bana yi muje ciki ma kibani gaskiya bazan iya hakuri nida Abuna ba, "you are jocking? "Am not, tasan ba karamin Aikin shi bane zai aikata, tundaga kofar main falon sukafara jiyo hayaniyar Y'an matan na hajiya, ya hade fuska yakara rike mata hannu gam duk da tana kokarin yasaketa, "stay still ko indaukeki gaban hajiya dole ta natsu, suna jin sallamar shi suka shiga taitayin su, gaba daya suka zubawa matar tashi ido tuni kowacce ta raina kanta, sunga kyau haduwa da kuma wayewa dole ya rika musu kallon Y'an kauye kuma munana akoda yaushe tunda yanada indiya,   Da ruwan masifa yafara "wato ku kullum kamar akuyoyi Sam bakwa girma ko, yafada yana watsa musu mugun kallo, itadai neman wuri tayi ta zauna bayan ta samu ya saki hannun ta, zamewa sukayi kowace ta kama gabanta shi kuwa zama yayi kamar zai shige jikinta "muje side dina mufito kafin ku gaisa da hajiya baby, nidai bazan iya wannan Abun kunyar ba ni nasan kunya idan kasaba yi a gidan mu nan bazan yarda ba. Dariya yayi, baby saidai kar akuma kin manta ranarda nazo na kwakuleki a gidan nan kenan,.. Kafin tayi magana suka jiyo muryar hajiya "oh ni baba na ka kawomin yata kuma kabarta a falo ka tsareta da shirmenka ko, shagwabe wa yayi kamar karamin yaro "hajiya nace muje dakina na gaji inason tausa taki, matsowa tayi tareda riko hannun ta tana cewa "mara kunyar banza da wofi taki taje taso kinji mu shiga ciki y'ar Albarka kiyi hakuri kinji da halin baba na, "kai hajiya yau ni zaki y'ar ki kama wannan ko da ban kawota ba ai, "ai Kasan batada kafa ko batasan hanya ba, juyowa tayi ta mai gwalo yace "lalala ni kikewa gwalo zamu hadu a gida, "Sai inrike ta a nan dama gobe zaka koma tashi yayi yabi bayanta, " kice zamu kwana tare kenan ba inda zanje kuwa, saida suka shiga dakin ta ta zame kasa tafara gaisheta tayi saurin dagata tashi y'ar Albarka Allah ya miki Albarka Fatima Allah ya Albarkaci zuri arku, ta Amsa a hankali, kanta a duke da kanta ta kawo mata kayan motsa baki Shima ya shigo, "wai yau nine bare aka ware ni, ka fita magana zanyi da suruka ta katafi dakin ka a gyare yake, "bakin shi ya turo. "Kai hajiya to tazo muje mana tare, nace ka fita ta tashi ta raka shi tareda maida kofar ta rufe, yayi dariya daman yasan kaunarda ke tsakanin hajiya da Yasmin tunfarko tun batasan cewa zata zamo matar shiba,   Zama tayi ta fuskance ya da kyau, "dama naso sai yatafi insa akaini gidan naku muyi magana akan babana Fatima nasan Kinsan komai dake faruwa, yanzu kinfini kusanci da babana kece matar shi duk yanda zakiyi a matsayin ki na matar shi ki taimaka mai Allah kuma ya raba shi da sharrin matan banza tunfarko sakacin shine, da yasaki jiki da yarinya mara tarbiya tayi sanadin fadawar shi harka da matan banza, Nagode wa Allah ma da baya wasa da salla baya shaye shaye da illar da zata yimai ba kadan bace don malamin dake bashi taimako yafada min anyita jifarshi da sihiri Kala Kala don dai yayi riko da ibada ne Abun baiyi wani tasriri a jikinshi ba amma wannan shedaniyar yarinyar ina kan kai kukana a wurin ubangiji Allah zai mana maganin ta cikin ruwan sanyi, kiyi hakuri haka Allah ya tsara Rayuwar shi tunfarko saidai mu tayashi da Addu a,   Shiru kawai tayi domin tanajin matukar bacin rai duk lokacinda ta tuna da Rayuwar shi ta baya wadda take kokarin taba farin cikin su a yanzu, hajiya ta fito mata da wani Dan madai daicin galan, ki rika shan wannan baida illa ga cikin ki Amma zakiji dadin Amfani dashi Zuma ce hadin Sudan nasa aka kawo muku keda yayyin ku ta ciro wata gumba mai kwakwa da su gyada da Aya tace kirika damawa da nono duk basuda illa kuma ko shekara zatayi bazatayi komai ba, godiya tayi. Sosai tareda jin matar ta kara shiga ranta ta diddila da murfi ta sha tareda karawa domin zumar harda dabino tanajin gardin ta sosai , tace kisha a hankali saboda zaki duk da batada damuwa Amma kodan gudun tashin zuciya, Kunya taji kadan ta rufe Domin ita dadi tayi mata kodan kwadayi zata sha ta, ta tanbayeta ya Y'an Aikin ta sunyi? "Eh kawai baba na ce ta tsaya kodan su gyaran gidan da girkin sojojin dake gidan " to Aikin bazai mata yawaba ko za a karo wata tsohuwar ne inbakya ra ayin Y'an matan, "aa itama ta isa zandauketa gobe mu koma BARIKI kafin ya dawo, "ai ba damuwa duka gidan ki ne, inkina bukatar wani Abu ki fada sai atanadar miki, godiya tayi sosai tana kara godewa Allah da yabata uwar miji ta gari, wayarta tayi kara ta daga ganin sunan shi ne yasa taki dagawa, Saida ya kirata sau uku taki dagawa, tana zaune tana kara kurbar zumar ta ya turo kofar tareda hade fuska, don wulakanci bakya ganin kirana ne? Kallon shi kawai hajiya tayi ta kada kai "Fatima tashi kije ya baki uwar da zai baki sarkin naci, shidai juyawa yayi ta mike tareda gyara gyalenta ta nufi gefen nashi gidan ba bakonta bane don haka tasan hanyar da zata sadata da gefen shi, batasan meke damun shi ba da ya dame ta sai tazo, tana shiga falon taji yayi sama da ita bai direta ko inaba sai kan gadon shi ya fara haukata ta fa zafafan touch, tareda hade bakinsu wuri daya tuni yaji gardin zumarda take sha ya mai welcome tuni yafara bata tsotso mai cikeda dokin Kasan cewa da ita, Duk ya rura mata jiki, haka suka farantama juna duk da kasanta na neman agajin gaggawa haka ta sake mai ya murjeta son ranshi sai la asar sukayi wanka suka fito domin tafiya, a falon suka samesu itada Y'an matan ta, "ai har cigiya na bayar ko kun wuce a she kuna ciki, itadai Yasmin kunya rufeta tayi ta dukar da kanta kasa "ina hutawa ne hajiyata gobe fa zankoma yanzu ma idan na shiga gida sai gobe idan zantafi zanfito, yafada ko a jikin shi, "to naji mara kunya a sauka Lafiya, shiga daki tayi ta fito mata da zumar ta da turarukan wuta ta hado mata tabawa cikin Y'an matan suka kai musu mota, ta rakasu da Addu a suka tafi cikeda farin ciki, shi ya tuka motar har suka isa gida Lafiya taso ya kaita gida yaki yace yaushe tabar gidan, ta kuma so ya kaita BARIKI yaki yace basai tajeba ga gidan ta, Shiru kawai tayi mai ita Kadai tasan me ta shirya bayan tafiyar shi,   A daren ji sukayi kamar kar gari ya waye saboda kar su rabu sun raya wannan daren hade da taimakon magun gunan da hajiya ta bata shi kanshi ya haukace da jin wani sabon gardi da galmi tayi mugun laushi koda Asuba saida ya kuma lallabe ta kafin yayi wanka, cikin kakin shi ya shirya tareda baza kamshi ya fito a sojan shi, karfe bakwai Ahmad yazo , rungume shi tayi tsam taji wasu irin hawaye masu zafi nabin kuncin ta tuni tafara jan sheshsheka ya tallsbota sosai a jikin shi, "karki karya min guiwa madam kiyimin Addu a sannan ki kulamin da baby na please take care of your self and my baby bakuda matsalar kudi kunada komai a hannun ki inkina son Aike you can send those soldiers, ya duka yabata kiss a cikin ta kafin ya bata a lips dinta saida ya lashe hawayen fuskar ta tas sannan ya saketa tareda yin dariya "haba matar soja ki zama jaruma mana yanzu idan baby yazo yaga zantafi yaga Maman shi na kuka Shima kukan zaiyi kenan, Murmushi tayi tareda cewa "kaje baban Auwal na jiranka Allah ya kare mana ku, "Amen sweet wife Allah yasadsmu da Alkhairi, bata iya rakashi ba saidai yana fita tasa kuka mai sauti ta koma dakin sai taji gidan ya mata mugun girma yanzu dama ganin shi tare da ita yasa Sam bata ganin girman gidan, komawa tayi tareda kunna wayar ta tafara chart a grp domin rage zaman Kadai ci,   A haka Rayuwa taci gaba da tafiya yanzu tana samun shi akoda yaushe idan ya kirata saidai kullum Kara tuna mata yake ta musu Addu a, tayi matukar kewarshi Shima haka ne a gefen shi saidai aiki bazai barshi yazo ba, a cikin wata daya duk sati suna haduwa a gidan su itada y'ar uwar ta sometimes ma tare suke zuwa gidan hajiya ta jajje gidan Y'an uwanshi dake nan kaduna suma sukanzo mata, ga cikin ta baya bata matsala Allah ya bata ciki mai saukin gaske Bayan wata uku itada Oga saidai waya ko video call duk lokacinda yayi video call da ita sai ya rikice mata ga cikin ta ya fara bayyana sai budewa takeyi tana Kara haskawa batada damuwar komai saita rashin mijinta, yau ma da sukayi waya rigima tasa mai ita dai Tanason ganin shi, dariya yayi "madam kina tunanin kinfini damuwa ne? Kawai ina matsewa ne ji nake ko yanzu kamar in janyoki a wayar nan inji ni a jikin ki, kullum hadarin wurin nan karuwa yakeyi duk lokacinda muke tunanin Abin yayi sauki sai su kuma bullo mana ta wani wurin don haka ko zamu samu shigowa sai karshen watan nan please take care of your self and my baby kice dadyn ta na missing dinta da Maman ta,   Tarasa dalilin da take yawan jin faduwar gaba gashi ya hanata zuwa gida ko zata rage damuwar sai yawan mafarkai da kuma take yi akan mijin ta kullum sai ta kira shi taji ko Lafiya yake yace mata kalau yake tadai Kara Addu a akan Wanda sukeyi, ganin hankalin ta bai kwanta ba Yau ta shirya ta tafi gidan hajiya tareda fada mata Abinda takeji, "nima Fatima kullum hankali na ba akwance yake ba idan na kirashi zai ce min kalau suke , A gidan hajiya ta kwana a ranar don bazata iya komawa gidan ba gaskiya hajiya sai Kara kwantar mata da hankali takeyi, da sassafe tana zaune akan daddumar salla tana lazimi wayarta tayi Kara hajiya ce ta mika mata gashi ana kiranki, saida gabanta ya fadi kira da sassafe waye wannan ganin bakuwar numba yasa gabanta faduwa, taga bakuwar numba, dauka tayi kawai tareda hello, "please am I talking to Mrs Muhammad Abdullah? Gaban ta ya mugun faduwa tareda cire wayar akunnen ta domin dagaji ba Alkhairi za a fada mata ba ta saki wayar hajiya dataga haka ta taso tareda daukar wayar jin Ana kan magana, tuni ta sulale kasa tayi zaman yan bori, jin salatin hajiya yasa ta dawo hankalinta, "Ba Abinda ya sameshi ko hajiya kifadamin Lafiya lau mijina yake kifadamin ba Abinda zai faru dashi yafada min zai dawo ya gan mu nida babyn shi, sambatu kawai take yi duk ta rude , hajiya tace shirya muje Asibiti mijin ki na can 44 ance Y'an fashi sun kawo musu hari wasu sun mutu tashi muje inga halin da yake ciki Fatima, ta fada jikinta na rawa.......     *Matar Soja* [9/20, 11:17 AM] Asli Smasher : (¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯) тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   Written by FENERH   *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby 55&56 A rude ta mike ko canja kayan baccin ma bataji zata iya yiba, dama da katon hijabi a jikinta suka fito harabar gidan motar ts suka shiga gaba daya ta gama rudewa ga wani irin juyi da cikin ta keyi, sai salati kawai hajiya keyi, ikon Allah ya kaisu Asibitin, hajiya tace yanzu ki kira mana number Ahmad muji suna ina, ? Anan taji hankalinta ya kuma tashi tunawa da Ahmad da tayi yakamata a ce shiya kirata ba wani ba Allah ya rufa musu Asiri kuwa, Tunda daga bakin gate suka fara tanbayar sojojin da aka kawo daga birnin gwari a yau ne ko jiya? Wani yace "oh MG Abdullah suna operation Lafiya dole word madam, ya nuna mata wajen gaba daya basa iya cewa komai karfin hali kawai takeyi ga hajiya ma gaba daya ta gama rudewa, a zaune suka samu Ahmad hannun shi nannade da bandages ga goshin shima da plasta tayi saurin karasawa wurin shi jikinta na rawa, duk ta rikice hajiya ce tafara cewa "Ahmadu ina baban nawa,? "Mama meyasa kukazo waya fada muku? "Wani yakirani a waya yanzu, yasmin ta bashi Amsa, "Oga na emagency ya samu rauni sosai akai da hannu koda muka iso nan baima sani ba zasuyi mai xray kafin musan koda wani raunin, kuka yasmin tasa mai cin zuciya tareda rungume hajiya da itama karfin hali kawai takeyi, "meyafaru daku ne Ahmadu,? "Wallahi mama tunfarkon watan nan sai ankawo mana hari Allah baya basu sa'a jiya kawai sunyi Ambushed din mune amma munkashe su sosai Oga yayi kokari sosai wajen fada dasu gashi ba muda makamin da sukeda shi, duk da yaji rauni haka yake fighting dinsu sai daga bayane ma muka gane yaji rauni bayan mun samu nasara akansu munkama wasu wasu sungudu sun kashe mana sojoji shida a ciki harda Oga umar makocina, Wani irin kuka ta sa Mai Kara "yanzu bazamu ganshi ba? "Sai sun kaishi resting room in sun gama dubashi, kutaya shi da Addu a kawai mama, "innalillahi wa inna ilaihirraji un, hajiya keta mai maitawa, wuri ta samu ta zauna Yasmin ma ta zauna har wani jiri takeji yana neman kadata, yanzu shikenan baban Amla ya rasu wayyo duniya duk da batada halin da mijin nata yake cikiba Amma ta mugun tausayawa Maman Amla, matsowa yayi yace ta aramai wayarta zai kira maryam,   Shiya fada mata halin da ake ciki tareda bata umarnin zuwa da breakfast saboda su hajiya , hankalin maryam ma yatashi ta kira su baba ta fada musu suma, kafin kice me Asibiti ya cika taf da Y'an uwa da abokan arziki harda Y'an Uwan shi duk sunzo kowa sai Addu ar Allah yasa suga Alkhairi sukeyi, yasmin dai tayi kuka hartaba uku lada sai lallashin ta akeyi "kidaina kukan nan haka kinga bake Kadai bace ga tea an hada miki kisha karki fadi kijama mutane wata damuwar, Hajiya keta lallashin ta mama ce tace barta hajiya tunda batada hankali tazama yare bazaki tayashi da Addu a ba zaki zauna kina kuka ko shine zaisa ya warke ko kuma kaddarar shi ta canja, "bita a hankali Saude, baba yafada yana maijin tausayin y'ar tashi, wasa wasa har karfe goma ba su sashi a idoba ga kukan ta yaki tsayawa kowa dake wurin ita yake tausayawa domin kukanta irin mai ban tausayin nan ne, jiya ta gama waya dashi yau akirata ya na cikin mugun hali ba Abinda take tunawa irin Alkawuran da yake mata kwanan nan "baby ina dawowa zamuje muma baby na shopping baby yafara kicking? Kullum maganarshi kenan babyn shi da kuma kewar ta, Shafo cikin tayi tareda runtse idanun ta tayi magana a cikin zuciyarta "insha Allahu babanka zai tashi ya zai yi wasa dakai my baby, duk hankalin su yagama tashi ganin har shabiyu ba wani magana sai likitoci ke fita da shiga masu kaki, sai kusan karfe daya suka kira Ahmad, yashiga saida ya dauki lokaci ya fito ta tashi da Sauri ta nufeshi "Lafiya baban Auwal? "Alhmdulillah kuzo keda mama ku ganshi basa bari mutane na shiga ciki ko yanzu na rokesu ne da kyar, cikin sauri ta wuce ko hajiya bata jiraba, saidai tundaga farkon dakin jikinta yayi mugun sanyi ganin sojoji Kala Kala a jere kowane da tashi matsalar wani ba hannu wasu ba kafafu wasu kuma bama Susan inda kansu yakeba, Wallahi Y'an uwa duk wadda tasan 44 gefen Y'an lfy dole idan har ta taba shiga saita koka sojoji ne daga meduguri sai ka musu kuka kaga mutum da ranshi ya rasa kafafu ko wani bangare na jikinshi saboda bautawa kasar shi wallahi kutaya sojojin mu da Addu a suna cikin hadari a Rayuwa wata ma mijinta zai mutu shekara guda bazata sani ba Wasu ko gawar su ba agani, Allah yasa mudace, Kamar wadda kwai yafashe mata takasa karasawa wajen datake tunanin MA dinta ne akwance hannun shi a nannade ga kanshi ma haka duk fuskar shi a kunbure kamar bashiba wani irin jiri yaso yarda ita hajiya ta rikota tamau duk da batada karfi, takarasa da ita cikeda karfin hali, kuka ne ya kufce mata ta rufe bakinta domin akwance yake kamar gawa ko motsi bayayi ga oxygen a hancin shi batasan lokacin da ta sulale a sumeba, da taimakon Ahmed suka fita da ita saida aka bata gado a wani word din suka daura mata drip tareda Allurai kafin ta farfado, ta zabura ta kuma sa kuka "mama ku ciremin ruwan nan zankoma wurin shi inganshi ya farfado!? Mama ma idanun ta sun ciko sosai don ta bata magun tausayi Aunty maryam kam saida tayi kuka ganin halin da mijin y'ar uwar tata ke ciki, "kiyi hakuri yasmin Kici wani Abu kinga kodan cikin ki likita ma fada yayi yace harda rashin cin Abincin ma ya janyo miki jiri, ki kwantar da hankalin ki da izinin ubangiji zai samu lfy, "mama bakiga halin da Muhammed ke ciki ba tafada tana wani irin kuka, kiyi hakuri kinfi mahaifiyar shi Sonshi ne ki kwantar da hankalin ki KO zata samu kwarin guiwa kina kallon tsohuwar nan akwai tawakkali da karfin imani,   Haka suketa mata Nasiha saida ruwan ya kare suka matsa mata tasha ruwan tea mai kauri saidai tana gama sha tafara kelaya Amai saboda yunwar da ta shigeta, maryam ta kuma hada mata ta sha kadan, ta mike ita dai zata koma wajen shi, sun canja mai daki saboda gudun hayaniya sunason idan ya farfado suga aikin da sukayi mai akai KO anyi nasara, dakin ta koma duk da nurses din sun so hanata ta shige tareda zama kusa dashi ta riko hannun shi mai lafiyar ta dora a saman cikinta tareda fara yimai magana a hankali, "my sugar please katashi babyn ka na son ganinka gashi yafara motsi, ina kewar ka please ka tashi bazan rika complain nagaji ba daga yau KO sau goma zakayi,   KO motsawa baiyi ba haka ta cigba da zuba mai sambatu daga karshe ta dora kanta saman hannun mai Lafiya, kallon kirjinshi fari tayi mai suma luf luf a waje ba Riga a jikinshi sai dogon wandon kaki kawai saboda kana nun ciwon dake kota ina a jikin nashi, duk da yana cikin ciwo muscle dinshi na nan sai Kara kunbura da sukayi , wata nurse ce ta matso tareda cewa "madam please karki dame shi fa bamason ana mai hayaniya, Itadai kokarin janyo zanin rufarda ke gefen gadon takeyi ta rufemai kirjin shi don wani irin kishi takeji yanda nurse din nan ke kalle mata miji ba Riga, "noo please madam he needs a fresh air so that the wound will heal quick, anki abarshi a buden shegiya wato ta kare Mai kallo, tafada cikeda masifa itadai nurse ba Hausa bataji Ashariyarda ake lafta mata ba ta juya ta fita tana mamakin yanda Yasmin keda mugun taurin kai taki KO bari ta kula da wannan handsome guy din duk dama wai bai da Lafiya baima san me akeyiba,   Sai kusan dare mutane suka watse anyi fama da ita ta tafi KO wanka tayi taki sallah kawai take matsawa tace sai ya farfado zatayi wankan hajiya tace abarta tunda Ahmad na kusa tunda shima bawai an sallame shi bane kawai ganin ciwon ogan nashi yafi nashi dole ya mike , gadon dake gefen nashi ta kwanta wayarta ta kunna da tun zuwanta bata koma kantaba gaba daya ta kasa bacci daga karshe ma dadduma ta haye tafara nafiloli, wajen karfe shabiyu ya bude idon shi, a hankali yakebin dakin da kallo ya hangota a zaune a sallaya, motsawa yayi domin kanshi da bakinshi sunyi mai nauyi sosai,   Saurin tashi tayi ta nufi gadon da sassarfa, idon shi dake cikeda ciwo ya zuba mata domin sunyi mugun ja da Alama yanajin ciwo sosai Amma yakasa cewa komai sai ido, " baban baby kafarka Alhmdulillah tafada cikeda farin ciki ta riko hannun shi sai wani irin hawayen farin ciki ke fita " Alhmdulillah kafarka Sannu my sugar, tafada ganin yana juya kai ta zabura batareda tsoran komai ba tafita, a nan ta samu likitan dake on duty ta kirashi jikinta na rawa, Yana zuwa ya saramai "tank God oga you are fine girgiza mai kai kawai yayi ya duba shi tareda zare mai oxygen din yace " madam congrats oga is Alright saidai raunin jikinshi da hannun shi da aka dora sai ankula kar aikin ya lalace, godiya tayimai yace zata iya bashi KO ruwan tea ne saboda yasha drugs dinshi, jikinta na rawa ta bude kayan tea da aka ajiye musu manya ta hada mai dama akwai katon plask ta zuba ruwan zafin tareda Ajiye hijabin ta domin likitan ya tafi, ido kawai yake binta dashi kayan baccin jiyane a jikinta, Masu santsi Riga da wando dogo rigar Mai hannun shimi ce KO bra babu a juk8nta, Da taimakon ta ta dagomai gadon ya zauna sai ido kawai yake binta dashi saida ta zauna yace "go and lock the door yafada dakyar kalmar tafito domin wani irin kishi yskeji ganin yanda yake hango kayanshi kar wani yashigo ya ganta yasan wani na kallar mai ita zai karasa shurawa for sure, Kallon shi kawai tayi ta taka ta rufe kofar da key tabarshi a jiki tana murmushin jin dadi wato yana ciwoma halin na nan cikinta ya koma zubawa ido yana hango yanda ya tasa yayi wata Ajiyar zuciya ta matso tareda dago cup din ta kai bakinshi, "spoon yace mata ta gane me yake nufi ta fara bashi a baki a hayana kare mata kallo don jiyake idan ya bude baki kamar kanshi zai cire, Saida yasha sosai kafin ta bashi maganin ta maida gadon ya kwanta still ido kawai yake binta dashi, sai a lokacin takejin bazata iya bacci ba wanka ba bathroom din da yake fes tashiga ta kwabe ta sirkq ruwa mai zafi sosai tayi wanka domin akwai komai sabo a ciki dakin special ne saida ta tsane jikin ta da towel kafin ta mayarda kayanta dole ta fito ya zuba mata idanun shi, "wanka yanzu da tsakar dare? Yafada dakyar, "um banyi wanka ba yau saboda kai, Bai kuma cewa komai ba sai ido ta rufe mai jikinshi saboda sanyin garin har bacci ya daukeshi ta zauna tareda zuba mai ido batajin zata iya runtsawa ganin mijinta a cikin wannan hali tasan don yana jarumin namiji ne har yake iya bude baki yana mata magana tasan da Lafiya lau yake da tuni ya makale mata irin kallon da taga yake aika mata dashi, Saida aka kira