DR. SAIF RETURN Complete Hausa Novel
*DR. SAIF Complete Hausa Novel*
_(return)_
©Ummu Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem
Haske writer's associated
(Home of expert & perfect writer's).
A hankali had'add'iyar motar tayi parking a harabar hospital d'in kusa da jerin gwanon motocin dake parke a wajen.
K'ok'arta ki fito Ayshaa kinji?, Naji wata murya ta fad'a daga cikin motar, "Aunt Salma bazan iyaba fa" wata siririyar muryar mace ta fad'a cikin shagwa6a, "daurewa dai zakiyi meye amfanin zuwa asibitin?.
Mintuna kadan wata matashiyar mace ta fito riqe da wata matashiyar budurwa dabazata haura sha bakwai ba kyakkyawace sosai kamar su d'aya da matar da alamu yayarta ce,
Tarairayota jikinta ta qara yi tana d'an murmushi gamida girgiza kai ganin yadda d'an zazza6i kad'an ta zauna sai shasshake mata take.
Kai tsaye office d'in babban likitan suka nufa bawani layi sosai daga Wanda ke ciki saikuma wasu mutum biyu masu jira, layi sukabi suma gaba d'aya Ayshaa ta kanannad'e Aunt Salma ta hanata motsin kirki sai faman 6ata fuska take kamar mai shirin sakin kuka.
Wad'anda suka shiga d'in basu wani jimaba suka fito sukuma suka shiga.
Had'add'en office ne daya wadatu da kayan zamani da ake qawata ofisoshi dasu sanyin A.C da qamshin air freshener da kuma na mamallakin mai office d'inne suka cakud'a suka bayar da wani irin daddad'an qamshi mai sanyaya rai da yanayi mai dad'i.
Idona ne ya sauka kan mai office d'in, fatabarakallahu ahsanul qaleeqeen, kalmar dana ambata kenan cikin raina saboda had'uwar mutumin tun daga zaunen zaka fahimci cewar giant ne ALLAH ya azurtashi da wani irin sirrin kyau mai d'aukar hankalin jama'a.
Idanunshi a lumshe suke ya dafe kanshi da hannu d'aya d'ayan kuma ya d'orashi kan table d'in gabanshi riqe da pen sosai yayi relaxing kan kujerar dayake zaune, a hasashena dai bazai wuce 31 zuwa 32 ba.
Sallamarsu ce tasa yad'an bud'e ido kad'an ya kallesu ya qara mayarwa ya rufe.
Duk da halin da Ayshaa ke ciki bai hanata ta6e baki ba, da jan k'aramin tsaki a ciki, Tunda suka zauna baice uffan ba haka suma basuce komiba bakajin komi sai sautin karatun Al'qur'ani mai girma daya kunna a wayarshi k'ira'ar khusary cikin k'arshen suratul baqrah kad'an kad'an sautin ke fita ta yadda idan baka kasa kunne sosai ba bata yadda zakaji.
Tuni Ayshaa tafara gunguni tanajan k'ananun tsaki, duk abinda take kuma yana kallonta ta qasan idonshi da tsakin datake masa.
Ganin shirun yana neman yin yawa yasa Aunt Salma ta bud'e baki zata fara magana, sai a lokacin ya d'ago ya zauna sosai kan kujerar tare da ware manyan idanunshi yana d'aga mata hannu alamun tayi shiru.
Shirun tayi kuwa cikeda mamakin irin Dr'n da ALLAH ya had'asu dashi yau, Ayshaa kam tuni ta shaq'a sosai jitake tamkar ta tashi ta shaq'o wuyanshi dan yadda ya raina musu hankali.
Kamar wanda akayiwa dole kokuma mai ciwon baki yace
"Ko zaki iya barina da patient d'in?"
Kamar wata doluwa Aunt Salma ta kad'a kai tana k'ok'arin raba jikinta dana Ayshaa databi ta kanainayeta, kamar zata saki kuka take fad'in
"Haba Aunt Salma bazan iya zama bafa", k'ok'arta dai little sis" Aunt Salma ta fad'a tana shafa kanta gamida ficewa.
Shirun ne dai ya qara ratsa wajen dan ba wanda ya q'ara ko tari cikinsu saima wani aiki daya tsira a laptop d'insa bayan ya saka suratul Ali imraan dan suratul baqrahn harta q'are.
Yana ganinta ta gefen ido sai faman lallanqwashewa take alamun zaman ya gundureta, Itakam Ayshaa ta d'au alq'awarin indai bashi ya fara tambayar ta abinda yake damunta ba bazata fara masa magana ba tunda shine likita shiya dace ya fara tambayar ta damuwarta.
Shima a nashi b'angaren hakanne indai bata fad'a masa damuwarta ba shikam bazai tambayeta ba dan yaga alamun yarinyar y'ar rainin hankali ce (Saif bakada gaskiya fa).
Wani dogon tsaki taja ta miq'e ta fice daga office d'in bayan ta jefa masa wata muguwar harara.
A hankali ya sauke idanunshi daga kanta bayan ta fice ya tsurawa table d'in gabanshi ido "wai yarinyar nan kuwa tasan wanda takewa tsaki? Kokuwa batasan yadda ya tsani tsaki bane? (Ina zata sani). ALLAH ya q'ara had'ashi da ita kuwa san tayi masa tsaki.
A reception ta samu Aunt Salma tana zaman jiranta, da sauri ta tashi ta tareta tana tambayar ta lafiya? Ganin yanayin yadda ta fito office d'in
"Wlhi Aunt mutumin nan mugun d'an rainin wayone" ta fad'a tare da hararar inda office d'in yake.
"Tunda dai ya dubaki ai shikenan naga alamun shi ai d'an jida kaine" Aunt Salma ta fad'a tare da jan hannunta, baki ta turo tace
"Nifa bai dubani ba, bai tambayeni abinda ke damuna ba nima kuma ban masa bayani ba
"Wato kowa yanaji da kanshi ko? idan shi bazaiyi magana ba ke bazakiyi ba?"
Baki ta tunzuro gaba tace
"Amma Aunt Salma shi...."dallah wuce muje malama", Aunt Salma ta katseta tana hararar ta.
Gaba tayi bakinta a d'ane tanajin tamkar ta koma ta gaggaya masa magana d'an rainin wayo kawai.
Da hanzari isah direba ya taso yana fad'in
"Kun fito Hajia?"
"Eh amma bata samu ganin Dr ba kaimu wani asibitin".
Aunt Salma ta bashi amsa tana shigewa motar batare data jira ya bud'e mataba.
Ayshaan ma shigar tayi shima ya zagaya cikin rawar jiki ya shiga ya tada motar suka fice daga cikin hospital d'in.
★★★
Bai q'ara duba kowaba ya had'a nashi ya nashi yabar asibitin yatafi gida.
Sallama yayi cikin wani qaton parlour dayasha q'awa kala kala na ababen more rayuwa.
Matashiyar budurwa ce y'ar kimanin 18yrs a zaune tana game a wayarta, kamarsu d'aya saidai ita tana da d'an duhun fata kad'an kuma yafita dogon hanci.
"Sannu da zuwa Yaya" ta fad'a bayan ta amsa sallamar tana cigaba da game d'inta dan tasan bama lallai ya amsaba.
A ciki ya amsa yana tambayar ta Mamie"
"Yanzu ta haura upstairs" tabashi amsa.
Kan cushion ya zube yana sauke numfashi, har ynxn tsakin da marar kunyar yarinyar nan tayi masa bai bar sukar ransa ba, yayi dana sanin barinta ta tafi batare daya d'au mataki a kanta na jiyake tamkar ya dawo da hannun agogo baya.
"A ah ikon ALLAH tunanin me Saifu yakene haka?"
Ya tsinkayi muryar Mamie tana masa magana, murmushi ya d'anyi yana shafa sumar kanshi mai laushi.
"Gajiya ko?" Ta tambayeshi tana murmushi.
"Gajiyar ma akwaita Mamie ga yunwa tun breakfast fa"
To kaje kayi wanka kafin Imaan takawo maka abincin".
Car key d'insa ya d'auka da manyan wayoyinshi guda biyu ya miq'e tsaye.
"Kaga daka aje iyali duk wad'annan abubuwan saidai kazo ka tarar da komi ready"
Mamie za'ayine fa ina lalubawa bansamu bane har ynx"
Baki ta ta6e tace
"Uhmm nagaji da gafara sa banga q'aho ba, ALLAH dai ya nunamin ranar da zanga matar Saifu inga wace kalace da tsawon shekaru ake lalubota"
Dariya Imaan tasaka tana toshe bakinta da hannunta, harara ya zabga mata tayi hanzariin daidaita fuskarta.
"Vry soon Mamie insha ALLAH" ya fad'i a hankali yana barin parlourn.
*DR. SAIF*
©Ummu Hanan
Bismillahir Rahmanir Raheem
Haske writer's associated
(Home of expert & perfect writer's)
Free page
No 2....
K'arfe 9:15 ya shigo parlourn gidan sanye yake cikin wasu riga da wando marasa nauyi farar riga da red color d'in wando,anja adon dogayen layika a gefe da gefen wandon da farin zare hular sanyi ce a kanshi mai laushi white an rubuta MY MAN agaban hular sai farin slipper dake sanye a k'afarshi mai taushin tsiya sai zuba daddad'an qamshi yake.
Kai tsaye upstairs ya nufa wajen Mamie yana stairs na farko yana shirin taka na biyu ya hango Daddy da Mamie zasu sauko downstairs da alamu rakiya tayo masa, da saurinsa ya juya zai fece kafin Daddyn ya hangoshi saidai ya makara dan daf dazai fice ya tsinkayi muryar Daddyn yana fad'in
"Karka sake ka fita ka makaro nariga na ganka"
Cak ya tsaya tare da runtse idanunshi yana dafe goshinshi q'asa q'asa ya furta
"Oh my gosh, dama bai fitaba?"
A sanyaye ya koma bakin stairs d'in ya tsaya tare da sunkuyar dakai.
"Barka da safia" ya fad'a bayan sun sauko har lokacin bai kallesu ba
"Barka dai uban y'an shiririta"Daddy ya fad'a yana kallonshi a kaikaice,ya d'ora da fad'in
"Wato Saifu idan ka sake ka shiga hannuna wllhy bazakaji da dad'i ba wato wasan b'uya ma ka fara dani ko, nagaji da nanata magana d'aya kusan shekara d'aya muna abu d'aya dakai, to anzo ga6ar da haqurina yazo karshe kaji na fad'a maka"
Kanshi a q'asa a hankali yace
"Ayi haquri insha ALLAH za'a duba"
"Okay bakama fara dubawar ba kenan?, rasa amsar bayarwa yayi still dai kanshi na q'asa sai faman susar k'eya yake.
Kai Daddy ya kad'a yace
"Good hakan yayi maka kyau" ya ka'rasa maganar tare da nufar k'ofar fita.
ALLAH ya kiyaye sukayi masa ya amsa tareda ficewa.
Marairaicewa yayi ya kalli Mamie zaiyi magana, bata kulashi ba ta nufi ainahin cikin parlourn kan cushion ta zauna, bin bayanta yayi ya zauna kusa da k'afafunta tareda kamo hannuwanta ya riq'e cikin nashi
"Dan ALLAH Mamie ku k'ara hakuri insha ALLAH nan bada jimawa ba komi zai zama labari".
"Ah to gara dai kayiwa kanka fad'a dai fisabilillahi ace kusan shekara d'aya muna magana d'aya dakai nagaji da gafara sa banga q'aho ba, ALLAH ya azurtaka da komi na rayuwa amma ajiye mace ya gagareka ga sadeeq nan da mahfooz (causin brothers d'insa) duk sunyi aure harda albarkar y'ay'a ga kuma Sameer nan k'aninka ne amma har ansa date d'in aurensa kai kana zaune wai ko bakada lafiya ne?"
Fuska ya b'ata sosai kamar zaiyi kuka yace
"Mamie please ki daina wannan maganar dan ALLAH".
Baki Mamie ta ta6e tace
"Ah ah to aida gaskiya ta, cikin y'an uwa ma ga y'an mata nan dayawa masu sonka ga yaran k'awayena da abokan Daddyn ka amma ka shafawa idonka toka kak'i saurararsu saboda ALLAH fa".
"Ni Mamie duk basu yimin ba wllhy".
Rank'washi Mamie ta sakar masa a kanshi tace
"Ai kaji matsalarka Abbana".
Wajen ya dafe da hannunshi kamar zaiyi kuka yace
" Da zafi fa Mamie"(uhm sai an fita ai tawa mutane muzurai).
Dariya Mamie ta d'anyi tana miq'ewa tsaye tace
"Bari in koma sama dan ALLAH ka daure dai babana a k'ok'arta a samo mana suruka".
Shima d'in tsayen ya miq'e yana fad'in
"Insha ALLAH Mamienah".
Daga nan ta haura upstairs shikuma ya shige part d'inshi.
WANENE SAIF???
Saifuddeen Sadeeq Matawalle wanda abokansa ke masa lak'abi da S.S Matawalle d'ane a gurin Alh Abubakar Sadeeq Matawalle babban d'an siyasane daya riq'e muq'amai da dama a cikin gwamnati inda daga baya yabar harkar ya komawa kasuwanci inda yake da manya manyan kamfanoni a fad'in Nigeria suna zaune a garin Abuja matarshi d'aya Hajia Hafsat babbar likitace a babban asibitin Abujan macece mai mutunci da kirki da sanin yakamata, yaransu uku kawai Aisha ce ta farko sai Saif data bawa kusan shekara takwas daga nan sai Zainab (imaan) data kasance y'ar auta inda tazararsu da Saif shekara goma dan har sun fitar da samun wata haihuwar kamar yadda suka fitar bayan haihuwar Aisha,cikin ikon ALLAH kuma aka samu cikinta.
Aisha tayi aure anan cikin garin Abujan tanada yara uku kauthar,hibbah,
*DR.SAIF*
©️Oum Hanan
Bismillahir Rahmanir Raheem
Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
Free page
No 3...
Aisha tana aure a nan cikin garin Abujan tanada yara uku kauthar hibbah sai d'an jaririn datake goyo areef.
Imaan tana shekarar ta tafarko a higher level.
Saif yayi gaba d'aya karatun shine a k'asar Egypt tun daga matakin secondary school har zuwa masters degree inda ya karanchi medicine dan tun yana k'aramin shi yake sha'awar irin aikin Mamien shi kodan ya taimakawa k'asarshi da y'an uwanshi musulmi, Daddyn shi yaso ya ya karanchi harkar zane amma ganin inda hankalinshi yafi karkata yasa ya k'yaleshi yabishi da addu'ar samun nasara, b'angaren ilmin addini ma ba laifi yana dashi dai dai gwargwado ya sauke Al'qur'ani mai girma da sauran littattafai tun kafin tafiyarshi Egypt.
Mutum ne shi mai k'wazo da jarumta a aikinshi da duk wani abu dayasa a gaba, hakan yasa bayan yasamu shaidar shi ta zama babban likita dactocin q'asar sukaso riq'eshi yayi aiki dasu shikuma ya k'ek'asa k'asa yak'i yarda dan acewarshi k'asarshi da mutanen cikinta yayiwa karatun shi, saidai yayi musu zaman 1yr kafin yadawo cikeda d'imbin nasarori da tarin yabo daga inda yabaro.
Tun kafin yadawo Daddy ya gina masa k'aton asibiti a matsayin gift d'inshi aka zuba ingantattun kayan aiki da k'wararrun ma'aikata.
Yana dawowa kuwa ya fara aiki, sosai asibitin ya samu karb'uwa gurin al'umma talaka da mai kud'i, talaka yana sonshi ne dan sauk'in asibitin dan basu tsawwala ba yayin da masu kud'i suke sonshi saboda kwarewar ma'aikatan asibitin.
Tun bayan dawowarshi da y'an y'an watanni Daddy ya tuntub'eshi da maganar aure, saiya kawo masa uzurin baisamu yarinyar datayi masa ba a lokacin.
Daddyn ya karb'i uzurin nashi bai takura masaba yace dai yayi k'ok'ari ya nemo wadda yakeso.
Tun daga lokacin Daddy da Mamie suka fara takura masa da maganar aure ganin bai k'ara tayar da maganar ba sam bai d'auki batun da wani muhimmanci ba, Mamie kam kullum addu'a take binshi da ita a cewarta taga kamar tsoron matan ma yake.
Miskili kafi mahaukaci ban haushi taken da kakarsa kemasa kenan Hajjah wadda ta haifi Daddyn shi, wataran suyi dad'i wataran arabu baram baram shida ita.
Ta bakin na Hajjahn kuwa Saif miskili ne na bada labari sosai magana kemasa wahala baida fara'a sam kullum fuskar nan tashi a cunkushe ko murmushi saita k'ure yakeyi tun Mamie namasa fad'a harta gaji ta daina danta lura abin a jininsa yake.
Imaan tana son taga ta sake da yayanta suna hira da wasa da dariya saidai ba damar hakan dan bata samu fuskaba shiyasa idan taje gidajen friends d'inta sai taita sha'awar su idan taga yadda suke sakewa da yayyinsu suna wasa da dariya saitaji dama itace gashi batada abokiyar hira saidai Mamie in Mamien bata nan kuwa saidai waya inta gaji tayi barci shiyasa bini bini tana gidan Aunt Aisha har gara yanzu data fara d'aukar lecture kullum tana busy karatun yakan d'auke mata hankali.
Mutum ne mai tsafta da son gayu kullum tsaf tsaf yana fitar da daddad'an qamshi.
Wannan kenan.
WACECE AYSHAA???
Ayshaa Thabit Mohammad d'iyace ga fitaccen d'an kasuwar nan Alh Thabit Mohammad, ba inda harkokin kasuwancin shi basu kaishi anan suka had'u da Alh Abubakar Sadeeq Matawalle suka k'ullah amintaka da juna saidai ba wanda yasan iyalin wani acikinsu, sai matan da suka had'a suke gaisawa ta waya yana zaune a garin kano da iyalanshi
Yaransu biyar duk mata ALLAH bai basu namiji ba.
Haleemah, Safiyyah, Salma, Fateemah sai Ayshaa y'ar auta, tagama secondary school d'inta inda kafin a samar mata jami'a tajewa Aunt Salma hutu dan suna d'asawa sosai da ita, duk sunyi aure, Haleemah da Safiyyah suna aure anan garin kano sai Fateemah dake aure a bauchi sai kuma Salma dake Abuja.
ALLAH ya azurtata da kyakkyawar sura da kyan diri komi dai Masha ALLAH.
Tanada surutu kuma matsiwaciya ce ammafa idan aka tab'ota.
★★★
Back to story...
"Aunt Salma kayan makeup d'ina fa sunyi k'asa wllhy" Ayshaa ta fad'a tana kallon Aunt Salma dake gyarawa Ikraam gashinta tanasa mata beats.
Harara Aunt Salman ta jefa mata tace
"Sai kace wata gwanar makeup d'in ko an siyo miki ma ai barinsu kike baki using dasu.
Shagwa6ewa tayi tace
"ALLAH Aunt Salma turarukana sunyi k'asa fa".
Shiru Aunt Salma tayi kafin tace
"ALLAH ya taimakeki akwai turarena daya k'are nakeso asiyomin inajin dad'in amfani dashi.
Tsaye ta miq'e tana fad'in
"Toh yaushe zanje inyi shopping d'in Aunt?".
"After asr sai isah ya kaiki", ta amsa mata.
"Yawwa my Auntynah" ta fad'a tare da bata peck a gefen kuncinta tare da nufar bedroom d'inta da d'an gudunta kamar wata karamar yarinya.
Da kallo kawai Aunt Salma tabita tayi murmushi gamida girgiza kai tana cigaba da abinda take.
★★
5:13pm ta fito parlourn sanye cikin arebian abayah blue black datasha adon manyan flowers whit color a gaban rigar tayi rolling da mayafin abayar kalar rigar, whit plat shoes tasaka da y'ar k'aramar purse riq'e a hannunta sai wayarta dake riq'e a d'aya hannun data d'aura bak'in agogo.
Farar powder kawai ta shafa a farar fuskarta sai whitlips da kwalli data zizara a idanunta wanda suka k'ara fito mata da kyakkyawar fuskar tata sai zuba kamshin humrah take.
Ganin Aunt Salman bata parlourn yasa kai tsaye ta nufi bedroom d'in Aunt'n, ta shiga da sallamarta, a gaban mirror ta sameta ta fito wanka tana shafa lotion, bakin gado ta zauna tace
"Aunt na shirya"
"Okay d'auko min purse d'ina a wardrobe"
D'aukowar tayi ta miq'a mata ta ciro kud'i tabata tare da nuna mata kwalbar turaren dazata siyo mata.
Sallama tayi mata ta fice.
Parking sukayi a bakin q'aton mall d'in kusa da wata bak'ar mota duk gilasanta tinted ne an bud'e k'ofar driver side mamallakin motar ya zuro k'afarshi d'aya waje sanye cikin bak'in covershoe kamar yadda wandonshi ya kasance bak'i sosai takalmin ya haska farar k'afar.