sallar Asuba ta koma bathroom tayo Alwala ta tada nafila kafin tayi sallar Asuba, tana zaune a wurin har gari yayi haske, bai kuma tashiba domin magun gunan akwai ma bacci da zasu taimaka mai, karfe bakwai Asibitin ya kuma cika har da su baba yauma mama ta kawo mata break fast din da takeso taci sosai domin hankalin ta ya kwanta tunda ya farka ta gani a daren jiya, koda hajiya ta iso taga fuskar ta da walwala tace "Alhmdulillahi Fatima daga ganin fuskar ki babana ya farfado KO, ? "Eh hajiya Amma kuma tunda ya koma bacci bai tashiba kuma har yanzu tafada muryar ta na karyewa, "Ai haka ma mungodewa Allah Fatima wasu ma ran suka rasa baki daya sai muyi mai fatan samun Lafiya kawai, tace tom Aunty maryam ma ta iso wurin, ta tanbayeta ya su Maman Amla ? "Wallahi zaki tausaya mata yasmin rashin miji ba wasa ba saikin zubar mata da hawaye, ta mugun jin tausayin ta tareda Addu ar Allah ya musu gafara, Mama ta matsa mata ta je gida ta huta tunda jikin da sauki kodan cikin ta, ita kanta bacci takeji sosai don bata runtsa ba Sam jiya, dakin ta koma ta dauki key din motar ta kafin ta matsa kusa dashi ta shafo gefen fuskar shi wurinda ba kunburi ta duka ta bashi kiss a goshi " Allah yabaka Lafiya Zuma ta, saida ya dan motsa idonshi kafin ya ci gaba da baccin ta tafi, Gidan ta ta koma tanayin fakin ta shiga tasamu baba jummai zaune ita Kadai tana kallo a falon, "uwar dakina Sannu da zuwa, "yauwa baba "ya mai jiki kuma jiya mai gadinki ke fadamin Allah ya Kara tsare su ya kuma bashi Lafiya Amen tace ta wuce dakinta kai tsaye bathroom ta shiga ta yi wanka tareda watsa kayan a dustbin ta dauro towel KO mai bata tsaya shafawa ba ta fada gado, bacci ne ya dauketa mai Lafiya, Bata farka ba sai karfe goma sha biyu ta mike bakinta daukeda salati, ta janyo wayarta taga time durowa tayi ta koma watso ruwa, cikin sauri ta shafa mai da humrar ta mai taushin kamshi kafin ta bude katon walldrp dinta ta ciro wata doguwar rigar voil orange mai kyalkyali taji aiki ga rigar ta mugun fito da surar kirjinta domin play ce ta kamata daga kirjinta zuwa kugunta daga kasa ta bude sosai, ta daura dankwali tareda dakko matching gyale light orange da takalmi ta yafa ba make up a fuskar ta KO kadan sai wet lips da powder, tayi matukar yin kyau sannan ta dauki wayarta da jaka ta fito, dakin da baba jummai take ta karasa Saida ta ciro dubu goma a Jakarta ta bata "gashi baba zankoma Asibiti don Allah ku dafa duk Abinda kuke bukata ba lallai indawo yauba ma, "to Allah yasaka da Alkhairi uwardaki na nagode sosai, ta juya dakinta domin tayi mantuwa brush dinta ta dauka tareda turare ta ciro wata rigar bacci da katon saabon hijab da single zani ta jefa a Jakarta sannan ta fita, ta matsu bata ga halin da yake ciki yanzu, Tukinta takeyi cikin natsuwa harta isa 44 bata tafi da komai ba saboda tasan Y'an uwa suna kawo Abinci ga su drink da ruwa katon katon jiya Aunty Halima ta kawo ba Abinda babu a wurin don haka gab da word din da yake tayi parking domin akwai gefen motoci , ta rufe motar ta nufi dakin cikin natsuwa, jinmuryar su hajiya dasu yaya Halima yasa ta san cewa ya farfado kenan, da sallama ta tura kofar ta shiga kanta akasa domin tasan idanun shi biyu karyasa tasha kunya, Tunda ta shigo ya kafeta da ido ko kiftawa bayayi wata irin wawuyar Ajiyar ya sauke har wani irin karkace wuya yayi baida muda su hajiya dake dakin ba don su mama tuni suntafi Aunty maryam kuwa na wurin mijinta a dakin da yake, dagashi sai Y'an Uwan shine a dakin, gaishe su tayi batareda tayi gigin daga kanta ta kalle shiba, hajiya tace to Fatima tunda kindawo bari mugudu mubaki wuri Kici gaba da wannan mijin naki, bude baki yayi yace "bayan ko kallo na ma takiyi hajiya zaku tafi kubarni da ita kuna ganin bata ko damu daniba, "Amma dai baba na duk kokarin da yarinyar nan tayi jiya nasan bata runtsa ba kodazu saida nasa baki ta tafi gida tadan huta, "To basai tazo ta rungume niba da tadawo kallifa inda ta wani makale, "oh ni jikar mutum hudu Kadai kula karka fama aikin hannun ka kaji mai likita yace ko, ? Barshi kawai hajiya yazai wani hanani yin Abinda naga dama Allah ne ya nufi zanrayu da yanzu nazama gawa don haka ku kyale shirmen likita, su yaya Halima suka yomai ca "to kar Allah yasa ka kiyaye jikinka zai fada maka ai shugaban marasa kunya hajiya ni natafi kutashi mu wuce, Itadai batace komai ba sai Addu a take karyabata kunya a gaban hajiya, suka fita gaba dayansu sukace sai gobe tunda Abin da sauki, suna fita ta bisu domin rakasu ta karbi yaron hannun salma wato karamarsu saida suka tafi dukansu ta koma dakin cikeda farin ciki, tarasa me yasa ya mata kwarjini takasa hada ido dashi Sam, tana tura kofar yace lock it and come closer yafada kai tsaye ta dago kai ta kalleshi for the first time tunda ta shigo yanzu akwai farar singlet a jikinshi, saidai wandon kakin ne har yanzu hannun shi na rataye da abin rataye hannu bandage din kanshi ma na nan saidai fuskar ta sauka yanzu sai dan kukkujewa da tayi a gefen, kafeta da ido yayi tareda zubawa surar jikinta ido ya kalli cikinta da ya bayyana kadan yayi murmushi, "come let me see my baby, Takawa tayi a hankali kamar mara Lafiya domin jinshi take kamar wani Bako ba MA dinta ba she can believe shine a kusa da ita she is missing him like hell ta zauna a gefen shi ya gyara zaman shi, tareda matsowa kusa da ita, "ya jiki? tace mai "am fine meyasa kika tafi Kinsan ina farkowa fuskar ki nakeson gani a kusa dani, naje nayi wanka ne na canja kaya, hannun shi mai Lafiya yasa bayan ya Kara matsota ya yaye gyalen jikinta tareda dora hannun shi saman marar ta kamar jira cikin yakeyi yako harba, tuni ya rude " baby na ya motsa naji baby kinajin yanda yakeyi? Yafada kamar ya shige jikinta, " uhm haka yakemun yanzu hardai idan inajin yunwa, " to kidaina zama da yunwa karki wahalar min da baby na please, Bata fuska tayi " kafi son baby dani ko? Dora hannun shi yayi a kirjinta ya shafo " soyayyar da nake miki ce tasa nake dokin ganin gu dan jini na daga gareki baby ina sonki sosai ko a lokacin da nake cikin halin nan nayi kokarin kare kaina saboda ke ne baby I want to live with you banason intafi inbarki wani ya Aurar min ke I dont want to shear you with any one, rufe mai baki tayi cikin sauri tana girgiza kai " no please muna tare dakai tare zamu mutu idan katafi nima mutuwa zanyi bazan iya Rayuwa baka a tareda ni ba Kasan yanda naji lokacinda aka kirani kana nan kuwa, I felt like kamar nima mutuwa zanyi zuciya ta har zafi takemun when I sow you hmm jinayi kamar jini na hawa kaina, Goshin shi ya daura a kan nata cikin natsuwa yace "kiss me please nayi kewar lips dinki sosai baby ina missing dinki gaba daya ma, yafada yana fitarda nishi Sam ya manta da ciwon dake hannun shi da kuma dokar likita na karya sake ya motsa hannun sai nan da sati daya, ba westing time ta kama lips dinshi tafara bashi sassanyar kiss birkicewa yayi jikinshi ya dauki rawa yakai hannun shi saman kirjin ta saidai rigar ta hanashi rawar gaban hantsi zare bakinshi yayi ya kallleta idanun shi duk sun shige ciki tsabar fitina "babyyyy ki cire zip din nan rigar ta takurani, zaro idanu tayi waje tace "noo Asibiti nefa " and so just do as I say my friend yafada yana jan numfashi, Batason ta batamai rai ta zuge rigar ta baya tareda dukarda kanta tana cewa "kar wani yazo please yagan mu "kowaye ma yazo shi zaiga Abinda zai dameshi ya Kara matsota saida ya sauke rigar ta sama yaja wani gauron numfashi ganin kirjin nata ba bra saboda yanzu damun ta takeyi kuma ma rigar nada breastcup, ganin sunkara cika ga bakinsu yayi baki circle din suna sheki tuni yakara rikicewa ya dafe dayan cikin rawar jiki tareda dora bakinshi akan dayan yafara birkitata saurin dafe gadon tayi da hannayen ta saboda wani irin mugun shock da taji har tsakar kanta kunsan Abinku da mai ciki gashi andade ba a haduba tuni tafara hade legs dinta tana turo mai kirjin shi kuwa sai budurin shi yakeyi, gaba daya ya gama rikicewa ga hannu daya a nade haka ya koma baya yana freeing wandonshi da yakejin ya mugun cika ita kuma kwanciya tayi rigingine tana jan numfashi don ya mugun tsokanota kirjinta sai sama da kasa yakeyi,............   Him kubawa dan dakin ku shawara baruwana uhm,   *Matar Soja* [9/24, 7:09 PM] Asli Smasher : (¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯) тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   Written by FENERH   *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby 57&58 Numfashi yakeja sosai kafin ya matso kusa da ita again ya saka hannun mai Lafiya ya dagota suna fuskantar juna dakyar yake iya bude bakin shi saboda tsabar fitina da kuma zafin da yakeji a hannun nashi, "baby yazakiyi dani? I really need this, yafada yana shafo saman kirjin ta dake Kara haukata mai kwakwal wa, tashi tayi ta Kara rungume shi tareda Dora Hannun ta ta tallabo bayanshi tana sakin numfashi, "sorry Zuma ka bari ka Kara samun sauki muna tare, no for how long zan jira "very soon zaka samu lfy banason wani Abu yasamu hannun ka kaga doctor yace karka motsa hannun aikin zai iya lalacewa "oh come on kyale wani zancen likita da zanbi in cutu, kawai ki Barni insamu natsuwa da iyali na, Dagowa tayi tana mai dariya "da hannu daya zaka samu natsuwar, "oh kina tunanin ko duka hannayen ne bazan iya more matana ba? just come and give me my thing please, yafada yana janyota zuwa jikinshi "please Zuma kaga Asibiti nefa kuma yazakayi wanka idan kasamu janaba? "I will do it, "how bayan ba ason ruwa yataba hannun ga kuma wa innan raunukan na jikin ka, sakin ta yayi tareda jabaya kawai ya runtse idanun shi yanajin wata irin fitina nakara taso mai, Tashi tayi ta gyara rigar ta tareda daura dankwalinta tace "kaci Abinci kuwa? Banza yayi mata domin tabata mai rai, tabashi tayi "Zuma ta, "please go yafada yana bude jajayen idanun shi da suka cika da fitina, fito da idanun ta tayi waje saboda ganin yanda ya mugun hade rai "fushi Kayi Zuma ta? "Nop. Kawai yace tareda komawa ya gyara kwanciyar shi, runtse idanun shi gam yayi, bugun kofarda akayine yasa ta tashi tsreda daukar mayafinta zata bude ya yi magana batareda ya bude idon shi ba, "kidaina fita da gyale and ki sashi akanki ki rufe jikin ki sosai, Murmushi tayi tareda yin yanda yace ta nufi kofar ta bude tsayawa tayi turus ganin wadda ke tsaye tuni fuskar ta ta canja taki matsawa a hanyar tareda kama kugu, "please ki ban hanya zan shiga inga halin da baby ke ciki, "waye babyn nidai nasan ba muda baby a nan and kibar nan kafin inyi disgracing dinki agaban duniya, "oh shut up ni zaki bawa doka inbi ke wacece,? "Ni matar MG Muhammad Abdullah kuma uwar ya'yan shi tafada tana shafo cikin ta, wata muguwar dariya tasaka "oh kin manta ni ce first love dinshi kuma nima ina dauke da cikin shi don haka bani hanya in wuce ko... "Ko me zakiyi? If you are dreaming of pushing me wallahi zanfada miki you better wake up cos hannun ki na taba ni kai forget about ki tabani iskar jikin ki ta wuce ta jikina in the name of zaki tabani wallahi saikinyi da kinsanin Rayuwar BARIKI, sannan da kike cewa ciki na shine wait and see very soon zaki fadi cikin uban waye kike kokarin likama miji na nasan duk Rayuwar da kukayi a baya mijina ba makaryaci bane ke ko kunya bakyaji ki dakko cikin shegen kizo mana dashi saboda ke y'ar marasa tarbiya ce kidawo gidan saurayi ki zauna, and don't think bansani ba I no everything nabarki ne Kici lokacin ki Amma tunda kin dakko kafarki kin kawo min har nan zako kisha mamaki, Ta gyara tsayuwa kafin ta mata mugun murmushi "first love my foo, to me yasa bai Aureki ba me yasa ke ke binshi shi baitaba binki ba can you tell me how many time yaje kofar gidan ku,? Duk namijin da yake sonki shi zai biki bake zaki rika binshi ba Amma dayake ke Rayuwar karuwanci ta Aure ki kullum kina hanyar gidan saurayi saboda a Sara, Wani irin bakin ciki ne ya turnuketa tareda wani malolo da ya taso mata tace "kin shigo cikin Rayuwa ta kin kwace min saurayi da mugayen Asirin ki da yana sona yana gudun bacin raina amma ko yanzu ai yafara karye wa tunda ya Barni a gidan shi kuma for your information muna tare dashi har gobe ya bukata zanbashi farin ciki baki isa ki hana ba, Wata dariya tayi "Allah uwar sharri naji kuma ko gobe yazo yace yana bukata kibashi idan ma yaci bai biyaki ba tunda sana ar kenan ku siyar a ci a biyaku taxi no garage ki kirani zan biya ki don ina son farin cikin mijina.... Wani irin takaici ne yasa ta dago hannayen ta zata gabza mata Mari ya daka mata muguwar tsawa "don't you dare, wallahi that's is your worst mistake da zakiyi a Rayuwar ki inkin tabamin mata, Dama tunda suka fara ya taso tareda zuba musu ido suna fadawq juna magana tareda jin dadin raddin yasmin saidai ganin tana shirin taba mai mata yatashi ba shiri, da kyar ya iso yana jin zafin hannun, yana zuwa ya riko Yasmin tareda shafo cikin ta ya manna mata kiss a goshi, kafin ya juyo kan zuby, "Me ya kawoki nan? Kinsan matsayin wannan kuwa? Let me tell you "she is my wife not my prostitute matata ce farin cikina uwar baby mai zuwa who are you da zaki zauna kina cacar baki da ita? Look zuby before you disgrace your self just leave, and don't worry you said you are pregnant with my baby ko? "Ya kalli shafaffen cikin ta "oh baby how are you? Am waiting for you your dady is waiting for you, Ya bata wani mugun kallo " ina kallon kine kawai tunfarko ke Kinsan ba Abinda ya shiga tsakanin mu dake so don me zaki yi ma kanki karyar ciki? And kisani inada file dinki na Asibiti I no bazaki taba iya daukar ciki ba tunda kin watsar da ya'yan ki wajen Abortion a u. s then daga yau kibarmin gidana kafin ma indawo BARIKI nabarki ne for the sake of our friendship bazan manta da Rayuwar da mukayi a baya ba but naga baki san kawai ciba daga yau karki kuma zuwa kusada gidana ko iyali na if not zan wulakanta Rayuwar ki zaki zama Abin kwatance forget your mother is some one in kaduna, Wallahi mune Nigeria gaba dayanta don haka get lost tayi mugun jin kunyar Abinda MA yayi mata ya akayi file dinta yaje hannun ta wanna sirrin ita Kadai tasan da shi ko Maman ta bata sani ba, lallai MA Aljani ne duk inda ta bullo sai ya ganota, Haka ta tafi batareda ta cimma burinta ba tana fita yasmin ta dauki Jakarta itama zata tafi, ya tare hanya tareda zuba mata ido, "ina zakije? "Gida, tafada kai tsaye, "why? "Kasata dawo kuzsuna tare dama tace kuna tare tuntuni nice na shigo cikin Rayuwar ku dama don haka ni na hakura dakai tazo kawai ta zauna Riko hannun ta yayi tareda mayarda ita cikin dakin kafin ya dawo ya rufe kofar ya zauna ya zuba mata ido na tsawan lokaci yana ganin yanda take kunbura tsabar kishi dake dawainiya da ruhinta, "Yasmin, yakira sunan ta kai tsaye "karki bata rawarki please kin kare ni a gaban ta kizo kuma kinaso ki kawo mana wata matsala, ", oh nice ma mai matsalar bayan ga matsalar da ka janyo mana A Rayuwa, meye Amfanin bin matan banza? Yau ga result nan Ina kwashewa idan wannan tazo gobe wata ce zata Kara zuwa suna min kallon Abinda nake takama dashi sunrigani sani to saime, Dariya maganar ta ta karshe ta bashi ya matso tareda zama kusa da ita yana Kara riko hannun shi domin mugun zafi yake mai, "yanzu tafiya kikeso kiyi kibarni bayan kin koreta? Harara ta maka mai zata tashi ya kuma zaunar da ita relaxed madam idan kintafi mezakiyi a gida bayan mijin ki na gadon Asibiti, "please ki kyale zancen zubaida daga yau tabar Rayuwar mu idan kuma ta dawo kiyimin duk hukuncin da zakiyimin Kece kawai nake tunani kece farin ciki na kece matar Aurena ba itsba I love you baby kinsani ba macen da zatayi min Abinda kikeyi inbita because I love you ki zauna close to me I need to see you All the time a round me, keda my little baby, now ki kiramin Ahmad a wayarki I lost my phone sai na siya wata nayi welcome back ko zaki siyamin ne Mrs Muhammad? Yafada yana Dan dukan kafadar ta cikin wasa, dole ta saki ranta ta ciro wayar tareda dialing number shi, Yana dauka yace "yadai madam Yasmin,? "Kazo yana neman ka, "waye? Yafada cikin tsokana, tako bashi Amsa tareda gimtsewa "mijina, dariya Ahmad yayi tareda kashe wayar, shikuwa wani irin sihirtaccen kallo yake binta dashi , kalmar mijina ya mugun burgeshi wani irin dadi yaji, ba bata lokaci Ahmad ya shigo dakin kai tsaye yace ya kira mai doctor please, Kallon shi tayi shine baka fadamin ba inje inkira shi, "saboda gani dan iska kije kina magana da wani katon banza ina kwance,, Shiru tayi kawai ya koma ya kwanta shikadai yasan me yakeji a hannun, ,likitan ya shigo ta gyara mayafin ta dakyau saboda oga kishi ,yace ya duba mai Hannun shi yana damun shi ko yama ciremai Abinda aka rataye shi kai tsaye,   Dubawa yayi tareda cewa "ai oga sai ankuma daurawa munfada maka karka yi sex da hannun ko ka motsa hannun da yawa aikin zai iya baci, wani mugun kallo ya watsamai kafin ya janye hannun ya fara zuba mai ruwan bala,i "kaje tunda sainayi sex ne zai lalace yanzu banyi ba ya lalace kaje idan nayi sex din na gama sai kadawo ka gyara hannun, Ahmad da Yasmin kamar su nutse a kasa saboda kunya, doctor yafara bashi hakuri ya bari ya gyara mai kar hannun shi ya samu matsala, ya cigaba da sauke mai , mutum baiyi ba ance yayi ai sai inyi gaba dayan kawai, Ganin fadan nashi na rashin dalili yayi yawa yasa Yasmin matsawa ta rage murya "please meye kakeyi haka kabari ya dubaka mana, "ok, ya koma ya kwanta likitan ya kwance tareda kiran nurse's guda biyu suka taimaka mai, su yasmin zasu fita yace ta dawo , a gadon ta zauna ya kwantar da kanshi saman laps dinta yace suyi aikin su Ahmad dai fita yayi Abinshi,   Runtse idanun shi yayi yanajin zafin yanda suke kara kwance wa rungume ta yayi gam ita kanta ta kawarda fuskar ta ganin yanda suke aikin lallai MA namiji ne haka yaji ciwo a hannun Amma yake wannan karfin halin data barshi sex din ma yi zaiyi don haka dole ma tayi nesa dashi kodan ya warke don inbata yi hakan ba kullum zai kuma bata aikin idan tana kusa, Saida suka yimai Allura kafin su tafi domin yasamu bacci kozai rage jin zafin bacci ya daukeshi ta gyaramai kwanciya kafin ta tashi tayi salla,   Bai farka ba saida safe lokacin duk Y'an Uwan sun zo likita ya ma hajiya maganar yakamata madam ta koma gida wani ya zauna dashi saboda gudun motswa jikin da yakeyi ko karyaje yayi wani Abunda zai janyo mai matsala ko aikin ya lalace akwai hadari sosai, dole hajiya ta murje tace yasmin ta huta ita zata zauna dashi don haka koda ya farko ta wuce gida Abinta dama ta shirya hakan, ya tanbayi hajiya, "ina baby ne momy na? Ta tafi gida naga batsjin dadi gwara taje ta huta a gida ni na zauna, Shiru kawai yayi ba haka rai yaso ba yakoma ya lafe,   A haka kwanaki ketafiya har saida ya kwashe sati daya Yasmin bata zuwa Asibitin saidai ta dafa Abinda tasan yanaso taba driver yakaimai ya kirata a wayar Ahmad har ya gaji taki zuwa yayi fushi ya kyaleta, saida ya cika sati biyu aka kwance hannun domin aikin yayi kyau sai Abinda ba a rasa ba, a ranar yace ya gama kwanan Asibiti gida kawai zaitafi likitan yace yabari ya kara sati kafin subashi sallama ya shafe idanun shi da toka yace in ya tashi tafiya ya hanashi inya isa, dole suka rubuta mai sallama tareda bashi umarnin zuwa check up bayan kwana biyu, haka dole hajiya ta hakura suka tafi wani irin mugun kewar yasmin din yake karaji kullum kamar ciwon da yayi jaraba aka kara mai ma yakeji gashi taki zuwa wurin shi dole shi ya bita,   Ana saukeshi hajiya tace ita basai ta shiga ba ya gaida yasmin din , tom yace ya shiga ciki cikeda dokin ganin ta, lokacin tana zaune a falon ta ta baje tana sanye da doguwar Riga mai Hannun shimi ta tufke sumarta ga cikin ta daya mata kyau das a gaban ta tana cin gyada dafaffiya don na musamman tasa mama ta dafo ta aiko mata, da sallama ya shigo tayi saurin dago kanta don batayi tsammanin ganin shi ba , baba jummai ta tashi tana mai barka tareda Mai ya jiki ya Amsa idanun shi na kanta tayi mai mugun kyau, tuni ya manta da komai ya nufeta baba ta wuce Abinta, tace la Zuma ta ansallame ka ne "? Tafada cikeda farin ciki tana kallon hannun shi mai ciwon tace Alhmdulillah Bata fuska yayi tareda zama gefen ta ya rungume ta "eh banda zuciya ai gashi ni da nadamu dake na matsa dole na biyoki ai, "oh sorry Zuma wallahi I did it for my on good gashi yanzu kawarke da ina kusa kullum sai ka bata aikin wurin jarabar ka, Zaro idanu yayi waje "lalala nine jarababben? "Eh kinci Abinci muje tun yanzu zan nuna miki kalar jarabar tawa yafada yana mai tayarda ita tsaye suka shige ciki, ranar taga jarabar kuwa domin ya murjeta sosai saida tace don Allah ya barta haka tagaji marar ta, dole ya barta badon yaso