Ta gefen motar tazo ta wuce ta shiga cikin mall d'in.
Cosmetics side ta nufa ta fara duddubawa tana zab'ar wanda takeso tunawa tayi da saq'on turaren Aunt Salma data bata sanin halinta na mantuwa yasa ta fara duddubawa ko zata ganshi anan ganin bata samu anan ba yasa ta fara baza ido wasu wuraren, can ta hangoshi cikin tulin wasu turarukan wajen ta nufa idanunta akan turaren ba zato taji tayi karo da mutum purse d'inta ta fad'i k'asa shima wanda sukayi karon man gashin dake hannunshi ya sub'uce k'asa.
A tare suka sunkuya batare da sun kalli junaba shi yakai hannu kan purse d'in ita kuma takai kan sportin waves d'in dake kusa da ita suka d'ago a tare da niyyar bawa juna haquri idanunsu suka sarq'e cikin na junah...
Mrs Salees Mu'az.
*DR. SAIF*
©Oum Hanan
Bismillahir Rahmanir Raheem
Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
Free page
No 4...
Zaku biya kud'inku ta wannan account number d'in
0781515544 ibrahim sani Access Bank.
Sai kuyi screenshot na payment dinku ta wannan number
09133396869
Kokuma katin waya na MTN ta wannan number dake sama.
Masu son shiga grup sai suyimin magana ta number dake sama
200 kacal ba yawa.
Saina jiku
Baki bud'e kowa ke kallon wanda ke gabanshi tuni fuskar kowa ta canza, especially Saif da dama kullum fuskar a cunkushe take saiya k'ara murtuke ta sam ba alamun rahma a cikinta.
"Mutane saikace makafi, suna ganin mutum bazasu iya kaucewa ba". Ayshaa ta fad'a tana jan tsaki tare da warce purse d'inta dake hannunshi ta dangwarar da man gashin dake hannunta a q'asa ta miq'e da niyyar barin wajen.
Sosai ranshi ya b'aci idanunshi har sun fara kad'awa.
"Wani tsakin kuma dai again?".
Ya fad'a cikin ranshi tare da miq'ewa cikin wani irin zafin nama.
Ba zato taji an turata wani d'an corridor daba komi a wajen, bayanta ya bigi bangon wajen.
"Ochhh"ta fad'a a hankali tana runtse idanunta saboda azabar zafin daya ratsa k'ashin bayan nata ta saki purse d'in hannunta q'asa.
A zafafe yake tunkarota da wani irin taku cikin ranshi yana ayyana irin punishment d'in dazai bawa mara kunyar yarinyar.
Wani masifaffen tsoro ne ya ziyarci zuciyar Ayshaa gabanta banda fad'uwa ba abinda yake amma tak'i barin tsoron ya bayyana a kan fuskarta harda k'arfin halin jefa masa harara nan kuwa k'irjinta kamar ya faso ya fito saboda tsoronshi, innalillahi kawai take ambata saboda batasan irin hukuncin dazai yanke mata ba kuma da ganinshi ba imani zaiyi ba.
Daf dazai k'arasa wajenta zuciyarshi tagama ayyana masa irin hukuncin dazai yanke mata dan haka yana zuwa baiyi wata wataba yasa hannu ya fisgota da uban k'arfi ta fad'a k'irjinshi hannu yasa ya d'ago fuskarta ta k'arfin tsiya.
Ganin abinda yake shirin yi yasa gabanta yayi mummunan fad'uwa ta shiga kakkauda fuska tana k'ok'arin tureshi saidai ko gezau baiyiba tamkar wani dutse yabi duk ya cumimiyeta.
Ganin ba iya k'wacewa zatayi ba yasa ta datse bakinta b'am, ganin haka yasa yasaka lallausan hannunshi guda d'aya ya toshe mata hanci ta yadda bata da damar shaq'ar numfashi.
Tuni numfashin Ayshaa ya fara kaikawo bai samu hanyar fitaba ganin haka yasa dolenta ta bude bakinta tuni ya shigar da nashi bakin cikin nata(wuuuuu Saif dama irin hukuncin kenan).
Wani mulmulallen abune ya tsayawa Ayshaa a maq'ogoronta tsabar bak'in ciki.
Wani mahaukacin kiss ya shiga yimata tamkar zai cinye bakin gaba d'ayanshi kala kalar mugunta ya dinga yimata a cikin bakin, tun tana k'ok'arin tureshi harta sadaq'ar tai laq'was a k'irjinshi tana shan nau'ikan azaba a cikin baki.
Sai daya d'auki mintuna yana gana mata axaba sannan ya saketa ya k'ara turata baya yabar wajen cikin sassarfa.
Duk yadda taso riq'e kukanta hakan ya gagara nan ta sulale k'asa tasaki wani irin kuka mai cin rai wata tsanarshi na ratsata sosai abinda yayi mata yayi mugun tsaya mata a rai ashe banda wulak'anci har iskanci ya iya kenan?".
Sai data dad'e tana zaune tana sharb'ar kukanta, kuma har lokacin ko mutum d'aya bai gifta ta wajen ba.
Purse d'inta kawai ta d'auka batabi takan body spray guda biyu data fara d'auka ba ta fice tana share hawaye.
Duk yadda isah ya dinga tambayar ta abinda ya faru k'in tanka mata yayi har suka k'arasa gida ta fice da sauri har tana had'awa da d'an gudu ta shige gidan, da kallon mamaki isah ya bita yana mamakin abinda ya faru da ita yaga dai k'alau suka fita da ita kuma harta shiga store d'in baiga wani canji a fuskarta ba, to ALLAH kad'ai yasa meya sameta.
Kan cinyar Aunt Salma ta zube tana k'ara sakin wani kukan, d'agota Aunt Salma tayi a rikice tana tambayar ta da lafiya?"
K'in amsa ta tayi ta cigaba da kukanta , da k'yar Aunt Salma ta rarrasheta gabanta sai fad'uwa yake tana tunanin abinda yasamu y'ar k'anwar tata.
"Tell me little sis meya faru haka?". Aunt Salma ta fad'a tana k'ara share mata hawaye.
Sai dataja majina sannan tace
"Aunt wani ne mukayi karo dashi a mall d'in".
Sakin baki kawai Aunt Salma tayi tana kallon Ayshaan da mamakin tab'ararta.
Tsaki ta d'anyi kafin tace
"Amma kedai Ayshaa anyi shagwa6a66iya wllhy, yanzu dan kunyi karo da wani shine abin kuka dan tsabar shiririta?"
''Aunt zafi fa naji q'aton kai gareshi fa,tace tana turo baki.
Dariya Aunt Salma tayi tace
"Kodai ke kikeda raki?, Tab'arar autanci kawai ke aiki dake, ALLAH ya kyauta miki ni d'agani inje inyi aikin gabana.
Tashin tayi ta figi purse d'inta ta wuce bedroom d'inta.
Purse d'in ta jefa kan gado ta fige gyalen datayi rolling shima ta jefa kan bed tabi bayansu jagwaf ta kwanta ruf da ciki, ganota kawai take wannan mugun Dr'n yana kissing d'inta wani bak'in cikin na k'ara shigar ta, kamar wadda aka zabura ta tashi da sauri ta shige toilet bayan ta zame abayar jikinta.
Wanka tayi ta matsa maclain a brush ta fara dirzar bakinta.
Tsaye tayi gaban mirror'n toilet d'in tana kallon bakinta dayai wani irin jawur ya d'an d'aga kad'an
Hannu takai kan lips d'in tana shafawa a hankali saboda irin zafin dayake mata.
"ALLAH ya isana ban yafeba wllhy mugu kawai", ta k'arasa maganar tana share wasu hawayen dasuka taho mata.
Fitowa tayi ta nemi wata doguwar riga marar nauyi tasa ta kwanta saidai duk juyin dazatayi saita shaq'i mayen turarenshi mai sassanyan qamshi daya cika dakin nata wanda yake jikin doguwar rigar data cire duk yabi ya cika d'akin, saboda irin kokawar dasuka sha yasa rigar tasamu rabonta sosai.
A fusace ta diro daga gadon ta dauki rigar ta cumimiyeta ta jefa wardrobe (kamar ita tayi laifin).
Saidai kuma wata sabuwa inji y'an caca qamshin mouth fresh d'in daya fesa ya addabi bakinta duk da brush d'in datayi hakan baisa ta daina jin kamshin ba a bakinta.
"Maye kawai".
Ta furta hakan tana turo baki gamida lumshe ido tanason yin barchi...
Mrs Salees Mu'az.
*DR.SAIF*
©Oum Hanan
Bismillahir Rahmanir Raheem
Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
Last free page
No 5...
Ga mai buk'atar cigaban book d'in nan zai tura 200 ta wannan number asusun
0781515544
Screenshot na payment kuma ta wannan number
09133396869
Ko kuma katin waya na MTN 200 a wannan number dake sama.
Ga masu son shiga grup sai sumin magana duka dai ta wannan number.
Saina jiku.
Kai tsaye gida ya wuce ranshi a b'ace yarasa minene had'inshi da yarinyar, tsaki yaita faman jerawa har ya isa gidan.
Daga yadda ya dinga matsa horn d'in a zafafe ya tabbatarwa da baba maigadi ba lafiya,dan haka cikin rawar jiki ya bud'e gate d'in ya shiga da motar.
Hannu kawai ya d'aga masa lokacin dayake masa sannu da zuwa dukda dai dama bawani sakar musu yakeyi ba amma yana tsayawa suna d'an gaisawa sama sama yaukam ko saurararshi baiba ya wuce yanada tabbacin tab'oshi akayi daga waje.
Imaan kawai ya tarar a parlour tana duba handout.
"Sannu da zuwa Yaya", ta fad'a tana binshi da kallo.
Uffan baice mataba ya nufi side d'inshi. "ALLAH ya shirya matar mutumin nan ta shiga uku wllhy" ta fad'a q'asa q'asa tana tab'e baki.
"Ke kuma kedawa?" Mamie da saukowarta kenan taji tana magana k'asa k'asa.
Baki ta turo tace
Mamie nida Yah Saifu mana ya shigo ina masa sannu da zuwa ko kallon inda nake baiyiba bare ya tankamin".
Murmushi Mamie tayi tana d'an girgiza kai tace
"Oh Imaan inda sabo fa yaci ace kin saba da halin Abbana a gidan nan".
Kamar zatayi kuka tace
"ALLAH Mamie banajin dad'i ace niban isa in zauna da d'an uwana muyi hiraba yaji damuwata ba muyi shawara a tsakaninmu".
"Toh yazaki? Haka yayi shi sai haquri".
Tun kafin ya shiga bedroom d'in nashi ya cire suit d'in ya fara b'alle bottom d'in shirt d'in ta ciki yana shiga ya jefasu kan sofa ya zame wandon bayan ya cire takalmin ya rage dagashi sai boxer da singlet farare ya shige toilet.
Shower ya sakarwa kanshi ruwan sanyin ya shiga ratsashi, idanunshi a rufe yake hango kissing d'in dayayiwa yarinyar duk da yayine dan punishment d'inta hakan bai hanashi shiga wani irin yanayi ba a lokacin kasancewar hakan bai tab'a faruwa dashi ba a tsawon rayuwarshi.
Sai daya dad'e a cikin ruwan kafin yayi off yasaka bathrobe ya fito da dan k'aramin towel yana goge sumarshi.
Shima d'in sosai kayan jikinshi suka samu tsarabar humrahr Ayshaan mai d'an banzan qamshin dad'i dan haka tuni dakin ya dauka, tsaki yayi ya yayibi kayan ya jefa a wardrobe(irin yadda Ayshaa tayi).
"Mayyar yarinya kawai, mara kunya" yace yana wurgi da towel d'in, bathrobe d'in ya cire ya ciro jeans blue da da red shirt long sleeve yasa ya fesa zaunannen turarenshi.
Parlour ya fito wajen Mamie sai cika yake yana batsewa.
Duk dai tasaba ganinshi cukulen hakan bai hana ta tambayeshi lafiya ba?"
"Nothing Mamie".
Ya amsa mata tareda miq'ewa ya k'ara yimata sallama ya fice.
Gidan mutuniyar tasa ya nufa Hajjah, 2dys bai samu ya lek'ata ba.
A parlour ya sameta ta k'urawa k'atuwar plasma d'in dake jikin bango ido tana kallon sunnah TV taci medical glass, tsaf tsaf da ita kamar koyaushe taci atamfarta mai kyau da tsada ta kafa d'aurinsu irin na tsaffi sai tashin qamshin turaren wuta parlourn yake.
Ciki ciki yayi sallama ya shiga.
Itama d'in a ciki ta amsa sallamar tare da juyar dakai tana tab'e baki,(rabuwarsu ta k'arshe da fad'a suka rabu shiyasa baikoma ba kuma sai ranar).
Shima d'in kujera yasamu ya zauna bai mata magana ba(kamar dole).
Ganin yak'i yimata magana wajen mintuna takwas yasa ta
Had'e rai sosai ta kalli sashin dayake yanata latse latsen waya tace
"Tashi ka barmin gidana, miskilin banza miskilin wofi ka wani shigomin saq'am saq'am dakai ko magana bakaimin ba dogon banza kawai".
Dariyarshi yaita k'ok'arin had'iyewa dan indai tace masa dogon banzan nan to yakaita maq'ura.
Fuskarshi ya daidaita dan karma yayi dariyar yace
Kaji min tsohuwa,aiba gidanki bane", har lokacin kanshi na q'asa yana typing a wayarshi.
La'ilaha illallahu Muhammadan rasulullahi wato kace gori kazo yimin dama? To ai dad'in abin d'ana ne ya ginamin mara mutunci kawai".
Ganin yadda ta daddage tana ta fad'a yasa ya ajiye wayar yataso yadawo kusa da ita yana murmushi ya kamo hannuwanta yana fad'in
"Haba My dear Hajjahnah kefa wani lokacin bakisan wasa ba nifa wasa nake miki".
Kafin tace wani abu wata budurwa ta fito daga bedroom d'in Hajjahn tanada k'iba sosai kuma gajeriyace bata cika tsayiba.
Tuni y'ar fara'ar dake kan Saif ta b'ace saboda ganinta.
Itakam wani kyakkyawan murmushi tasaki tasaki ajiyar zuciya tana lumshe ido tare da bud'ewa a kanshi.
"Yah Saifu" ta ambata tana wani ma'qe murya tare da zama kusa dashi a hannun kujera.
"Ya kike?" Haka kawai ya fad'a tare da miq'ewa ya d'auki wayarshi ya fice ko sallama ma baiyiwa Hajjahn ba.
Baki sake duk suka bishi da kallo.
''ALLAH ya baka lafiya toh" Hajjah tace tana kyab'e baki, mutum saikace mai jinnu? Yanzun nan ka ganshi fuskar da d'an rahma anjima kuma ya tamketa tam toh ALLAH dai ya sauk'a".
D'an murmushi Safnah tayi dan tasan ganinta ne yasa ya fita.
ALLAH ya gani tana matuk'ar k'aunar Saif kuma tanaji cikin ranta zata iya komiye dan taga ta mallakeshi tun tana yarinyar ta ta taso da sonshi ta ginu ta rayu akan k'aunar shi kuma tanajin babu abinda zai mata katanga dashi.
Safnah d'iyar yayar Daddyn Saif ce suna zaune a garin kaduna tayi karatu har zuwa matakin degree daga nan tasamu aiki a gidan radio dayake ta karanci aikin jarida ne.
Y'ar gayu ce sosai akwai kuma d'aukan wanka, itace y'a ta biyu a gurin Hajia safina sai k'annenta uku mata biyu namiji d'aya.
Yanzu ma takanas ta d'auki hutu a gurin aikinta duk dan saboda Saif d'in.
''Hajjah zanzo inje can gidan Daddyn".
Safnah ta fad'a tana kallon Hajjah.
"Ai saiki ta zuwa dama ai nasan abinda yakawo ki garin nan shikuma wanda kike danshi baisan kinayi ba". Hajjah tace tana miq'ewa tsaye ta shige d'aki.
"Koma dai meye naji kuma nagani, zan kuma dauki duk wasu tarin k'alubale indai akan Yah Saifu ne".
Ta k'arasa maganar tana miq'ewa ta shiga d'akin datake sauka idan tazo.
★
Cikin y'an kwanakin sam Aunt Salma bata samun zama saboda bikin sister'n mijinta da za'ayi sai shirye shiryen biki sukeyi.
Yau alhamis ta kasance ranar kamu, ba yadda Aunt Salma batayi da Ayshaa ba akan ta shirya suje k'ememe tace ita bazata ba dataga zata matsa mata kuwa tace kanta ke ciwo,dolenta ta k'yaleta.
Ita kuwa Ayshaa hayaniyace kawai bataso shiyasa tak'i zuwan.
Haka Aunt Salma suka shirya itada Ikraam suka tafi suka barta ita kadai a gidan.
Wanka ta k'ara yi ta d'an murza mai sama sama ta bud'e wardrobe da niyyar d'aukar kaya idanunta suka sauka kan doguwar rigar data saka ranar dataje shopping, siririn tsaki taja tare da janyo rigar taji waiko har yanzun akwai k'amshin turaren ajiki, aikuwa tana kaita wajen hancinta taji k'amshin ya bugeta.
"Da k'yar idan mutumin nan ba maye bane" ta k'arasa maganar tana sakin wani tsakin gami da wurga rigar inda ta d'auko ta d'auki wata armless pich color tasa tasaka hula tabi gab'ob'inta da body spray ta k'ara kwanciya tare da janyo wayarta ta kira Ammi sukasha hirarsu.
Imaan ce da Safnah zaune a parlour suna hira.
Cikin takunshi na nutsuwa da mazantaka ta k'akk'arfan namiji majiyin k'arfi ya shigo main parlour din.
Sanye yake cikin 3qtr na farin wando da green d'in riga mai yankakken hannu k'aramin towel ne rataye a kafad'arshi hannunshi riq'e da ruwan Swan k'aramar roba sai d'ayan hannun dayake amsa waya, ga dukkan alamu dai daga gym yake dan har lokacin da ragowar gumi a fuskarshi duk daya goge.
Sallama kawai yayi a ciki dan ba wanda yaji sallamar ma.
Bai kalli ko sashin dasuke ba ya wuce.
Safnah da tunda ya shigo parlourn idanunta suke kanshi tamkar zasu fad'o tsabar kallo, gaskiya ne tasan idan tayi gamdakatar da mallakar Saif tasan ta tserewa sa'a namijine d'aya da d'aya a hakan ji take tamkar ta tashi ta rungumeshi taji d'umin jikinshi ta shaq'i mayen turarenshi dayake sakata cikin wani mood mai wuyar fassara, tasan kuma hakan bamai yiwuwa bane dan ko hannunshi tayi gigin tab'awa to ranar ta bani da masifarshi da bala'i dan akwai ranar datayi hugging d'inshi ranar har marinta saida yayi shiyasa nesa nesa dai.
Imaan dama tunda ta d'ago ta kalleshi ta maida kanta k'asa ta cigaba da chatting d'inta.
Wajen TV stand ya tsaya ya d'ora robar ruwan akai yana cigaba da wayarshi da sam ba'a jin miyake cewa.
Tuni Imaan ta tashi tabar parlourn Safnah data k'urawa bayanshi ido ta kasa jurewa a hankali ta tashi ta nufeshi ta zare towel d'in gabanta sai fad'uwa yake.
Kamar daga sama yaji kamar ana tab'a gefen fuskarshi, juyowa yayi yaga waye yayi arba da Safnah hankalinta gaba d'aya yana kan lallausan sajenshi, towel d'in ya warce yana binta da wani irin mugun kallo tuni jikinta ya fara rawa.
"I will call you later" ya fad'a da sauri yana katse wayar.
"Mahaukaciyar inace ke? Ban hanaki tab'amin jiki ba? Idan kika kuskura hakan ta k'ara faruwa zan baki mamaki", ya ka'rasa maganar yana nunata da d'an yatsansa yabar wajen a fusace.
K'walla ce takawo idanunta tasa bayan hannunta ta share.
"Bazata gajiya ba, da haka har zuwa lokacin da hak'anta zai cimma ruwa.
Friday.
Ranar ake dinner d'in farida k'anwar Kabeer mijin Aunt Salma.
Da farko nok'ewa tasoyi dan batayi niyyar zuwa ba Aunt Salma tace sam bata isaba dolenta taje.
Haka nan badan ranta yasoba ta shirya cikin lace silver color da adon golden na flowers da aka mammana duwatsu doguwar riga mai rafa daga k'asa ta bud'e sosai saman kuma ya tsuke sosai rigar tayi mata kyau ta fitar da shape d'inta, ture kaga tsiya kawai tayi da d'ankwalin lace d'in ta yafa k'aramin Vail silver ta d'aura silver agogo sai jewelry d'in datayi amfani dasu duk silver ne, kyau kam tayishi Masha ALLAH duk da bawata kwalliya a fuskar powder ce kawai da lipstick da kwalli kamar yadda ta saba, tamkar ka sace ka fece sai zabga k'amshi take wayarta kawai ta d'auka ta zura plat shoes ta fito.
Gidansu Kabeer d'in suka nufa daga can zasu wuce Hall d'in da ake dinner.
Sai wajen 7:45pm sannan aka fara tattafiya dan har taso ta koma gida wai tafasa zuwa saida Aunt Salma tayi mata jan ido sannan ta haqura.
Hall d'in cike yake da mutane tako ina.
Amarya tasha kyau sosai itada angonta.
Nan aka fara gabatar da dinner.
Gaba d'aya zaman wajen gundurar Ayshaa yayi taita sakin k'ananun tsaki tana yamutsa fuska, duk yadda taso tafiya kuma Aunt Salma ta hanata dole sai lokacin da aka tashi.
Sai wajen k'arfe 11:22pm sannan aka tashi.
Ganin Aunt Salma ta tsaya wajen wasu friends d'inta yasa tayi gaba dan tagaji da tsayuwar.
A hankali cikin nutsuwa take takawa ta shiga duddubawa amma bataga motar gidan ba, kiran Aunt Salma tayi ta fad'a mata tace ta fita daga can waje isahn bai shigo cikin Hall d'in ba.
Takawa ta farayi a hankali kamar wadda ke tsoron taka k'asa.
Tana tafe tana masifa ita kad'ai cikin ranta na abinda yasa isahn bai shigo cikiba dan tafiyar akwai d'an tazara kafin a fita waje kasancewar babban hall ne.
Wani santsi ne taji ya kwasheta da batasan ko meyeba, ido ta runtse sosai tana kiran sunayen UBANGIJI gashi babu d'an abinda zata kama ta riq'e, gaba d'aya ta gama sakankancewa sai takai q'asa amma saita tsinci kanta bisa wani faffad'an k'irji.
"Alhmdllh" ta furta can k'asan ranta jin batakai ga k'asan ba, amma kuma waye haka ya tareta? K'amshin turaren jikinsu ne ya had'u a lokacin ya bada wani kalar qamshi mai masifar dad'i.
Yana ganin ta gama daidaita ta yadda koya saketa bazata fad'i ba ya tureta daga k'irjinshi.
A hankali murya q'asa q'asa tamkar mai rad'a yace
"Nonsense"
Kamar walk'iya yabar wajen, sai qamshin turarenshi dayabar mata.
"Nonsense?" Ta k'ara maimaita kalmar cikin al'ajabi, kaji wani d'an rainin hankali wayace ya taimaketa? Zaizo yana fad'a mata magana, sosai kanta ya kulle jin irin k'amshin turaren wannan mugun Dr'n to kodai shine? Ta jefawa kanta tambayar, "No impossible mezai kawoshi gurin nan?, Mutum da garinsu kice maizai kawoshi?
Koma dai meye damuwarshi ce ba tata ba sai data d'an jima a wajen tana ta kallon hanyar dayabi kamar zata k'ara ganinshi sannan ta tafi...
Mrs Salees Mu'az
*DR.SAIF*
©Oum Hanan
Bismillahir Rahmanir Raheem
Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
Ga masu buk'atar cigaban wannan book d'in zasu tura 200 ta wannan account number
0781515544
Ibrahim sani Access Bank.
Shaidar biyanki ta wannan number
09133396869
Ko kuma katin waya na MTN ta wannan number dake sama
Ga masu son shiga grup sai suyimin magana duka ta wannan number dake a sama.
.
No 6...
★
Suna komawa toilet ta shiga tayi wanka kota warware gajiya dan tib'is take jinta.
Tana fitowa ta zura dress night riga da wando light purple ta kwanta.
Asubah tagari
Mutuniyar Saif.
★★★
K'arfe bakwai da y'an mintuna ya fito cikin shirin fita.
Yau shigar hausawa yayi maroon d'in shadda gezner sai maik'o take da k'yalli, ya kafa hula zannah kalar shaddar wrist d'inshi d'aure da bak'in agogo na fata daya haska farin hannunshi sai bak'in takalmi half cover da yasaka sosai yayi kyau kayan sunyi matuk'ar amsarshi kasancewar bai cika mu'amala da manyan kayaba shiyasa duk lokacin dayasa yakeyin kyau sosai.
Safnah kawai ya tarar a parlourn kamar mayyah sarai kuma yasan dalilin zaman nata saboda dashine.
"Wow wow" kalmar data dinga ambata kenan cikin ranta lokacin data ganshi ba k'aramin tafiya da imaninta yayi ba taji tamkar taje gareshi.
"Good morning Yah Saif" tace cikin kashe murya tana wani fari da idanuwa.
Baima kalleta ba bare yasan anayi
"Morning" kawai yace mata ya stairs jin kamar ta biyoshi yasa ya juya ya zabga mata harara tare da cewa
"Ina zaki?"
Dabarbancewa tayi ta rasa abinda zatace masa karshe dai tace
"Zanje gaida Mamie ne Yah Saif"
"Meyasa tun d'azu bakije ba? C'mon friend b'acemin dagani".
Juyawa tayi kamar zatayi kuka ta koma parlourn ta zauna.
Tsaki yaja ya cigaba da taka stairs d'in cikin nutsuwa.
Knocking yayi a k'ofar bedroom d'in Mamie'n ta bashi iznin shiga.
A hankali ya murd'a handle d'in k'ofar ya shiga, a zaune ya sameta kan sofa tana karanta hisnul muslim har k'asa ya durk'usa ya gaisheta ta amsa tareda yimasa addu'a kamar yadda ta saba.
Sallama yayi mata tabishi da fatan nasara a aikinshi.
Har yakai bakin k'ofa tayi kiranshi ya dawo, littafin ta ajiye tare da maida dukkan hankalinta kanshi tace
"Babana ina maganar mu ta kwana ne, har yanzu banji ka k'ara cewa komiba?"
Kai ya sunkuyar tare da sa hannu ya turo hular gaban goshi ya shiga shafa k'eya.
"Ahmm Mamie, d'agowa yayi ya kalleta yaga yadda ta tsura masa ido saiya kasa cigaba da maganar dama kuma ba abin fad'ar.
Kai ta kad'a tace
"Alamu sun nuna har yanzu bakayi wani motsi bako?"
"Ai Mamie....''dakatamin ai me?" Mamien ta katseshi
"Munyi waya da Daddynku d'azun nan(yayi tafiya ne Mexico), yabani saq'o in fad'a maka kafin yadawo ka tabbatar kana da abinda zaka fad'a masa in kuma ba hakaba shi yana da abinda zai fad'a maka".
"Mamie saura fa one week yadawo for God sake taya zan nemi mata cikin sati d'aya" yayi maganar kamar mai shirin kuka.
"Kaci gidanku" Mamie data rasa abin fad'a dan takaici ta sakar masa dak'uwa
"Inace fin shekara muna fama dakai?,to nidai y'ar saq'o ce kuma na isar tashi kaje ALLAH ya kiyaye".
Da "Aameen" ya amsa ya tashi ya fita.
Har lokacin Safnah na parlourn, tana ganinshi kuwa ta miq'e
"Yah Saifu" tamkar kurma haka ya wuceta ya fita daga parlourn.
K'ugu ta kama da duka hannayenta tana kad'a kai kamar k'adangaruwa lallai taga alamun saita tashi tsaye a kanshi yanada taurin kai dana zuciya wannan abinda take bazai kaita ko inaba zata tafi amma zata dawo da shirinta dolene ta mallaki Saif a matsayin mijinta.
Yana shirin tashi daga aiki Mukhtar yayi sallama office d'in ya shigo.
Mukhtar abokinsa ne da suka had'u a Egypt lokacin dayaje karatu, tun dai baya kulashi harya fara biyawa ta kanshi saboda ganin yanada hankali kuma yanayin abinda yakaishi q'asar, sosai suka qulla abokantaka kuma akayi sa'a shima d'an Abuja ne shikuma engineering ya karanta, yanada surutu sosai abinda ke had'asu fad'a kenan da Saif idan ya isheshi da magana shima bashida auren yanadai niyyah.
"Mr Man harka tashi kenan?"
"Eh" kawai yace masa yana cigaba da zura laptop d'inshi a jaka.
"Muje kawai to ka saukeni"
"Saboda kai bakada motar ne ko yaya?"
"Wllhy yanzun nan nataho da ita ta lalacemin a hanya na kira bakanike za'a gyara".
Tafe suke a motar Mukhtar duk ya cika Saif da surutu yana bashi labarin yarinyar dayake so
"Oh my God Mukhtar wllhy ka isheni kaina harya fara ciwo" Saif ya fad'a yana dafe goshinshi.
Dariya Mukhtar ya d'anyi yace
"Wai dan ALLAH kai sai yaushe zaka fito mana da girlfriend ne musha biki?"
Tsaki Saif yayi yace
"D'an iska maganar ka kenan dama ta aure gara ma dai kayi mu huta ".
"Toh kaiya gani mr man? Aure ai abin sone''.
Shiru Saif ya d'anyi tunawa da yayi da abinda Mamie tace Daddy yace a fad'a masa.
"Yadai?"
Mukhtar yayi tambayar yana kallonshi.
K'aramin tsaki ya saki ya d'an shafi gefen girarshi yace
"Yanzu haka fa case d'in da muke da maigida(Daddy) kenan ya uzzuramin da maganar aure wllhy d'azu Mamie tacemin yace kafin yadawo in tabbatar nasamu yarinyar danake so inba hakaba shi yanada wadda zai had'ani''
"Das vry good, Daddy ya burgeni sosai fa" Mukhtar yace yana dariya.
Harara saif ya jefa masa bai daice komiba ya cigaba da tuk'inshi.
"Haba mutum yana fama da cuta yayi aure ya huta yak'i, gara suyi maka hakan ai''.
"Cutar uban me nake da ita?''
Saif yace yana masa wani irin kallo.
Dariyar shak'iyanci Mukhtar ya saki yace
"Man mubar maganar nan kawai amma nina sani kanada buk'atar mace a kusa dakai''.
"Nina fad'a maka haka munafuki?"
''Baka fad'a ba amma nina sani ai sau nawa ina kamaka kana shan lemon....bugu ya kaiwa bakinshi yai saurin kaucewa yana dariya.
K'wafa yayi yace
"Zanci ubanka ne vry soon wllhy".
Shidai Mukhtar dariya kawai yake masa.
★★★
7dys After.
Week end ne ranar dan haka har wajen tara da rabi yana barci.
Ringtone d'in wayarshi dake kan bed side drawer ne ya katse masa barcin, hannu yasa ya janyo wayar yana sakin d'an tsaki.
Tuni ya wartsake sosai ganin sunan Dad dake yawo saman screen d'in, kwananshi d'aya da dawowa kenan kuma yasan maganar da za'ayi masa.
A sanyaye ya tashi ya zura ash color d'in jallabiyyah saman boxer'n dake jikinshi ya zura slipper white ya d'auki wayarshi ya fita.
Suna zaune a parlour suna jiranshi, tun dayaga Daddy ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya yana girgizasu yasan ba za'a raga masaba danko sallamarshi sai Mamie ce ta amsa.
Kusa da k'afafun Daddyn ya zauna yana satar kallon Daddyn gaba d'aya ya gama tsarguwa.
"Barkanku da safiya", yace kanshi a q'asa.
Ba wanda ya amsa sai sunanshi da Daddyn ya kira.
A hankali ya amsa tareda d'agowa ya kalleshi.
"Yanzu Saifu ka kyautawa kanka ka kyauta mana kenan?''
Yawu ya had'iya ya k'ara k'asa dakai yace
"Daddy kayi hakur...."stop" Daddy ya katseshi a zafafe, lallai yasan daddy yakai maqura.
"Ina tarbiyyah da ilmin addinin da muka baka? Banyi zaton haka daga gareka ba Saifu.
Sosai kan Saif ya kulle dajin maganganun Daddy sunsha bambam da maganar auren dayake masa kafin yagama tunanin yaji abinda yasa kanshi yayi wani irin mugun sarawa
"Wace yarinyace aka ganku da ita a shopping mall kana kissing d'inta???"
A razane ya d'ago ya zubawa Daddy idanunshi yanajin wata irin fargaba da fad'uwar gaba.
Kan Mamie ya maida idanunshi itama yaga fuskar nan tata a had'e ba alamun fara'a.
"Innalillahi wa inna ilaihi rajioun" ya ambata cikin ranshi yana dafe goshinshi saboda irin sarawar da kanshi keyi.
"Tambayar kafa nakeyi Saifu" muryar Daddyn ta katseshi daga duniyar rud'anin daya tafi.
"Muna jinka"
Mamie tace a hasale.
Sam saiya rasa abinda zai fad'ar gaba d'aya kanshi ya kulle da wannan lamarin.
"Okay tunda bakada abin fad'a ni ina dashi, inaso ka bud'e kunnenka sosai kajini wannan yarinyar da aka ganku tare zansa a bincikomin gidansu zamuje muyi magana dole zaka aureta dan bazaka b'ata mata rayuwa a banza ba kuma cikin 2months nakeso ayi komi a gama understand?"
Cikin kid'ima ya bud'e baki yace
"Wllhy Daddy abinda kake zat....."banason wani dogon magana dole ayi abinda nace ka riga da ka b'ata min suna hankalinka ya kwanta" daga haka ya tashi ya fice gaba d'aya daga gidan.
Wajen Mamie ya rarrafa ya kamo hannuwanta ya zuba mata idanunshi da suka sauya launi lokaci d'aya girgiza mata kai ya shiga yi yarasa mema zai fad'a mata.
"Wllhy kabani kunya Saifu yaushe kazama haka?"
"Wllhy Mamie kinji na rantse miki sam abinda kuke zato bashi bane kun bani tarbiyyah mai kyau taya zan aikata abinda kuke zargi a kaina, ko a lokacin danayi zaman k'asar waje ban aikata wannan mummunar d'abi'ar ba bare yanzu dana dawo gida gaban idanunku Mamie please kiyi tunani fa" ya k'arasa fad'a yana k'ara damk'e hannunta sosai jijiyoyin kanshi duk sun tashi rad'a rad'a.
"Toh idan ba haka bane yane Saifu?, Tabbas ance an ganka da yarinya a shopping mall".
"Mamie nifa...."kayi kissing d'inta ko bakayi ba?" Mamie ta katseshi, bai saba yiwa Mamie k'arya ba hakan yasa duk ya dabarbance.
"Mamie punishment d'inta fa nayi bawai da wani niyyah nayi ba''.
"Punishment kamar yaya?" Mamie ta tambaya.
"Mamie yarinyar ne batada kunya an tab'a kaita hospital d'ina in dubata tayimin tsaki kuma muka had'u a Mall nan ma tayimin tsakin kuma Mamie kinsan banason ana min tsaki shine nikuma nayi.....shiru yayi ya kasa k'arasawa sai sosa kai yake.
Harara ta zabga masa tace
"Shine da sakarci da wauta kayi kissing d'inta? Haka ake horon?.
Baki ya d'an turo yace
"Ni Mamie narasa me zanyi mata ne".
Tsaki tayi tace
''Toh kajawa kanka ai''.
Dan ALLAH kiyi wani abu akai Mamie please help me".
Kai ta girgiza tace
''Karma kasani a ciki kasani sarai idan yayi magana baya canjawa dan haka kayi addu'a kawai ALLAH yasa hakan yazama alkhairi".
Ji yayi tamkar ya d'ora hannu bisa kanshi yayita ihu ko zasu fahimci halin dayake ciki.
A nan ta tashi ta barshi yanata saq'e saq'en zuci, zaici uwar yarinyar nan kuwa.
Mrs Salees Mu'az
*DR. SAIF*
©Oum Hanan
Bismillahir Rahmanir Raheem
Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
Ga masu buk'atar cigaban wannan book d'in zasu tura 200 ta wannan account number d'in
0781515544
Ibrahim sani Access Bank
Shaidar biyanki ta wannan number
09133396869
Ko kuma katin waya na MTN ta wannan number dake sama
Ga masu son shiga grup sai suyimin magana duka dai akan wannan number dake sama nagode
Ku garzayo ku samu naku koda kudinka saida rabonka♀️♀️♀️♀️.
No 7...
Ya dad'e nan zaune yana faman tufka da warwara kafin ALLAH ya bashi ikon tashi jiki ba k'wari ya nufi side d'inshi.
Kan sofa ya zube yana sauke wani nannauyan numfashi komi ya gama kwance masa, wai taya hakan ta kasance bayan yasan lokacin da abin ya faru babu kowa a wajen(Taya zaka sani dama ka hau gajimare).
Kacokam ya d'ora laifin kan yarinyar dan dabata yimasa rashin kunya ba bazai san ma da itaba bare yayi mata abinda bai dace ba gashi yanzu ta taro masa match gurin Daddy, taya ma zai iya duban wannan y'ar yarinyar a matsayin matar aurenshi? Tsaki yayi ta faman saki shi kad'ai ya rasa mafita kan al'amarin.
Hannu yasa ya janyo wayarshi da tun shigowarshi ya jefata kan bed ya shiga lalubo number Mukhtar.
Bata jima tana ringing ba yayi picking.
"S Matawalle how far?"
Bai amsashi ba sai tambayarshi dayayi yana ina?
"Ka ganni nan ta wajen unguwar ku Baba ya aikoni kawo saq'o wajen wani juyawa ma zanyi yanzu" Mukhtar ya bashi amsa.
"Okay please kazo gida ka sameni yanzu inason ganinka".
"Lafiya dai?"
"Sai kazo d'in dai kawai ina jiranka".
"OK am coming", Mukhtar ya fad'a sukayi hang up d'in wayar a tare.
Ba'a d'au wani lokaci ba danko tashi daga inda yake baiyiba yaji muryar Mukhtar d'in suna gaisawa da Mamie.
Sallama yayi ya shigo bedroom d'in ya zauna bakin gado yana kallon Saif d'in.
"My friend what's wrong with u, me yake faruwa ne?"
Mukhtar ya tambaya idanunshi akan Saif.
Tasowa yayi daga jinginar dayayi da bayan kujerar yace
"Mukhtar akwai matsala fa".
"Uhum"
Mukhtar yace yana neman k'arin bayani.
A tak'aice yabashi labarin yarinyar had'uwarsu ta farko a hospital d'inshi da second had'uwarsu a shopping mall da kuma irin hukuncin dayayi mata, ya gangaro kan maganar da Daddy yayi masa d'azu da kuma hukuncin daya yanke akai.
Dariya Mukhtar ya saki sosai harda dukan gefen inda yake zaune.
Baki sake Saif yake kallonshi wani mugun haushi da takaici suka lullub'eshi.
A fusace yace
"Kaifa mugun d'an iska ne Mukhtar yazan kiraka inyi sharing problem d'ina dakai ka kama yimin dariya mahaukacine ni?" Ya k'arasa maganar yana nuna k'irjinshi da hannunshi.
Cikin dariyar Mukhtar ya shiga girgiza kai yace
"Wllhy dariya kabani S Matawalle ya daga yarinya tayi maka tsaki ka hau baiwar ALLAH da kiss? Tsabar dama a kusa kake karasa punishment d'in bata sai kissing, kaga malam kawai kayi aure ka huta wani shan lemon tsami da kissing duk bazai kaika ba malam".
Wani haushi ne ya turnuk'e Saif ganin irin fassarar da Mukhtar yayi masa tamkar ya tashi yayi ta jibgarsa.
A zafafe yace
"Dan ubanka ce maka akayi da wata niyyar nayi hakan? Wllhy zan maka rashin mutunci kasan halina sarai banza mahaukaci" ya k'arasa fad'a yana komawa ya kwanta a bayan kujerar.
"Niko nasan bakada mutunci Matawalle''.
Mukhtar d'in ya fad'a har yanzu da ragowar dariyar akan fuskarshi.
K'wafa kawai Saif ya saki yana jijjiga kai dan ya kaishi karshe.
Tasowa Mukhtar yayi ya dawo kan hannun kujerar da Saif d'in yake zaune ya zauna ya bugi kafad'arshi yace
"Dallah malam wasa nake maka fa".
Bai tanka shiba sai jijjiga k'afa yake fuskar nan tamau dama ba fara'a ba.
"Yanzu ya kakeso ayi?" Mukhtar ya tambaya.
Banza yayi masa baice komiba.
Da k'yar Mukhtar ya shawo kanshi yace
"Shawara zaka bani yadda zan gujewa wannan abinda Daddy yakeson lik'amin".
"OK ga shawara".
A dak'ile yace
"Ina jinka".
"Me zai hana idan kaje wajen yarinyar dan nasan dole su Daddy zasu nemi dakaje ku gana da ita kaja mata dogon warning kan karta sake ayi auren koya kace?"
"I will try" yace a tak'aice.
Wata dariyar Mukhtar ya k'ara saki yana toshe bakinshi.