ba ya janyota zuwa jikinshi, "sorry na tara ne dama a matse nake Ina son inzo inyi juye wannan matsalar ta kunno kai don haka ki yi hakuri yau ba bacci da dare sai najini normal, Zaro ido tayi cikeda shagwaba "kai haba babynka fa ya gaji, "naki wayon ai natanbayi doctor ko akwai matsala yace babu saidai ma ya kara mai karfi come and tell me the screat naji kin kara galmi ne baby dariya yabata sosai ta tashi yabi bayanta da kallo yana jin kamar yadawo da ita ya kara baya tunanin zai gaji da zumar da yake zuka a jikinta,   ******************* Bayan sati biyu yana kwance tana gefen shi da cikinta da ya turo sosai kamar na wata bakwai, "please kabarni inje please kaga har Aunty maryam zataje, toshe kunnuwan shi yayi da filo, ta fisge tareda samai kukan shagwaba, da Sauri ya tashi ya rungume ta "meye haka baby? Ai kaine ina ta magana kaki amsani tunfa da kadawo banfita ba kullum ina kulle kana gurzata nidai kabarni inje zangon kaga Auren y'ar baban zango za ayi baidace ba idan naki zuwa, sakin ta yayi ya zuba tagumi kafin ya fara magana, "Bazan iya bari kitafi kibarni nikadai ba bafa ranar zaki dawoba, "to ai kwana hudu zamuyi kawai. "Four days????? Aa wallahi bazan yarda ba tab kwana hudu kibarmq wa ni aa, ya koma ya kife tareda juya mata baya ta cigaba da kuka, tissue ya janyo a kwali a gefen gadon ya mika mata , "idan ya kare zan dakko miki wani a store, wani takaici taji ta jefeshi da kwalin tareda Kara sautin kukan ta, yasa dariya, wayarshi tayi kara yasa hannu ya janyo tareda kallon ta " is my mother please quit kafin kijamin, Shiru tayi yana picking tasa mai ihu tareda matsowa kusa da shi, saida wayar ta fadi a hannun shi saboda ihun da tayi ta tsorata shi, "Innalillahi baby kina haukane wai? "Psycho ce ni ko mental asylum ne a kaina kana son hanani zumunci kawai Allah bazan yarda ba, "oh come on ni ban hanaki zumunciba impact ina zuwa ssuka yayi ya bude drowa ya ciro bandir na kudi kusan five hundred ya ajiye mata a kafarta kibayar akai musu inya miki kadan zankara miki baby Amma please kibar zancen tafiya wani wuri kibarni I can't, "oh ni ba mutum bace kake tafiya kabarni, tafada tana sharce hawaye, dariya yakeson yi ba hali, "nafison ganin ki cikin gidana akoda yaushe baby please kiyi hakuri Wallahi idan kika tafi nima kukan zanyi, yafada yana mata wani irin salo don dai tabar zancen tafiya, Karar wayarshi ta kuma dawo dashi don rigimar Yasmin tasa ya manta da kiran hajiya, da Sauri yayi cutting ya kirata, tana dauka tafara tanbayar shi lfy? " hajiya please ki bata hakuri wai zango takeson zuwa tayi har kwana hudu nace tayi hakuri taki, " eh lallai baba kaso kanka da yawa to kajini da kyau ka barta ta tafi ko inbata ma rai banson kwazaba da naci da ikon tsiya, "haba hajiya ya zan iya kwana hudu bata tare dani, " oh daman damun ta kakeyi da fitinar ka yarinya da cikin tana fama shiyasa tun dawowar Asibiti sau biyu kawai kazo kana like da ita a cikin gida kana zuwa check up din ma kuwa? " eh muna zuwa tare da ita kuma hajiya damata kenan fa ina gama hutu aiki zankoma banason in rasa koda second daya tare da ita please hajiyata karkiyimin haka, "Kasan Allah ka barta ko inzo indauketa tadawo nan gidana har saita haihu tukuna nadawo da ita, "tab kice zakizo kidauke mu dai hajiya yafada a hankali, "Ai najika rasa kunya bude bakinka da kyau kafada kuma karkaji da wai inji kabar y'ar nan ta tafi, bata wayar ma. Ranshi a bace ya mika mata tareda tashi ya shiga bathroom suka gama wayar da hajiya tace idan ya hana ta kirata tafada mata, tace tagode, zanturo driver yakawo miki tsaraba ki kara, ta kara yin godiya tana tsallen murna yafito rai a hade, ta bashi wayar tana mai dariya, "saiki hada mana kayan mu don idan kinbarni ba Abinda zanyi a gidan kuma k8shirya bazan taba kwana nikadai ba kuma koda yaushe muna tare don haka tare zamuje, Itadai oho tunda zataje bakomai........     "Hmmmmm to type is not easy wallahi kuyimin Afuwa ga rashin light two days don haka muci gaba da gashi my fans     *Matar Soja* [10/2, 10:24 AM] Asli Smasher : (¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯) тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   Written by FENERH   *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby 59&60 Tashi kawai tayi cikin murna ta dauki wayarta ta kira Aunty maryam, "Aunty gobe nima tare zamuje, tace " tom Allah yakai mu su mama sun wuce su tun shekaran jiya, ido ya zuba mata yana kallon yanda take ta faman ciro kaya ta sakko da akwatin ta karama guda daya ta zuba kayanta wajen Kala biyar kafin ta dakko wata katuwar akwati tafara loda kayan da takeson rabar wa idan taje can, " malama ina nawa kayan? "Wai da gaske kakeyi zakaje? " ok bari kigani, ya matso tareda bude gefen kayanshi ya fara jefa mata kisaka a jakar ko ki samin nawa daban, marai raice fuska tayi " haba Zuma please kadaina wannan wasan mana sai kace nikadai ce mai miji zamu wani je biki tare? "Eh mijin ki daban ne kuma wallahi tare zamuje Inba hakaba sai dai kowa ya zauna don ma ina gudun fushin hajiya ne da ba inda zakije min da ciki abashi wahala a banza saboda bikin wasu ni a batamin nawa hardworking din,   Batada zabi tana kallo ya hada Abinda duk yakeso kafin ya fita , baidawo ba sai dare lokacin tagama hada musu dinner ta yi wanka tana zaune a falon hannun ta rike da bowl dauke da d'an sululu yaji yaji da manja sai faman hadiya takeyi, da sallama ya shigo hannun shi dauke da manyan ledoji na wani tsadden store ya ajiye a kusa da ita tareda zuba mata ido yana kallon yanda take hadiyar yaji , " baby meye haka kikeci? Dakyar take iya magana tace " baka sanshiba, "Amma na hanaki durawa baby na yaji ko Karfa ki haifarmin yaro da kukan banza saboda cin yajin ki, bata rai tayi please Zuma wallahi inbanciba Sam banajin dadin Abincin " ok tom kirika ci kadan ok tace taci gaba da ci saida tayi kat ya mike ya karbi bowl din ya kai kitchen yazo mata da fresh milk da cup da kanshi ya zuba ya mika mata " oya kisha wannan tom tunda kingama shan yaji, kamar zatayi kuka tace " kai don Allah zanyi Amai banason ta, " eh kisha ko zakiyi Aman daga yau duk kika ci yaji sai kinsha wannan, bataso ba haka ta sha cup daya, ya zauna kusa da ita tareda shafo cikin ta da ya matsu bai ga ya kara girma ba, kwanciya tayi a jikinshi, " Zuma gobe ne fa tafiya ta, " tafiyar mu dai, yafada tareda janyo ledar ya ciro wasu set din baby masu shegen kyau da tsada ga , ta waro idanun ta waje " Zuma wasu kaya kuma? " eh naje yima na tsaraba ne nagansu sunyi mani kyau na siyo su, " meyasa kake kwaso kayan baby girl don Allah kaida zaka kawo unisex, Baruwanki kuma nasan zan samu baby na, " meyasa kake son mace? " saboda mace ta haifeni kuma mace nake Aure don haka enough of your question's , tsaraba na moto gobe zamuje dasu sannan sakonki ma na nan daga Maman ki Hajiya don yanzu duk kinture min fada kin maye kujerar, " eh ai mama na ne tun farko kasani ina sonta itama tana sona tun bansanka ba, Zama yayi kusa da ita ya shafo fuskar ta dake dauke da fara' a " keep smiling my lovely wife you look more prettier when you smile, " indai ina tareda gwarzon mijina bazan taba daina farin ciki ba mijina abin Alfahari na nafi kowace mace sa ar samun gwarzon namiji a duniya, rungume ta yayi tsam saida tayi y'ar Kara ya sassauta " karki sa infara tafiya ina yanga kinafasa min kai sosai, gaskiya ne ai, ok naji muje ciki inbaki wani darasi kadan, bata fuska tayi " banason darasi? " me kikeso tom? A kunnen shi ta rada mai a kunne, dariya yayi tareda mikewa ya sunkuceta " muje cikin angama madam your wish is my command , lafewa tayi a faffadan kirjin shi tana shakar kamshin shi mai kwantar da zuciya har gobe bataga kamshin da baya fita kanta ba kamar na gwarzon mijin ta, Sai a tsakiyar dakin su ya direta, tareda zare rigar jikin shi ya cillar ya zame wandon ma tana kallon shi saida ya cire komai nashi ya tsaya mata zigidir ta zuba Mai ido tana dariya " Zuma bakajin kunyata wai? Harara ya zabga mata " banason gulma inane baki leka ba a wannan jikin da zanji kunyar ki come on do as I do now sai kin cika Alkawarin ki ke kika samun rai, "angama habebi maida wukar anything for my Zuma, a hankali ya zare rigar jikinta yaja daga baya ya zuba akan gadon tareda zubawa kyakkyawar surar ta mai tafiya da tunanin shi ido yana wani irin cin yaji kamar yaune karon farko da yafara ganin surar jikinta nonuwan ta masu haukata shi ya zubawa idanu sunkara kunbura suna sheki gasu tsaye cur sun cika kirjinta gefe daya kuma hip's dinta da ke bajewa gwanin sha a wa Wanda daga gani cikin yafi zama a cikin su ya zubawa idanu tareda lashe baki kamar sabon maye tuni sandar sojojin taku ta tashi tafara haniniya tana wuntsil wuntsil kamar zata cire saboda kwadayin ganin kayan aikinta, Idanun shi sunkankance kamar d'an maye ya mika mata hannu " come to me my wife before I loose control please, ya fisgo maganar dakyar, ta fara takowa tana girgiza mai kirjin ta, wata uwar mika yayi tareda dafe kan jelarshi " wayyo Allah na baby zaki kasheni please come, gaba daya ya rikice ya fita hayyacin shi saida takawo gab dashi tayi saurin juyawa ta dauki towel " saikaci Abinci Kayi wanka tikun tafada tana fita da d'an gudunta zuwa kitchen, ji yayi kamar ya fisgi numfashi ya mugun sa rai don haka mikewa yayi yana hada hanya ya fita haka nan don yasan bakowa gidan yama kulle kofar shigowar baba jummai kuwa tuni ta tafi gidan ta, yana hada hanya ya shiga kitchen din lokacin ta gama shirya komai a ture zata dauka taji ya tsikara mata sandar sojojin a bayanta tareda birkito da ita cikin zafin nama, " please baby kidaina yimin kwalelen jikinki I can't take it kina rikitani, jikinshi na rawa yake fesa mata maganar a kunne tareda fisge towel din ya dora bakinshi akan nata cikin zalama kamar bai taba yin sex da itaba yakeji ya jinginata a jikin drowar kitchen din, hannayen shi duka biyu ya maida kan breast dinta yafara basu wata wawuyar mutsika kamar zai ciresu, tace "Asshh baby zafi tafada bayan ta zare bakinta, '" kibarni kawai yasmeeen " yafada yanajan sunan ai kece kika samin rai, ware kafarta yayi ya shiga tsakiyar ta tareda saita kanshi yana kokarin connecting network tayi saurin dora hannun ta saman sandar sojojin tashi tace " baby kitchen ne fa? " so what ya fada tareda cire hannun ta ya maidashi kafadar shi ya saita kanshi yafara kokarin inserting dakyar ya samu ya shiga tareda tallabeta kamar baby yafara having dinta a kitchen din, " hold me tighter baby yafada yana fitarda mugun nishi wani irin dadin ta yakeji baisan canja wurin yin sex ma nada wani sirri ba sai yau, shidai ihun shi kawai ya farayi saboda dadi daga tsayen ma ba karamar haka tashaba itada ba a tsayen takeba tayi mugun gajiya amma shi kamar doki kamar ma kara mai karfi akeyi, jin yana zunguro mata mara tafara rokon shi "Zuma please NA horu muje daki don Allah Wallahi nagaji Abincin kafa nazo dakko ma please kabarni haka bazan kuma gudu ba na tuba Ina bayako jinta saima kara narke mata yake yana kiran sunan ta cikin shauki ganin zai kawo ya damke bombom dinta da karfi ya kara tura mata ita har karshe ya saki kara mai karfi tareda hade bakinsu jikin shi na wata irin rawa rukunkumeta yayi gam tareda zamewa Kasan tiles din kitchen din da ita duk da sanyin Kasan baiji ba domin ya hada zufa sosai ta dafe marar ta don wani irin juyi takeyi, kara janyota yayi tareda cewa " sorry my honey kece ai kina haukatani kullum dadi kike karawa, bugun kirjin shi tayi cikin shagwaba " bawani kawai mugunta ne kake mun kullum sai ka gama kafaramin dadin baki, dariya yayi ya kara shigewa lallausan jikinta, muryar shi ya kara kwantar wa " sorry baby am serious kullum jinki nakeyi kamar sabuwa dadin ki kullum karuwa yakeyi wallahi baby koda ace za a sakamin wuka a wuya sai na kara Aure bazan iya rayuwa da kowace mace ba meye zatabani Wanda bakida shi Baby tun ranarda nafara taba jikinki nafara release din da bantaba yiba duk romancing Y'an mata danayi bantaba samun gamsuwar da kika sa najiba ranar kintuna ranarda nayi kissing dinki a kitchen dina na Bariki,? Ranar nasan kin kwana kina tsine ma kakanni na ko? Dariya tayi tunawa da Abinda yafaru lokacin baya ta shige kirjinshi dakyau " Kasan me? Ko a lokacin da nakoma gida Banji bacin raiba saima shaukin yanayin da muka kasance a hankali na gane cewar soyayyar ka ta shigeni tun ban taba sanyaka a idanu na ba narasa dalilin da yasa naji na tsani Rayuwar da kakeyi a lokacin a she ina kishin kayana ne, tafada tana shafo sandar da haryanzu bata gama kwanciya ba, " karki sa inkuma turmusheki a Kasan nan fa, tayi saurin zare hannun ta, yayi Dariya tareda cewa " ana tsoron bulala ta gaskiya, " eh ai bulalar takace ba laifi akwai kauri da zafi kuma, " kinga ranarda nafara ganinki da Emanuel naji wani iri duk da nasan ba soyayya kikeyi ba I felt some how fuskar ki taki barin zuciya ta a hankali tunanin ki yazamar min damuwa daga ganin farko bayan mugun kallon da kike watsa min, the day I sow you with let umar I felt like shooting him bansamu relief ba saida na kirkiro laifi na labta mai at last ma kulle shi nayi for seven days bayan na fitar dashi ne nabashi warning akan kar inkuma ganin shi tareda ke if not zan yimai sanadin aikin shi baby sai daga baya na bashi hakuri tareda fadamai reason dina nakuma rokeshi yafiya baby ina son in kula da iyalinshi sosai yanzu, ajiyar zuciya ta sauke, Allah ya gafarta mai, Ameen, baki tanbayi Emanuel ba? " baka koreshiba, ' nadawo dashi yana gidana yanzu ai bazan manta da sanadin farin ciki na ba banmanta ranarda kika fadama zuby ta fitar miki a gidan miji, " wow I felt like you are my wife for real that day, labarin su sukasha sosai a kitchen din kafin ya dauketa cikin so da kulawa suka je suka sheka wanka da kanshi ya shafeta da mai ya ce ta zauna ya kawo Abincin, wani irin sonta yakejin yana kara ratsashi, Abincin yaci sosai yana zuba santi tareda bata Abaki dakyar taci sau biyu tace ita ta koshi yabata juice fresh yourghout ya dakko yace shi zatasha ta bata fuska please kaban juice din nakeso, " doctor yace kidaina shan zaki kinga wannan yafi Amfani a jiki kisha kibari inkin haihu kaci gaba da shan zakin ki but now um um, fushi tayi tareda hayewa gadon ta lullube saboda sangarta da ssmun wuri, ya tashi ya fitarda komai ya dawo bayan ya wanke bakinshi ya dakko wani irin sweet my madara da kamshin strawberry ya jefa bakinshi, Hawa yayi tareda yaye bargon ya shiga bayan ya kashe hasken wutar dakin ya kunna bedside lamp blue, shigewa yayi jikinta tareda dora hannun shi saman kirjin ta ya tura ciki yafara matsawa, " baby ki juyo insha inji ko sunfara tara ruwa, cikin sauri ta juyo kabarni inyi bacci don Allah karfe kusan sha daya fa ga tafiya gobe da wuri, juyowar da tayi yasa yayi kasa kadan ya manne fuskar shi saman kijin yana shakar kamshin ta tareda goga fuskar shi saman su " na dauka anfasa tafiyar baby please ki tura musu sako kawai muyi zaman mu banason kiyi nisa dani, "um um nidai muje taren ai bazan yi ma nisaba " promise? " yeah, ok to kibani insha dazu bansamu nashasu ba, yazatayi da mayen mijinta da kanta ta cirosu ta manna mai a baki ya cafka kamar wani jariri harda ajiyar zuciya, tuni labari yasha bambam don saida ya kuma kafin suyi bacci,     Karfe shida ta tashi ta zuba wanka tareda shiryawa bayan ta hada musu breakfast duk da irin gajiyar da MA yatara mata jiya tana dokin shiga cikin daginta, saida ta caba adonta cikin wani fitinannen leshi maroon yaji stones yana daukar ido rigar fubu ce saboda tafi son saka dogayen riguna masu walawa saboda Sam batason cikinta yatakura saitaji numfashin ta na shirin daukewa, zama tayi gefen gadon ta shafo fuskar shi zuwa kirjinshi dake cikin jallabiyar da yayi salla bai cireba ya kwanta da ita " Zuma ta please katashi kashirya, bude idanun shi yayi ya kalleta tayi masifar kyau ga sumarta ta gyara tana lilo a gefen wuyanta kara juyowa yayi ya janyota zuwa jikinshi, " you look beautiful baby na, tank you please get up, " mezanyi miki? Shure Shure ta fara tana zungureshi, yayi wata irin mika tareda bajewa saboda irin yanda takeyi ya mugun tafiya dashi, ai tana kallon gaban rigarshi ta mike da Sauri cikeda tsoro, ya kwashe da dariya tareda sanya hannu ya shafo abarshi " ke kinga kin korar min mata ko ki kwanta haka nan, Kallon ta yayi cikin tsokana " tace bazata kwantaba saitaci Abincin ta mai dadi " nidai gaskiya katashi kawai kaga yanzu karfe bakwai nasan kafin ka gama training ka shirya sai munkai tara, su Aunty nasan NA jiran mu, kara bajewa yayi yace ki kirata kiji, wayar ta ta dauka a kan drower tayi dialing number Aunty maryam, tana dauka tace" Aunty na karfe nawa zamu tafi, ? "Ai saidai ki tanbayi mijinki yaushe zsku tafi ni yanzu haka munkusa isa garin zango Kinsan daurin Auren yaune fa karfe shabiyu baban Auwal naso ya halarta, sannan kiyimana godiya Yasmin megidanki ya mallakawa baban Auwal sabuwar mota kirar Lexus, yanzu haka muna ciki sai dai fatan Allah yakara mai budi da kuma daukaka, kallonta yakeyi yana murmushi ta zare wayar a kunnen ta ta zuba Mai ido wasu hawayen farin ciki suka biyo kumatunta, ta karasa jikinshi ta fa she da kuka tank you baby tank you, ko jiya baba yace inyi ma godiya kamusu Alkhairi mai girma shida baban zango duk da bai fadamin komeye ba nagode baby,. Manne bakinta tayi saboda rashin sanin irin godiyar da zatayi mai saida ta birkitashi soasai ta zare bakinta tareda daga jallabiyar shi yana kallon ta ya taimaka mata taciremai ta cire tata tareda zame boxer dinshi ta kalli yanda take kokarin wawurota saboda zillon da takeyi wannan jinyar da yayi kamar Ankara mata Lafiya, da kanta tafara bashi hot romance tareda hayewa ruwan cikinshi, ranar badon ta rufe bakinshi da nataba ihun da zaiyi sai masu gadi sunjiyoshi ta kaishi garin maji dadi tabashi kaya yakarba, yasamu gamsuwa fiyeda tunani saida ta bashi natsuwa ta lafe a kirjinshi yanata famar binta da kisses masu zafi najin dadi, " baby in haka ake bada tukuicin godiya gobe ma zsnkuma yin Abinda za abani irin wannan mai dadin, dariya tayi cikin dauriya ta tashi don taji jiki tasan maza NA kokari wallahi sosai saudaya kawai amma kamar bayanta zai cire lallai maza nada karfi na musamman   Wanka sukasha ta kuma maida kayanta kafin su karya ranar hakura yayi da training ya saka wata shadda kalar leshin ta tana maiko ya murza hula zanna tareda daura sabon agogon Gucci ta zuba Mai idanun ta tana bashi wani irin kallon so gaskiya ita Mai Sa a ce ya fito sosai ingarmar mijin nata inbatayi karya ba saitace ma yafita kyau, matsowa yayi ya ce " madam ciromin shoe please, tashi tayi ta ciro mai wani budadden takalmi sabo ta ajiyemai ta ciro nata baki da jakarshi tareda gyale kato zata sa yace " wait da kanshi ya bude walldrp dinta jerin hijabai ya ciro mata wani dogo mai hade da gyale har kasa ya ce kisa wannan, ba musu ta karba tasa jakun kunan su ya fita dasu waje kafin ta kwaso Mai wayoyin shi harma da jakar laptop dinshi da tasan yake yawo da ita baba jummai tasamu tana gyaran kitchen and tace " baba zamu tafi don Allah idan kin gama kibawa masu gadin key sai mundawo ta zaro dubu goma ta mika mata sai godiya takeyi saboda murna, A harabar gidan ta sameshi yana magana da sojojin, yana hangota ya karaso tareda rikota suka nufi wajen gate din, " baga motocin mu ba a wacce zamuje? "Yarana na jiran mu a waje dasu zanje, " haba dai so kake asamun ido a wurin nidai muje mukadai, " Kinsan doka ce bazasu Barni inyi doguwar tafiya ba security ba is impossible, badon taso ba haka ta hakura ya bude mata katuwar motar tashiga convoy din suka dauki hanya ta lafe a jikinshi tareda ciro wayarta ta kira Aunty maryam, tace suna zuwa yanzu, Karfe sha daya dai dai convoy dinshi suka shiga babban garin mai tarihi na zango wata, ita ta fada mai sunan Unguwar hausawan ya fadawa driver Kasan cewar sun san kangarin har layin sun sani, Dankam kofar gidan nasu na gado yake Wanda baban zango ne kawai a cikin shi sai ya'yan shi Y'an Uwa ne birjiki harda su ismail dake gefe tareda Ahmad suna hirar cikin Abokan ismail wasuma don sunga sojane suke kara wani shigemai kunsan mutanen da farin jini sanin ogan nashi na zuwa yasa yazo da kakin shi, Dosowar motocin yasa wasu mutanen mikewa da niyyar gudu don suna shiga layin wasu suka diro daga hilux domin clearing hanyar dauke da bindigogin su, mutanen garin da sukasan irin Rayuwar da ake ciki da kuma sanin cewar garin nasu akwai kabilanci yasa duk suka tsure, Su baban zango da baba suna zaune sura dattijai ana jiran lokacin daurin Aure yayi suka saki fara a don sun san su waye suka iso don