"Mtssww, banza baka da aikin yine". Saif ya fad'a tare da tashi ya cire jallabiyyahr jikinshi ya shige toilet.
★★★
Daddy ne a zaune a office d'inshi yana rubuce rubuce a wasu takardu.
Wayarshi dake kan table d'in gabanshi ta fara neman agaji, hannu yasa ya d'auko ta ya duba sunan mai kiran sannan yayi picking ya kara a kunne tare dayin sallama.
"Barka da war haka yallab'ai" aka fad'a a d'aya b'angaren.
"Barkan kadai Mustapha ina fatan ansamu gamsasshen bayani akanta?" Daddyn ya fad'a.
"K'warai kuwa yallab'ai".
"Ina jinka" Daddy ya buk'ata.
"Yallab'ai ita yarinyar ma asalinta ba y'ar nan bace daga kano take tazo gidan yayarta ne mijin yayar ma'aikacin banki ne amma wanda ya bani bayanin yace wai y'ar gidan Alh Thabit Mohammad ce a kanon".
"Alh Thabit Mohammad? Daddy ya maimaita sunan cikeda mamaki.
"Eh yallab'ai haka akace".
Tuni fuskar Daddy ta washe da farin ciki da murna.
"Masha ALLAH kawai yake nanatawa.
"Shikenan Mustapha zan nemeka akwai special gift dazan baka naji dad'in labarin nan sosai".
Godiya wanda aka kira Mustapha yayita zubawa cikin farin ciki.
"Alhmdllh d'iyar Amini nace ma ashe insha ALLAH Saifu bashida wata mata sai ita.
★
Da dare.
Mamie ce zaune kusa da Daddy taci kwalliya cikin had'add'en lace mai adon duwatsu blue color.
Daddyn ta kalla dayake ta aiki a system tace
"Nikam Daddy (itama haka take cemasa).
Akwai maganar danakeso muyi"
"Uhmm ina jinki" yace yana rufe system d'in ya matsar da ita gefe.
Zamanta ta gyara tace
"Maganar Saifu ce da kuma hukuncin daka yanke d'azu kace dole ya auri yarinyar da aka gansu tare kana ganin hakan zai yiwu kuwa ya fad'a min komi baisan taba ba kuma soyayya suke bafa taya za'ayi aure a haka saboda ALLAH''.
Dariyar su ta manya ya d'anyi yace
"Mamien yara dama ina shirin fad'a miki fa y'ar gidan Alh Thabit cefa yarinyar nasa anmin bincike kinsan dama kuma ya fad'a min yanada d'iya a Abuja to tazo gurintane ALLAH ya had'asu dashi kinga yanzu bawani kace nace dolenshi ya aureta matsawar dai batada tsayayye dan naga alamun idan bahaka mukayi masa ba banga ranar dazaizo yace ga yarinyar dayake so ba".
"Alhmdllh gaskiya naji dad'in wannan maganar ALLAH ubangiji yasa alkhairi insha ALLAHU ma batada tsayayye''. Mamie ta fad'a cikin murna alamu sun nuna tayi farin ciki sosai da maganar.
★
Nan da nan Daddy yasa aka nemo masa Kabeer sukayi magana, shima Kabeer d'in yayi farin ciki q'warai hakama Aunt Salma dayake fad'a mata.
Daddy ya kira Abba babansu Ayshaa yayi masa bayanin komi shima d'in dai murnar yayi tare dasa albarka, nan da nan kowa yasan da maganar yayin da a gefe d'aya kuma Saif da Ayshaa basu san wainar da ake soyawa ba shi Saif ma duk zatonshi Daddy ya haqura da zancen dayaga bai k'ara yimasa maganar ba shima saiya basar ta cigaba da harkokin shi kawai.
Kabeer ne da Aunt Salma suka samu Ayshaa da maganar, kuka tasaka musu akan ita batason aure karatu zatayi, da k'yar suka lallab'ata ta hak'ura amma duk da haka cikin ranta bawai ta hak'uran bane wane ma irin aure za'ayi mata tana y'ar yarinyar ta da ita, tun kafin taga ko wanene akeson lak'aba mata taji sam bai mataba, tasan dabarar dazatayi rashin mutunci zata kafta masa dolenshi ya fasa dan ita bata shirya aure yanzu ba.
★★
Yana shirin shigewa side d'inshi bayan dawowarsu masjeed sallahr asbah shida Daddy, Daddyn ya kirashi.
Dawowa yayi ya d'an rissina yana sauraron Daddyn.
"Am anjima ka shirya kaje gidan su yarinyar nan ku gaisa zan tura maka address d'in gidan
"Dad ban gane yarinyar dakake magana ba" yace kanshi a q'asa yana shafa k'eya.
"Eh ai bazaka saniba tunda a tunaninka na manta da maganar, to tana raina kuma nasa an bincika min a tak'aice dai d'iyar babanka na kano ce"
Da sauri ya kalli Dad yana mamaki.
"Q'warai kuwa dan haka kasa a ranka idan kaga ba'ayi auren nan ba to dama can ALLAH baiyi matarka bace ka fahimta?".
Kai kawai ya d'aga masa bai iya cewa komiba.
Anan Daddy yabarshi tsaye cikin tunani.
★★
Tun bayan breakfast data koma bata k'ara tashi ba sai daf da sallahr zuhr dan wasu masallatan ma har sun fara tayarwa.
Toilet ta shiga tayi wanka da brush ta fito, sama sama ta shafa cream saboda zafin da garin yafara d'auka, doguwar rigar material tasa mara nauyi ta fesa turare, k'aramin gyale ta d'aura a kanta kasancewar a off take yasa ta zura slipper ta fice.
Kai tsaye kitchen ta nufa dan tun kafin ta fito k'amshi ya cika mata hancinta.
Aiki tasamu Aunt Salma da mariya mai aikinta suna tayi su d'ora wannan su sauke wancan.
"Naga alamun yau manyan bak'i garemu a gidan Aunt irin wannan delicious food haka?" Tace tana zama akan wani high stool dake kitchen d'in.
"Babba ma kuwa bak'on" Aunt Salma ta amsa mata.
Hannu takai kan wani plate da aka zuba wani lafiyayyen meatpie akai takai baki ta gutsura ta fara taunawa ido ta lumshe tace
"Wow yummy, Aunt abokin uncle Kabeer ne zaizo?"
"No wajenki dai zaizo" Aunt Salma ta bata amsa.
Tuni ta had'e fuska ta dangwarar da sauran meatpie d'in data gutsura akan plate d'in ta tashi ta fice tana turo baki.
"Zakici k'aniyarki ne" Aunt Salma tace ta juya ta cigaba da aikinta.
Murmushi kawai mariya tayi itadai haka nan kawai Ayshaan take burgeta.
★★★
K'arfe hud'u da y'an mintuna Aunt Salma ta shiga bedroom d'in Ayshaa, kwance ta sameta tana wani barcin.
"Kedai bakya gajiya da barci yarinyar nan saikace kasa'' Aunt Salma ta fad'i tana tashin Ayshaan.
Tashi tayi tana murza idanuwa kamar barcin bai isheta ba.
"Kinsan dai kinada bak'o kuma kinxo kin kwanta bazaki tashi ki shirya ba".
Baki ta turo batace komi ba dai.
"Oya maza ki tashi ki shirya" Aunt Salma ta umarceta tana ficewa daga bedroom d'in.
Maimakon ta tashi ta shirya d'in saita janyo wayarta ta hau game.
Mamaki da takaici ne suka kama Aunt Salma lokacin data dawo taga Ayshaa ta duk'ufa kan waya.
"Wane irin iskanci ne haka Ayshaa?" Aunt Salma ta fad'a a fusace tana shiga cikin d'akin, da sauri ta ajiye wayar ta shige toilet da gudu tana turo baki.
K'wafa Aunt Salman tayi ta fita.
Koda ta fito mai kawai ta shafa ta d'auko wata riga da siket na atampa tasaka ta shafa powder da lipstick ta zauna.
Aunt Salma data k'ara dawowa tasaki baki tana kallonta.
Fuska ta d'aure sosai tace
"A haka zakije wajen bak'on naki saboda bakida kai?"
"Aunt Salma menayi kuma dan ALLAH?"
Harara Aunt Salma ta zabga mata tace
"Ban saniba, dallah malama wuce ki cire kayan nan ki canza wasu".
Ganin fuskar Aunt Salman a tamke yasa ta nufi wajen wardrobe kamar zatayi kuka.
Kafin ma ta k'arasa Aunt Salma ta rigata ta bud'e ta ciro mata wani material pink color da touch d'in green doguwar rigace mai hawa biyu yayi kyau sosai material d'in, mik'a mata tayi tace ta cire kayan jikinta tasasu, dolenta ta karb'a ta canza sun mata kyau kuwa sosai.
Stool ta nuna mata na gaban mirror tace ta zauna, ba damar musu ta zauna kamar zatayi kuka.
"Dan ALLAH Aunt Salma kimin light makeup banason heavy d'in nan''
Bata kulata ba dai ta cigaba da yimata kwalliyar.
Kamar yadda ta rok'a d'in light d'in tayi mata, tayi kyau kam har ba'a magana d'auri tayi mata na zamani itadai idone nata.
★★★
Da wuri ranar ya tashi daga aiki dan Daddy saida ya k'ara kiranshi a waya ya tuna masa ya kuma ce ya tabbatar dayaje a ranar dan bazai karb'i uzurinshi ba.
Wanka yayi ya shirya cikin jeans blue da shirt mai dogon hannu brown color ya d'aura brown d'in agogo takalmi ma brown sawu ciki.
Masha ALLAH, kyau kam yayishi sosai har ba'a magana turaruka ya fesa masu sanyi da dad'in k'amshi.
Wayoyinshi ya d'auka da car key d'inshi ya fito parlourn.
Mamie da Imaan suna zaune a parlourn suna kallon tashar zee aflam, kusa da Mamien ya zauna yana fad'in
"Mamie zanje can d'in"
"Ina fa?" Cewar Mamie.
"Can inda Daddy yace inje" yace yana ta faman cika yana batsewa tamkar zai fashe.
"Toh kumbure kumburen kuma na menene?" Tace tana kallonshi.
Baice k'ala ba ya mik'e yana shirin tafiya.
"Zo nan" Mamie tayi kiranshi.
Dawowar yayi ya tsaya.
"Dubeka saboda sakarci da shirme a haka zaka tafi gidan surukan kuma zuwan farko?".
"Mamie da aibu ne a shigar tawa?"
"Ban saniba oya b'acemin dagani kaje ka canzo kayan nan kasa manya".
Baki ya bud'e zaiyi magana ta watsa masa harara, dolenshi ya juya ya koma part d'inshi.
Imaan da tun d'azu take b'oye dariyar ta tasaki dariyar tana kallon Mamie.
Harararta Mamie tayi tace
"ALLAH ya taimakeki ya ganki".
Da sauri ta toshe bakinta tana zaro ido tare da waiwayawa.
Milk shadda yasaka sai d'aukar ido take aikin shaddar coffee color ne hakan yasa ya sanya hula coffee yasa bak'in agogo da bak'in takalmi half cover, sai yafi yin kyau a wannan shigar, Mamie kanta tsayawa tayi tana kallon yaron nata.
Murmushi tayi tace
"Ko kaifa babana yanzu basai kaje da mutuncin kaba".
Murmushi shima yayi da iyakacinsa labb'ansa yayi mata sallama ya fice.
Yana jinta tana cewa dan ALLAH ya saki fuskar nan tashi kar yaje ya tsorata d'iyar mutane.
Toh gadai Saif a hanyar gidansu Ayshaan ko wace waina za'a soya
Mrs Salees Mu'az
*DR.SAIF*
©Oum Hanan
Bismillahir Rahmanir Raheem
Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
Ga masu buk'atar cigaban wannan book zasu tura 200 ta wannan account number d'in
0781515544
Ibrahim sani Access Bank
Shaidar biyanki ta wannan number
09133396869
Ko kuma katin waya na MTN akan wannan number dake sama.
G masu buk'atar shiga grup sai suyimin magana duka dai ta wannan number ta sama.
Ku garzayo ku samu naku koda kudinka saida rabonka♀️♀️
Saina jiku.
No 8...
Yana tafe yana ta sakin k'ananun tsaki shi kad'ai mamaki ma yake wai shine zaije zance gurin wannan yarinyar abu kamar wasa yana neman zama babba.
Maigadi ne ya sanarwa Aunt Salma da zuwanshi, key d'in sitting room tabashi tace ya bud'e masa ya shigar dashi ciki.
Saida tasa mariya takai masa abubuwan da aka tanadar masa sannan ta leq'a d'akin Ayshaan.
Tana nan zaune kan stool d'in inda ta barta.
"Ai saiki taso kije gashi can yazo".
Bata amsa ba ta mik'e sai faman cuno baki take, medium size Vail pink color Aunt Salma ta d'auko mata ta yafa mata a kanta ta fesheta da turaruka ta d'auko hill shoes mai mad'auri tace tasaka haka nan dai tanata k'unci ta saka sannan ta kamo hannuwanta zuwa parlour.
Hannun nata ta saki tace
"Kuma wllhy saura kije ki nuna masa halin naki na rashin kunya(k'yaleta Aunt Salma Saif dai dai yake da ita ).
Ita mamakin su Aunt Salman da mijinta take sai wani rawar k'afa suke sai kace wani d'an sarki ne ko d'an shugaban k'asa zaizo, abin haushi yake bata.
Tana turo baki tace
"Aunt Salma duk kunbi kun wani rud'e keda mijinki akan wannan mutumin kamar wad'anda yayiwa asiri".
"Asirin yayi mana''
Aunt Salma ta amsa mata kai tsaye.
"Wllhy ki kiyaye kuma ki iya bakinki". Taji Aunt Salman ta fad'a tana daf da fita daga parlourn, baki ta ta6e tayi gaba tana k'unk'uni dani kaina banjin abinda take fad'a.
Tunda ta doshi hanyar sitting room d'in haka nan batasan dalili ba taji gabanta sai fad'uwa yake saita alak'anta hakan da tsayawa da namiji da zatayine a karon farko a rayuwarta dan ita sam bata kula samari.
Ta d'an jima a bakin k'ofar tanajin tamkar ta koma, haka nan dai tayi k'arfin halin d'ora hannu kan handle d'in k'ofar ta bud'e ta shiga da sallama ciki ciki.
Yana tsaye ya juya baya ya rungume hannayenshi a k'irjinshi ya k'urawa wani k'aramin frame mai zanen flowers ido.
Jikin kujera ta jingina tana k'arewa bayanshi kallo ta matsu ya juyo taga wanene shi d'in.
A hankali cike da nutsuwa ya juyo gaba d'ayanshi idanuwansu suka had'u, wani irin fad'uwa gabanta yayi taji jikinta yana neman fara rawa.
"Dama shine bak'on nata?, ba shiri ta zauna a kujerar datake jingine duk tabi ta tsorace dan ma batasan ya gane tana jin tsoron nashi shiyasa ta aro jarumta ta d'ora a fuskar ta.
A hankali ya shiga takowa kujerar datake facing tata ya zauna ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya, fuskar nan tamau kamar wanda aka aikowa saq'on mutuwa.
Cikin dakiya da son bada haushi Ayshaa tayi wata dariyar rainin hankali tace
"Au wai dama kaine bak'on da aketa faman zuzuta zuwanshi? Uhm kai yanzu kaga nayi kala da matar da zaka aura,tun wuri ka janye maganar aurena dan bazan aureka saboda bana sonka a k'ara gaba ko za'a samu wasu taya Ayshaa dai tace batayi" ta k'arasa maganar tana wani yatsina fuska gamida tab'e baki kamar wadda taga kashi.
"Na shiga uku ALLAH yasa kar yayimin wani abun" ta fad'a cikin ranta bayan ta gama maganar dan dama kawai k'arfin hali tayi amma gabanta sai fat fat yake.
Tashi tayi zata lallab'a ta gudu, sam bataga tasowarsa ba sai fisgar dayayi mata ya jefata kan kujerar data tashi ya kuma d'ora k'afarshi d'aya akan kujerar yayi mata rumfa ya rutsata.
Tuni ido ya raina fata tayi tsuru tsuru sai raba idanuwa take, k'irjinta sai dukan uku uku yake.
D'amk'ar daya yiwa tsintsiyar hannunta ne yasa ta sakin wata siririyar k'arar dabata shirya yinta ba, matseshi yayi sosai idanunshi akanta yana mata wani mugun kallo fuskar nan tashi a had'e ba alamun wasa sam.
Sosai ta marairaice fuska tamkar zata saki kuka saboda zafin dayake ratsa hannun nata, d'ayan hannun nata ta d'ora kan hannunshi daya riq'e mata nata hannun ta shiga k'ok'arin cire nashi hannun idanunta sai shek'i suke saboda k'wallah data taru a ciki.
"Meye haka wai, malam ka sakar min hannu" har lokacin bata daina k'ok'arin cire hannunshi ba.
"Kalleni nan" yace mata murya ba alamun wasa.
Banza tayi masa ba kuma ta d'ago kan ba.
"Ba dake nakeba" ya daka mata tsawa.
Ayshaa tun tana k'arama ta tsani tsawa tana matuk'ar tsoronta shiyasa tayi hanzarin d'agowa ta zuba masa idanunta da suka cika fal da hawaye k'iris suke jira su zubo.
Shima idanun ya tsura mata cikin had'e rai yace
"Abokin wasanki ne ni? Ko kinga nayi kala da wanda zaki fad'awa maganganu son ranki, ba ra'ayin kainane ya kawoki wajenki ba dan ki kiyaye mara kunya kawai.
"Nidai to ka sakar min hannu tunda niba y'ar iska bace" tayi k'arfin halin fad'a.
"Nikuma babban d'an iska ne mai lasisi,kuma wllhy ki shiga hankalinki rannan kiss ne kawai yau kuwa mai gaba d'ayan zanyi"
Ido ta k'walalo sosai tana kallonshi jin abinda yace
"Lallai wannan ashe d'an iskan ne dai da gaske, bari ta rufawa kanta asiri su rabu lafiya kar yaje ya cuceta a banza dan da ganinshi ba tausayi da imani a cikin ranshi.
Ajiyar zuciya ta saki saboda sakin hannunta dayayi, har lokacin kuma yana rank'wafe a kanta.
''Ko akwai magana ne?" Yace mata idanunshi na yawo a fuskar ta, "she's beautiful fa saidai rashin kunya datayi mata yawa.
A hankali ta girgiza kai.
Wani d'an murmushin mugunta yasaki ganin yadda tayi laushi lokaci d'aya.
"Sannan inaso in miki warning kije kisamu magabatanki da maganar ki kafe bakyason aurena duk yadda za'ayi dake kice bakyaso kin fahimta?".
"Kai kaje ka fad'a mana" ta fad'i k'asa k'asa tana turo baki.
Hannu yasa ya gwab'e bakin yace
"Bakin bazai mutu ba ko? Kika k'ara min rashin kunya saina cinye wannan d'an banzan bakin mai kama da gidan tsutsa na rashin kunya".
Bakin nata ta dafe ta shasshake fuska kamar zatayi kuka cikin ranta tace
"ALLAH zai sakamin ne mugu, dama da ganinka kalar mugaye gareka".
Tsaye ya tashi tare da zura hannayenshi duka a aljihun wandonshi idanunshi har lokacin suna kanta, sosai yake yaba kwalliyar tata cikin ranshi.
Itakam kanta na k'asa jira take ya bata umarnin tafiya dan tsoron tashi ma take.
Inda aka jera masa kayan da aka kawo masa ya nufa ya d'auki glass cup ya tsiyayi had'add'en zob'on da akayi masa.
Tasowa yayi hannunshi d'aya a aljihu d'ayan kuma riq'e da cup d'in.
"Mugu sai kace gidansu".
Ta fad'a a ranta tana harararshi k'asa k'asa yadda bazai ganiba(saidai k'asa k'asan Ayshaa).
Gabanta yazo ya tsaya ya fara shan lemon a hankali, sai satar kallonshi take.
"Tashi kije" yace bayan ya k'ara zama akan kujera yana cigaba da shan lemonshi.
Cikin sauri ta tashi dama kamar akan k'aya take.
Sai dataje bakin k'ofar ta tsaya tare da juyowa ta murgud'a masa baki tace
"ALLAH zai sakamin ne wllhy cin zalina dakayi, kuma bazance banaso ba inka matsu kai kaje ka fad'a".
Bakin ta k'ara murgud'a masa ta fice da sauri.
Kai kawai ya kad'a k'asa k'asa yace
"Zan kamakine yarinya zakisan kin murgud'a min baki".
Zob'on kawai yasha sai meatpie daya d'anci kad'an ya tashi ya bar gidan.
Da kuka ta shiga parlourn kamar wadda akaiwa duka, fitowar Aunt Salma kenan daga bedroom zata shiga kitchen ta ganta.
Kamata tayi tana tambayar ta abinda ya faru take kuka.
"Ni wllhy Aunt Salma bana sonshi dan bakisan waye bafa".
Murmushi Aunt Salma tayi tace
"Wanene?''
Cikin kuka tace
"Wannan mugun nefa Dr'n da mukaje yayi mana wulak'anci".
Aunt Salma duk da tasan kowaye hakan bai hana ta nunawa Ayshaa mamakin taba, nan ta shiga kwantar mata da hankali tana nuna mata tayi babbar sa'a idan ta aureshi jinta kawai take amma badan ta yarda ba.
Wajen Mukhtar ya nufa daga nan.
"Ya mutumin yana ganka hakane kamar irin sabon angon nan, koda yake ai kakusa shiga daga ciki".
Harara ya zabga masa yace
"Kaga malam ba neman magana ya kawoni ba yarinyar nan fa taurin kai gareta wllhy tace bazata fad'a ba".
Baki Mukhtar ya k'unshe yana y'ar dariya, wato ya samu daidai dashi kenan.
"Toh yanzu dai tunda hakane muje wajen Hajjah kawai mu fad'a mata abinda ke faruwa".
''Kuma fa ka kawo shawara, hakan ma za'ayi".
Toh ko Hajjah zata goya masa baya???
Mrs Salees Mu'az
*DR. SAIF*
©Oum Hanan
Bismillahir Rahmanir Raheem
Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
Masu buk'atar cigaban wannan book d'in zasu tura 200 ta wannan account number d'in
0781515544
Ibrahim sani Access Bank.
Shaidar biya ta wannan number
09133396869
Ku garzayo ku samu naku koda kudinka saida rabonka.
No 9...
Tafe suke a motar Mukhtar zasu gidan Hajjah kan maganar Saif d'in, Mukhtar d'in ke driving Saif na zaune a gefenshi kanshi a k'asa yana latse latsen wayar tashi na k'aida.
Juyowa Mukhtar yayi ya d'an kalleshi yace
"Nikam S Matawalle inyi maka wata tambaya mana".
"Uhum"
Yace batare daya d'ago kaiba.
"Dan ALLAH wai miyasa bakason yarinyar nan ne?''.
''Meya shafeka?''.
Ya jefa masa tambaya a maimakon amsa.
"Tambaya cefa kawai nayi".
Mukhtar yace yana tab'e baki.
Numfashi ya d'an sauke tare da kashe wayar ya zurata a aljihun gaban rigarshi yace
"Ra'ayi".
"Ra'ayi kamar yaya?'' Mukhtar d'in ya tambayeshi.
"Eh saboda banason auren k'aramar yarinya".
"Why?"
"Saboda raini yake jawowa, yarinyar nan duka batafi 17 ba I think imaan ma ta girmeta fa, kana tunanin akwai abinda zata iya yimin?".
"Shege hankalinka na wajen kuwa, to ai wannan ba matsala bane".
"Mts Mukhtar ka dameni fa I'm tired ka k'yaleni da maganar mara kunyar yarinyar nan" ya k'arasa fad'a yana lumshe ido.
Kai kawai Mukhtar ya girgiza yana tab'e baki ya cigaba da driving d'inshi.
A parlour suka samu Hajjah mai aikinta na shafa mata man zafi a k'afafunta yauma dai kamar kullum tsaf da ita parlourn sai tashin k'amshin turaren wuta yake.
Da murnar ta ta tarbesu tana musu sannu da zuwa suka gaisa da Mukhtar dan Saif sama sama sukayi gaisuwar.
Mai aikinta tasa ta kawo musu abinci funkaso ne da miyar taushe tasha naman rago da man shanu.
"Uhm azo aita min muzuran banza da wani ciccin magani kuma an iya cinyemin abinci''. Hajjah ta fad'a tana kallon gefen da Saif yake.(Hajjah da neman rigima).
Sarai yasan dashi take ya share ya cigaba da cin abincin shi gefe d'aya kuma yana danne dannen waya.
Mukhtar ne kawai yayi dariya yana kallon Saif d'in da kamar ba kanshi ake maganar ba, yarasa irin halin abokin nasa shidai haka ALLAH yayi shi sam magana bata dameshi ba farkon had'uwarsu a sch ma yayi zaton kurma ne sai daga baya ya gane ba wani kurumta tsabar miskilanci ne kawai ke d'awainiya dashi.
Sai bayan da suka ci sannan Mukhtar ya fara yimata bayani kan abinda ya kawosu, kasak'e Hajjah tayi tana sauraronshi kafin tace
"Amma ni Saddiqun cemin yayi sun daidaita kansu ai".
"To nidai Hajjah ma na bashi shawarar ya hak'ura kawai ya aureta gaba zaiji yana sonta ya nace shidai baya sonta wai tayi masa k'ank'anta''.
"Eh ai kasanshi da shegen son girma kamar gyambo, kuma zan yiwa Saddiqun magana amma saidai yaci darajarka in dan tashine bazan yiba miskilin banza''.
Dariya Mukhtar yayi yace
''Toh nagode sosai Hajjahn mu ALLAH ya bar manake".
"Inako ALLAH zai barni d'annan saidai fatan cikawa da imani ai".
"Hakane Hajjah nagode".
Tankau Saif bai tanka musu ba(ALLAH ya shiryeka to).
Sallama sukayi mata ko ince Mukhtar yayi matasuka tafi.
Bayan kwana biyu Hajjah ta kira Dad tayi masa magana kan auren da sukeso suyiwa Saif ashe dama bayason yarinyar.
Bayani yayi mata yadda abin ya faru ya kuma sanar mata d'iyar abokinshi na kano ce.
Sai kuma ta koma murna dan tasan Alh Thabit sosai yawanci indai ya shigo Abuja yana zuwa ya gaisheta yayi mata alkhairi mai yawa.
After two days Saif yaxo gidan Hajjah jin yadda sukayi da Dady.
Yau dai fuskar a d'an sake take da y'ar fara'ar.
"Hajjah ya kukayi da Dady ne an fasa d'in?''
Kallon banza tayi masa tace
"Saboda ALLAH yaushe ka zama haka Saifu?''
"Me nayi?''
Ya tambayeta cikin mamaki.
"Yanzu saboda ALLAH ka kama yarinyar mutane a titi da tsakar rana ka dinga shan bakinta'' wani takaici ne ya rufeshi ya runtse ido tare da dafe goshinshi, ji tsohuwa da b'aro zance.
"Eh ka rufe ido mana to aure kaida ita babu fashi kamar anyi an gama ne''.
"Kinada matsala wllhy matar nan''.
Ya fad'a cikin jin haushi yana shirin tashi dama a kusa da ita ya zauna dayazo.
Cazbahar datake ja ta d'aga da niyyar tsula masa tana fad'in
"Gyatumarka ce mai matsala d'an k'aniya kawai"
ya kauce amma duk da haka saidata sameshi a gefen wuyanshi, ficewa yayi hannunshi akan inda ta sameshin ya barta ita kad'ai sai faman b'ab'atu take.
Ta cikin mirror'n motar yaga inda ta sameshi da carbi har gurin ya d'an tashi yayi jawur abinka ga farar fata ba quality hannu yakai wajen yana shafawa.
"Tsohuwar nan fa ta shammaceni wllhy yace cikin ranshi yana k'ara duban wajen.
Yanzu dai ta tabbata saiya auri yarinyar kenan bashi da sauran mafita kuma.
★★
Tunda Safnah taji labarin auren Saif hankalin ta yayi matuk'ar tashi, gaba d'aya tasa damuwa cikin ranta kullum cikin tunanin samun mafita take da hanya da zatabi ta lalata auren, a ganinta ba wadda ta dace da Saif sai ita dan tafi kowa k'aunarshi tafi kowa sonshi baza tayi dakon soyayya na tsawon shekaru ba a banza wata daga sama tazo lokaci d'aya ta lalata mata komi.
Fahimtar da Hajia safina tayi na d'iyar tata na cikin damuwa yasa ta zaunar da ita ta tambayeta damuwarta taso b'oye mata sai ka tayi tunanin gara dai ta fad'a mata k'ila akwai taimakon dazata bata.
Bata b'oye mata komiba ta sanar da ita irin halin datake ciki.
Murmushi uwar tayi tace
"Akan d'an wannan abin kika sawa ranki damuwa? Toh kwantar da hankalinki indai Saif ne kin sameshi kin gama duk hanyar dazan bi inga kin mallakeshi zanbi kisa ranki a inuwa zamuyi magana da Hajjah in fara jin ta bakinta ki cire damuwa a ranki kinji".
Tuni fuskar Safnah ta washe jin abinda mamanta tace cikin tsananin farin ciki da murna tace
"Nagode sosai Mama".
Kafad'arta Hajia safina ta dafa tace
''Ba komi kedai ki jiraci lokaci kuma ki zuba ido kiyi kallo''.
To fah shin zasuci nasara kuwa.
★*★*★*
Gaba d'ayansu ne a parlourn Mamie tana duba wani book da dactoci daya shafi harkar lafiya, imaan kuma na kwance kan kujera da waya a hannunta.
Sai Saif dayake zaune a k'asan lallausan carpet d'in dake shimfid'e a k'asan parlourn, kusa da k'afafun Mamie ya mik'e k'afa ya d'ora system kan cinyarshi yana sarrafata.
Farin wandone tas a jikinshi ya wuce gwiwarshi amma bai kaimishi har can k'asa ba, sai riga red color mai gajeren hannu hakan ya bayyanar da cikakkun fararen damatsanshi mai cikeda kwantaccen gashi, farar P.Cap yasa a kanshi ya maida gaban hular baya yayi kyau sosai duk da kayan ma bawai na kwalliya bane amma sai suka haskashi.
Kamar wadda aka mintsina Imaan ta ajiye wayar ta ta tashi zaune tana fad'in
"Dan ALLAH Yah Saif yaushe zaka kawo mana Aunt Ayshaan mu gaisa ALLAH inaso in ganta''. Duk a tsorace tayi maganar dan tasan halinshi yanzu ya iya d'aukar zafi daga y'ar wannan maganar.
Aikuwa kamar tasani dan wani mugun kallo ya watsa mata daya d'ago.
Kai ta sunkuyar tana wasa da yatsun hannunta.
Rufe littafin Mamie tayi ta ajiye gefenta tace
"Daina hararar ta dama nima inason inyi maka maganar ya kamata a kawo mana ita mu gaisa".
Rai ya had'e sosai yace
"Dan ALLAH Mamie ki bar maganar nan kawai"
"Bazan barta ba kuwa, ai y'ar gidace kuma ko babu Aunt'nta anan garin zata iya zuwa gidan nan tayi zaman ta koka manta amintakar dake tsakanin Daddy da Abbanta?''
''Nidai Mamie dan ALLAH....''karma ka b'ata bakinka dole zaka kawota zanyiwa Daddynku ma magana a fad'awa Auntyn nata".
"Mu bama gayyarta". Yace k'asa k'asa.
"Magana kake?'' Mamien ta tambayeshi.
Kai ya girgiza yace
"A'ah" kamar ba maganar yayi ba kuwa.
Kai ta dungure masa tace
"Ai na jika kuma dolenka ka kawota kana jina?" Ta k'arashe maganar muryarta ba alamun wasa.
Badan yasoba ya amsa da "Toh" yana rufe system d'in ya mik'e tsaye.
Koda zai fita daga parlourn sai daya k'ara hararar Imaan, ta sunkuyar dakai tana k'unshe dariyarta, koma dai meye zataga Auntyn ta.
Da daren Mamie tayiwa Daddy maganar shima d'in ya goyi bayan ya kawotan asan juna.
A washegari Daddy ya kira Kabeer ya fad'a masa, shikuma ya sanar da Aunt Salma.
Koda ta fad'awa Ayshaan zumb'urar baki tayi tace ita ba inda zata, saida Aunt Salma tayi mata da gaske sannan.
Washegari Daddy yacewa Saif yaje ya d'auko ta.
Takaici duk ya rufeshi sai kace wani driver'nta zata gane kurenta ne, gashi bashi da damar musawa dan Daddy ba raga masa zaiyi ba.
Sanin halin Mamie tana iya maidashi idan taga yasa k'ananun kaya tace gidan surukai zaije shida bama shiga zaiyi ba, hakan yasa yasaka wani yadi coffee color da akayiwa aiki da bak'in zare wrist watch da takalmi duk kalar kayan yasaka baisa hulaba saboda damunshi datake har ciwon kai take sashi shiyasa koda yasa manyan kayan bai cika sa hula ba.
Sumar kanshi tasha gyara da mayuka masu matuk'ar kyau da k'amshi.
Upstairs ya hau yayiwa Mamie sallama dan bai sameta a parlourn ba ranar ma saida tayi masa gargad'i kan sakin fuska shi sai abinma yaso bashi dariya dayake ba saba yin nata yayiba ya maze yai gaba abinshi.
Maigadi yace ya shiga ya sanar da zuwanshi dan bawai phone number d'inta yake da itaba.
Tana bedroom tana ta nuk'u nuk'un shiryawa Aunt Salma ta sanar da ita zuwanshi.
Batace komi ba ta cigaba da laluben mayafin dazai shiga da coffee'n atampar ta.
"Wai bada Ayshaa nake ba".
Aunt Salma tace a fusace dan Ayshaan tana neman ta kaita bango.
"Gani nan fa Aunt''
Tace a marairaice tana turo baki.
"Toh kiyi sauri dai ba dad'i mutum yazo yaita jira" ta juya ta fita.
Riga da zani ne na atampa coffee a jikinta zanin bamai ado bane rigar ma ba wata kwalliya a jiki sai dai yanayin shape d'in d'inkin rigar datasa yayi mata d'as a jiki d'auri tayi mai hawa hawa ta yafa babban mayafi akanta kalar kayan da adon golden a jiki tasa bak'in takalmi ta fito.
Sallama tayiwa Aunt Salma data kasa ta tsare a parlour.
Itama sai data ja mata kunne akan saura taje tayita kumbure kumbure acan inda zata d'in dai gidane nanma.
Tun daga nesa ya tsura mata idanunshi, yana kallon yadda take tafiya kamar mai ciwon k'afa sai wani rangaji take.
"Nidai wllhy cutata kawai za'ayi, wannan y'ar yarinyar ba abin kirki zatayi ba" cikin ranshi yayi maganar yana k'ara ware manyan idanunshi akanta.
Ayshaa da neman fad'a tana k'arasawa ta bud'e back seat ta shige ta basar abinta.
Mamaki ne ya kashe Saif a zaune, wai mi yarinyar nan ta taka ne? tama raina masa hankali kenan, wato ga driver'nta yazo ta wani kame a baya.
Baiyi magana ba ya tada motar maigadi ya bud'e masa gate ya fita.
Gaba kad'an da gidan yayi parking ya ciro waya ya shiga danne danne.
Baki ta tab'e itama ta kama waya sukai ta dannawa.
Tsaki Ayshaa ta fara saki dan fa zaman ya fara isarta, shikuma taga kamar ba abinda ya dameshi.
Shima d'in gajiyar yayi ya kashe wayar ya cillata front seat.
"Tashi ki dawo gaba". Yayi maganar batare daya juyo ya kalleta ba.
"Naga aikoka akayi ka d'aukeni" tace kanta tsaye tana wani yatsina fuska.
Kutt! Saifa yayiwa yarinyar nan da gaske wllhy.
A fusace ya bud'e ya fita ya bud'e back seat d'in.
"Tashi ki dawo gaba nace" cikin tsawa yayi mata maganar.
Ayshaa da tsawa ke tsoratata tuni jikinta ya d'an fara rawa dan ta tsorata ainun amma tsabar taurin kai yasa batayi ko gezau ba.
Numfashi ya shiga saukewa a fusace yana kad'a kai, batayi aune ba taji ya wani irin fisgota kafin tayi wani yunk'uri ya cillata front seat bayan ya d'auke wayarshi.
Kici kici ta fara da niyyar fitowa,(kuji fa rigima reader's).
"I will slap you idan kika kuskura kika fito wllhy".
Yace yana mata wani mugun kallo tuni ta shiga taitayinta damafa ba fitowar zatayi ba.
Tsaki yaja ya zagaya ya bud'e driver side ya shiga ya rufe, relaxing yayi kan kujerar tare da runtse ido, yanzu a haka zata zama matarshi? Tun yanzu ta fara sashi magana yanzu da babbace yaushe zatayi haka kanshi harya d'an fara sarawa saboda tada jijiyar wuyan data sashi.
Ta gefen ido ta dinga hararar shi tana murgud'a masa baki(ALLAH yasa ya k'ara cafke bakin♀️♀️).
Saida ya d'anji yasamu nutsuwa sannan ya tada motar yajata a zafafe tamkar itace mai laifin suka tafi.
Mrs Salees Mu'az
*DR. SAIF*
©Oum Hanan
Bismillahir Rahmanir Raheem
Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
Masu buk'atar cigaban wannan book d'in zasu tura 200 ta wannan account number
0781515544
Ibrahim sani Access Bank.
Shaidar biya ta wannan number
09133396869
Ko kuma katin waya na MTN ta wannan number dake sama nagode
Ku garzayo ku samu naku koda kudinka saida rabonka.
No 10...
Ko tari ba wanda ya k'ara yi a cikinsu tunda suka tafi, sai sharara uban gudu yake tamkar zasu bar gari, tsaki yake ja lokaci lokaci yana furzar da iskar bakinsa.
"Hmm munga tsaka ma k'arewar tsaki" cikin ranta tayi maganar tana d'an tab'e baki, baisan hidimar datake ba dan bai k'ara kallon sashin datake ba.
Yana yin parking ta fice da sauri, saidai kuma dolenta ta tsaya dan saiyayi mata jagora tunda ba tab'a zuwa gidan tayi ba.
Sai daya b'ata lokaci kafin ya fito daga motar tana tsaye tana jiranshi, yana fitowa yayi gaba bayan ya rufe murfin motar, bin bayanshi tayi tana kallon yadda yake takunshi cikeda nutsuwa da kamala.
Saida yaje bakin k'ofar main parlour na gidan sannan ya d'an dakata, sai a lokacin ya juya ya d'an kalleta.
"Gaba d'aya yarinyar nan batada laka ma wllhy ji yadda take tafiya fa,a ranshi yayi maganar yana k'ara k'are mata kallo.
Sai bayan data k'araso sannan ya kama handle d'in k'ofar ya murd'a ya shiga ganin tak'i biyoshi yasa ya juya yayi mata wani kallo, binshi tayi tana d'an tura baki.
K'asa k'asa yayi k'wafa dan ya hango Mamie a parlourn.
Sai a lokacin suka jera suka shiga cikin parlourn, da gudu Imaan ta taso ta rungume Ayshaa tana dariyar farin ciki
"Oyoyo my Aunt Ayshaa" tace cikin murna tana kama hannunta ta nufi wajen Mamie dake zaune kan cushion fuskarta d'auke da mad'aukakin murmushi.
Kanta a k'asa ta shiga k'ok'arin durk'usawa a k'asa kusa da k'afafun Mamien, da sauri ta rik'ota ta d'an rungumeta tana fad'in
"Your highly welcome my dear daughter".
Itadai Ayshaa duk kunya saita kamata.
Kusa da ita ta zaunar da ita hannayenta na riq'e da nata.
Imaan ma kusa da itan ta zauna suka sata a tsakiya.
"Ina yini Mamie''. Ta fad'a cikin siririyar muryarta kanta a k'asa.
"Lafiya k'alau mamana kina lafiya? Ya Auntyn taki?"
Cikin jin kunya tace
"Lafiya lau tace a gaisheku".
"Ina amsawa mamana". Mamie ta amsa cikin fara'a.
Gaisawa sukayi da Imaan har lokacin bata yadda ta d'ago kaiba.
"Wannan yarinyar munafuka ce wllhy ji yadda take wani k'asa k'asa dakai kamar ba yanzu ta gama min rashin kunya ba". Yayi maganar cikin ranshi yana kallonta, dan tun shigowarsu yaga ba'a ta tashi ya nemi guri ya zauna ya fara sana'ar tashi ta danna waya.
Ganin yadda take ta jin kunya tana faman sussune kai Mamie tace
"Ki saki jikinki mamana nan mafa gidanku ne kin manta ma kin tab'a cemin zakizo min hutu wata waya da mukayi da Amminku ta bani mu gaisa".
Murmushi kawai tayi ta d'aga kai.
Tuni Imaan ta fara cika mata gabanta da kayan motsa baki, saidai tak'i cin komi saida Mamie ta matsa mata sannan ta d'an zuba juice ta sha ta d'an ci shawarma kad'an.
Saif kuwa tuni ya fece daga parlourn ya shige side d'inshi.
Sunata janta da hira, duk dan ta sake ta dai d'an fara sakewa dan taga Mamien bata suruka da ita, sosai familyn suka burgeta taji tana sonsu(amma fa banda Saif).
Suna nan zaune Dad ya shigo shima yaji dad'in ganinta ainun.