Aunty maryam ta musu bayani, A dai dai kofar gidan motocin suka tsaya aka budemai ya fito, rike da lafceciyar wayarshi ta yayi ya zagayo cikin sauri ya bude mata gefen da take da kanshi. Gaba daya kallon shi akeyi wasu na ganin tsantsar kyanshi da haduwa wasu na ganin tsantasr kudi da mulki Amma ya budewa matar shi mota, ga sojojin shi sun kame kamar yaki, a hankali ta zuro fararen kafafun ta dake cikin bakin plat shoe dinta domin sun mugun rike mata saboda zaman kusan hour biyu da tayi, ya rikota a hankali ta sakko tareda rike west dinta yana mata Sannu, Baban Zango da yasha malum malum harda rawani ya taso cikin farar shaddar shi ta salla da taji guga yana sabata cikeda farin ciki da kuma murna lallai ba sai dan da ka haifa kawai kake Alfahari dashiba domin wani irin Alfahari yakeji a yau ganin kamar MG Muhammad Abdullah a gidan shi kuma surukin shi, yafara musu Sannu da zuwa, yayi saurin mikawa baban hannu tareda tsugunawa, zamewa tayi ta nufi cikin gidan ko wayarta bata dauka ba bare jaka don ta matsu tasa Y'an Uwan ta a ido, Ahmad ya karaso tareda saramai ya harareshi " Come on we are de same hare stop disgresing me, hannu ya mika mai suka nufi wurin su baba da zaka iya hango tsantsar farin cikin shi, yau yana Alfahari yana Hamdala ga ubangiji haihuwar yaya mata ta zamo mai Abin farin ciki shikan me zaiyi Inba godiya ga ubangiji ba ganin wannan Abun kawai ya isheshi farin ciki ganin y'ar cikin shi kamar sarauniya Alhmdulillah yafada a kasan zuciyar shi, Karasowa sukayi suka tsuguna suna kwasar gaisuwa mutane sai hannu suke bashi suna jin hannu mai mugun laushi , zama yayi cikin tsofaffin baban zango jikin shi na rawa ya bude shagon kofar gidan shi da ya gyara shi tsaf saboda taron yau don yasan dole zaiga manyan baki a gidan nashi ya sa an baza shinfidu na Alfarma na sabbabin daddumai Yasmin kuwa tana shiga gidan kowa yataso ya fara mata Oyoyo Y'an uwa dan kan da gida harda wa inda ta dade bata gani ba, Aunty maryam ta zake anata aiki da ita su mama kirjin biki kuwa ko kallon ta batayi ba ita ta matsa tadan rungume ta " Oyoyo momy na kowa na murnar ganina banda ke, " eh matsa min ina aiki mara kunya mijinki duk yakara bataki, dariya tayi kawai ta nufi dakin mama hindatu " ina kike mamana mai sona? Fitowa tayi cikin jin dadin muryar ta " ga yata ta iso, suka rungume juna ta dagota " mama irin wannan kyau da kiba da kikayi tun yanzu wannan ciki naki idan yakai wata Tara yake nan? Turo baki tayi " ni banyi kiba ba mama, dariya Su Aunty maryam suka sa mata " ai barta mama bata ganin kanta ne, haka sukayita raha tuni ta manta da Alkawarin su da mijin ta ta rsshe cikin Y'an uwa faten tsaki Aunty maryam ta zubo musu harda zee din ismail duk suka hadufaten irin na zage zagi yaji Rama da Albasa ta bude ciki tana zabga yaji tana warba, Shikuwa MA tuni yasa Anema musu masauki wani katon hotel a garin Ahmad Yamai booking shida ismail wa inda sun zama Abokai yanzu baba yasa an hada musu tuwon shinkafa miyar taushe lafiyayya da zabi gashin kauye suna diga ga zobon gargajiya duka aka jera musu sojojin shi ma anbasu nasu, yaci sosai ba kyama yana ci suna hira karfe sha biyu aka daura Auren baban zango ya ce shine zai wakilce su Yabada Auren Abin ya mugun burgeshi sun yi matukar bashi girman da bai taba tunanin zai samu ba don haka take ana gama wa yafara rabon kudi a wurin maroka sun rude sai zuba roko suke suna Allah ya baka shugaban sojoin Nigeria baki daya yana Amsawa saida kyar yasamu ya fita cikin mutanen da taimakon sojojin shi motar ya shiga ya zauna tareda bude Ac saboda zafi yaciro wayar shi ya kirata sai yaji wayar na ringing a cikin jaka a gefen shi, budewa yayi ya ciro tareda kallon cikin jakar yaga katuwar robar yajin ta ya ciroshi yana murmushi ya jefa cikin Aljihun motar , Ahmad ya kira yace ya bashi number Aunty Maryam, ya bashi yakirata lokacin wayar na ganin Yasmin tana daukar su hoto itada baby NANA taga number shi, dariya tayi don tasan kwanan zancen tace "hello zuma ba wani come out saboda kar inkiraki kika bar wayar a mota tom ki fito ko inshigo ciki yanzu, cutting yayi batareda ya jira Amsar taba tabi wayar da kallo tana dariya " ba inda zani zamuga karshen rashin kunya inbika ka kunya tani gaban su baba ga mutane a waje naki wayon.......   "Allah mai iko mutum sai Allah, tom nidai ina rokon ku duk wadda ta siyamin wayar nan da nake typing tazo ta kwace indaina rubuta blue novel, ko kuma mai siyamin datar da nake posting ta daina saboda inasa batsa a littafina, don Allah inbaku karantaba ya kukayi kukasan ina rubuta batsa wa nsyima dole idan gyara zakumin ku yimin zan saurareku banda lokacin duk wadda zata zageni ni ba irin sauran writers bace da zan bata lokacina ina zage zage ko Allah ya isa ko wa yaji da zunubin da yake kwasa kullum bana bukatar karin wani, masoyan Asali ina godiya sosai naji na hakura zankarasa wannan littafin domin ku ina Alfahari daku masoya a duk inda kuke kuma blue novel yanzu ma zamu fara rubutawa wadda tafasa lalacewa Allah ya........ Nop bazan karasa ba masoyi kuci gaba da gashi nidin daice taku,     *Matar Soja* [10/3, 9:49 AM] Asli Smasher : (¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯) тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   Written by FENERH   *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby 61&62 *Aha masoyan korai kunayi inajin dadi kuna bari inajin haushi, a gaskiya comment dinku jiya ya zaburar dani fiye da tunanin ku naji dole in muku typing a yau naga masoyan Asali naga masu kaunar FENERH fisabillahi ina matukar godiya agareku Allah yabar kauna*   Gyara kwanciyar ta tayi dai dai tana wasa da nana akan gadon mama hindatu tayi haka ne don gujewa hayaniyar da tayi yawa a cikin gidan saboda taro shiyasa ta shige kuryar daki, ganin kusan minti goma bata fitoba ya tura mata text akwai tsarabar ki kizo ki sa a kwashe su zamu wuce masaukin mu yanzu inason inyi wanka, budewa tayi ta karanta ta goge tareda ci gaba da Abinda takeyi, Fitowa yayi daga cikin motar cikeda tunanin mafita, da Sauri ya karasa wurin da baba suke zaune yace "baba bismillah, baba ya mike cikeda jin dadin kamar wannan babban mutum din mai matsayi yana bashi girma a baynar jama' a dole yayi farin cikin samun suruki nagari, wurin motar suka karasa ya bude boot din dake shake da kayan rabon da yazo dashi gefe daya kuma drinks ne a dayan motar dasu ruwan gora shake yasa aka fara fitar dasu ana jerawa dakin waje shaddodin baba ya kira baban zango yace yasan inda zasu ajiye wannan in angama taro a rabawa Y'an uwa, bayan hilux kuwa kayan Abinci ne shake irin su shinkafa taliya su jarkokin mai da sauran tarkace yace akaiwa Amarya gara, su baba sun rasa bakin godiya baban zango yafara share kwalla, "Allah ya kareka muhamdu Allah ya tsareka, kullum Alkhairin da kake mana baya karewa muna godiya Allah ya biya, Wata jaka ya fitar katuwa ya kalli gefen su ismail ya daga mai hannu, cikin girma mawa ya matso yace " ranka ya dade gani Allah yasa ba laifi nayi ba? Koda yake aini akayiwa kulli ta kafa rike hannun shi yayi tareda daukar jakar gefe daya sukabar su baba nata godiya, " ai harda kafafu ma nayi maka idan ta kama har dungure zan iya maka akan my Yasmin, please muje ka rakani wurin ta inaso ma in gaida su mama inyi musu Allah sanya Alkhairi, dariya ismail yayi sosai tareda cewa " yanzu zaka iya shiga ciki kuwa akwai fa mata cike Koni na kasa shiga ciki tundazu, " me I can't nakirata taki fitowa bazan iya five minutes bangantaba muje ko inshiga ni Kadai, aa muje bari inkira Ahmad mu tafi baki daya,. Ahmad ya matso tareda karbar jakar suka shiga cikin shine agaba kamar d'an gida su baba na ganin su Abin ya mugun burgesu ganin yanda ya dauki kanshi d'an gida ba girman kai, kamshin shi yafara sallama a tsakar gidan kafin suji sallamar shi , gaba daya matan ido suka zuba mishi don da yawa basu sanshiba, Aunty maryam ta matso cikin sauri suka fara gaisawa su mama sai kai da kawowa sukeyi, mama hindatu ce da tafito daki rikeda d'an bokiti a hannun ta tafara Maraba da surukaina ku iso, gaisawa yafarayi da matan kafin ayi musu jagora zuwa cikin falon mama hindatu dakin ba laifi don akwai kujeru harda kayan kallon ta gefe kuma katon deep freezer dinta ne datake sana ointa dakin duk da ana biki tsab yake domin duk yawancin mata na sauran dakunan gidan da kuma tsakar gidan, Tana kuryar dakin taji muryar shi tayi saurin zabura ta mike zaune tareda dafe kirjin ta ya shigo? Ta fada a bayyane NANA ta kalla dake baccinta ta zuro kafa ta leka ta window tana kallon yanda yake gaisawa da matan har zuwa lokacin da aka shigo dasu ciki, komawa tayi ta zauna tana fargabar Abinda zai biyo baya, shikuwa yagama baza idanun shi a cikin gidan kaf bai gantaba, bayan sungaisa dasu mama hindatu itama mama ta shigo ya musu Allah sanya Alkhairi suka fara zubamai godiya domin baban zango ya fada musu komai, mama hindatu ta kalleshi tace "ka ciri tuta ba yanda yaya baiyi da shi ya koma cikin gari yaki Amma sanadinka ya Amince muna matukar godiya, "bakomai mama Addu ar ku nake nema kawai, mama ta fita ya ce " banga yasmin din ba? " ai tana ciki, Aka kira mama hindatu a waje ta mike tareda cewa Mama ki fito ga mai gidanki duk da nasan kina jin komai, Aunty maryam ta shigo musu da kayan motsa baki irin na biki dasu drinks Zainab ma ta shigo taga Wanda ya taimaketa yarabata da kishiya, Yasmin kanta ya daure sosai jin godiyar dasu mama keyi kuma gazancen komawa gari da taji mama hindatu nayi to me hakan ke nufi? Ko shine godiyar da baba ya mata a waya, Aunty maryam ta shigo ciki tace " malama kifito MA na kiranki kafin ya shigo, hijabinta ta mayar ta mike tareda fitowa cikin sanyin jiki, tunda ta fito ya zuba mata ido kamar ya hadiyeta ba ruwanshi da idanun su ismail da kuma yaronshi Ahmad, tashi yayi kawai ya nufeta ganin takasa karasowa yana isa ba westing time ya rungumota su Zainab dake gefen mijinta ta zaro ido tareda rufe wa da hannun ta, Ahmad dariya kawai yayi don yasan zaiyi Wanda yafi wannan, Aunty maryam ta fice Abinta saboda ita suruka ce ai, hannun shi ya dora saman cikin ta " how are you my baby momy ta hanani jin duminka tundazu ko sorry ya dan duka yayi kissing cikin ta zuba mai ido kawai don tasan baiyi ko kashi goma ba a cikin kashi Dari na rashin kunyar shi, Dariya ismail yakewa Zainab dake rufe ido saboda kunyar Abinda MA keyi da mugun kishin Yasmin takeji don tasan komai akan su har maryam ma kishin ta takeji saidai yau ta yarda shirme kawai take zubawa domin taga mazajen su tasan ko maryam ta wuce da Ajin ismail bare kuma yasmin matar oga kwata kwata tana hango tsantsar soyayyar da MA yake wa yasmin tundaga yanda yake rawar jiki akanta duk ya wani makale mata kamar chewing gum, kokarin raba jikin su takeyi domin matsawa su gaisa da su Ahmad, ya kara kwakume ta a jikin shi suka zauna a kujera daya yana zura hannu ta cikin hijabin ta batareda sun ankareba ita tasan bata isa ta hanashi abinda yakeyi ba tasan ta na hanashi zaiyi Wanda yafi hakan, gaba daya ya gama takurata, gaisawa sukeyi cikeda kunya tace yaya ismail ya gida naga madam ai tundazu, Sannu yaya Ahmad, ranki ya dade ai kibari mu kwashi gaisuwa irin wannan yanga da akewa ogan mu ai dole muyi biyayya, "yazanyi ismail ai tana garani don taga bazan iya mata kishiya ba, fisge Hannun shi dake yawo tayi kan cikin ta ta watsa mai harara harda murguda baki ka auro uku who care? " I care couse nasan sai gidana yazaba filin wrestling don bazaki barsuba and the truth bazan iya hakura dake ko NA one day ba muna gida daya inje wajen wata ke Kadai nake raayin ajiyewa a gidana you are my one and only ba wata saike baby, wani irin dadi taji tareda rungume shi tana bashi kiss a baki gaba daya ta manta da mutane a dakin, dariya ismail ya kwashe da ita "sister irin wannan kishin haka? Ahmad kuwa cewa yayi " madam mudake kokarin karo muku Abokan zama kar aikin ya muku yawa, " kubarmu ya kashemu aikin zamu iya, Zainab tafada tana mikewa don itama badai kishiba, Haka suka yita hira tsakanin su kafin maryam ta shigo da Leda " ga ankon ki ki shirya muje wurin Amaren suna gidan baba liman, " kai Aunty nida nake shirin tafiya da madam masaukina, gaskiya da sake bawani inda zataje, kallon shi tayi cikin bata fuska karka mun haka please banga Amarya ba fa kuma yanzu aka fara biki kasan Al adarmu taron yau da gobe ne kabarni inshiga cikin Y'an uwa don Allah, "Ayi mana hakuri in low yau da gobe ne kawai, " to Aunty bari inje zandawo zuwa 4 kuje kuma karta wuce can banason yawo naga mazan garin nan akwai kallo, dariya yasa ya ciro bandir na kudi sababbi kusan guda uku ya mika mata gashi idan zaki raba ga sakon Hajiya nan na jiya, godiya tayi tace " please kabayar akawomin jakata da sauran kayana, Wani kallo ya jefa mata "muje ki karbo da kanki, tare suka fito sun burge duk matan dake cikin mama kanta duk kunyar da takeji yau ta ware ido ta kalli yaran nata biyu rak masu tarin Albarka tareda Kara godewa Allah, tasan ba duk mace keda sa ar da tayi a duniya ba, a waje ma kallon su akeyi har ya bude motar ya fito mata da jakar ta ta kaya kafin ta bude sit din baya ta ciro hand bag dinta tareda daukar wayarta, yana kallon ta jama a NA kallon su saida ta rufe zata juya yace wait, matsowa yayi gab da ita " please be careful karkiyi yawo kafin indawo, and naso muje tare kwadayi nakeji baby, sorry zamu koma gidan mu ai jibi hmm yace kawai yace bye, ya shige ta wuce ciki aka jashi zuwa masaukin shi, Kayan da Hajiya ta aiko mata tafara budewa taga turarukan wuta a kwalabe masu kyau da kuma manyan gorunan humra masu tsada da kamshi kowane yakai goma ta dauki waya tanajin dadi takira Hajiya, tana dauka tace " ina cewa akiramin ke sai gaki kun isa Lafiya? " momy na Lafiya lau wallahi rigimar babankin nan ya hana inkira tunjiya inkiraki inyi godiya sai yanzu ya bani kayan ma, dariya tayi ai baba na sai shi to kuma kayan Amarya ne kibata banaki bane, " kai momy Nifa? Ta fada tana shagwaba, " banson haka yasmin ki barmata inkin dawo zansa aka wo miki naki kibata duka kinji matar baba, tafada cikin lallashi tace " tom na hakura momyna nikadai, ta kashe wayar ta na jin dadi Aunty maryam da mama da suka shigo suka kalleta farin cikin dake bayyane a fuskar wannan family bata boyuwa, " Yasmin ke mai sa ace, inji Aunty maryam, samun miji irin MA uwar miji tagari haka, dariya tayi tareda matsowa ta rungume su, da kuma samun iyaye nagari da y'ar uwa irin tawa sai anyi babban searching a fadin duniya, mama tace Allah ya Albarkace ku yanda kuka zama silar farin cikin mu Allah ya baku farin ciki mai dorewa yabaku makoma ta gari. Amen sukace sunajin dadin Addu ar uwa mai matukar tasiri A Rayuwar ya'ya Mama hindatu taji dadin turarukan Tanata godiya, harda cewa tayi a hadata da hajiyar suyi godiya, Wanka suka kumayi dakin maman su dake cikin gidan da suke sauka a lokacin kuruciya idan sunzo suka shirya NANA na wurin mama hindatu Auwal na wurin su baba a waje, suka caba ado kana ganin su kasan YA'YAN GATA ne su ata ko ina takalma iri daya suka saka da jakarsu y'ar dai dai Atanfar ta mugun karbarsu ga dinkin yayi matukar kyau yasmin ma saboda kibar cikin da tayi kayan dakyar ya shigeta fadin kyan da tayi bata bakine maryam ma Masha Allah bazakace ta haifi yara biyu ba, sudai sunga ribar AUREN SOJA don suna cikin farin ciki,suka fito da gyale iri daya kamar Y'an biyu kowa na Masha Allah, mama hindatu tace " to ke nan zakibar sarkin rigimar nan? Ina kunun ta da madara? " ba dadewa zamuyi ba ai suna uwar dakan ki, tom cikin kudin da MA ya bata taba Aunty maryam daya mama daya tace su raba da mama hindatu , suka fita zuwa gidan baba liman da yake ba nisa da gidan, jama a sai kallon su sukeyi duk inda suka ratsa, wani irin farin ciki yasmin takeji tareda godiya da Allah da yasa suka Kasan ce cikin inuwar Aure ita da MA basu yi HARAMTACCIYAR SOYAYYA ba a waje da yanzu bata cikin wannan kwanciyar hankalin da wannan cikin da kowa ke jiran fitowar shi take iya fita ba kunya da a Bariki ta sameshi da saidai ta zama mujiya cikin dangi, Amarya tayi farin cikin ganin ta tareda rungume su duka tana cewa " ai na dauka bazakizoba, don naga Aunty maryam ita tunda safe kafin infito gida, yasmin tace ni na isa inki zuwa Aurenki, nasani ko zai hanaki makale matan mijinki ai bazan mantashiba ranar da yasa mu barin daki wai zakuyi magana ga ranar daurin Auren ku ma da ya kwakume ki a gaban mu, dariya sukasa tace " ku koyi irin namu mu ba ruwan mu ko gaban su baba yi mukeyi, Sai dariya ake musu a cikin Y'an matan suma suka shige ana yi dasu Kasan cewa da yawa Al Adar bahaushe Amarya bata cika zama gidan iyayen ta ranar Aure ba, Gaba daya ta manta da wani MA ta shige cikin Y'an Uwa ana ta hidima yadawo yanata kiran wayar ta kusan yakira kusan sau goma bata daga ba wayar na jaka, saida sukayi sallar la asar ta bude jakar taga miss call rututu harda Ahmad ta zaro ido tareda calling dinshi back ya yi saurin daga kiran tareda cewa haba madam ina kuke oga duk ya rikitani wurin nemanki, Gamu nan zuwa yanzu, ta yima Aunty maryam magana suka tashi Amaren ma sungama shirin komawa cikin gida domin shirin kai Amarya, tindaga nesa ta hango yanda yake daukar ido cikin white men material mai tsada yayi matukar kyau kanshi ba hula , duk taron matan da suka jero tashi kawai yake gani, tayi mugun kyau saidai ganin ta da gyale yasa yaji ranshi ya kuma baci tun kafin su iso ya daure fuska ya shiga mota, maryam tace " kije lallashi ni dai nashige ciki, Motar ta isa ta bude ta shiga ta rufe tareda matsawa jikin shi wayarshi yake dannawa batareda ya kalleta ba, tace " sorry Zuma, kallon ta yayi da idanun shi da sukayi ja saboda kishi da takaici, " Sorry for not picking my call or for wearing this net ya fada yana taba gyalenta, " gyalen fa nada kauri zuma, Amma nafada miki fa banaso yafada yana dagota yana kallon ta kalli nan dinki ya bayyana sosai gashi kinyi ado sosai kafin inganki wasu banzaye sunganki baby inada kishi mai zafi akanki don't you know that? Shiyasa nakasa barinki taho ke Kadai and tundazu nadawo ina jiranki nakira kinki dagawa saboda ina damun ki KO? " baby ina sonki sosai Kinsan soyayyar ki a jini na take bana ganin kowa sai ke, I felt incomplete without you Around me. Hade bakin su tayi ya runtse idanun shi yana Amsar salon kissing dinta mai rikitashi, na tsawon lokaci don tasan ba a ganin su motar mai duhu ce ta zare bakinta yana jan numfashi kamar an kwacewa yaro nono a baki, idanun shi ya juye ya kalleta, tareda riko hannun ta ya dora akan sandar sojan shi, taji irin kunburin da tayi jarabar ta motsa, tadan matsa kadan " sorry my zuma har muje gida bari in lallashe ta, wani Abu ya danna a jikin motar kamar intercom yake yana nuna danja ta waje driver ya shiga motar ya tayar, yace " I can't baby muje kawai kibani hakki na gaskiya, karmuyi haka please Zuma, shige mata yakara yi tareda fara lalubar ta don bayajin zai iya zuba mata ido yanzu bayan ta takalo shi wallahi shidai yanada mata bazai cutuba, Shiru kawai tayi ta boni wa ya aiketa kissing dinshi ma bayan tasan halin kayanta, Suna isa ya cire hannun shi a jikinta ya fito dakyar yake bude ido ya bude mata side ta fito ya kankameta don idan yace zai tafi da kafafunshi za a ganoshi duk da Ana ganin shi ansan a hannu yake, dakin da yakama ya bude suka shiga itadai sai Shiru, tundaga kofar dakin yafara zuge zip din rigarta yana bin jikinta da kisses duk inda ya samu sai ya manna mai tuni ya gama rikicewa yafara rikitata kamar ya shekara baiyiba, tace "zuma kabini a hankali please nifa idan kana haka tsoro kake bani kuma baka min ta wasa jiya fa kwana mukayi kana Abu daya dakyar yake iya magana " leav me ai kece kikaja kuma kece kika sa na zama haka bazan iya hakura da gidan dadin nan ba baby I can pay any prize to get in, anything for this sweet thing, yafada yana dagata zuwa bed din tuni yafara ba kanshi farin ciki, saida ya kwashe hour daya kafin ya samu natsuwa ya lafe ajikinta yana zuba numfarfashin gamsuwa, wani baccin wuya ne ya kwashe yasmin ya dago tareda zubawa kyakkyawar fuskar ta ido yana fitarda murmushi mai kyau tareda manna mata kiss a lips dinta masu kyau, " anything for you my sweet wife I can give my life to save yours, ya fada yana manne naked body dinshi da nata shima baccin ne ya kwashe shi basu farka ba sai magrib ita tafara bude idanun ta Ta tuna inda suke ta zabura tareda dafe marar ta data rike gam tace Auchh, saida ya tashi da sauri ya riketa " yadai baby " marana ya rike, sorry yafada tareda kwanto da ita jikinshi ya fara shafa wa har ya saki ta tashi tareda cewa ya saki zanyi wanka muje ka mayarda ni gida kaga za aga rashin kunya ta yanzu gashi zamuje kai Amarya ma, bata fuska yayi baice komai ba ya koma ya kwanta yace jekiyi inkin fito zanyi nawa, kallon shi tayi tasan bai shirya Abin arziki ba tunda baice suyi tare ba, haka tashiga don tanajin kiran salla ta yi wanka tareda daura Alwala ta fito daure da towel tace nafito, tashi yayi ya shiga batareda ya rufe jikinshi ba tabi abs dinshi da kallo da manyan muscle dinshi da kallo tana girgiza kanta, saida ya dauki minti talatin yafito daure da guntun towel a west dinshi, Jallabiya ya ciro yasa ya ciro mata wani hijabi cikin kayanshi ya mika mata tareda kayan bacci ta waro ido don batasan lokacin da ya saka a kayanshiba kut me yake nufi da ita haka?............     "Mahassadanka fadawwnka ikon Allah Alhmdulillah Ala kulli halim godiya nake Aunty Aisha dahiru much love Allah yakarq shirya zuri' a ya kuma kara budi da Arziki, uwar dakin MA ummi zaria jinjinar bangirma hussy Ali godiya mara adadi suwaiba ina tsananin yinki Ummu sayyid and nur mom soja ina matukar godiya ki kara nema mana kariyq a daki mai tsarki Allah ya kawomin ke nija Lafiya bazan taba suya in manta da Albasa ba Ummu jidda I love you All masoyan Asali samunku a Rayuwar NAFISA Alkhairi ce much much much love [10/4, 8:02 PM] Asli Smasher : (¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯) тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   Written by FENERH   *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby 63&64 *Y'an mata Adon gari naku daban ne kanni na MARYAM HARUNA, y'ar dakina love you beb tareda ke my MEENAH inayinki irin sosai dinnan Hmmmmm FAUZIYA kema ta musamman ce a gareni Allah yabar kauna, my takwarori NAFISA &NAFISA kuna cikin zuciyar FENERH, Ummi KHADIJA nima ina sonki my friend, ina Alfahari da soyayyar ki Ummu surayya y'ar mutan Niger Allah ya karo kauna da SOYAYYA a tsakanin mu masoya*   Umarnin shi tabi sukayi salla tare yana idarwa ya mike tareda janyo wasu kuloli da baban zango yace asaka mai su a mota dazu bai budesu ba saboda yana sauri ya je yaganta, soyayyun kaji ne na Hausa jar suya da kuma rice and stew yaji namomi nasu daban mama ta girma musu bisa umarnin baban zango uban gayya, farin ciki yaji ya rufe shi yanda suke mugun bashi girma da mutun tashi yana mugun ganin girman surukan nashi Sosai, tasowa tayi cikin sauri domin yunwa takeji sosai, bajewa tayi ta cire hijabin tareda saka hannun ta ta cire daya tafara ci yana kallon ta tareda murmushi ya zubawa kirjinta dake bayyane ta cikin rigar baccin don bata saka ko bra ba saboda kirjin ta na zafi yana hango niple dinta a bayyane, Cin namanta takeyi hankali kwance yace " baby Kici a hankali karki shake fa, " Yunwa nakeji tunda mukazo naci Abinci ban kuma ciba fa, tafada tana bata fuska, wani irin kallo yayi mata " baby me yasa zaki horamin kanki da baby da yunwa idan baki ga Abinda kikesoba why don't you call me sai in nemo miki ko ta kama a koma kaduna ne a nemo idan babu a nan, dariya tayi, " yanzu zuma sai a je kd nemo min wani Abu? Matsota yayi ya sanyata a tsakiyar shi tareda dora hannun shi akan Abinda ke tsole mai ido, kafin yakarasa da hannun shi ta cikin rigar baccin nata yafara massaging yana lumshe idanun, mamaki yake bata sosai idan taga yana wani Abu ace mutum bai gajiya Sam da cakudq mace, " sorry baby kiyi hakuri da mijinki ko kinaso inkoma Rayuwar bayane? Inason wannan Yafada yana kara matsatsu, fita hanyar shi kawai tayi tacigaba da durin ta saida ta ci sosai ta gyara zama tace zuma kaima kaci tom, narke mata ya kara yi, "kibani zanci, zagewa tayi tabashi sosai yaci Abincin domin mama akwai hannu a wajen girki, saida yayi kat ya fara tanbaya, " baby waya dafa Abincin nan? " mama ce duk da bana wurin sukayi nasan test din girkin ta, " kice a wurinta kika iya girki, I thought ke kikayi don kamar girkin ki, murmushi tayi " mama na girkin ta daban ne ai, tun muna primary tafara koya mana girki, dayake ni inason girki nariga Aunty maryam iyawa, rungume ta yayi tareda bata fake a goshi, " Rayuwar gidan ku is simple Abin yana burgeni, kara shigemai tayi tace, "Familyn ku ma zuma ba bayaba kai d'an gatane sosai ga ka da yayyi masu sonka ga uwa ta gari duk da bansan baba ba Amma nasan wannan gida yasamu bango mai karfi tunfarko, ajiyar zuciya yayi " ban yi wayau sosai da baba na ba ya rasu Hajiya ta kula damu har muka kawo wannan lokacin da taimakon Y'an Uwan shi duka, Hira sukasha akan Rayuwar su, basu Ankara ba sai kusan takwas da rabi suka shiga wanka tare sukayi salla ta feshe jikinta da wani hadin humra mai kamshi ta haye gadon don ta Riga ta hakura da maganar komawa don tariga ta gano shi bazai mayar da itaba don haka murjewa zatayi tabi zabin ranshi kodan yanda yake nuna mata kauna da kuma kyautatawa Rayuwar ta tayi Alkawarin daga yau bazata kuma musa mashi ba inda akan Abinda bai sabawa ubangiji bane don A yau takara sanin girman soyayyar da yake mata , yayi mamakin lokacin da ya shigo Don har tsoron shigowa yayi kartace yazo ya maida ita saidai yasha mamakin yanda yasameta a baje, kafin ya bude baki yayi magana ta tashi tare da cewa " Zuma bacci nakeji kazo kasan kasabamin bacci a manne da jikinka please come, ta fada tana mika mai hannu, jikin shi na rawa ya cire jallabiyar ya matso tareda Ajiye mata fresh milk din da yazo dashi, Tashi tayi ta zare rigar jikinta ta cillar a kasa tareda kwanciya tana lumshe idanun ta, ta mugun bashi mamaki ba bata lokaci ya kwanta a gefen ta batareda ya tabata ba sai kallon so kawai da yake binta dashi hannun shi ta janyo ta dora saman boobs dinta, ya zaro ido tareda dagowa yace " baby Kinsan me kikeyi kuwa? " uhm am trying ta make my happiness happy, " noo am not selfish baby nasan kingaji ga kuma baby na kar injimai, kawai inaso inganki ne a kusa dani ba sex ne kawai dalilin manne miki ba I really need the whole you around me you are my breath, Yayi maganar kamar wani karamin yaron dake bukatar lallashin uwarshi, tashi tayi ta turashi ta haye ruwan cikinshi, " baka isa ba malam saifa Kabani hakkina ka dakko ni ka biyawa kanka lokacinda kakeso nima yanzu kwadayi nakeji ka sosamin ko in sosawa kaina, kallon ta yakeyi yanda ta ci serious kamar ba ita ke korafin yana damunta ba kullum, ita kuwa tayi hakan ne kawai don farantamai ta hanyar da tasan ita kadaice damar da takeda ita wajen faranta mai, ganin yana kallon ta ta duka tareda doramai dukiyar rugar a bakinshi tareda danne mai hannci gaba daya dasu tuni yaji numfashin shi yafara canjawa tuni ya harba jirgi sama ya cafke don yana bukata kuma bazai taba gajiya da itaba har abada kawai daga kafa yakeyi don kar ya cutar da ita, Ta mugun bashi wuta ranar Wanda sai ga mazajen na fitarda kwalla a karon farko harda shashsheka yana kamkameta tsab a jikinshi, tank you baby you make my night seriously, duk da karfin hali tayi saida ta tsokaneshi dangwalo hawayen tayi tace " mazaje sunyi kuka a hannun baby yau, " eh ko gobe kika kuma min irin wannan bulalar sai nayi Wanda yafi wannan ma, " Aikuwa I will try harder just to see this precious tears masu tsada, fadin farin cikin da ya kwana ciki ranar bata lokaci ne he have the best moment bazai taba manta zuwan su zango ba a tarihin su, Ta shige jikin mijinta suka shaki baccin su, A gidan kuwa ba Wanda ya nemeta don Ansan tana tareda mijinta mama ce ta tanbayi maryam " ina y'ar uwar ki? Lokacin ana shirin kai Amarya, tace suna tareda mijinta bata kuma cewa komai ba, har aka dangana Amarya da gidanta suka dawo don babane yayi jagorar kai Amarya a motarshi yace duk Wanda yaga daki ya koma gida bamai kwana tunda sungama shirya mata dakinta, Iyaye kudaina Al adar kai Amarya kuce wai sai Ankwana an bude kai za a watse wace irin Al adace wannan mazajen da basuda hakuri yanzu suna rawar kafa su shige daga ciki, nafarko ga dorawa miji nauyi idan baida karfi na biyu tsoffi na can na bacci ya kira Amaryar shi susha Amarcin su aikin banza wannan ai muguwar Al adace , ni munkai Amarya muna Y'an mata mijin yakirani gefe muka sirrinta tuni na rako mai ita sai fa safe ta rika tsinema zuri'a mu kab ta kwashe musu Albarka don haka ku daina wani takura kanku wallahi saboda kwadayin shayin gidan Amarya ko banzanr A Ada,     Cikin farin ciki suka tashi tana yin wanka ta janyo kayanta najiya zata mayar ya ce ta tsaya, wata doguwar rigar Abaya mai tsada mai fadi ya bata light green ta hadu sosai irin ta haddadun matan nan ce gyalenta nada fadi sosai don haka tasaka tana dariyar halin shi wato ya shiryama kwanan su kenan, shima cikin material na maza kalar kayanta ya saka fited bai sa hulaba ya dauki mata jaka tareda rikota suka fito, lokacin karfe goman safe mutane sunfiffito a harabar hotel din ko ina suka ratsa idanun jama a kansu, what a perfect couple sunyi mugun match motocin shi na jere ya bude mata tashiga ya shiga shima suka kama hanya ya janyo laptop dinshi ya bude ta zuba mai ido yanda yake aiki cikin aji da natsuwa ya wani kame kamar bashi ya gama mata kuka ba, jin take soyayyar shi na kara narkar mata da zuciya, dole ta zage ta kara rike kayanta kar a kwace mata shi, don ko wace mace dole tasoshi ga kyau ga kudi ga mulki ga kuma iya tarayrayar mace dole mata su like mai, Su baba na kofar gida da fadawan su domin angano su din sun cancanci hakan don sun wuce da tunanin Y'an Zango irin wannan suruki da sukeda shi sai abin kari suke ci, motocin shi suka tsaya saida ya karasa aikin shi ya rufe tareda ajiyewa ya fita ya zagaya ya bude mata motar don yanzu tariga tagama sabawa da halin shi tasan duk in sun fita tare shike bude mata mota bayan anvude mai, bayason ana bude mata, fitowa tayi ya dakko mata Jakarta suka jera saida ta gaida su baba kafin ya mika mata Jakarta ta wuce ciki sunata sa Albarka baba bakinshi har kunne ganin yanda Autar tashi ta zama kamar sarauniya, zamanshi yayi cikinsu kafin su ismail da Ahmad ma suka iso don su tare suka kwana a dakin ismail dake gidan, baban zango yace ismaila kuje ku karya naku na shago Abin karin tashi kuje muhamdu, to yace suka wuce ismail yafara cewa "Allah yasa ka iya shan koko ranka ya dade? Dariya Ahmad yayi " ai oga yafison gargajiya ko kasan garin yin miyar kuka kanwata ta siye zuciyar oga, dariyar shakiyanci suke mai sosai yace " ai sai na bude restaurant na kuka soup da tuwo da sunan Yasmin saboda history, dariya suketa mai ismail yagama fahimtar cewa wato karamin mutum shine yafi kowa girman kai a Rayuwa ba Wanda ya gaji Arzikiba,   Ita kuwa tana shiga aka fara yimata tsiya abokan wasa " idon ki ke nan manya? "Eh ko idon ya canja ne? Ta fada cikin mayar musu da Amsa don bata jin kunyar komai yanzu yanda mijinta ya dorata kan darasin itama yanzu batasan kunya ba Sam, matsawa tayi ta gaida su mama dake yanka alayyahon wainar da zasuyi yau, " mama hindatu tace " yata kin iso? " eh mama na nakaina ina Abin karya war mu Kubani na Muhammad inkaimai bai karyaba, Ajiye wuka mama tayi ta kalleta " barnan mara kunyar wofi Aike zaki fada mana Abinda ya dace ko, dariya Aunty maryam tayi ganin dramar da suke tace " ke mai miji ankai musu nasu zo ki karya kema, tashi tayi tana dariya mama hindatu tace " banga laifinki ba wallahi mazan zamanin nan kama Abinki y'ar nan kinji, " nagode mama na tafada suka shige falon ta, maryam tace " kin boni kema kin zama kalar mijinki Koda yake ai sai hali yazo daya ma ake haduwa dama kema ba kunyar ce dake ba kalli kinbi miji kunkwana hotel Amma kinshigo ko a jikin ki mirsisi, "toh yace muje sai inki kuma tunda kowa yasan inda naje meye na kunbiya kunbiya bayan gama cikin shi a marata, dungure mata kai tayi ta fita " Allah ya shirye ki wallahi, Ameen tafada tareda bajewa tafara karin ta,   Karfe goma sha daya suka shirya domin zuwa gidan Amarya a lokacin gidan ya kuma taruwa domin taron ranar don yanayin tasu Al adar, Kiranshi tayi tafadamai kafin su fito don gudun rigima lokacin yana dakin ismail yana aiki da laptop dinshi, ta canja cikin wani leshi riga da sket baki mai shegen kyau da tsada ta sako hijabi gudun rigima tayi kyau itada Aunty maryam da wasu mata guda biyu Ya fito tareda tsayawa yana jiranta, tana karasowa ya matso yana zuba mata ido duk shigar da tayi saita fita daban a cikin mata, matan suka gaisheshi tareda wucewa kadan su basu wuri ganin ya tsare gida, tace "ina ya Ahmad yaban key din motar shi muje da ita da d'an nisa kadan, " ok ko inkaiku ne? "Aa ka barshi yanzu zamu dawo eh kifa shirya gobe zamu koma tunda angama taron, " ok tace duk da ba haka tasoba taso ta zaga dangi, Key motar Ahmad ta karba ita ta jasu da kanta yana kallon ta har tabar wurin wani irin jin dadi yakeyi idan ya kalleta komai tayi burgeshi takeyi, yakoma yana maijin shaukin ta, su baba ma duk akan idon su suka fito har lokacin da sukabar kofar gidan Aunty maryam na gefen ta matan na baya,.     Sai yamma suka dawo lokacin gidan duk an watse sai su mama da sauran yaran gida da Zainab, ranar sunyi kwanan hira domin dolen shi hakura yayi ya kyaleta saidai Yabada umarnin akwasomai kayanshi a hotel shima zai kwana cikin su Ahmad, duk da basu kwana daki daya ba sunkwana waya abinsu, Su Ahmad sai toshe kunnen su sukayi har sukayi bacci idon shi biyu, haka itama maryam tayi bacci tabarta, yace is better su kwana suna waya da ya kwanta shikadai bazaiyi bacci mai dadi ba, Haka suka raba dare kafin yabarta ta kwanta ya janyo laptop yaci gaba da aiki har Asuba su Ahmad suka ganshi a inda suka barshi, " oga Kayi bacci kuwa? " Nop ba baby ai ba bacci, Ismail yace " tom kaji manya masu SOYAYYA lallai kanwata na wuta, harda gobara ma yi takeyi indai my yasmin ce, Ajiye laptop dinshi yayi suka fita domin zuwa masallaci, Saida yadawo masallaci ya kwanta bacci baitashiba sai karfe goma, yasmin ce ta shigo dakin cikin Adonta ta haye katuwar katifar tareda shige wa jikin shi, "Wake up my sleeping beauty, tana manna mai kiss a baki, a hankali ya bude idanun shi akanta kafin ya karasa waresu ganin ta Bako mayafi, yabata fuska haka kika fito? Hijabinta ta nuna mai, gashi can nacirene kaga kwalliya ta kawai, tashi yayi zaune tareda tallabota kan kafafun shi, " kinyi kyau sosai my beautiful wife, " tank you my lovely and handsome man, dadin maganarta yaji yace baby " Kinsan nifa yanzu haka ina bukata, ya za ayi? In rufe kofar ne? Ta fada kai tsaye " um um kishirya mutafi gidan mu yanzu, " angama mijin Aljannah am ready to go, Ya ji takara girma a idanun shi yanda take mai biyayya ba musu yaji dadi sosai tareda dirowa bathroom din ismail tashiga ta hada Mai ruwan wanka tarakashi yayi tana tayashi har suka fito ta ga jakarshi ta bude tareda ciromai wani kayan shadda ce blue sabuwa dal itama ta war ware mai tabashi yasa ta tareda feshe shi da turare suka fito yanajin kanshi kamar yafi kowa sa ar mata, cikin gida ta shiga ta kwaso kayan ta tareda yi musu sallama, Aunty maryam ta kalleta " waike da gaske tafiya zakiyi? " wait and watch sai kun zo, " haka mukayi dake bayan gobe zamu zaga dangi, mama hindatu ta fito mata da bokitan kayan garar da akayi su dibulan alkaki dasu cin cin tabayar akai musu mota tanata shi Albarka tareda cewa sai munshigo yasmin nice mai wankan jego insha Allahu, waje ma su baba nata godiya haka ta shiga motar suka wuce, suna kama hanyar ta baje a jikin shisai bacci bata farka ba saida suka isa kd ya tasheta, ganin sun nufi hanyar Unguwar dosa yasa tace, " me zamuyi a nan? Banza ya mata, tundaga nesa ta fara zaro ido ganin gidan su ya canja baki daya takasa cewa komai saida suka faka ya bude mata tafito tana bin gidan da kallo an hadeshi da dayan incompleted building din dake gefen gidansu harda katon gareji anata aikin kawata gidan da fenti mai kyau, ta kalleshi baki bude, yaushe aka fara wannan aikin? Kafada ya daga mata Alamar oho suka shiga cikin gidan da yazama two side plat biyu right and left sai tsakar gidan da zasu iya haduwa a tsakiyar in sunso maidan girma tsarin gidan yayi masifar yin kyau, wasu irin hawaye ne sukafara fito mata ta kalleshi wato shine godiyar da ake mai tun tuni shine yasa su mama hindatu sukace zasu dawo kd, rungume shi tayi tana kuka, " mezanyi infaranta maka my zuma for making me happy All the time? " Kici gaba da sona da bani kulawa that's All I demand baby, yafada yana lashe tears dinta da halshen shi, "Zuma ka gama min komai I can re pay you no matter what, "baby meye don nayiwa mahaifana hidima don't you agree they are my family to? Ko ke Kadai keda su? "Aa nakane kaima tank you, "no stop thanking me am doing my duty as good son ne baby mezanyi da kudin in na Ajiye inban wadata family naba hajiyata ba Abinda zatayi da kudi yaranta mata sunyi mata hidima tunban tasoba dangin mu kuma kin sansu na fada miki yanzu haka my Auncle kudi yake bani he don't care Abu daya yarage min in wadata matata itama kafin yarana su zo badon na raina Arzikin ku ba, meye Arziki ko hadin kansu baba kawai babban Arziki ne I like them Wallahi so much like my family, Saida ya zaga kowane part da ita taga iri daya ba banbanci kafin su tafi gida, itakuwa me yarage mata a duniya? Babu sai fatan dacewa gobe kiyama kawai ********************* Haka Rayuwar take ta tafiya yau fari gobe tsumma har cikin yasmin yakai wata tara, yayi mugun girma gaba daya ta kunbura tawani irin budewa sometimes inta zauna sai antaimaka mata ta tashi hajiya ta karo musu mai aiki wata tsohuwa domin komai bata iyayi gashi ya koma aiki kullum saidai kiran waya ba adadi kafin yadawo daga office, tunda cikin ta ya girma hankalin shi ya tashi don ko matsa mata bayayi yanzu saboda condition dinta yauma suna baje baba jummai sai matsa mata kunburarrun kafafunta takeyi tana mata Sannu, " baba ki huta kibarni haka ai nariga nasaba yanzu ' "aa y'ar nan wannan kunburi naki ai ba na Lafiya bane idan kika kasa mikewa fa gwara dai inyi miki yanda kafar zata sake, nagode tafada domin tanajin dadin yanda take matan, sallamar hajiya yasa ta tashi cikin murna hade da shagwaba " Oyoyo momy NA, dakyar take daga kafa, " Fatima na shigesu yarnan wane irin hawa kikayi haka ni jikar mutum hudu, kukan shagwaba tasa mata " wallahi ni ma tsoro nakeji ko jiya munje Asibiti likita yace is normal, tom Allah dai yaraba Lafiya, ina baba na yake? " baidawoba sai karfe biyu, ok ina jiran shi ai mara kunya nace yakawon ke yaki har ki haihu tunda yace bazaki gida wanka ba, Shiru kawai tayi itama Tanason tafiya gida tunda yanzu su mama hindatu duk suna nan zata samu kulawa sosai Amma yaki shiyasa bata ce komai ba don tasan halin kayanta bazai yarda ba, Kinga tunda nafara maganar ya guji gidana to ina jiranshi mara kunyar da yayarku nace ta mai magana sai ce mata yayi shi ba inda za ace mai da mata wani wankan jego, to nazo da kaina, dariya tayi ta makale mata a jiki tareda cewa momy na me za akawo miki? " aa akoshe nake ina jummai ta kawon zobo inkunyi irin Wanda kike aikamin din nan " ai kuwa akwai baba jummai, ta kirata suka kara gaisawa, don Allah kikawo ma momy na zobon nan, to uwar gida, ta juya ta kawo mata, shikuwa a office sauri sauri yake yaje ya ganta don Sam bai cikin natsuwa, Saidai yana isowa yaci karo da drivern hajiya ya bata rai "kaida waye kukazo? " hajiya ce na kawo, ya shiga gidan fuska tamke, dakyar yake gaisheta, " oho inkaso ma karka gaisheni mara kunyar banza kawai ba Abinda zai hanani tafiya da ita kai ko tausayinta bakaji yarinya tayi irin wannan nauyin Amma jarabarka bazata kareba, " nifa hajiya ba wani jaraba da nake binta da ita ki tanbayeta munfi sati biyu ban.... Yi mun shirru shiryayyen banza, yayi dariya kasan ciki itama tana yi musu yace wallahi ba inda matata zataje nama dauki hutu don in kula da ita saita haihu, don haka muna nan tare, ya wuce Abinshi bakinsu sake wato akan yasmin rashin kunyar shi a bayyane take, Yana shigewa tace " ikon Allah Fatima kiramin hindatu a waya inji, mama hindatu takira mata tana dauka ta mika mata Gata momy, "Assalamu Alaikum, Amsawa tayi tagane muryar hajiyar don yanzu mugun zumunci sukeyi a tsakanin su don har gidan suke zuwa, "Hajiya Amina kece? " eh hindatu nace wai bazakuzo ku murje ku dauki y'ar kuba harta haihu gaban wannan mara kunyar, yarinya duk ta kunbura haka, tunda ku surukaine ya barku ai, dariya mama hindatu tayi tace " aa hajiya Amina barsu kawai inta haihu ni zanzo inzauna da ita tunda bai ra ayin hakan kubarmai matar shi " oh kice kema kina goyan bayanshi bani Saude, mika mata wayar tayi dama tanajin su tana musu dariya, , "barka da rana hajiya Amina, " barka dai Saude ke ma kina bayan dan naku ne ? Aa ni ba ruwana maganar kuce iyayen yara keda hindatu nawa ido, " to magana daku batada rana sai Anjima ta katse tareda tashi, Yasmin ni natafi gidana tunda suma su hinden duk bakinsu daya,..............   Please masu neman littafin nan su nemi wannan number please ko masu nema daga farko wallahi I can't send it to ta private da kuke bina Inada uzurori da yawa please, 0706 096 4645     *Matar Soja* [10/6, 9:43 AM] Asli Smasher : (¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯) тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   Written by FENERH   *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby 65&66 *Masha Allah, maman sadiq ina godiya a gaskiya comment dinki yasani farinciki sosai har narasa da bakin da zangode miki tareda ke Habiba lawan ina godiya masoya domin kuwa kuna fahimtar sakonnin cikin wannan labarin nawa da nake kokarin aikawa Allah yabar kauna nagode*   Hajiya natafiya ta shiga dakin tana daga kafa dakyar yana ganin ta yayi saurin tasowa ya riketa yana mata Sannu, saida ya zaunar da ita a kasa domin batason zama a sama Sam yanzu shima ya zauna a gefen ta, "Ina hajiya? " ta tafi, " meyasa baka tsaya kunyi magana ka shigo kabar ta, please ka shirya kaje ka bata hakuri Am not happy the way you behave, Gyara zama yayi ya riko ta, "kema kina bayan su ne baby? " Nop zuma soyayyar ka gareta yasa take sona nima take kula dani duk Abinda takeyi is for your on happiness ne, wallahi kowa murna yake tayani da samun uwa tagari kamar hajiya, don ni a matsayin uwa nake ganin ta ba uwar miji ba zan iya fada mata Abinda bazan iya fadawa su mama ba itama a matsayin ya ta dauke ni ba suruka ba, how many women ke fuskantar matsalar uwar miji a duniya? Am such a lucky girl best husband good mother in low and the best family, " please am begging just once do as she demand da nan da gidanta duk daya allow me to go please hubby,   Wani irin farin ciki yaji har kasan zuciyar shi ya shafo fuskar ta, yakara ganin darajar ta a idonshi yanda take respecting mahaifiyar shi, yasan zataso zuwa gidan iyayenta ta haihu Amma ta zabi gidan hajiyar shi just saboda ta faranta mata, " wow my wife I love you more and more, because of you baby I can do anything Koda banaso, don haka kishirya muje inkaiki gidanku gobe, " Nop gidan hajiya zanje nidai, tafada cikeda shagwaba "ok naji tunda hakan kikeso, Kokarin tashi tafarayi kafafunta suka rike gam, yayi saurin mayarda ita " Ina zakije? " zankawo maka Abincin ka ne, hade fuska yayi " what is that? Bana fada miki kidaina wahalar da kanki ba yanzu idan inaso nasan inda zanje indakko ba, " sorry zuma nariga nasaba yana min wani iri innaga kana komai da kanka, pray for me inhaihu Lafiya inci gaba da kulawa dakai , " baby Koda yaushe Addu ata akanki ne, Allah ya saukeki Lafiya ya fito min da baby na lafiya, Ameen Zuma tafada tana shafo kyakkyawar fuskar shi, cikinta ya dafa da yayi mugun bajewa ta KO ina a jikinta ga kirjinta ma sun kara cika hips dinta ya kara budewa, ya mike tareda dagata, muje ki motsa jiki yanda doctor yace, da taimakon shi ta tashi ya riketa suka fita harabar gidan dai dai motar hajiya nafakawa, " momy na ta dawo zuma ta saki hannun shi ta nufi motar dakyar, Fitowa hajiya tayi tareda riketa " ina zakije Fatima kina fama haka? " nan bayan lambu zamuje mudan zagaya likita yace inrika dan zagayawa lokaci lokaci, " to nadawo sai kinhaihu in koma Fatima nakasa natsuwa dana koma hankali na yaki kwanciya nabar yaran a gidan da masu aiki kodan hankali na ya kwanta in ina ganin ki, Wasu irin hawaye ne suka cika mata ido ta rungume ta tareda cewa " ina sonki momy na da baki dawo ba ma gobe zandawo gidanki ya y'ar da, " kedai barni dashi dani yake zancen Ai mara kunya, sosa keya yayi tareda matsowa yace " sorry momy na Kinsan tunda kika tafi y'ar ki ta titsiye ni dole inkaita wurinki dole na hakura tunda kinzo ma shikenan, ko tankashi batayi ba tayi cikin gidan shi ya kwaso kayan ta datazo dasu suka koma ciki yasmin ta kara ganin kimar hajiya sosai a idanun ta, Yanzu wata sai tace uwar miji tazo gidanta me tazoyi sa ido saboda andauki uwar miji enemy wallahi mata a gyara da bata haifaba ina zaki ganshi ki Aura ai duk Abinda tayi bata cancanci rashin kunya ba da wulakanci, Daki na musamman ta ware mata tareda kayanta tasa aka zuba mata duk Abinda take bukata sanin hajiya bata zama gidanta ba fura tasa ya cika mata firij da fura da kuma galuluwan nono, macece y'ar hutu mai sanin ya kamata tana zuwa ta hada mata wasu sake sakin daman Akwai wa inda ta fara bata tunfarko saboda zaki, tayi mugun jin dadin yanda hajiya tayi mata don MA yafada mata ko SALMA dake karama a cikin yaranta mata bata je gidanta ta zauna ba sai Yasmin y'ar gatan kowa,   MA ma yau cike yake da farin ciki don tunda yake Bariki yayita kokarin taje tun yana shi daya taki zuwa Amma saboda yasmin yau har zama zatayi a gidanshi, kallon yasmin yakeyi a hankali ya furta " NURUL HAYAT wato ta zamar mai haske a Rayuwa samun ta a Rayuwar shi haske ne ta rabashi da sabo mafi girma ta zamo uwar gidan shi kuma uwar yayanshi very soon insha Allah, hirar ta takeyi hankali kwance ya mike ya koma dakinsu ya kwanta tareda sa hannun shi kasan kanshi yana kallon saman pop din dakin nasu, wayar shi ya janyo ya bude fuskar yana kallon hoton dake kan fuskar wayar nata da ya dauketa lokacin da suka taba zuwa Abuja tun bata tare ba, tayi kyau sosai jin yake shaukin sonta nakara kowane nama na jikin shi, yarasa wace irin soyayya yake mata da kullum karuwa take karawa bata raguwa shiyasa yaji bazai iya bari tayimai nisa ba ko gidan hajiya data nace zataje ya yarda ne don gudun fushin ta kawai amma kafarshi kafarta ai yanada part a gidan don ko gidansu mama taje yanajin kullum can zai wuni, Wani irin bugawa yakejin kirjinshi nayi saboda soyayyar ta runtse idanun shi gam yana dafe kirjin shi, ya dauki lokaci a haka, jin ana shafa fuskar shi a hankali cikin wani irin salo tuni tsigar jikinshi ta mike ya bude idanun shi ahankali wa inda ke cikeda shauki, hannun shi ya dora saman nata, " tunanin me kakeyi my zuma? " tunanin numfashin Muhammad nakeyi, yafada kai tsaye, " ina yake numfashin? " kece numfashi na baby I can do without you, I love you more and more every second, Allah ya kawomin baby na lafiya, wani irin sanyi takeji a jikin ta saboda dadin kalamanshi ta gyara zama dakyau ta mike kafa ta dago kanshi tareda jingina da gadon ta dora kan labs dinta, gyarawa yayi ta dora hannun ta saman sumar kirjinshi da yariga yacire riga tun shigowar shi tuni yafara mika tareda rike hannun ta, " please baby karki taboni kinga kina fama da kanki, tausayi ya bata yanda yayi maganar don ya mugun daga mata kafa kusan sati biyu saidai sometimes tana ganin yana shan drugs ko yayi ta juyi da dare, Dukawa kadan tayi duk da cikin yatokareta ta manne bakinta da nashi tareda murza niple dinshi a hankali dayan hannunta ta tura ta cikin boxer dinshi tuni ya fara loosing control yafara fitarda nishi sama sama kamar mai Asthma ya mugun rikicewa mantawa yayi da condition dinta ya kwantar da ita, tuni tafara data sanin Abinda tayi ita tasone ta dan mishi oral play ya rage zafi gashi gabadaya yafita hayyacin shi don bayaji baya gani haka yake sarrafata cikin zafi zafi ga bukata ga zafin soyayyar ta da yake ji don haka yanzu da ya samu dama tuni yafara fayyace mata hanya mafi dadi, Kuka tafara saki a hankali don jin take kamar yana kokarin tura mata wani Abu a marar ta Sam batajin wani dadi sai wuya dukan bayanshi takeyi duk da bai danneta ba, " zuma please kadaina zan mutu zafi marata ciki na babynka, ina bayaji yayi nisa saida ya samu natsuwa ya zabura yana salati " innalillahi baby ganin yanda take fitarda numfarfashi sama sama tana dafe ciki, da kanshi ya ciccibeta zuwa bathroom domin tsarkaketa ganin yanda duk ta fita hayyacinta, wani ruwa hade da d'an jini yagani kadan yana bin kafafunta ido ya zaro cikin tsoro " oh my god baby blood ! Yafada cikin tsoro bata iya magana saboda ciwon da marar take mata cikin sauri ya wanke mata jiki shima ya watsa ya dakko ta cikin gaggawa yake komai ita kuwa sai cije baki take saboda Azaba doguwar rigar fubu kawai ya sura mata tareda hijabi ya dagata ganin ta kasa tafiya haka ya kuma cirata cak suka fito shima Jallabiya kawai yasa da boxer ya dauki key din motar ta yana Fitowa falon hajiya yasamu zaune suna hira da tsoffin gidan masu aiki, saurin tasowa tayi " lafiya baba? Yakasa bata Amsa tabisu cikin sauri "ikon Allah bata dade da shiga cikiba lafiya lau me yasameta ko Abun ne yazo? Shidai a matukar rude yake , a baya ya zaunar da ita hajiya ma tashiga dama hijabin ta na jikinta yaja a sukwane, wani private hospital dake Unguwar rimi mai kyau ya kaita dama a nan take awo cikin sauri ya faka ya kuma daukarta ya shiga da ita, cikin gaggawa suka karbeta suka fara bata kulawa hajiya duk hankalin ta ya tashi, likita yafito yana musu magana " ranka ya dade lebour ne Amma da sauran lokaci yanzu tafara inaga tayi Abinda ya tsokano nakudar ne , hajiya tayi carab, "ai bata aikin komai batayi komai ba, " ai ba sai aiki ba ko kila me gida ne ya jangwalo nakudar don ruwa ma nata zubowa a jikin ta kadan kadan da Alama ruwan nakudar ne ke dan zuba don haka zamu bata pills dazasu kara mata karfi nan da tirthy minutes kafin ta gqlabaita, "ok go and take care of my wife please, banason wani dogon turanci, Harara hajiya ta watsa Mai " dama nasani don kayita matsawa y'ar mutane da tsohon ciki yasa kaki yarda a dauketa gashi ba aje ko ina ba ka takalo mata Nakuda bata shirya ba wallahi Allah ya shirye ka baba, sosa keya yayi duk da tabashi dariya bai iya cewa komai ba don hankalin shi ba akwance yakeba, ganin har minti talatin Shiru ya fada dakin kai tsaye nurse din na oga please you are not Allowed, " ok stop me yabasu Amsa ganin yanda take gumi duk ta fita hayyacinta yasa yaji mugun tausayin ta ya rufeshi tallabo kanta yayi kan labs dinshi, " Allah ya saukeki lafiya my life hannun shi ta damke tamau kamar zata balla shi likita ya shigo tareda saka mata pills din a kasan halshen ta yace ta rufe bakin ta zai narke a hankali, " oga hope kunzo da kayan baby'? Sai yanzu ma ya tuna da wani zancen kayan baby, tashi yayi ya koma mota hajiya na tanbayar lafiya yace kayan haihuwa sukace akawo, " to mu koma in hado ni bandauka haihuwar bace ai, No bazan iya barinta ba intafi bari inkira waya, wayar shi ya dakko ya kira Aunty maryam ya mata bayani, tace ok bari taje ta hado kayan haihuwar, tana zuwa, cikin rawar jiki ta saba nana dama Ahmad na gidan ya kaita gidan yasmin din ta dakko duk Abinda ake bukata dama sun shirya komai tuntuni, hardakaton plask ta taho dashi, Shikuwa cikin lebour room din ya koma ko minti goma ba ayiba nakudar tata so gadan gadan tuni ya hana likitan tsayawa cikin dakin. Saidai nurses kawai dashi don ganin andaga mata kafa dashi ake karbar haihuwar su kansu nurses din ya mugun burgesu daga gani yasan kan aikin shima, Nan basu san don Yasmin ya Dage yasan wasu Abubuwan ba kodan irin wannan ranar, da taimakon shi kan baby ya fara Fitowa, daga karshe ma sai dai suka koma taimaka mai kawai don yayi kane kane duk ya hada gumi mugun jarumta ya nuna a lebour room din Yasmin kuwa duk Azabar lebourn da takeyi batayi ihuba irin na wasu shashashun mata wai mace na labour tai ta kware baki don iskanci tana ihu ni nafada duk macenda keda bakin ihu ranar lebour dadi ta samu bata sha wuyaba, Sai Addu oin da take taja a hankali da salatin Annabi, har sukayi nasar fito da katon baby girl kyakkywa fara sol, da ita tuni ya rude ganin kwanshi a duniya ko kyamar jinin baijiba ya manneta a kirjinshi yana bata sumba, "Alhmadulallah baby nasamu baby girl dina yafada wasu irin kwallan farin ciki na zubomai, ko cibin ba a yankeba, nurse tace, "sir it seem like another one is coming cikin rudu yace " what tareda mikawa nurse dayan bayan ta yanke cibin ta daure zaren a cin y'ar uwar gudun komawar nahaifar, ai kuwa wani irin nishi tayi, sai ga wata katuwar baby kamar ta farkon, tuni ya gigice yafara sambatu identical twins oh my god baby kin haifamin twins kyawawa kamarki Allahu Akbar yaketa nanatawa, suka fara kokarin fitarda mahaifar, domin ganin duk ta gala baita, saidai suna dannawa sukaji cikin still da saura tuni suka fara kokarin fitarda abinda ke cikin, batareda sun koma kan oga MA uban rawarkafa duk hankalin shi yakoma kan ya'yan shi, sai kisses yake basu, jin wani kukan babyn bayan wa inda ke tareda shi yasa shi dago kanshi ya kallesu, suka mikamai yaron " congratulations sir madam ta samu triple baby's two girls one boy , kasa karbar yaron yayi ya nufi yasmin da ta koma kamar matacciya, " nurul hayat kin gama da Muhammad Abdullah baki daya na gama zama bawanki a duniya kin gama bani komai farin cikin Muhammad,   Bakinta ya tsotsa kadan tareda riko hannun ta gam, " please sir she need rest bari mu gyarata kuma zamu mata stitches , ina kayan baby's jikin shi na rawa ya fito baki har wuya dai dai Aunty maryam na zuwa da akwati karama, maidauke da kayan, hajiya jiki na rawa tace babana yaya " tahaihu hajiya Y'an uku mata biyu da namiji, Alhmdulillah Alhmdulillah Allahu Akbar suka fara nanatawa itada Su Ahmad da maryam nurse ta fito ta karbi kayan ta shiga dasu ciki yace saidai susa daban daban don baisan me zai haifa ba don duk scarning dinta daya suke gani, Allah ya boye musu Ashe uku ne ringis a cikin, Nan kowa yafara kiran dangi ana shela yasmin Y'an uku, gyarata sukayi tsab kafin su kaita restiing room tareda daura mata drip bayan sun mata stitches din suka bata Allurori domin tayi mugun laushi, maryam ta kira su mama ai tuni mama hindatu ta mike tafara rangada guda mama ta fito " lafiya hinde? " ke lafiya takawo hakan nayi kishiyoyi harda miji sabo badole ba, yasmin yan uku cankis Allahu Akbar, mama ma tace Allahu Akbar ikon Allah dama wannan ciki saidai biyu ko uku naso inyi magana nayi Shiru kar in tsorata ta Allah Mai iko, Cikin lokaci kadan mama hindatu ta hada mata farfesun zabi mai yaji tareda kayan kamshi da kuma kunun kanwa ta saba hijabi, " yaya Saude kya aikan kayana daga baya ni natafi kyafadawa malam, " toh uwar ya mai zumudi bazama ki kira ki fada maiba, ? " ai sai kiyi, tayi tafiyar ta tana cewa " inna tsaya cewa ma ki shirya muje zakice bazaki ba sai yaya ya sani niko bazan iya jiraba don haka kyabada sako, Dariya sosai mama saude keyi " to ya da uwarta ni mezanje inyi ko rashin godiyar Allah, wani irin farin ciki mama keji sosai bataki tajeba Amma kara irin ta malam bahaushe ta zauna tabar mama hindatu ta tafi, Uban gayyar kuwa dakyar ya bar yaran Aka dauka saida hajiya tace " baba banson rashin kunyar ka kabamu yara mugani kabi ka kwakume su don rashin ta ido kaje Kayi wanka ka canja wannan kayan ko kai Kayi nakudar sai haka " Ai wallahi da ni akayi hajiya, Nifa na ciro biyun, " wuce kaban wuri tace don ita ke jimai kunyar idon maryam, itadai dariya takeyi ita ai yanzu ta saba, dakyar yabar Asibitin yaje gida ya canja kaya tareda nufar central ya jibgo kaya bayan hilux guda ya shako kamar hauka komai uku ya ware daki ya zuba kafin ya koma Asibitin lokacin an cika dakin tab da Y'an uwa don harda yayyin shi, kowa sai barka yakemai yana Amsawa ba kunya bacci takeyi sosai saboda Allurar baccin da suka mata, " likita yasama domin yanason a sallameta suje gida don yaga Sam bazata samu hutu a nan ba saboda mutanen dake tururuwa , idan ta tashi zamu iya baku sallama don ba wani matsala, " kudi ya ciro bandir batareda kirgawa ba ya ajiyemai yana godiya, likita kuwa tuni yafara washe baki yana godiya shima, yana Allah ya mai maita, Kafin ya koma dakin ya ratsa mutanen ya janyo kujera ya zauna kusa da ita yana kallon yanda duk ta zurma saboda wahala a yau yakara sanin darajar uwa da kuma sanin mutumcin ya mace domin ganin yanda take nakuda yasan iyayen mu mata jarumai ne, duk namijin da baitausaya wa mace ba bazai gama lafiya ba domin sudin sune jigon Al Umma, "baba kazo kafita da kin nan kana mutane wuri kana ganin jama'a Amma don rashin kunya ga surukai ko a kwalar ka Yaya Halima tace " Ai indai babanki ne hajiya kinfi kowa sanin hali, banza ya musu tareda mikewa ya koma gadon da aka jera ya ran suna shirye cikin kayan sanyi masu kyau, ya tsuguna yabasu kiss a kumatu da d'an karamin bakin su, " yanzu wa innan ya'yan shi ne? Alhmdulillah yau farin cikin da yake ciki Sam baki bazai iya fayyacewa ba, "ya'ya uku duka shi Kadai , Mama hindatu dake cikin su tace " kubsrshi irin wannan Abin farin ciki hajiya Amina wallahi banga laifin shiba, '" hinde nariga na gano ki don haka ma na tattaro na dawo gidan don naga ba wani takamai burki zakiyiba yazo yana cutar da yarinya a banza bayan sunkuto wa innan masu jajayen kunnuwa, shidai dabino ya ciro tareda tattaunawa ya dauki tafarkon domin anyi musu shaida Inba haka ba Sam baza agane matan ba sai namijin da yake shi daban ne, huduba ya musu tareda Ajiyesu ya tashi, " please yaya Halima kar a rika daukar su duk Wanda yazo ganin su ko munkoma gida ya gansu a gadon su banason a jagwal gwalamin yara suzo suna zazzabi, "Ikon Allah yau ina ganin Abun da ya isheni baban hajiya zoka fita inji babbar yayar su, dariya ya fice bayan ya kara kallon farin cikin ruhin shi, mota ya koma ya zauna tareda kiran Ahmad, " please zanyima transfer ka nemo kaji da ragunan da za a gasa ma masu zuwa barka da sauran Abubuwan Amfani , nan ya turamai kudi masu nauyi, don ina Fadin yawan su wasu zasu sa rai Sai kusan karfe takwas ta farko lokacin daga hajiya sai mama hindatu, duk sauran sunyi gida. A hankali ta bude idanun ta lokacin kuma ogan ya sawo kai dakin wani zafi takeji a kasan ta ware idanu tayi, hajiya ta matsa ganin tana motsi, " Sannu y'ar Albarka kintashi,? Da sauri ya karaso wurinta, mama hindatu ma ta matso, " Sannu mama da kokarin sunkuto wa innan kishiyoyin masu jajayen kunnuwa, " Sannu baby yace tareda riko hannun ta da ba drip ya ce " ya kikejin jikin ki akwai wani Abu dake damun ki? Girgiza mai kai kawai tayi tana baza ido domin ganin me ta haifa, tuni tazaro ido don dazu bayan daya yafito taji lokacin da akace akwai wani, " zuma yara nawa na haifa,? " su mama suka jera mata ya'yan agefen ta, kallon su takeyi tana tasbihi a cikin zuciyar ta " ya'ya uku duka? " eh baby yaran mu ne duka da muka haifa, wani irin kwalla taji ya ciko a idanun ta, Allahu Akbar Allah Mai iko, ita yasmin ce ta haifi triple baby's, Mama ta ce a dagata taci Abinci don cikin duk sun rarakeshi, Shi ya taimaka mata ya dagota tana runtse idanun ta don zafin stitches din takeji sosai, farfesun da yake cikin kula ta zubo mata a plate don har yanzu da zafin shi sosai sannan ta tsiyayo mata kunun kanwar tace " maza bude baki ki d'ura duka kinga dole mu cike gurbin wa innan masu jajayen sawun da Abinci, bata fuska tayi shima kofin kunun kanwar ya kalla, " meye wannan za a dura mata? " kai yimin Shiru nima shi nasha lokacin da nakeda cikin ku don ruwan nono yazo da baka kawo yanzuba har kaga wannan rana, " mama banason kunun kanwa, tafada a hankali, " kunji ko itama bataso kubata tea, mama hindatu tace " ai shine ke saukarda ruwan nono da wuri d'an nan kana ganin ya'ya har uku in batasha ba suka tashi ai akwai aiki kana ganin shi namijin ma tunda yazo duniya yake wawure wawuren hannu mayunwaci, "Toh in hakane baby shanye kar yarana suyi kuka in sun tashi suna son ma'man su, harara ta watsa Mai kawai ya karbi plate din naman da hannun shi yake bata, saida taci sosai harda kari ta shanye romon, ya bata kofin kunun shima saida ta shanye tuni taji karfi a jikinta ba kamar dafarko ba dataji kamar jiri, Likita ya kira yabasu sallama bayan ruwan ya kare suka tafi gida baki daya, Tasamu Aunty maryam agidan sunata shirya dakin yaran da uban ya ware musu An jera gadajen su masu kyau kowane ga walldrp na gadon d'an dai dai gwanin burgewa ta gyara dakin mai jegon ma ko ina na baza kamshi ga sabon bedsheets mai laushi ta baza, masu Aikin ma sai farin ciki sukeyi anata kaida kawo duk da dare yayi, ruwan wanka mama hindatu ta hada mata tace tube muje ingasa ki, " kai mama wankan jego zakimin,? "Banson shirme wa innan dirka dirkan yayan su ratso jikinki sannan inbarki ba wankan Arziki ai sai ki rube, barganin rawar kafar da mijinki Kayi inhar baki samu wankan farko mai kyau ba matsala zaki fuskanta nan gaba don haka wuce muje, hajiya ma tace " kedai Yar Al barka wuce a gyara ki kizo ki kara Abinci kafin wa innan yaran su tashi, sunema Abinci, Hajiya tayiwa yaran wanka fes ta shiryasu cikin wasu kaya iri daya masu kyau iri daya sai banbancin na namijin, uban ya shigo dakin rikeda katon din ruwan zam zam da zuma ya zauna yana daukar su kamar yamayarda su ciki, " hajiya