Har k'asa ta durk'usa ta gaisheshi ya amsa cikin fara'a yana tambayar ta mutan gidan, ta amsa masa kanta na k'asa.
"Amma zaki kwanar mana nan ko?" Daddy ya tambayeta yana miq'ewa tsaye.
A hankali tace
"Ai su Aunt Salma basu saniba".
"Wannan ai ba matsala bane zan kira shi maigidan Salman in fad'a masa da nan can ai duk d'aya ne".
Ba dan ranta yasoba ta amsa da "Toh" dan bazata iya musu dashi ba amma harga ALLAH bataso kwanannan ba dan duk jinta take a d'add'aure.
Saif bai masan da maganar kwana ba, saidaya fito da niyyar maidata Mamie take cemasa kwana zatayi.
Baki ya d'an tab'e ya juya ya koma part d'inshi, shi haushin ma yadda suke ta wani jida ita yake(d'an black stomach).
Suna k'ok'arin tashi daga parlourn sakamakon kiran sallahr maghreeb da akayi ya fito cikin shirin tafiya masallachi, jallabiyyah ce a jikinshi milk color sai counter daya mak'ala a d'an yatsanshi sai bulala k'amshi yake da alamu wanka yayi.
Ido suka had'a da Ayshaa a sace suka jefawa juna harara yadda Mamie bazata gani ba saidai sun riga sun makaro dan tsaf ta gansu, murmushi kawai tayi cikin ranta tace
"Ashe itama dai maman nawa A ce.
Bedroom d'in Imaan suka nufa Mamie ma ta tafi nata.
Alwala sukayi sukabi jam'i a masallachin kusa da gidan.
Da suka idar ma zamansu sukayi cikin d'akin suka cigaba da hira, dan tuni ta sake da Imaan surutu ne ya had'u da surutu.
Album d'in hotuna ta d'auko mata tana gani suna hira pictures d'in Saif kala kala yawanci ma duk ba nan k'asar aka d'aukeshi ba saidai ta tab'e baki ta wuceshi, tsaf Imaan ta lura da ita y'ar dariya tayi cikin ranta tace
"Hmm duk kugama iyayinku muna nan zaku jone". Dan tun zuwansu ta kula sam basu shiri.
Suna nan zaune aka kira sallahr Esha'e suka bada farali, nan suka cigaba da hirarsu har lokacin da Mamie ta leq'o ta kirasu suzo suyi dinner.
Itadai Ayshaa bataso ma cin abincin tare ba, haka nan dai ta tashi suka fito dinning area d'in.
Taji dad'i da bataga Dady a dinning d'in ba dan tunanin ta ta yadda zataci abinci a gabanshi gara gara ma Mamie.
Saif d'inma addu'a take ALLAH yasa kar yazo(k'arfin hali mutum da gidansu).
Aikuwa addu'arta bata ciba dan suna zama Mamie tace Imaan taje ta kirashi.
Dawowa tayi tace
"Yace wai ya k'oshi".
"Kije kice masa ya fito kafin ranshi ya b'aci. Tasan sarai zuwan Ayshaa ne yasashi fad'ar haka.
Imaan d'in ce tayi serving d'insu bayan ta dawo.
Fried rice with chicken sai farfesun naman rago da kunun aya saikuma had'add'en shayi dayaji kayan k'amshi.
Basu dad'e da fara ciba sai gashi ya fito rannan a had'e sai wani cin d'aci yake yana shan k'amshi.
Kujera yaja ya zauna ya fara latse latsen waya, ba wanda ya kulashi har Mamie saida taga abin nashi bana k'are bane, spoon d'in hannunta ta ajiye cikin plate d'in ta had'e rai sosai tace
"Wai shin Saif dinner kazo yi ko danne dannen waya kazo yimana nan?".
Wayar ya ajiye kan table d'in, tea kawai ya had'a ya d'auki cup d'in da wayarshi yacewa Mamie saida safe.
"ALLAH ya tashemu lafiya''. Mamie ta amsa tana binshi da kallo.
Manage please
Mrs Salees Mu'az
*DR. SAIF*
@Oum Hanan
Bismillahir Rahmanir Raheem
No 11
Ayshaa dake tsakurar abincin ta d'an ta6e baki tana satar kallonshi ta gefen ido cikin ranta take fad'in
"Mutum sai iyayi da feleqen tsiya kamar mace, ta tabbatar iyayin mutumin nan yafi nawasu matan dayawa.
Batare daya kalli sashen da Ayshaa take ba yabar wajen cikin takunshi na qasaita da gayu.
"A'ah mamana ya haka?,sai juya spoon kike baki cin abincin?" Mamie tayi maganar tana kallon Ayshaa fuskarta d'auke da murmushi.
Murmushi itama Ayshaan tayi tana k'ara yin k'asa da kanta bata iya cewa komiba saboda kunya.
Dariya Imaan ta d'anyi tace
"Mamie Aunt Ayshaa fa kunyar ki takeji wllhy ta kasa sakewa dake amma da muka shiga bedroom d'ina d'azu bakiji surutu ba". Ta k'arasa maganar tana kallon Ayshaa dake d'an harararta ta gefen ido.
"Toh ai kuwa gara ta daina kunyata tun wuri dan ni matsayin d'iyar cikina na d'auketa itama kuma inason ta d'aukeni matsayin uwa kinji mamana?".
Kai Ayshaa ta d'aga tace a hankali
"Insha ALLAH Mamie".
"Yawwa d'iyata ALLAH yayi muku albarka yasa albarka cikin aurenku''.
Imaan ce kawai ta amsa da
"Aamin''
Ayshaa kuwa k'asa ta k'ara yi da kanta.
Bayan gama dinner ne suka koma cikin ainihin parlor'n suna kallon tashar zee Aflam jefi jefi kuma suna d'an ta6a hira duk da har lokacin Ayshaa bata gama sakin jiki ba.
K'arfe goma da y'an mintuna Mamie tace su Ayshaa suje su kwanta dan ta kula da hammar da Ayshaa ta fara.
Sallama sukayi mata suka wuce bedroom d'in Imaan.
Sai datayi wanka dan tayi mugun sabo da wanka kafin ta kwanta.
Sleeping dress Imaan ta bata tasaka doguwar rigace har qasa mai d'an k'aramin hannu tana da kauri sosai rigar tasa hula ta kwanta tana kallon Imaan tana duba wasu books d'inta na school itama phone d'inta ta d'auka ta shiga candy crush game ta fara bugawa bayan ta karanto addu'ar kwanciya barci.
Ba'a jimaba Imaan ta tattara books d'in ta ajiyesu kan side drower ta hawo gadon ta kwanta itama addu'ar tayi suka hau hira da Ayshaa kafin barci ya d'aukesu.
★★★
Saida sukayi adhkar bayan sallahr asubah kafin su k'ara kwanciya, Imaan bata dad'e tana barcin ba ta tashi saboda lecture datake da ita taso dai ace ranar batada lecture su k'ara shan hira da Ayshaa.
Sai data gama shirinta tsaf sannan ta tashi Ayshaa dan suyi sallama koda zata dawo bata sameta ba duk da tasan da wuya Mamie ta barta ta tafi da wuri.
"Imaan Ina zuwa haka?".
Ayshaa ta fad'a tana d'an mutstsuke ido.
Side bag d'inta ta k'ara gyarawa tana fad'in
"Wllhy Aunt Ayshaa school zan shiga inada lecture yau kina nan ai har yamma ko?''.
"Anya kuwa?'' Ayshaa ta fad'a tana hamma alamun barcin bai isheta ba.
Baki Imaan ta turo tace
"Kai dan ALLAH Aunt Ayshaa bazaki jirani ba nasan Mamie ma bazata barki kitafi da wuriba, ALLAH dama ki k'ara kwana".
Hararar wasa Ayshaa ta jefa mata tace
"Lallai fa in k'ara kwana ba lallai ma kidawo kisameni ba''.
Marairaicewa tayi tace
"Shikenan ai Aunt Ayshaa ba komi, nima insha ALLAH zanzo kwanannan''.
Komawa tayi ta kwanta tana fad'in
''Tohm ALLAH ya kawoki Ina zuba ido".
Har takai bakin k'ofa ta juyo tace
"Aunt Ayshaa idan kinyi wanka ki zab'i kayan da sukayi miki kisa".
Daga kwancen ta amsa mata da "Toh" tana lumshe ido.
***
Sai wajen k'arfe goma da kusan kwata sannan ta tashi, wanka tayi ta shafa mai powder kawai ta shafa sai lipstick da kwalli ta bud'e wardrobe d'in tana neman kaya.
Sai data dad'e kafin ta zak'ulo wata doguwar riga ta atamfa ash color da coffee da black mayafinta ta yafa ta fesa turare.
Tanaso ta fita tanajin kunya, kawai sai Mamie ta ganta da kayan Imaan zamanta kawai tayi bakin gadon ta d'auki waya ta fara danne danne.
Da sallama Mamie ta shigo tana fad'in
"Mamana har yanzu barcin ne?".
"Na tashi Mamie" Tace tana ajiye wayar a gefenta.
Har k'asa ta zamo tana gaishe da Mamien, ta amsa mata fuskarta d'auke da fara'a.
Da kanta ta kamo hannunta suka fito parlor'n itadai kanta na k'asa tana raba idanuwa.
Har gaban dinning ta kaita taja mata kujera ta zauna tana fad'in
''Oyaa maza kiyi breakfast mamana".
Kafin tayi magana Saif ya shigo cikin parlor'n sanye cikin riga da wando na companyn DKNY dark blue ce rigar mai dogayen hannu sai light blue d'in jeans kayan sunyi matuk'ar amsarshi rufaffen bak'in takalmine a k'afarshi sai bak'in agogon fata dake daure a kyakkyawan farin hannunshi mai cike da kwantaccen gashi, kyau kam yayishi Masha ALLAH dole mata su dinga crushing akansa tun kafin ya shigo parlor'n k'amshin shi yafara yiwa parlor'n sallama sosai Ayshaa ta bud'e k'ofofin hanci tana shak'ar k'amshin mai dan karen dad'i dan ba k'aramin dad'i k'amshin yayi mata ba.
Fuskarshi a had'e sosai tamkar baisan wani abu dariya ba koda yake ba yinta yakeba.
Sallamar ma kanta bata fitoba dan Ayshaa badan da Mamie ta amsaba tayi zaton ma baiyi sallama ba.
Har k'asa ya durk'usa ya gaida Mamie ta amsa cikin sakin fuska.
Ganin Mamie a wajen ne yasa tace masa
"Ina kwana''.
Shima din dai ganin Mamien ne yasa ya amsa mata ciki ciki da
"Lafiya".
Daga haka bata k'ara cewa komiba shima din baice ba yafara yiwa Mamie sallama.
"Breakfast fa?''.
Mamie ta tambaya tana binshi da kallo.
Kanshi ya shafa yana fad'in
"Mamie nayi late ne bazan tsaya yiba''.
"Toh ai shikenan ALLAH ya kiyaye ya bada sa'a, karka manta dai da zaka maida mamana gida kadawo da wuri''.
Kamar bazai amsaba kafin yace
"Toh" yayi gaba cikin takunshi na mazantaka.
Kai Mamie ta girgiza cikin ranta tana tunanin yadda auren Saif da Ayshaa zai kaya yadda ta lura da halin ko in kula da sukeyi da junansu but tanaji a jikinta aurensu alkhairi ne da iznin ALLAH ba za'a biye musuba musamman ma Saif datake ganin kamar matsalar tafi daga gurinshi.
Tare suka yini da Mamie ba laifi ta d'an sake da Mamien, kafin Imaan ta dawo taji dad'i sosai data tarar da ita bata tafiba
Daf da sallahr la'asar yadawo gidan lokacin bakowa a parlor'n sai TV datake ta faman yi ita kad'ai.
Apartment dinshi ya nufa yayi wanka ya d'aura alwalah, boxer ya zura da jallabiyyah milk color ya fesa turare ya k'ara fitowa.
Har lokacin ba kowa, kai tsaye ya wuce masjeed dan yin sallah.
Lokacin daya dawo yasamu Mamie a parlor'n.
"Yaushe ka shigone?".
Mamie tace tana binshi da kallo.
Hannun kujera ya zauna yana fad'in
"Ban dad'e ba ba kowa time d'in dana shigo".
"Dinning ta kalla kafin ta juyo wajenshi tace
"Ga lunch nasan dai da k'yar idan kaci abinci".
Idanunshi ya d'an lumshe ya bud'e yace
"I'm full Mamie naje wajen Mukhtar hajiyanshi ta tsareni saida naci abinci''.
"Okay, saika d'an huta kazo ka maida mamana gida".
Had'e rai yayi batare daya ce uffan ba.
"Bada Saifu nake ba wai?''
"Toh Mamie". Ya amsa badan ranshi nasoba gani yake kamar an maidashi wani driver.
Tashi yayi ya wuce side d'inshi Mamie ta bishi da ido tana girgiza kai.
***
After some minutes.
Cikin wata dakakkiyar shadda mai yarari ya shirya kalar ruwan k'wai d'inkin zamani rufaffen takalmi yasa black color da black wrist watch baisa hulaba illah sumarshi datasha gyara take ta faman zuba k'yalli da k'amshi saboda mayukan dayayi amfani dasu.
Turaruka ya fesa kusan kala uku ya d'auki wayarshi da car key d'inshi ya fito parlor'n sai wani cin d'aci yake yana basarwa.
Mamie na k'ok'arin shiga kitchen ya shigo dan haka ta dakata tana kallonshi tace
"Tafiyar ta tashi ne?".
"Eh Mamie, ayi mata magana Ina waje''. Yace yana nufar k'ofar fita sai tsaki yake saki cikin ranshi, dan a gajiye yake hutawa yaso yayi bayan dawowarshi.
Yana shirin fita ya tsinkayi muryar Mamie na fad'in
''Yawwa na manta in fad'a maka ka biya da ita gidan mamana (Aisha yayar Saifun) tun jiya da Imaan ta fad'a mata tazo take ta damuna akai mata ita su gaisa yanzun nan ma sai data kirani".
Juyowa yayi kamar zaiyi kuka ya rasa ma abinda zaice dan takaici an maidashi wani driver kawai, bazai iya yiwa Mamien shi musu ba hakan yasa yace
"Toh" ya fice da hanzari.
Kaya sosai Mamie ta had'awa Ayshaa dasuka had'a da kayan makeup tuli guda da turaruka harda atamfa da material guda d'ai d'ai sannan ta bata 50k tace inji Daddy yace a bata k'in karb'a tayi saida Mamien ta nuna mata b'acin ranta sannan ta amsa tayi godiya sosai.
Exchanging numbers sukayi da Imaan sannan sukayi sallama da Mamie Imaan ta rakota harabar gidan ji take tamkar kar Ayshaan ta tafi dan kwana d'ayan nan datayi ta d'ebe mata kewar datake fama da ita.
Yana zaune ya fito da k'afa d'aya waje d'ayar kuma tana ciki, sai faman danne dannen waya yake fuskar nan a tamke tam, zuwansu baisa ya d'ago kaiba haka kuma bai bar abinda yakeba.
Imaan ce ta bud'e mata front seat ta shiga ta zauna suka k'ara yin sallama tabar wajen tun kafin ya d'ago ya sauke mata kwandon masifarshi dan tasan a kusa yake.
Gefe ta juyar da kanta tana kallon furannin dake cikin farfajiyar.
Ganin sun d'auki fin ten minutes a haka yasa ta juyo ta kalleshi yana nan a yadda yake kamar ma ba alamun zai daina.
Batasan lokacin data saki tsaki ba duk da cikin ranta taso yinshi batasan ya akayi harya fito fili ba.
Da sauri tasa hannu ta damk'e bakin nata tana d'an zaro ido tana addu'ar ALLAH yasa hankalinshi nakan wayar baiji ba, duk yana kallonta ta gefen idonshi cikin ranshi yake fad'in
"Badai zata daina yimin tsaki ba yarinyar nan".
Ganin bai d'auki wani mataki ba yasa ta sakin ajiyar zuciya tana hamdala cikin ranta ta juya ta cigaba da kallon shukokin ta d'au niyyar indai suka k'ara minti goma a haka fita zatayi tayi tafiyar ta dan bazata zauna zaman jiranshi ba.
K'arar rufe murfin motar ne yasa ta waigo ta kalleshi, baki ta tab'e tana yamutsa fuska.
Da uban gudu ya fice daga gidan alamun dai ranshi a b'ace yake.
Tafiyar kurame dai akayi a motar dan uffan ba wanda ya k'ara cewa, sai amsa waya dayake yi akai akai yadda yake maganar ma abin saiya bata haushi sai wani yanga yake kamar baison magana kokuma mai ciwon baki.
A haka dai suka k'arasa gidan Aunt Aisha, sosai tayi murna da ganinta tuni ta cika mata gabanta da kayan ciye ciye da drink's.
Saif tunda suka gaisa da Aunt Aisha bai kara cewa komiba ya shiga aikin latse latsen waya Aunt Aisha tasan halin d'an uwanta sam shi ba'a zama ayi hira dashi dan haka batabi takanshi ba ta maida hankalinta kan Ayshaa.
Yana jin Aunt Aisha tana cewa Ayshaa sai tayi hak'uri da halin k'anin nata wani irin bahagon mutum ne da ba'a gane masa murmushi kawai Ayshaa tayi cikin ranta take fad'in
"Ita Ina ruwanta dashi yayi harkar gabanshi tayi tata.
Itama kyautar turaruka ta bata dazasu tafi.
Lokacin data shiga motar yayi relaxing ya d'ora kanshi kan seat d'in idanunshi a lumshe.
Ta gefen ido ta d'an saci kallonshi tana tab'e baki.
"Mutumin nan ya cika k'uncin jaraba wllhy, koda yake Ina ruwanta da wani k'uncin shi yaje yai tayi shi yaga zai iya''. Cikin ranta tayi maganar tana d'an d'aga kafad'a.
"Ban hanaki yimin tsaki ba?".
Ta jiyo muryarshi ba alamun wasa.
Da sauri ta kalleshi gabanta na fad'uwa.
Yana nan a yadda yake ko motsi baiyi ba baikuma bud'e idonshi ba.
Tsuru tayi tana raba ido tana tunanin dama d'azu yajita?
*DR. SAIF*
@Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No 12.
Shiru tayi tana wasa da gefen mayafinta, duk tsoro ya kamata kar yace zaiyi mata abinda yayi mata a Mall.
"Ko bakya ji?''.
Ya fad'a a fusace yana bud'e idonshi tare da ware mata manyan idanunshi akanta.
Cikin turo baki tace
"Nifa banyi maka ts.....ba shiri tayi shiru saboda bige mata baki dayayi, bakin ta dafe saboda zafin dataji ya ratsata tuni k'wallah suka fara cika mata ido cikin ranta take faman jera masa ALLAH ya isa.
"Kin maidani kurma ne ko meye? Ki maida hankalinki idan baki daina min rashin kunya ba zakisha wuya ne stupid girl kawai''. Ya k'arasa maganar yana tada motar ya figeta da gudu bayan an bud'e masa gate.
Baki ta k'ara turowa tana kallon gefen titi, itadai bazata yafe ba mutumin nan yasan takan mugunta ALLAH zai saka mata ne.
A bakin gate d'in gidan Aunt Salma yayi parking alamun bazai shiga ciki ba.
"Get out of my car". Abinda ya fad'a kenan bayan yin parking d'in nashi.
"Ai ko baka fad'a ba''. Tace tana d'an tab'e baki.
Jakar kayan da Mamie ta bata da wanda Aunt Aisha ta bata ta d'auka ta fice tana harare harare.
Kai ya kad'a yana sakin k'aramar k'wafa kafin ya k'ara tada motar yabar unguwar.
Fitowar Aunt Salma daga bedroom kenan taji ana danna door bell, k'arasawa tayi ta bud'e, Ayshaa ta fad'a jikinta tana murnar ganinta.
''I miss u Aunt Salma, kwana d'ayan nan danayi duk kewarki ta dameni". Ta k'arasa maganar cikin shagwab'a tana d'an turo baki.
"Miss u too little sis". Aunt Salma tace tana riq'o hannunta suka k'arasa cikin parlor'n bayan ta maida k'ofar ta rufe.
Kan cushion suka zauna Aunt Salma na fad'in
"Sai kuma mukaji waya zaki kwana''.
"Wllhy Aunt Salma Mamien shi ne da Daddy sukace in kwana wllhy Aunt baki ganiba dukansu masu mutunci kinga ma abinda suka bani, nan ta fara nunnuna mata kayan da wanda Aunt Aisha ta bata sai yabonsu mutuncinsu da karamcinsu take.
"Kai Masha ALLAH angode musu qwarai, kice ga inda Dr yayi gadon mutunci". Aunt Salma ta k'arasa maganar cikin sigar zolaya.