ina baby? "Wanka ake mata, " zaro ido yayi " wake mata wanka? " Wanda ya isa " haba haba ya za a mata wanka inma bazata iyaba basai a kirani ba ni inyimata tunda matata c... Tsit yayi ganin kallon da hajiyar ta watsa Mai ya sosa keya yana dariya kasa kasa, ta fito daure da katon towel ta naatse ido don taji ruwan zafi mama ta matse ta sosai ga nonon ta da aka danna wai don ruwan yazo, saurin tarota yayi " lafiya baby? " ruwan shegen zafi wallahi, ......... Kana magana ranka zai baci hajiya ta tari numfashin shi don tasan zai kuma. Yaron yafara kuka ya karbeshi tareda rungume shi yana d'an jijigawa kadan kadan " mika mata shi ta bashi nonon hinde ai kun wanke nonon ko? "'Eh sosai kuwa ta bude ta bashi, yanzu nonon nashi aka wanke gaskiya bazai yarda ana mata wanka na gobe shi zai wanke kayarshi, tana tura baki hajiya ta tashi ta fita don bazata iya ganin buhu buhun rashin kunyar baban ta ba, mama hindatu tace " taimaka mata tabashi bari in hado mata wani Abun taci mai nauyi Tana fita ya zabura ya maida kofar ya garkame ya haye gadon tareda rungume ta tsam " tank you tank you baby, Auch tace domin tanajim zafi a kasan ta bata ma iya hade kafar sosai, " sorry sorry my dear tundazu nake bukatar privacy nida iyali na su hajiya sun hana, bakinta ya kama yabata short kiss tareda zame towel dinta ya zubawa kirjin nata ido " wow sun kara kunbura yarana zasusha dadi, yaron ya dago akan laps dinshi tareda dukawa bata zataba ya saka bakinshi akan niple dinta, yadan zuka kadan, " wow yummy, baby akwai ruwa Ashe, kallon shi takeyi tareda mamakin kullum karatun rashin kunyar shi hawa yake don yau yayi digiri, dayan ya kuma zuka kadan kafin ya manna bakin yaron da kamar ankoya mai sha, Ta runtse idanun ta saboda zafin yanda yaron keja, " yadai? " zafi, dage gira yayi " Hmm Amma da babanshi yasha har wani lumshe ido kikeyi ko in kama dayan ne shi yasha dayan? Yanda bazakiji zafi ba? " naki wayon bayan kaine ma ka janyomin ciwon nakudar dazu Ai wallahi zuma kai karshene, " hhhhh ai gashi yarana sun zo duniya ina kallon su inajin dadi, baby a matse nake kema Kinsan nayi mugun kokari shiyasa bansan nayi aika aika ba, ai hajiya ta gano har ta titsiyeni, nashiga uku da gaske? Uhm to meye mutum da matar shi, Tom nidai ka bude kofar kar mama ta dawo taji ta A kulle, saida yaron yasha sosai kafin ya koma bacci ya karbeshi ya shinfide a gadon, tashi tayi A hankali zata mike ya maida ita " ina zakije? Kaya zansaka, da kanshi ya ciro mata kayan bacci masu kauri riga da wando harda bra shi ya taimaka mata tasa kafin ya shafeta da Mai ya manna mata kiss " I love you my happiness, yafada tareda nufar kofar ya bude, yana budewa mama hindatu ta shigo da tuwon semo miyar kuka taji manshanu da namomi tace " maza kici ki kwanta don gobe Y'an barka bazasu barki ba marayam suntafi tace ta zo ta kuma ganin yara taji dakin a rufe, sosa kai yayi tareda cewa " ai shiryata nakeyi shiyasa na rufe dakin, itadai sai Shiru don bacci takeji sosai ta dan ci sosai da tea mai kauri ta kwanta ya rufe ta da duvet kafin ya fita a dakin................     "Ahayye mata ku shirya kwasar shagali ranar akwai shaku shaku dole muyi kara, I tunda bamuyi na biki ba Aisha dahiru ku shirya keda Ummu jidda mai zuwa biki da kulan rangem zamu debo rice ranar nidai zanje cin kauri naji zancen raguna tun yanzu don haka nayi gaba sai kunzo ina gidan MA sai anyi suna,     * Matar Soja* [10/8, 11:52 AM] Asli Smasher : (¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯) тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   Written by FENERH   *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby 67&68 *Masha Allah, haduwa dake haskene marubuciya mai tashe ga sanin ka idar rubutu, ina matukar kaunar ki Har cikin zuciya ta, dake nake my eloquent writer you are the best Among the rest kedince dai HASSANA DAN LARABAWA marubuciyar cin Amanar ruhi Allah yakara daukaka ki ya kareki daga sharrin mahassada ina jinjina* Hajiya da mama hindatu kuwa raba dare sukayi saboda farin cikin da suke ciki a yau Har karfe goma sha biyu suna hira a tsakanin su Ya shigo falon ya " har yanzu baku kwanta ba? " eh ai farin cikin da muke ciki yau bazai bari mu runtsa ba, to saida safenku, ya fada tareda nufar dakin Yasmin din, ido kawai suka bishi dashi, yana shiga ya zubawa Y'an matan shi ido daketa cilla hannuwa da kafafu da Alama yaran nada hakuri, wani irin dadi yakeji yanzu shine da yara har uku, matsawa yayi ya dakko dayar ya shinfide ta kafin ya ciro dayar ma Uwar ya kalla da namijin dake kwance a gefenta da Alama ya kuma shan nonon ne, Matsar dashi yayi ya kwantar da babbar ya fara kokarin ciro mata nonon, saida ya kallesu sun wani irin cikowa ya manna mata ta cafke, saida uwar ta bude idanun ta, " Sorry sun tashine sunajin yunwa, " runtse idanun ta tayi domin zafi takeji sosai akan nonon nata, saida ta tashi zaune tabawa dayar kafin ta koma ta kwanta. Ya gyara yaran tareda zuba musu ido baijin yau zai iya kwantawa, Alwala ya dauro ya fita zuwa falon yaga sun tashi yadawo tareda tada salla, har zuwa Asuba yana kan dadduma har saida ya sallaci Asuba kafin ya tashi, ya shiga bathroom ya hada mata ruwa mai zafi ya dawo A hankali ya tasheta, dakyar take bude idonta. " muje kiyi wanka, bata fuska tayi "zuma banason wankan nan na ruwan zafi, " come on tashi kafin su mama su tashi suce su zasuyi miki banaso, " yanzu zuma kai zakamun wankan? Yaye bargon yayi tareda dagata cak ya Ajiyeta yafara zame kayan jikinta, tana kallon shi ya barta da pant din dake bra saida suka shiga bathroom ya dora hannun shi zai zame pant din tarike, "please bari in cire da kaina " blood, cire hannun ta yayi tareda zamewa ya cire pad din yana cewa " babyn ma ni nacire jinin ne zanyi kyama baby is you fa my wife my life the mother of my children my happiness, don't doubt my love for you baby, tana kallon yanda yake komai ya cire pad din ya saka a Leda tareda jefawa dustbin, sakata yayi a bathtub din duk da zafin ruwan haka ta zauna yana ratsata ya zubawa kirjinta dake kara cika ido tareda dauke kanshi gudun matsala, Saida taji dadin kasan ta sosai domin saida tayi kusan sau uku yana canja ruwan kafin ya tara na wankan ya sasukayi zafi sosai kafin ya wanketa tas, ya koma sakin ya ciro mata new pant ya saka pad ya shigo tareda dagata saida ya goge mata jiki sosai da towel kafin ya bata ta zura ya bata katon towel ta fito, tana kallon ikon Allah wane irin mijine Allah yabata ba kyama ba nuna gajiyawa a lamarinta,, da kanshi ya shafeta da Mai ya ciro mata bra da kuma sabon kaya riga da zani ta saka domin tace batason sket tayi wani irin shar da ita tana kyallin jego, zama yayi tareda zabga tagumi ya zuba mata ido kamar ya hadiyeta, gyara zama tayi tareda daukar sarkin tsotson da yatashi ta ciro nono da ya mugun cika tafara bashi tana cije lips wasu irin hawaye ne kebin kumatun shi, tayi saurin kallon shi, "Zuma lafiya? " Hmmm baby is happiness make me cry me Zanbaki baby for this beautiful Angel's dakika bani, hannu tasa tareda shafo tears din " don't want anything only your love zuma Kabani komai Arayuwa saidai Aljannah kawai nake nema a karkashi ka kamun Abinda bakowace mace kesamun irin shiba, "baby kingama samun Muhammad Abdullah nakine mulkinki ne sai yanda kikayi dani baby ni ai yanzu ba sauran mata a duniya saike Kadai nake gani, kinban farin ciki kin cikemin kowane gurbi da yarage a rayuwata and today you gave me the must happiness in the world that's my beautiful baby's so me ya rage mun a Rayuwa? Matsowa yayi da sauri ya tare kan yaron datake kokarin saki wajen sauraren kalamanshi masu shegen dad'in saurare " zaki yarmin da yaro saboda soyayyar babanshi, ya fada yana mata dariya, " kokaga laifina ai sai sakaryar mace zatasamu miji irin nawa ta tsaya wasa, dadin kalaman ta yaji ya rungume yaron tareda dora lips dinshi asaman bakinshi ya lashe nonon da ya d'an bata d'an mutsilin bakin tareda bashi kiss tana kallon shi "baby yaron nan duk ke ya biyo Y'an mata na ne suke kama da ni, matsar da fuskar ta tayi ta zuba musu ido tabbas ubansune yaran, "kamun wayau zuma bayan ni nasha wuya, " a ina ai tare mukasha wuyar nama fiki nida na dage wajen aiki badare ba rana ina hada gumi this is my hardworking, dariya tayi, " um baki tanbayi sunan da na basuba? Meye sunan? Babar hajiya Amina kenan dayar mama saudat sai baban zango Mahmoud, wani irin farin ciki taji sosai ta kalleshi tarasa bakin da zatamai godiya saidai hawayen farin ciki kawai, tace tank you zuma ta, don't tank me, ok I love you, " uhm that's my baby, love you more, Tace "ina su mama? Suna daki mana, to kafita karsu zo suganka a nan, " na nawa bayan a gaban su na shigo nan suna kallona suma sunsan bazan iya nisa da family na ba, sakin baki tayi " a nan ka kwana? Eh don nayi kokari ma ban rungume ki ba nasha wa innan, yafada tareda taba cikakkun kirjinta, " baby sai kara cika sukeyi yarana zasusha dadi ko za asanmin ne nima,? Yafada yanayi kamar wani shagwababbe, "karufa min Asiri mana inshayarda ya'ya in shayarda uba? "Uhm dama ai kinsaba shayarda ubansu please ko yanzu kar a hanani, " please kafita haka karsu hajiya su shigo kaga gari ya waye kama barni da bayanin kai kamun wanka, kiran hajiya ya hanashi fadar Abinda zai fada " baba kafito mu shirya ta haka banson shirme fa, " kushigo mana ai hira mukeyi kawai hajiya, mama hindatu ta fara shiga da cup da tea mai kauri ya mike yana gaishesu cikeda girma mawa, tace " barka dai dan nan ya kwanan kishiyoyina lafiya lau mama ya riko hannun hajiya " ina kwana Momyn Yasmin, dariyar sunan da ya bata tayi " au kayarda anture ma gwamnati yanzu? Badole naba tunda kikazo gidan nan kika kwana saboda ita yanzu ni ai kin yadani , Eh ai dolena ne tunda bakada kunya muna gidan nan ka tsallakemu ka shigo dakin mai jego ka kwana inni ka renani surukar kafa? Sosa keya yayi. Mama hindatu tace " bakomai d'an kwarai banga laifinka ba yara uku ina zaka iya nesa dasu, " nagode mama wallahi ban iya bacci ba saboda farin ciki jiya yanzu zanje inrama baccin A musu wanka intafi dasu dakina duk Wanda yazo suna wurin babansu, " ikon Allah, hajiya tafada, mama hindatu tace " ke kinyi wanka daga gani ko? " eh yayi saurin fada nagasa ta da kyau mama har sit bath tayi, " to Sannu da kokari, " hajiya ta juya Hinde bari innemo mata Abu mai nauyi bazan iya da d'an kiba, dariya sukeyi gaba daya, mama hindatu ta wankesu ya ciro musu kaya iri daya kafin ya koma dakinshi yayi wanka kafin yadawo ya kwashesu suka koma dakinshi ya kunna room heeter ya jerasu ya haye gadon yazuba musu ido kafin bacci mai cike da ni ima ya kwasheshi, Su hajiya sunji dadi sosai na sunan da yasa ma yaran mama hindatu ta kira mama a waya " tunda kinki zuwa gashi snmiki takwara ai keda malam, taji mugun farin cikin abin itama tace " Au sunji suna mai dadi dole su kwaikwaya kajimin yara, Karfe goma gidan yafara karbar yan barka tuni anfara dora tukwanen Abinci duk Wanda yazo saidai yaga uwar ba ya'yan, hajiya sai fada take daga baya dak in taje da kanta taga suna bacci hankali kwance Suda rigimammen ubansu ta fara kwaso biyun kafin ta koma ta dauki dayan, su Aunty maryam ma sun iso itada Amira da wasu matan barikin kowa yaga gidan sai yasan Yasmin na cikin daula tundaga harabar gidan bare ka shigo cikin falon, A harabar gidan ake gashin naman mahauchi aka kawo musamman yake musu gashin sai diga yakeyi su Meenah na lashewa nidai ina kitchen don nafison kajin danaga ana soyawa, nazage inata dan Dane, Gida yacika tubarkallah yan uwa harda gayyar sodi don ni mamaki Bariki Auren Soja fan's suka bani duk su suka cinye komai ranar ko waya ce suzo? Kula yasmin take samu sosai MA sai faman narkar musu da nera yakeyi don ana jibi suna ya Sa Ahmad ya shigo musu da akwatuna kowa saiti biyu yaran uwar kuwa saiti hudu ga sabuwar venza golden colour Abin Masha Allah kawai zamuce, wani irin murjewa take karayi ga gyara na musamman da mama hindatu ke mata ciki da waje su baban zango da baba sunzo sunga yara mama dai tace sai bayan suna bazata zoba, Zainab din ismail ma kullum da ita ake wuni, Ana gobe suna ma a gidan suka kwana domin shirya kayan rabo daki guda aka jibga kayan rabon dake dauke da hotunan baby's din kitso zainab ta yarfawa mai jego MA dai ya hakura dole don yanzu Sam duk kwakwarshi baya samun ganin ta daya shigo yake fita saboda mata gidanshi na Bariki ya koma ya basu wuri, Yauma karfe goma ya shigo domin yana son ganin ta gaskiya, wayar ta ya kira tana dagawa yace " please kizomin da yarana ina dakina, tashi tayi cikin sauri ta feshe jikinta da turare tareda murza humra ta dauki babbar wato Amina wadda suke kira da Ummul khair ta saba ta a gefe daya ta dauki saudat wato Ihsan kamar yanda maryam ta musu lakani, saida ta shiga dakin nashi taji karar ruwa a bathroom ta shinfidesu ta koma daki domin dakko Abu khair wato baban zango tana shigowa tasameshi yana daure da towel wani kallo ya jefa mata tareda sauke Ajiyar zuciya, ta gyara tafiyar ta ta matso tareda doramai shi akan cinyarshi har tana shago kirjinshi dake kwance da suma baka suduk yaja mugun numfashi tareda shakar kamshin jikinta gefen shi ta zauna tareda manne mai, tuni ya fara hawa network yau fa kwana shida rabonshi da ita gaskiya yayi kokari yana ganin irin wann cikar kuma tana wuceshi a banza gaskiya yana cutuwa , Jin yayi Shiru yasa ta zsgayeshi da hannayenta tareda dora kanta saman kafadar shi, " mijin Aljannah ya akayi? Numfashi yaja dakyar tareda juyowa bayan ya gyara yaran, rungume ta yayi tsam yana Ajiyar zuciya, ya bata tausayi sosai don tasan kwanan zancen, hannun ta ta dora saman kirjinshi tafara shafawa tana magana a hankali " farin cikin Fatima meye damuwarka bayan gani akusa dakai kasan banason inganka a cikin damuwa, a hankali ya bude bakinshi adai dai kunnen ta " Kinsan damuwar mijinki ko zaki iya bashi magani? Juya bakinta tayi dai dai kunnen shi tace " sosai kuwa idan banbaka maganin matsalar kaba kanada wata matar ne bayan ni? " dole infaranta maka megidana, hannu tasa tareda zame rigar jikinta ta sama da hannu daya hannu daya kuma ta na shafo kirjinshi da shi cikin natsuwa, Ta fara lasar kunnen shi cikin wani irin natsuwa tana rikitashi tuni towel din jikinshi ya balle don mugun rawa jikinshi yakeyi ta kife kanshi a saman luntsuma lumtsuman maman ta dake cike kamar su fashe, ya fara yawo da fuskar shi akansu yana bata wani irin salo da yasa tuni suka fara tsiyaya kamar fanfo yayi saurin maida bakinshi tareda zame bra din ya danne bakin dayan saida ya rage ruwan da bakinshi kafin ya koma ya lashe dayan tas tareda rage musu cika kafin ya hade bakinsu jikinshi wani irin shaking yake ya rasa inda zai tsoma ranshi jinta atareda shi muguwar matsala ta karamai, ganin yanda yake fitarda numfashi mai zafi yasa ta kwantar dashi dama kafarshi na kasa ta zame tareda bashi mamaki mafi girma domin socking take bashi mai rikitarwa tuni hawaye suka fara bin fuskar shi yana mummurza kafafunshi yayi matukar kokari da baiyi ihuba a yau don ta mugun rikita mai kwakwal wa, Saida taga yasamu natsuwa itama ta barshi ta nufi bathroom ta hada ruwa ta dawo tareda dagoshi yana langabe mata kamar jariri tace " baby muje Kayi wanka, " bazan iya tashi ba ai kin karar min da ruwan jiki tas yau, " Au haka zakace min? Dariya yayi tareda mikewa ya daura towel din da ya kwance " sorry my sweet wife kin gama min komai bakisan yanda naketa lallabawa bane yau kinragemin damuwar duk da banyi nutsoba kinshayarda ni zumarki mai dadi, tank you, rufemai baki tayi da hannun ta yayi saurin biting din ta cikin wasa " na fada miki inzaki rufe min baki kisa murfinshi, dariya tayi tana yarfe hannun " ina murfin? " come let me show you tayi saurin zamewa don tasan mezaiyi, kafin ya dawo ta fitar mai da kaya ta Ajiye tareda kwashe Wanda ya cire, yana Fitowa yaga kayan ce kiban singlet da short kawai anan zankwanta da yarana   In sun tashi yazakayi dasu ga Abulkhairi da tsotso kamar babanshi, tafada tana dariya, matsowa yayi tareda cewa " kinmanta na tsotsa dazu zanbashi Wanda nasha dazu , fita tayi da gudu tabarshi yana bin bayanta da kallo tareda girgiza kai " love you baby, yafada tareda hawa gadon ya shiga tsakiyar yaran shi ya musu Addu a tareda tofesu ya na kallon yanda sukayi bulbul " dole kuyi kiba yarana kuna kwashewa dady gara, yafada tareda mannawa hajiyar shi kiss yanason yarinyar sosai kodan ita tafara Fitowa ita yafara runguma, kafin ya mannawa Ihsan ya shafo y'ar fuskar ta, kafin ya koma kan Abulkhair ya ce " kai yaron Momyn kane my boy, I love you All my beautiful Angel's, yafada kafin yayi bacci,   Ita kuwa tana shiga zainab da Amira suka ce " Wallahi gidan nan akwai buhu buhun rashin kunya yanzu kina jego kika tssllkake mu kikaje wurin miji harda murza turaruka, "yasan ranku sa idawa mijina na bukata ta sai intsaya yanga kawai, munshiga uku kin gama lalacewa yasmin, nafasan me kuke tunanin munyi to da yau nasamu tsarki sai nabashi full kulawa, don haka kuciremin eye's, " Kuth kuce za ayi gwarne kenan? Ko duk shekara zsn haihu ina ruwanku matar so ke gwarne, "Aunty maryam tace " Au kuma bayan kingama zagin nayi gwarne? Ai ni Aunty banga laifinki ba Ashe haka Abin yake Aunty ki kara tamke baban Auwal badi Musha suna, " aa wannan sai ku marasa kunya kuma ai ke zamuyiwa wannan Addu ar mudawo mudibi wata garar, zama tayi tareda bata fuska, "bakyasona Aunty? Dariya suka sheke dama Abun burgace kawai baikai cikiba, " haba bakwa ganin yanda nasha wuya yara uku harda stitches, "Habawa dadi miji ai duk cikin soyayya ne, munace Kince da kin warke bashi zakiyi, kwanciya tayi ta basu baya sunata mata tsiya, sunsha hira kafin su kwanta, Washe gari suna antashi da kimtsa gidan Abincin suna booking yayi a hotel harda su snacks komai a wadace aka kawo gida ya cika makil da mutane maijego sai shiga da fita takeyi cikin suturar Alfsrma angon karni kuwa Bariki suka hada wata kwarya kwaryar liyafa shida yaranshi da kuma Abokan aiki, Ranar tasamu gift kamar bagobe don har Y'an Bariki Auren Soja kowace batazo empty ba sunkwashi gara kuma sun yi Abin Arziki don mota mota narika ganin suna fakawa sunci uwar Ankon kampala ishurunka maraya sai rawar kai sukeyiwai su sun hadu saidai tunda suka shiga sukaga manyan mata don duk Y'an uwa sun hadu tagefen MA da yasmin anata harkar Arziki har harabar gidan Har makota sunsan yau Ana suna gidan MG Muhammad Abdullah ba wata bidi'a Amma Abinci duk hadamarka sai ka barshi iyakar kwadayinka yaran sunsha kyau da haduwa ranar sai canji ake musu kamar uwarsu, Can na hango su Aunty hajiya sa a gefen mai jego tasha dauri tareda my little Ummu kulthum nafara tanbayar kaina yaushe tasan yasmin? Kafin infito insamu su maryam Haruna menah my takwara da su k&k su suwaiba harma da hussy Ali a tsakiyar su Aunty maryam anata hira kowacce Jakarta fal da kayan suna da aka kwasa, bangama mamakiba saida naga Aunty Aisha dahiru a cikin daki ita da su mama hindatu ana shirya tafiya da Mai jego bayan taci rangem bakinta duk maiko na fito don baza ayi shawar daukar yasmin ina wurin ba.........   "Jinjinar bangirma zuwa gareki zainab Adam maman jibiril makociyata uwar gida a wurin lcpl Muhammad gombe sgnt to be insha Allah very soon Allah yakaresu a duk inda suke ina yinki Allah ya biyaki ladan ruwan da kike zubo min daga sama     "masoya munzo gangara da izinin Ubangiji komai yayi farko zaiyi karshe zankammala labarin Auren Soja soon ina matukar godiya da Addu oin ku Allah yasaka da Alkhairi Addu ar ku nada matukar tasiri A Rayuwa ta ina godiya Allah yabar kauna inayin ku fisabillahi,   *Matar Soja* [10/11, 7:22 PM] Asli Smasher : (¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯) тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs. INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/ FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/ TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09 *BARIKI* _Auren Soja_   Written by FENERH   *Dedicated to* Fiddausi mainasara feby 69&70➡   Alhmdulillah Anwatse taro lafiya yarage daga mai jego sai su mama hindatu da hajiya Aunty maryam ma ta nufi nata gidan ba karamin Alkhairi tasamu ba a wannan haihuwar daga Y'an uwa da Abokan arziki Yaranta na samun kulawa sosai, mama hindatu taso tafiya da Yasmin gida kodan rawar kafar da taga MA nayi kar suje su cutar da yara tunda Yasmin din ma batawa kanta fada Amma ya murzawa idon shi toka yace Sam ba inda za akaima i mata da yara dole suka hakura don har su baba aka fadama suyi mai magana baban zango ya hau fada "hindatu Al Ada ko addini kubar yarinya a dakin mijinta kici gaba da kula da ita in ta cika sati biyu ki tattaro kidawo tunda uwar mijinta na nan kuma tanasa ido, baba ma ya yarda da maganar kanin shi dole hakan suka hakura, tuni sun fara tsumata domin gyara hanyar da ya'ya uku suka fasa, gyara suke mata na musamman harda hajiya ta gayyato wata y'ar Niger tazo ta fara gyara ta, su hajiya sun sami lafiya domin sati daya da suna MA yaje jaji yin wani aiki na kusan wata daya, ita kanta Yasmin taji dadin tafiyar don mugun tausayi yake bata don tasan halin kayanta mayenta ne idan suna kusa da juna baya iya hakuri, don koranar da zaitafi saida ya latseta ciki da waje kafin ya wuce, Sati biyu mama hindatu ta shirya komawa gidan ta Hajiya da kanta ta mata Alkhairi bare uban gayyar da ya bata dubu Dari harda zannuwa masu tsada itada mama kafin ya tafi yasmin ma ta kara musu, saida tayi kuka saboda murna tace " nikam bana kishi da wainnan kishiyoyin gaskiya ga takwaran me gida ga kuma kuma kishiyar saurin kwarai Allah dai ya raya manasu akan sunnah, hajiya tace Amen, kamar karta tafi sukeji, driver yakaita gida cikeda harkar arziki, gida yarage daga hajiya sai masu aikin, yaran sunyi bulbul dasu kyansu na kara Fitowa da wayau, kullum sai sunyi waya da ubansu sama da goma yana tanbayar yaranshi,   Yauma suna kwance a gefen hajiya itama tana zaune suna hira ya kira wayar ta ta dauka tareda yin sallama, Ajiyar zuciya ya sauke, " baby ina kewarki fa kinsani gaskiya zanshigo, " ga momy na zaune, tayi saurin bawa hajiya wayar, dariya yayi wato bazata iya Amsa mai ba tunda tana kusa da hajiya, saida suka gama gaisawa kafin ta tashi ta fita, "my beautiful wife say something are you missing me too? "Sosai ma ai basai na fada ba, ya dauke ne? "Mene? "Jinin. "Aa ta "har yanzu? Tree week's fa baby, "idan ya dauke zanfada maka kazo ai nima ina kewar ka sosai mijina, "tanks my wife, I love you , yana kashewa tace tab bangama hadewa ba nasan kana zuwa saika tsoma inkasan ina sallah, dole intaimaki kaina ai don kana shiga kaji canji daraja ta zata iya raguwa, sorry zauji kainakewa tanaji, ita kanta tasan tanashan gyara ga na HQ gana ciki duka y'ar Niger ke mata ga wani irin murjewa da takarayi tayi shar da ita, tasan oga na ganinta zai rikice, Saida suka kwashe sati uku cur kafin yasamu shigowa kaduna saboda wani couse sukeyi na karin girma ranar surprise yayi musu suna baje a falon ta yaran na cikin gadajensu dake falon don baban ko ina ya Ajiye musu gadaje, akwai a dakin shi akwai anata kuma, Abulkhair ne kawai ke kan kafar hajiya, " Fatima wannan me gidan sai kin dage akwai tsotso shiyasa yafisu karfi duk da shine karami, "wallahi momy har ma kar dare yayi mai hakuri sai momy na ko Ihsan tana taba rigima, dariya hajiya tayi tana mejin dadin yanda yasmin ke mata kara a KO ina tana kiranta Momyn ta don haka take karajin sonta har cikin jinin ta, Ai da wuri zaki fara basu Abincin su bari baba yazo don ma kinada wadatar ruwan nonon da akwai damuwa shayarda ya'ya uku, Sallamar shi ya katsesu tareda zubamai ido cikeda mamakin ganin shi, tunda ya iso ya zuba mata ido kamar baitaba ganinta ba don tayi kyau sosai cikin super din dake jikinta green ta zubo kana nan kalabarta a kafada tana daukar ido tayi wani irin cika mai burge duk wani namiji, itama kallon shi takeyi yanda yayi kyau a cikin kakin kanshi ba hula sai boot dinshi dake sheki Alamar sabuntaka yayi mata kyau sosai, wurin mahaifiyar shi ya karaso tareda daukar yaron ya fara gaisheta, " Sannu Hajiyar yasmin " yauwa mijin yasmin dina shigowar bazata Kayi mana? "Wallahi momy bamu dade fa da gama waya dashi ba baifada min zai shigoba, wani Abu kallo kawai yake aika mata don hajiya na wurin ne yasa bai isa jikinta ya rungume taba, bin ko ina na jikinta yakeyi da kallo kamar zai cinyeta duk dokin ganin yaran shi da yakeyi maman su ta daukemai hankali saida hajiya tace kawoshi ni inshiga ciki lokacin sallah yayi kar ya dameta don shi rigimamme ne, mikewa yasmin tayi ta nufi kitchen yabi bayanta da kallo tana juyamai kwakwal wa, da gayya don tasan ya gama sumewa, hajiya ta ganoshine tsab yasa ta basu wuri, wani irin Y'ar yaji tsigar jikinshi na tashi ya mike tareda leka fuskokin Y'an matan shi ya basu fake a kumatu " sorry my girls mom is calling yafada tareda nufar kitchen din cikin saurin shi,   Drinks da Abinci take shirya mai don Yau ma yayi sa a sunyi tuwon nashi don hajiya hanata cin kowane irin cima takeyi saboda cikin yaran, saurin karasawa yayi ya karbi tray din tareda Ajiyewa a gefe ya shige jikinta yana zuba mata numfarfashi da sambatu, " baby you no I came only for you jan Ajinfa kinbirkitani baki daya wallahi muje dakina , yana kwakume da ita suka fito, suka hadu da baba jummai, ta fara mai barka da zuwa yace " baba don Allah ga yarana a falo a kula dasu, tace to ranka ya dade angama, kunyar Abin yasmin taji tace, "please bari indakko Abu a dakina ina zuwa, "Nop muje tare kawai I can't wait any longer baby, one second zuma I will be back, baisoba haka yabarta, ita kuwa tayi mugun kaduwa da ganin shi don Sam bata shirya maiba gashi wani hadi ake mata Wanda zai dauki nan da sati kuma jiya aka fara tafison sai angama ta kara kame Abinta a hannu,   Dakin ta ta koma cikin sauri ta makala pad tareda kara turare a jikinta ta fito, Koda ta shiga har ya cire kayan jikinshi yarage dagashi sai boxer yanata zarya tana shigowa ya matso a sukwane ya shige jikinta yana zuba mata kalaman yadda yayi kewarta na tsawon sati biyu, birkici mata yayi domin kamshin jikinta na musamman ne yana kara daga mai hankali da kuma rikitar dashi don bakaramin gyara tasha ba kamshin ya huda ko ina na jikinta, sai bin jikinta yake da hancin shi yana zuba mata santin yanda ta canja, Daga karshe gadon ya mayarda ita yafara rabata da kayan dake jikinta cikin rawar jiki, jikinshi yayi sanyi lokacin da yakai wurin pad ya marairaice tareda tsagaitawa, "baby why baki fadamin ba kika bari nasa rai,? "Ai baka fadamin zaka dawo ba dana fadama kuma har yanzu banyi Arba in ba, kallon ta yayi da idanun shi da sukayi jawur saboda fitina, " baby yana zuba sosai har yanzu let me see, ya fada yana kokarin tura hannun shi, tati saurin riko hannun shi "oh my Zuma kasan ina son farin cikin ka kuma nima ina kewar zumar miji na bakai Kadai ke son kasancewar mu a inuwa daya ma nima ina ina bukatar kasancewa da farin ciki na, A haka ta mai dabaru domin ragemai zafin da ya debo kuma yasamu natsuwa sosai yanata gode mata tareda makaleta, sai gab da magrib ya koma jaji bayan ya gama wasa da yaranshi ta cika mai tumbin shi da dishes dinta masu dadi,   A kwana a tashi ba wuya gashi har sun cika kwana Ar abin da haihuwa hajiya ta koma gidanta ya rage daga ita sai su baba jummai a gidan oga MA kuwa ya kusa kammala couse dinshi ya dawo, tayi yawon Arba in dinta gidajen Y'an uwa sosai ko gidan su ma kwana tayi domin mama Sam taki yarda taje gidan ta sai su babane suka je kusan sau uku ganin takwaran baban zango da kuma uwargidan shi inji baba yaran sunada shiga rai sosai don ranar da ta kwana gida ma a wurin su baba yaran suka wuni sunkasa fita saboda yaran masu mugun shiga zuciya, mama ma duk karar ta saida ta makale yaran, ranar sunga gata sosai a gidan, daga gidan su gidan ismail taje yayi matukar farin cikin ganin ta a gidan shi, zainab dake fama da tsohon cikin ta haihuwa ko Yau ko gobe itama taji dadi sosai ganin uwar gidan MA a gidan su da kyawawan yaransu, daga karshe ta d'an gana da Bariki domin shirin ta, gidan Aunty maryam ta sauka itama tayi farin cikin ganin ta, suka baje sukasha hirar su ta zumunci kafin suje wurin matar umar taga tayi mugun laushi kamar ba masifaffiyar matar nan ba, tayi murna sosai tareda yi mata godiya akan Alkhairin da oga MA ke musu akoda yaushe, harda kukanta, ta kara Mata wani Alkhairin sannan suka nufi gidan ta masu gadin nata kwasar gaisuwa, Ganin uwar gidan oga Yau tundaga kofar gidan take kallon gidan tana tuna Rayuwar baya da duk tarihin da suka kafa a cikin gidan suna dawo mata kamar a mafarki Yau itace matar mai gidan har ma da Albarkar yara uku, Emanuel suka samu a baje yana minshari a falon suna shigowa ya zabura tareda ware idanun shi, "madam, cikin tsananin murnar ganin ta, yafara karanta mata surutai tareda karbar Abulkhair dake hannun ta Su Ummul khair suna bacci Abinsu a gidan Aunty maryam shi da yake rigimamme ne baya zama, umarni ta bashi ya sa akwashe mai duk tsofaffin kujerun da furniture's din dake gidan duk da ba Abinda sukayi tunda ba a zama a gidan, don Tanason ta yi mai Alkhairi shima don shine tsanin haduwar ta da farin cikin Rayuwar ta, uban ya'yan ta kuma, a ranar tasa aka kawo mata sababbi dama ta gama tsara komai cikin awowi kadan gidan ya sauya ta tsara komai yanda takeso da haddadun furniture's din da tayi oder daga wani fitattaccen company Fadin haduwar gidan bata lokacine, maryam ma ta so ta canja mata tace bataso kayan ta basuyi komai ba yaushe ma aka sa mata su bazata yarda a siyar da dukiyar baba ba, suka sa dariya domin tuna dramar filin baba da baban zango ya siyar domin kashewa yasmin kunya saigashi sun zama rabon maryam, Sai karfe goma ta samu natsuwa a dakin Aunty maryam suka baje bayan sunci sunyi kat ta kira farin cikin ta don kashe wayar tayi tun dazu don batason yasan shirin ta, tafison ta zauna kusa dashi don tasan bayajin dadin tafiya cikin gari kullum idan yatashi aiki dole ta rungumi mijinta su zauna a wuri daya ko ya maida hankalin shi akan aikin shi, Wayar yayi picking cikin sauri " tank God baby har zanbiyo hanya inzo kaduna inata kiranki tun da rana wayar ki a kashe what's wrong? "Nothing my zuma ya kake wayar ce bansan inda na jefarda itaba ina hidimar yaranka, "ya yarana suke? Lfy lau suke gasunan suna bacci, " gobe zamu dawo mun kammala cikin ikon Allah , Alhmdulillah, zuwa yaushe zaku shigo? "Da wuri zamu shigo naso ma mudawo Yau kuma wani Abu ya hana but get ready for me am coming to my honey tomorrow, "Allah ya kaimu, am do me favour please ka zo barracks ka tahomin da sako kafin ka iso wurin Aunty maryam,, "An gama uwar gida na, "kuma Amarya tafada cikin sauri tana hade rai, hhhhh kedin ce uwar gida kuma Amaryar Muhammad Abdullah insha Allah my wife, tayi dariya " tanks mijin Aljannah, Aunty maryam ta fadawa yanda sukayi kafin suyi bacci, tunda gari ya waye suna karyawa ta bar yaran tareda shiga gidanta ta bawa Emanuel ATM yaje mata kasuwa ya karo mata kayan Amfani don babu wasu Abubuwan don ba ya zama a gidan, lafiyayyan girki ta fara shirya mai masu lafiya kafin ta bazawa gidan ta kamshi ta ko ina, saida ta kammala sannan takira Aunty maryam tace akawo yaran suma ta kara gyarasu, wasu kaya ta ciro musu sabbi iri daya masu kaki sai T-shirt dinsu na matan pink sai nashi blue da d'an takalmansu ta shafe su da kamshi kafin ta shiga ta gyara kanta, itama, cikin kana nan kaya ta shirya kamar yaran wandon kaki na Mata mai kamar roba tasaka ya kamata dam da T-shirt dinshi anyi rubutu da golden *ARMY WIFE*a gaba da bayan rigar Sannan ta kwashe yaranta suka fito falon don ta sallami Emanuel don batason ya ga kwalliyar da zatayiwa mijinta, so take ma idan yazo ya canja mai aiki don zata dawoda su baba jummai Bariki, don baidace suna cakuduwa da katon namiji a cikin gida ba,   Idan kagansu kamar kasace su ka gudu saboda kyau da haduwa, MA kuwa yana shigowa cikin Kd Bariki ya nufa domin karbar sakon uwar gida duk da yaso ya wuce wurinta kai tsaye don mugun dokin haduwar su yakeyi umarni ya ba Ahmad su wuce zai karbi sako wurin Aunty, dariya Ahmad yayi "ni zanfara ganin madam kenan duk da ina kawaici, " ai umarnin my wife ne dole inje Bariki daba haka ba baka isaba, haka suka shiga ciki tundaga bakin gate din ya hango motar ta a cikin harabar yace " waccan motar yasmin ce me takeyi a nan Kodai...... Ya kasa karasawa ya bude motar ya fito batareda ya jira Anbude mai ba Ahmad ma yasan tana ciki don maryam ta fadamai plan din yasmin din,   Ganin falon a bude yasa ya shiga cikin takunshi mai tafiya da zuciyoyin Y'an mata hannun shi cikin pocket din Aljihun wandon shi na kaki, da sallama yasa kai cikin falon, taurarin shi suka farayimin welcome wato iyalin shi dake cikin shiga irin ta kakin jikin shi sunyi matukar haduwa da tafiyar da zuciyar Wanda akayi domin shi, wani irin farin ciki yaji ya ziyarci zuciyar shi, ta zabura tareda tashi ta nufo shi yana binta da ido cike da so da kuma burgewa, " Oyoyo dadyn mu ya iso tafada cikin karairaya da kuma jan hankali, bude hannun shi yayi ta fada tareda bashi Peck a kumatu, "what a surprise madam, " you like it? Ta fada, "yes I really love it my wife ya baza idanun shi cikin falon yana kare mai kallo, " wow hajiya Fatima Mrs Muhammad Abdullah kina ji da kudifa irin wannan gyara haka, . Kada mai idanun ta tayi masu daukar hankali " to ya don ranka mijina ya tsayamin yace inyi komai bakomai dagani ba kari, "yes dagake ba wata my wife kin isheni Rayuwa farin ciki na, muje inga yarana, daukar su yayi daya bayan daya sunata washe baki kamar sun san ubansu " Masha Allah yarana sunkara wayau zan nemo musu Abinci tunda na dawo don wannan ya mana kadan mu hudu, yafada tareda shafo kirjinta dake cike tam suna tsole mai ido, Tashi tayi barshi da yaran tareda nufar kitchen domin bashi Abinci yabita da ido yanajin soyayyar ta nakara huda kowane sashi na tsokar jikin shi "Alhmdulillah kawai ya iya furtawa, saida ta jera mai komai kafin ta zauna gefen shi ta dauki wayar ta tana kashe musu hotuna tareda yaransu sunyi kyau sosai hotunan sun dauku shima yasa tashi wayar yafara daukar ta kafin ya dauki yaranshi, saida suka gama ta fara rage mai kayan jikinshi sannan ta ce ya sauko yaci Abinci ta kwashe kayan zuwa cikin dakin su, saida yaci yayi nak suka kwashe yaran zuwa daki domin ya watsa ruwa, driver ta kira tareda bashi umarnin kawo su baba jummai Bariki sannan a kulle gidan, don ta d'an kwaso Abinda zasu bukata zuwa weekend, don haka takeson surika yin weekend a gidan su idan sunso,   Bayan ya fito da kanta ta shafeshi da mai tareda fitomai da singlet na kamo da guntun wandon shi ta bashi, "Yau shigar kaki zamuyi a gidan nan nida yara na,? " har ma da maman su ta fada tana dariya, "but taka mata mamansu tasan cewa jaririnta najin yunwa fa sosai , yazakiyi da yarana kiji da babansu ko za a kaisu wurin Aunty? Yafada yana karkace mata kai domin tasan fa dauriya kawai fa yakeyi, "Haba zuma itama fa mijinta na bukatar ta bakai Kadai ke son Abin ba, tafada cikeda tsokana, "nafishi matsuwa shi baidamuba, bawani kawaici yakeyi bakamar kaiba, " yeah I can't hide how I feel about you my wife kullum kara haukatani kikeyi da salonki, kada mai idanun ta tayi tareda matsawa jikin shi, "karka damu nayima sabon tanadi a bed my zuma, "Allah my wife tank you, muje Abani na matsu fa, Na sa akawo su baba jummai ka bari su iso sai in bar musu yaran sai... Ta fada tareda dage mai gira daya, "ok matso dai infara jin dumin jikin ki tom, ba musu ta shige jikinshi tareda hade bakin su wuri daya tuni yafara sakin layukan da yake , sallamar su baba jummai ya dawo dasu don har ya fara kokarin cire rigar jikinta, saurin janyewa tayi tareda saita kanta, shi kuwa zubewa yayi a gadon ya na maida numfashi, saida ta dawo dai dai sannan ta fita bayan ta dora hijabi akan kayan jikinta, ta yi musu Maraba, " hajiya nan muka dawo kuma? Eh baba sannun ku da zuwa Bariki, yauwa ina jikokina? Bari in kawosu ga dakin ku can baba ta nuna musu dakin dake cikin falon kafin ta koma saman ta kwaso yaran ta kawo musu, saida ta nuna musu komai na gidan kafin ta koma wurin oga, ban bitaba don banason susani bin motar dare zuwa legos yau, Saida nasan komai ya natsa nakoma dakin naga yanata zuba mata godiya tareda Alkawura masu girma dayake ta mata ji yake kamar ya tsaga jikinta ya shige tayi mugun haukatashi a shinfidar shi yau,, **************** Bayan shekara goma sha biyu yara ne a baje a katon falon su dake Unguwar rimi su kusan shida sunata guje gujen su bayan uku manyan sai wasu masu binsu guda biyu sai maza daga gani suma twins ne sai kuma daya karami dan kimanin wata hudu da da kuma y'ar kimanin shekara biyu dake gefen shi wata hamshakiyar mace na hango cikin tsadden leshin ta Senegal style yaji aiki saida ta matso na gane cewar Hajiya yasmin ce sai su Ummul khair da suka yi girma sunkara kyau Abin sha awa kayan su iri daya sai kuma Y'an biyun da ta kuma haihuwa bayan su wa inda basu canjawa suna ba sai kuma small yasmin da kuma Muhammad da take goyo yanzu , suna ganin ta suka fara natsuwa " momy wallahi Abulkhair ne duk keta cin zalun mu tundazu sai bin mu yakeyi da gudu gashi ma har yajima Ihsan ciwo. "Dukan ku kuzo nan ku kunayi me kuke nunawa kannen ku kowannen ku yazo nan kai dukan ka na daban ne bakaji ko kafi kowa fitina yau sai jikin ku ya gaya muku, tuni Ummul khair ta fara kuka don batason Abinda zai taba lafiyar jikinta, "Momy sorry please we wants repeat it again please momy suka fara bata hakuri, shigowar uban ne yasa gaba daya sukaji sanyi a ransu don bayason Abinda zai taba mai yara, "who is going to beat my pride? "Dady! Suka ruga a guje wurin shi harda small yasmin da ke gefe ita tana wasanta da Teddy bear, suka makalkaleshi dukansu, yace "wait let me carry my sweety ya daga yasmin domin yarinyar ba inda tabar uwar ta shiyasa yake jin sonta sosai a yaran nashi, Ummul khair ta bata fuska "dady mu baka murnar ganin mu sai little ko? " nooo ni na isa come my momy kuzo daddy ya muku tsarabar da kuka ce, suka fara ihu tareda fita harabar aguje harda Y'an biyu Abulkhair ne ya tsaya yana bata fuska " dady nifa? "Go and carry your gun my soldier, kaima na siyo ma, ai tuni ya bisu yarage daga shi sai matar shi tuni ya matsa jikin ta " my lovely wife mun tuba nida yarana don naga laifin su ya shafeni ko welcome ban samuba, "ban isaba my zuma yaranka ne basajin magana, " Ayi musu hakuri madam muntuba, yafada tareda kama kunnen shi, "ok for the sake of their father Amma zanyi mai bulala anjima, "Oh ayimin a hankali kar asa babansu kuka, zokiji yafada tareda matsawa ya mata rada a kunne. today you are a General wife jibi zamuje hanging rank don haka get ready Mrs MA tayi matukar farin cikin matsayin da mijin ta yakai wannan matsayin ta rungumeshi tareda cewa dole yau in wanke maka wannan Albishir din da ka bani, "yes please muje daga ciki I deserve it, "kai aa kafa girma yaranka na gida, bawani zansa akaisu gidan hajiya tace akawo su yanzu daga gidan ta nake, Ok my zuma muje in hada musu kayan su, ina name sake dina? Nuna mai keken yaran da yake ciki tayi yana wasan shi, yayi saurin matsawa " oh sorry my love maman ka ta hana inganka in ina kusa da ita bata barin inga kowa come to dady my baby, yadaga shi sama yaron nata dariya, Shigowar yaran kowa da kayan shi sunata murna da tsalle yasa yaji wani irin farin ciki, sunata godiya "dady tank you Allah yakara budi harda little itama ta na godiyar cikin gwalancin ta yayi dariya, "god bless my children suka Amsa baki daya da Ameen ya fara kashe musu hotuna yana makale gefe da uwarsu, kana ganin familyn kasan an ginashi akan turba mai kyau ilimi addini iya tarbiya, sai ince TAMMAT BIHAMDILLAH   "Iyaye mata mu dage wajen koyawa yaran mu dabi'u masu kyau kamar godiya ga yaro gaisuwa sallah tun basu iyaba har su iya kamar yaro karami ku rika nunamin hanyar masallaci tun yana karami zai tashi da Abin a cikin zuciyar shi godiya ga yara tanasa farin ciki a zuciyar mahaifin su naso in tsawaita Abin Amma akwai Uzuri Allah yasa mu Amfana da Abubuwa masu Amfani wa inda basuda shi mu watsar Allah ka yafe mana kurakuran mu Allah yasa mu dace duniya da lahira,   "dukkan godiya ta tabbata ga ubangiji na mai kowa mai komai Allah ya karo da din tsira ga shugaban mu Annabi Muhammad S. A. W , masoya ina matukar godiya da gudun muwar ku a wannan labari nawa da kuma comments dinku zafafa Allah yabar kauna, Jinjinar bangirma ga dukkan Grps dina BARIKI AUREN SOJA BARIKI AUREN SOJA 2 FENERH FANS GRP BENEFICIAL WRITERS GRO SIDIYA FANS GRP BOYAYYAN AL AMARI FANS PROFICIENT WRITERS FANS REAL SMERSHER FANS Da ma sauran Grps din da ban kiraba sunada yawa masoya ina matukar godiya sai mun hadu a sabon littafina mai sunan............ WANAKE AURE? Labari ne mai cikeda sarkakiya tareda sabon salo da kuma soyayya mai cikeda sadaukar wa masoya sai kunjini, An dauko wannan littafi daga shafin www.dlhausanovels.com.ng ku ziyarci shafin na www.dlhausanovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from www.dlhausanovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT __ *Matar Soja*

Post a Comment for "BARIKI Auren Soja Complete Hausa Novel"