Tuni Ayshaa kuwa ta tamke fuska ta turo baki gaba tace
"Ta6! Wllhy Aunt Salma shi kad'ai ne mara kirki kema ai kinsani yayi miki kingani mugu ne yanzu mafa sai daya dakarmin baki saboda mugunta". Ta k'arasa kamar zata saki kuka tana shafa d'an k'aramin bakinta.
Dariya Aunt Salma tayi tace
"Rashin kunya kikayi masa ai naji dad'i da kika had'u da irinshi zai saita miki zama''.
Baki ta tura ta tashi ta shige bedroom d'inta ita tayi fushi.
Da kallo Aunt Salma ta bita tana murmushi gami da girgiza kai.
★
Two Weeks After.
Cikin y'an kwanakin magana ta kankama inda aka kai kud'i tare da sanya rana, duka 3 months akasa Daddy ya roq'i alfarmar hakan dan yadda ya matsu da Saif yayi aure.
Saif bak'in ciki kamar yayi me, patient's kuwa ranar sunsha jaraba ba ruwanshi da wai mutum mara lafiya ne zai rufeshi da masifa su kansu ma'aikatan hosp d'in kaffa kaffa suka dingayi ranar dan abu kad'an mutum zaiyi ya hau kanshi da fad'a badai wanda yasan dalilin fad'an nashi.
Itama ranar Ayshaa harda d'an guntun kukanta, gani take kamar an cutar da itane ga karatu datake masifar so tayi ji take dama ALLAH bai had'ata da Saif ba tasan da yanzu tana nan zata fara karatun ta cikin kwanciyar hankali, tun ranar daya dawo da ita bata k'ara jin d'uriyarshi ba kuma bawai hakan ya dameta bane tunda bason ganinshi ma take ba.
Ran da akasa ranar da daddare Mukhtar yazo wajenshi, bayan sun gaisa da Mamie ya wuce side d'in Saif.
Tun daga bakin k'ofar daddad'an k'amshi yafara yiwa Mukhtar sallama.
"Shege mayen turare". Mukhtar d'in ya fad'a yana murmushi.
Baya parlor'n dan haka ya kutsa kai cikin bedroom d'in bakinshi d'auke da sallama.
Can gefen gado ya ganshi ya jingina da pillow k'afafunshi a mik'e da labtop akan cinyarshi yana sarrafata, sanye yake cikin bak'in wando 3qtr da farar riga mara hannu sai hular rigar dake kanshi ya d'an zameta baya.
Ciki ciki ya amsa sallamar Mukhtar d'in yana cigaba da abinda yake.
D'ayan gefen Mukhtar ya zauna ya d'an kishingid'a kan pillow yana kallon Saif sai wani cin magani yake.
Tsaki yayi yace
"Nifa S.Matawalle ba zuwa wajenka ba wulak'anci wllhy ji dan ALLAH kamar irin baka sanni d'in nan ba''. Ya k'arasa maganar yana jefa masa harara.
Kamar bazaiyi magana ba kafin yace
"Na gayyato kane?'' Na sani ai munafurci ya kawoka".
Dariya Mukhtar yasa yace
"Daga zuwa in tayaka murna sai kace nazo munafurci''.
"Murnar ubanka zaka tayani''. Ya fad'a a fusace yana jifanshi da harara.
Zaro ido Mukhtar yayi yana dariyar shak'iyanci yace
"Me yay zafi haka Matawalle?"
K'aramin tsaki Saif yaja yana rufe labtop d'in ya d'orata kan bedside drower ya juyo yana kallon Mukhtar da idanunshi da suka d'an canza kala kad'an.
Baki Mukhtar ya d'an kama yace
"Wai mutumina yana ganka hakane?''.
Hular kanshi ya zame ya shiga shafa sumarshi yana lumshe ido gaba d'aya an b'ata masa budget d'inshi shifa sam a tsarinshi ba auren k'aramar yarinya sai gashi zai b'ige da auren wadda iyakacinta secondary school kuma marar kunya baison mace mai surutu yafison miskila irinshi(A haifi kurame kenan).
Mukhtar ya tashi zaune yana fad'in
"Nifa seriously S.Matawalle nazo ka rakani wajen Ayshaa mu gaisa asan juna yadda ko a hanya muka had'u bazata wuce in wuce ba".
"Wllhy Mukhtar zan maka rashin mutunci idan baka daina min zancen yarinyar nan ba".
Murmushi Mukhtar yayi yana tab'e baki yace
''A gama cewa dai ba'aso da bak'in rai nasan hakan bazai hana idan anyi auren ka dinga sulalawa wajen yarinyar dakake rainawa kana sauke damuwarka ba".
Rarume ramume yafara kan gadon neman abinda zai jefi Mukhtar d'in dashi saidai ba komi sai k'ananun pillows sukuwa ya d'auka ya jefa masa tanajin wani takaici saboda Mukhtar yace zai nemi wani abu a wajen Ayshaa.
Cab'e pillows d'in yayi yanata k'yalk'yala dariya, dama tsokanarshi kawai yazo yi ya kuma sashi magana.
Tashi yayi yana cigaba da dariyar shi yace
"Toh sainazo ka rakani d'in". Ya fice da sauri ganin Saif yana niyyar mik'ewa tsaye.
Komawa yayi ya zauna yana shafa kanshi, saikuma ya d'an saki murmushi yanason Mukhtar kamar yadda shima yake sonshi abota ce suka k'ulla ta ALLAH da Annabi ta yadda idan d'aya ya shiga damuwa d'ayan yakejin kamar shine acikin damuwar, Mukhtar yasan takan tsokana da sashi magana duk yadda yakai ga rashin son magana indai yayi niyya to saiya sashi yayi saboda yadda zai dinga tsokanarshi bashida wani aboki daya wuceshi. Har yanzu idan ya tuno maganar da Mukhtar d'in yace zai nemi wani abu gurin Ayshaa sai yaji dama Mukhtar d'in yana kusa ya kafta masa rashin mutunci, k'wafa yayi ya mik'e ya shige bathroom.
★★★
Weekend ne washegari ba aiki dan haka yasha barcinshi sosai sai wajen k'arfe sha biyu da y'an mintuna ya tashi, wanka yayi, yayi shirinshi cikin k'ananun kaya black jeans da red shirt mai dogayen hannu black agogo ya d'aura yasa black shoes sawu ciki, sai jacket ash color daya d'ora kan rigar yayi matuk'ar yin kyau cikin kayan sai zuba k'amshi yake mai dad'i.
Phone d'inshi ya d'auka da key d'in motarshi ya fito tareda rufo k'ofar side d'in nashi.
Kai tsaye dinning ya nufa saboda cikinshi daya fara sauyawa alamun yunwa dan jiya da dare coffee kawai yasha ya kwanta duk da dama bai cika cin abu mai nauyi da dare ba.
Yana cikin zuba tea a cup Mamie ta fito itada Imaan.
''Gud morning Yah Saifu''. Imaan ta fad'a tana d'an rissinawa.
"Morning". Yace shima yana zamowa ya gaida Mamie ta amsa tana fad'in
"Yau weekend anata shan hutu ko''.
"Eh,Mamie". Yace yana komawa kan kujerar ya cigaba da had'a tea d'in.
"Am idan zaka fita zaku tafi da Imaan ka sauketa gidan su mamana".
Cak ya tsaya da had'a tea d'in yana kallon Mamie shifa baison abinda zai dinga had'ashi da wannan yarinyar''.
"Meye kake kallona ko bazaka bane?". Mamie tace fuskarta ba alamun wasa, dan yadda ya had'e ran nan yana iya cewa Imaan d'in bazata ba ya soke tafiyar Imaan kuwa tuni ta sulale tabar wajen ta koma cikin parlor'n tana addu'ar ALLAH yasa ya barta zuwa.
Kai ya d'an juyar ya b'ata fuska sosai yace
"Mamie driver bazai iya kaita ba, sauri nake ni please". Ya k'arasa yana wani marairaicewa duk dan kar Mamien ta takura masa.
''Ai daya sani bazance ka kaitaba tunda kai bakasan zuru ba tun ranar daka maida mamana gida ka k'ara zuwa gidan?''.
Kai ya girgiza kawai batare dayayi magana ba.
K'aramin tsaki Mamie taja tace
"Kanada matsala babana, a haka za'ayi auren?, Ba zuwa ba waya ta yaya zaku fahimci juna fisabilillahi fa babana''.
"Mamie to me zanje inyi dan ALLAH wajen k'aramar yarinya ta raina mutane kawai". Baki Mamie ta kama tana kallonshi yadda yayi kicin kicin da fuska.
Kad'a kai tayi tana fad'in
''Koma dai jaririyace a haka zaka aureta, kagama break d'in kuma ka kaita idan zaka dawo kuma ka biya ka taho da ita".
Badan yanaso ba ya amsa mata, itakuma tabar wajen.
Sama sama yayi breakfast d'in ya tashi ya nufi k'ofar fita, wani mugun kallo yabi Imaan dashi sannan ya fice, gwalo tabi bayanshi dashi sannan ta tashi tabi bayanshi.
Mrs Salees Mu'az❤️
*DR. SAIF*
@Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No 13.
Imaan tasha hantara a hanya tamkar zai rufeta da duka, itadai damuwarta suyi su isa kafin ya maujeta.
A bakin gate yayi parking ya kalleta ya zabga mata harara yace
"Fitar min a mota".
Mamaki ya kama Imaan nufinshi nan zai ajiyeta?.
Cikin tsoro muryarta na d'an rawa tace
"Yah Saifu Mamie fa tace ka shiga ku.....baki ya bige mata tare da daka mata tsawa, ba shiri ta fice tana dafe da bakinta kamar zatayi kuka.
Da gudu ya figi motar yabar layin, riq'e k'ugu tayi tana binshi da kallo har motarshi ta b'ace mata da gani.
"Huhh mutumin nan dole mu dinga sashi a addu'a banda jaraba da masifa da k'uncin tsiya ba abinda ya iya masifaffe kawai", baki ta tab'e ta juya ta nufi gate d'in tana lalubo phone d'inta cikin side bag d'inta dan kiran Ayshaa.
Ayshaa na kwance bayan ta gama karatun Alqur'an a wayarta ta ajiyeta gefe barci nason d'auketa kiran Imaan ya shigo mata, picking tayi idanunta a lumshe tayi sallama
Amsawa Imaan tayi tana fad'in
"Aunt Ayshaa gani bakin gate d'inku".
Zaune ta tashi da sauri cikin murna tace
"Dan ALLAH da gaske kike koda wasa?''.
Dariya Imaan tayi tace
"ALLAH kuwa Aunt Ayshaa da gaske nake".
"Ok Ina zuwa''.
Hand up d'in wayar tayi ta tashi ta yafa vail d'in doguwar rigar dake jikinta ta zura slipper ta fice.
Kai tsaye bakin gate d'in ta nufa ta bud'e k'ofar gate d'in, Imaan d'in na tsaye ta riq'o hannunta suka rungume juna suna dariya cikin farin ciki.
K'ofar ta rufe suka nufi cikin gidan hannunsu riq'e dana juna.
"Zauna bari in kirawo Aunt Salma". Ayshaa ta fad'i bayan shigarsu parlor'n.
Bedroom d'in Aunt Salma ta shiga tana sallama, Aunt Salman tasamu tana jera kayanta cikin wardrobe wanda aka kawo daga gurin wanki da guga.
Kallonta Aunt Salma tayi tace
"Wannan fara'ar kuma fa?"
Jikin mirror ta jingina tana fad'in
"Wllhy Aunt Salma Imaan ce tazo yanzun nan".
"Imaan, Imaan". Aunt Salma tace cikin rashin fahimta.
"Sister'n wannan Dr'n".
"OH lallai ta kawo miki ziyara kenan, toh sannunta da zuwa kije gani nan zan fito''.
Fita tayi ta koma wajen Imaan suka gaisa tana tambayar lafiyar Mamie.
Aunt Salma tazo suka gaisa tana tambayarta su Mamie.
"Lapia k'alau wllhy Aunt Salma tana gaisheku keda Ikraam,(tasan sunanta tun zuwan da Ayshaa tayi har picture's d'inta duk tagani a wayar Ayshaa kuma tana d'an yawan d'orata kan status d'inta).
Cikin murmushi Aunt Salma tace
"Muna amsawa, Ikraam taje weekend gidansu abbanta sai gobe zata dawo insha ALLAH".
"Ayyah ALLAH sarki ALLAH ya dawo da ita lapia". Imaan tace tana murmushi.
Hannun Imaan Ayshaa ta kamo tace
"Taso muje ciki".
"Haka zaki jata bataci komiba?''. Aunt ta fad'i tana kallon Ayshaa.
"Aunt Salma abawa Mariya takawo mata bedroom d'in". Ta bata amsa suna nufar inda zai sadasu da bedroom d'in Ayshaan.
Kan bed suka zauna suna k'ara wata sabuwar gaisuwar.
Da mamaki Ayshaa tace
"Wai waya kawoki ne naganki a bakin gate ba'a shigo dake ciki ba?''.
''Hmm bari kawai aikin mutumin kine wllhy".
Yamutsa fuska Ayshaa tayi tace
"Wa fa?''. Duk da tasan dai bazai wuce mara M d'in yayanta ba.
"Wa kika sani banda Yah saifu, ai sai shi dama a fusace yake ance ya kawoni shine ya zubeni a waje ya k'ara gaba''. Ta k'arashe maganar tana turo baki.
Dariya Ayshaa tayi tana shirin magana Mariya tayi sallama ta shigo hannunta d'auke da babban tray da aka d'ora ruwa da cup da juice sai sauran tarkace dai na snacks a wani plate d'in daban.
Gaban gadon ta ajiye ta gaishe da Imaan sannan ta fita.
Ayshaa ta zubawa Imaan juice ta mik'a mata.
Karb'a tayi ta fara sha kafin ta d'ago ta kalli Ayshaa tace
''Baki tambayeni lafiyar mijinki ba?".
Hararar ta Ayshaa tayi batace komiba.....duk yadda Imaan taso suyi hirar Saif Ayshaa tak'i yarda, dole ta hak'ura suka shiga wata hirar daban.
Yini guda ranar suna tare, sai wajen 6:12pm sannan Imaan taji kira ya shigo wayarta, lokacin ma suna zaune suna tashan hirar duniya dan wani irin mugun shak'uwa da sabo ne ya k'ara shiga tsakaninsu.
Ganin sunan Yah saifu yasa tayi saurin yin picking dan jinkirin d'agawar ma wani laifinne mai zaman kanshi a gurinshi dama gashi yana jin haushinta.
"Ina jiranki". Abinda ya fad'a kenan yayi hanging d'in wayar.
Tashi tayi ta d'auki mayafinta ta yafa ta rarumi jakarta ta sak'ala tana fad'in
"Toh Aunt Ayshaa sai mun k'ara had'uwa".
B'ata rai Ayshaa tayi tace
"Waike dagayin waya kin wani zabura kin fara shiri sai kace wadda dama take kan k'aya''.
Hannunta Imaan ta kamo ta mik'ar da ita tsaye tana fad'in
"Hmm bazaki gane bane Yah saifu bayason jira sam yanzu ba k'aramin aikinshi bane idan na b'ata masa lokaci yayi tafiyar shi ya barni''.
Baki Ayshaa ta tab'e cikin ranta take fad'in
"Jarababbe, a haka kamar bazaiyi masifa ba yayita wani k'asa k'asa da idanu taja tsaki.
ta janyo gyalenta na Pakistan d'in datasa, pink d'in wandone sai riga green iya gwiwarta anyi adon pink d'in duwatsu masu kyau da tsari ajikin rigar rolling tayi da mayafin kalar pink ta zura farin takalmi plat dake gaban gadon suka fice suka nufi bedroom d'in Aunt Salma danyi mata sallama.
Kyautar kayan kwalliya da turare Aunt Salma tayiwa Ayshaa sannan ta rakota har bakin k'ofar parlor'n tana bata sak'on gaisuwa gurin Mamie.
Duk zaton Ayshaa da Imaan yana wajen gate shiyasa ma ta fito, saikuma suka hango motarshi cikin harabar gidan Mukhtar na tsaye jikin motar yana danna waya.
Cogewa Ayshaa tayi daga nesa tana fad'in
"Toh Imaan nagode fa sosai da ziyara sai munyi waya ki gaida Mamie sosai dan ALLAH''.
Kallon ban ganeba Imaan tayi mata tace
"Haba Aunt Ayshaa mu k'arasa mana kinga mafa tare suke da Yah Mukhtar saiku gaisa.
Yana daga cikin motar yake hangosu a tsaye alamu sun nuna cewa Ayshaan ce tace bazata k'araso gurin motar ba Imaan din ke lalla6ata.
Tsaki ya saki ya maida kanshi kan wayar da yake latsawa.
"Nidai wllhy dan kin takuramin ne amma da bazanje ba". Ayshaa tace tana d'an hararar Imaan d'in.
Dariya Imaan tayi tace
"Eh, naji dai Yah Mukhtar bazaiji dad'i ba ace kin ganshi kuma kin koma kar laifin Yah saifu ya shafeshi". Ta k'arasa maganar tana jan hannun Ayshaan suka nufi wajen motar.
"Amma dai S.Matawalle mugun bahamage ne wllhy, yanzu wannan zuk'ek'iyar yarinyar yake wani b'acin rai da damuwa da k'untatawa kanshi dan zai aureta?, Mukhtar ke wannan zancen zucin lokacin dayake k'arewa Ayshaa kallo sanda suka nufosu.
Sallama sukayi bayan sun k'arasa Imaan tace
"Sannu da zuwa Yah Mukhtar Ina yini?''.
Murmushi yayi ya amsa yana maida wayar cikin aljihun wandon jeans d'in dake jikinshi ya hard'e hannayenshi a k'irjinshi.
Itama Ayshaa gaisheshi tayi, ya amsa yana tambayarta mutanen gidan ta amsa da suna lafiya.
Tsayuwarshi ya gyara yana fad'in
''Yau dai ALLAH ya nuna min wife to be d'in abokina Ina muku fatan alkhairi ubangiji yasa alkhairi a cikin aurenku''.
''Aamin Aamin Yah Mukhtar". Imaan ta amsa cikin jin dad'i, Ayshaa kuwa kauda kai tayi tana duban wani b'angaren daban.
"Toh Ayshaa saifa anyi hak'uri da halinmu dan mutumin nan nawa zama dashi sai hak'uri amma idan kikayi hak'uri kika fuskanceshi yanada kirki sosai kuma yanada dad'in zama hakane Imaan?''. Ya maida maganar kan Imaan.
"Nidai Yah Mukhtar bazan d'orar ba wllhy". Tace tana d'an turo baki.
Hararar ta yayi irin ba haka yaso ta fad'a d'in nan ba ta kwafsa masa, baki ta k'unshe tana y'ar dariya, itama Ayshaa dariyar ta d'an yi dan abin yabata dariya q'warai koma meye dai damuwarshi ba tata ba.
D'an mulkin kuwa yana mota ba alamun ma zai fito, sai tsaki yake saki akai akai cikin ranshi yake fad'in
"Ko uwar me yake fad'a haka?, Shiyasa baiso zuwa dashiba ya matsa masa.
itama kuma yaga alamun yarinyar ba biyawa ta kanshi zatayi ba, hakan yasa ya matsa daidai window motar ya k'wank'wasa glass d'in, sai dayaja aji ma kafin ya zuge glass d'in idanunshi kuma nakan wayar hannunshi.
K'asa k'asa Mukhtar yace
"Wai Matawalle wani irin wulak'anci ne wannan? Kana sane fa yarinyar nan tazo gurin nan amma kayi zamanka kak'i fitowa ku gaisa''.
Tankau Saif bai tankawa Mukhtar ba sai relaxing daya k'ara yi kan sit d'inshi yana wani lullumshe ido tamkar mai jin barci.
"Ko bakaji wai". Mukhtar ya fad'a cike da jin haushin halayyar abokin nasa aita faman magana wani tym d'in yai fumfurus yana kallon mutum batare daya kula mai maganar ba alhalin kuma yanaji, su Mamie ne kawai baya yiwa haka.
Lumshe ido yayi, ya bud'esu duka kan Mukhtar d'in cikin sanyin muryar shi yace
"Mukhtaaar kasani fa banason damuwa, kanafa takuramin dayawa".
Ayshaa kam labarin da Imaan ke batane yasata tsayawa da tuni ta bar wajen dan ta kula kamar lalla6ashi Mukhtar yake ya fito.
Imaan dariya take cikin zuciyarta, wato saidai a fafata kenan shi yanajin kanshi itama haka, har mamakin Ayshaan take na yadda take nuna halin ko in kula da yayan nata bayan shi d'in one in town ne mai gwara kawunan y'anmata d'ai d'ai macen dazatayi arba dashi bai tafi da imaninta ba, ko cikin y'an uwansu na b'angaren Mamie da Daddy akwai y'anmata masu d'inbin yawa dasuke so da k'aunarshi dan dai kawai basu samun fuska ne, amma ita Ayshaa ba ruwanta taji dad'i ma da Ayshaan take haka dan irinsu Yah Saifu idan suka auri macen da take mugun sonsu toh fa sai ALLAH dan ta shiga uku ta lalace da wulak'anci.
Magiya Mukhtar ya fara yimasa yai banza dashi saima rufe ido dayayi ya d'ora hannunshi kan goshinshi yana d'an bubbuga d'an yatsanshi manuniya kan goshin nashi.
K'wafa Mukhtar yayi ya tashi tsaye yace
"Banza mara mutunci,bakaji dad'in halinka ba wllhy, yayi tsaki ya k'ara gaba.
Yana jinshi uffan baice ba bashi kuma da niyyar cewan, Mukhtar kad'ai ke gaya masa magana son ranshi wadda duk yaga dama batare daya d'auki mataki ba.
Wajensu Ayshaa ya koma yana murmushi yace
''Toh amaryar mu zamu wuce sai mun k'ara zagayowa kenan?''.
"Hmm ni bana gayyarku". Ta fad'a a zuci a fili tace
"Okay godiya nake, Imaan karfa ki manta da sak'on gaisuwata gurin Mamie".
Insha ALLAH Aunt Ayshaa nagode sosai''. Imaan ta amsa tare da bud'e back seat ta shiga shikuma Mukhtar ya zagaya ya shiga front seat, Saif ya tada motar yana jiran maigadi ya bud'e masa gate, yana bud'ewa kuwa ya fice da gudu had'uwarsu dashi ta fahimci bai iya bin mota a hankali ba uban gudu yake shararawa, tsaki taja tana tab'e baki ta juya ta koma ciki.
★★★
KADUNA.
Safnah.
#Comments.
#Vote.
#Share.
Gyara ko k'orafi za'a tuntub'i wannan number
09139964697.
Mrs Salees Mu'az❤️
*DR. SAIF*
@Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No 14.
Shiru motar ta d'auka bayan tafiyar su Imaan kuwa kanta na k'asa bata k'ara gigin d'agowa ba tun had'a idon da sukayi da Saif ya jefa mata wani mugun kallo tana jin Mukhtar na faman zaginshi kan abinda yayi masa bai tanka masaba dama kuma yasan ba tankawar zaiyi ba.
Koda yayi parking bai fitoba Imaan ta fito shima Mukhtar fitar yayi yana cewa
"Idan kagama bak'in ran naka Ina ciki zamu gaisa da Mamie, tare suka jera da Imaan suka nufi cikin gidan.
Mamie na parlor tana kallon tana sauraron karatun Alqur'ani mai tsarki a tashar Alqur'an TV suka shigo parlor'n.
Fad'ad'a fuskarta tayi da fara'a tana amsa sallamar su, gefenta Imaan ta zauna shikuma Mukhtar ya zauna a 1sitter dake facing d'insu yana gaida Mamie ta amsa cikin sakin fuska kafin ta kalli Imaan tace
"Inata zuba idonki tun d'azu naji shiru mamana ta riq'e ko?''.
"Wllhy Mamie, yanzun ma kamar kar in taho tace tana gaisheki Aunt Salma ma tace a gaisheku''.
"Ina amsawa fatan duk suna lafiya''.
''Lafiya k'alau Mamie".
Kallon Mukhtar Mamie tayi tace
"Ya naganku ku biyu kawai Ina abokin naka?''.
Dariya Mukhtar yayi yace
''Yana can Mamie a mota yana bak'in rai''.
Girgiza kai Mamie tayi tana murmushi kafin tayi magana Saif ya shigo parlor'n bakinshi d'auke da sallama, k'asa ya zauna kusa da k'afafun Mamie yana mata barka da yamma.
Tana amsawa kuwa yatashi yabar wajen ya nufi side d'inshi Imaan ma ta tashi ta nufi nata bedroom d'in.
Mukhtar kuwa saida suka d'an tab'a hira da Mamie sannan ya tashi yayi b'angaren Saif.
Zubar ruwan dayaji a bathroom ne ya tabbatar masa da Saif d'in wanka yake, kan sofa ya zauna ya zaro wayarshi ya fara latse latse(zama da Saif shima ya koyi danna wayar tsiya).
Bai dad'e da zamaba Saif ya fito daga toilet boxer ne kawai a jikinshi sai k'aramin towel dayake kanshi yana goge sumarshi.
Ko kallon inda Mukhtar yake baiyi ba ya nufi wajen mirror ya d'auko cream yadawo gefen gado ya zauna yana cigaba da goge jikinshi sannan ya fara shafa man a jikinshi dariya ma yaba Mukhtar ganin yadda yake wani basarwa yana hura hanci, wayar hannunshi ya ajiye kan cinyarshi yana kallon Saif d'in yace
"Gaskiya Matawalle abinda kake bai daceba kag...... kamar jira yake dama ya katseshi da fad'in
"Ubanka nayi banason iskanci fa".
Ido Mukhtar ya d'an zaro yana y'ar dariya yace
"Yi hak'uri bawan ALLAH maida wuk'ar, nidai shawara zan baka karka yadda Ayshaa ta sub'uce maka wllhy da kake ik'rarin yarinya ce tsaf zata d'auke maka duk wata damuwarka malam".
"Banason shawarar taka". Yace yana mik'ewa ya isa wajen mirror ya ajiye cream d'in ya k'arasa wajen clothes d'inshi yana neman kayan dazai saka.
Mik'ewa Mukhtar yayi yana tab'e baki yace
"Aikin gama ma ai ya riga yagama mutumina saidai hak'uri, nina wuce saimun k'ara had'uwa''.
Bai saurari cewar Saif ba ya fice yana dariya abinda ya k'ara harzuk'a Saif kenan lumshe ido yayi tare da hura iskar bakinshi yana sauke numfashi.
★★★
KADUNA.
Safnah.
Tunda taji labarin auren Saif hankalinta yayi matuk'ar tashi abin ya mugun d'aure mata kai ganin cewa itadai bata tab'a jin ko ganin ance yau ga budurwar Saif ba saidai kawai aji maganar aure katsam? Tun kafin taga matar dazai aura tajj tayi mugun tsanarta saboda tana k'ok'arin rabata da rayuwarta dan Saif shine mahad'in rayuwarta kamar zata zauce tsabar bak'in ciki uwar ce tasata a gaba tana rarrashi da nuna mata karta damu da aurenshi itama dole saiya aureta koda kuwa yanaso ko bayaso tayi mata alk'awari, hakan yasa ta d'an kwantar da hankalinta ammafa zuciyarta cike take da fargaba da tashin hankali ganin abin take kamar ba gaske ba, wannan wace mai sa'ace haka da har Saif ya bud'e baki ya furta mata kalmar *SO* lallai da sake bazata tab'a bari Saif ya kub'uce mata ba, a shirye take tsaf tarasa duk wani abu data mallaka indai zata samu Saif d'inta bugun numfashinta.
Ko a wajen aiki saida aka gano tana tare da damuwa musamman ma k'awarta aminiyarta Mansurah itama d'in data fad'a mata damuwarta kwantar mata da hankali tayi ta nuna mata cewa saidai idan bataso mallakar Saif ba amma ita zata taimaka mata zata kaita inda za'a share mata hawayenta ta saki ranta Saif saiya zama nata kuma saita juyashi a hannunta yadda take so da wannan maganar Safnah taji hankalinta ya k'ara kwanciya take jin tamkar ma ta auri Saif ne ta gama.
Afwan batawa dai.
Ko burin Safnah zai cika na auren Saif???.
#Comments.
#Vote.
#Share.
Hanyar gyara a bud'e take
09139964697.
Mrs Salees Mu'az❤️
*DR. SAIF*
@Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No 15.
Gaba d'aya zaman garin na Abuja ya gunduri Ayshaa kawai so ta ganta a gida jikin Amminta dan haka ta uzzurawa Aunt Salma itafa gida take son tafiya, duk wani rarrashi da ban baki Aunt Salma tayi amma Ayshaa ta k'ek'asa k'asa tace itadai wllhy gida zata, ba yadda Aunt Salma ta iya dolenta ta fara yimata shirin tafiya badan ranta naso ba dan Ayshaa tana d'ebe mata kewar su Ammi.
Ranar alhamis tunda safe direban su Aunt Salma yatafi kai Ayshaa gida kano ta dabo tumbin giwa koda me kazo an fika.
Tayi matuk'ar murna da ganin Amminta ta rungumeta tana kukan shagwab'a, itama Ammin cike da jin dad'in ganin autar tata ta d'ago fuskarta tana murmushi tace
''A'ah yau naji shagwab'a kukan kuma na meye?''.
"Ammi nayi missing d'inki ne sosai wllhy". Ta k'arasa maganar tana share hawaye.
Murmushi Ammi tayi tana tayata share hawayen tace
''Toh kukan ya isa haka tunda kin ganni ya zakiyi kenan idan kikayi aure''.
Jin kalmar aure yasa ta k'ara rushewa da wani sabon kukan Ammi ta shiga rarrashinta tana k'ara kwantar mata da hankali itadai harga ALLAH tana matuk'ar son auren nan duk da bawai ta tab'a ganin yaron bane amma ya kwanta mata a ranta fatansu dai ALLAH ya zaunar dasu lafiya ya kad'e duk wata fitina.
Lallab'ata tayi tace taje bedroom d'inta tayi wanka tazo tayi lunch, tashi tayi tana faman matse ido ta d'auki hand bag d'inta ta nufi bedroom d'in nata jitake dama bataje Abuja nan ba da yanzu tana nan hankalinta kwance zata cigaba da karatun ta.
Mamie ma a bakin Imaan take jin tafiyar Ayshaa da sukayi waya take fad'a mata tabbas datasan da tafiyar da Saif zatasa ya maidata yanzun ma kuma dolenshi bayan kwana biyu yaje wajenta su kuma gaisa dasu Amminta.
***
Bayan sati biyu.
Gama dinner d'insu kenan ya tashi zaibar wajen Mamie ta dakatar dashi, komawa yayi ya zauna yana sauraron ta bayan ya kalli Imaan, tasan ma'anar kallon dan haka ta tashi tabar wajen duk da bata gama cin abincin nata ba, saida Mamie ta yagi tissue ta goge bakinta sannan ta maida hankalinta kanshi tace
"Naga alamun idan na zura maka ido to kai bakasan abinda ya dace da wanda bai dace ba ko?".
Da alamun rashin fahimta yake kallonta yace
"Mamie meya faru?''.
"Maganar mamana mana, saboda ALLAH tunda ta tafi ka kirata a waya koda sau d'aya ne? Kayi tunanin zuwa inda take ku gana da ita ku gaisa da iyayenta da y'an uwanta?''. Mamie ta k'arasa maganar tana kafeshi da idanunta.
K'asa yayi da kanshi yana sosa k'eya, shifa harga ALLAH yama manta da wata Ayshaa sam badan yanzu da Mamie tayi maganar taba saboda ba'a gabanshi take ba kuma bai masan ta tafi ba (zakayi bayani ne d'an k'wal uba).
Mamie ta cigaba da fad'in
"A haka zasuji dad'in baka y'ar kana nuna baka damu da ita da al'amuranta ba, kar kayi la'akari da amintakar dake tsakanin Daddy da Abbanta bazasuji dad'i ba koni da ace misali yaronsu ne yake yiwa Imaan haka dole zanji ba dad'i, to ka kiyaye banson muyi ta magana d'aya dakai akanta kafi kowa sanin idan raina ya b'aci bazakaji da dad'i ba''.
"Insha ALLAH Mamie zan gyara". Yace har lokacin kanshi na k'asa.
Murmushi Mamie tayi tace
"Toh ko kaifa, abinda taimaka maka ma maman nawa zatayi yadda kake gwaron nan'' tayi maganar cikin zolaya tana y'ar dariya dan Mamie macece mai barkwanci da wasa da dariya.
"Haba Mamie dan ALLAH". Yace yana b'ata fuska.
"Atoh ai gaskiya na fad'a kaida Mukhtar d'in bansan wanda yafi wani shiririta ba shima har yanzu ya kasa tsayawa ya fitar da matar aure sai shirme kuka iya''.
Girarshi ya d'an sosa yana fad'in
"Mamie yasamu wadda yakeso matsalar dai daga gidansu yarinyar ne wai akwai wanda babanta yayiwa alk'awarin aure".
"Tohh, ALLAH dai ya zab'a mafi alkhairi".
Da "Aamin" ya amsa yana shirin tashi Mamie ta k'ara cewa
"Zauna ai bamu gamaba.
Komawa yayi ya zauna yana addu'ar ALLAH yasa ba cewa zatayi yaje ba.
Aikuwa dai addu'arshi bata ciba dan tun kafin ya k'arasa zama yaji Mamie tace
"Ahm, jibi idan ALLAH ya kaimu tunda weekend ne saika shirya kaje ko''.
"Amma Mamie kin......hannu ta d'aga masa alamun yayi shiru, shirun yayi kuwa yana d'an lumshe ido.
"Bazan karb'i uzurinka ba malam kayi abinda nace kawai inba haka ba kuma ranka ya b'aci''.
Numfashi ya sauke yace
''Toh Mamie zanyi yadda kikace insha ALLAH''.
"Tashi kaje ALLAH yayi maka albarka". Tayi maganar fuskarta a had'e.
Tashi yayi yana satar kallonta yaga yadda ta had'e rai duk saiyaji ba dad'i sam bayason Mamien shi taji ba dad'i akanshi.
"Mamie nace fa zanje". Yayi maganar cikin shagwab'a kamar k'aramin yaro bayan ya matso kusa da ita ya kama hannayenta.
Fuska ta saki tace
"Toh naji jeka saida safe''.
Sakin hannunta yayi yana fad'in
"Good nyt Mamie".
"ALLAH ya tashemu lafiya". Ta amsa masa shikuma yabar wajen.
****
Washegari Mamie ta kira Ammin Ayshaa suka gaisa bayan sun d'an tab'a hira take fad'a mata zuwan Saif, Ammi tace
"ALLAH ya kawoshi lafiya".
Mamie ta amsa da
"Aamin" tana tambayar Ayshaa, Ammi tace yanzun nan ta shiga bedroom d'inta, Mamie na y'ar dariya tace
"Toh a kiramin d'iyata kuma mamana mu gaisa".
Dariya Ammi tayi ta juya tayiwa salamatu mai aikinta dake ta shirya lunch a dinning table alamun tazo da hannunta.
Da saurinta ta k'araso ta d'an rissina tace
"Hajia gani".
"Kiramin Ayshaa a bedroom''
''Toh Hajia''. Ta fad'a cikin girmamawa tare da mik'ewa ta nufi inda zai sadata da bedroom d'in Ayshaan, Ammi kuma suka cigaba da hira da Mamie.
Tana shirin shiga toilet tayi wanka salamatu tazo tace Ammi na kiranta, k'aramin hijab tasaka tabi bayan salamatun zuwa parlor.
Kusa da Ammi ta zauna tana fad'in
"Ammi gani".
Wayar ta mik'a mata tace
"Mamien kice daga Abuja zaku gaisa''.
Murmushi tasaki tana karb'ar wayar ta kara a kunnenta, cikin ladabi kamar tana gabanta ta gaisheta ta amsa murya a sake ta d'ora da fad'in
"Sai kuma Imaan take fad'amin kin gudu kano ko sallama babu''.
Murmushi tayi cikin jin kunya tace
"Mamie nayi kewar Ammi ne shiyasa na gudo".
Dariya Mamie tayi tace
"Toh ai mun kusa d'auke ki gaba d'ayanki kizama tamu".
D'if tayi ta rasa abinda zatace jin haka yasa Mamie tace tabawa Ammi wayar , Ammi ta mik'awa wayar bayan tace a gaida mata Imaan.
Ammin ma sallama sukayi suka kashe wayar.
Tana shirin tashi taji Ammi tace
''Gobe idan ALLAH ya kaimu Saifullahi zaizo saiki shirya''.
Zama ta koma tayi, haka nan batasan dalilin fad'uwar gabanta ba, tana turo baki tace
"Ammi mezaizo to yayi?''.
"Ban saniba". Amsar data samu kenan a wajen Ammi tana mik'ewa ta nufi dinning inda salamatu tagama shirya komi tun d'azun.
Tashi tayi tana zumb'uro baki ta tafi bedroom sai faman k'unk'uni take.
#Comments.
#Vote.
#Share.
Mrs Salees Mu'az❤️.
*DR. SAIF*
@Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No 16.
Washegari tunda ta tashi ta lafke ita a dole batada lafiya, Ammi batabi ta kanta ba dan tasan k'arya take bawata rashin lafiya.
Ammi da kanta ta shiga kitchen tare da taimakon salamatu suka shirya had'add'un girke girke kala biyu sai snacks da coconut juice sai zo6o da shima yasha had'i na musamman.
Ranar Saif ya dinga nema neman uzurin dazai bawa Mamie wanda zai hanashi zuwa kano saidai bai samuba dan haka ya hak'ura kan dole yafara shirin tafiya.
Dakakkiyar shadda bugaggiya da take ta faman k'yalli da maik'o wadda kallo d'aya zakayi mata ka fahimci cewar naira tayi kuka gurin siyanta, riga da wandone d'inkin zamani da kad'an rigar ta wuce masa gwiwarsa milk color ce da akayiwa aiki da light coffeen zare ya murza hula zanna bukar mai adon milk da coffeen zare links d'in hannunshi ma coffee ne sai agogon fata coffee dayayi mugun hawa da dutsen azurfar hannunshi takalmi yasa coffee mai mad'auri kamar sandal ya feshe jikinshi da turaruka masu matuk'ar k'amshi (dole ya dinga sace zuciyar yan mata), yayi kyau ainun Masha ALLAH.
Duk shirin nan dayake fuskar nan kamar kullum tana tamke, tsaki kuwa yayishi har ba adadi gaba d'aya baison tafiyar nan zai yitane kawai saboda Mamie.
Side d'in nashi ya kulle ya fito, ganin Mamie a parlor'n ne yasa ya d'an saki fuska ya k'arasa kusa da ita ya zauna.
"Masha ALLAH". Mamie ta fad'a tana kallonshi ganin yadda yayi matuk'ar yin kyau, Imaan ma na daga gefe tana yaba kyawun yayan nata saidai ba damar ta fito ta fad'a.
Cikin murmushi Mamie tace
"Harka fito kenan?''.
"Eh, Mamie ayi mana addu'a''. Yace yana mik'ewa tsaye.
"Toh ubangiji ya kiyaye ya kaika lafiya ya dawo dakai lafiya, Imaan d'auko min wata jaka a side drower''.
Tashi Imaan tayi ta haura upstairs ta d'auko ta kawo mata wata y'ar kyakkyawar jakace pink color mai zanen flowers ta mik'a masa tana fad'in
"Ga sak'ona wajen mamana ka gaishesu da kyau.
Karb'a yayi yana b'ata rai yace
"Nifa Mamie kamar ma kinfi sonta yanzu''.(d'an bak'in ciki).
Dariya Mamie tayi cikin zolaya tace
''Ai hakane ma ka cire kamar d'in".
"Kai Mamie ai tawace ni kad'ai".
Mamie tana dariya tace
"Ina kakai sauran?''.
Murmushi ya d'an yi yace
"Suma karasu kawai ake".
"Hmm wani lokacin kamar bashi ba". Imaan dake gefe kan kujera ta fad'a cikin ranta tana d'an tab'e baki.
Dariya Mamie tayi tace
"Toh naji sauka lafiya dan ALLAH kayi tuk'i a hankali dan nasan halinka sarai baka yiwa mota ta sauk'i shiyasa nace ma ka tafi a jirgi kace kai tafiyar mota zakayi, ALLAH ya kiyaye hanya''.
Da "Aamin", ya amsa yana tashi tsaye ya nufi k'ofar fita.
"Yah Saifu a gaisheta ALLAH ya tsare''.
A ciki ya amsa mata da
"Aamin" yana k'arasa ficewa daga parlor'n.
Parking lot ya nufa ya shiga motarshi ya zauna sosai idanunshi a lumshe ya fara karanto addu'a, ringing d'in wayarsa ne yasa ya bud'e idonshi ya sauke su kan wayar dake gefenshi wadda bayan shigarshi ya jonata a charge my friend sunan daya gani yana yawo bisa screen d'in wayar shareta yayi bai d'aukaba har kiran ya katse wani ya k'ara shigowa ya k'ara katsewa bai d'auka ba, sai daya gama addu'arshi tsaf sannan yasa hannu ya cirota yabi kiran Mukhtar d'in.
Koda Mukhtar d'in ya d'aga ma shiru yayi baice komiba, Mukhtar yace
"Banza d'an wulak'anci uwar mi kake inata kira baka picking?''.
"Ban saniba malam fad'a min dalilin kiran Ina sauri".
"Kana gidane?". Mukhtar ya tambaya.
Sai dayaja aji kafin yace
''No, Ina motane yanzu zan wuce kano wani abune?''.
"Me zakaje yi kuma kano?, Kafin yace wani abu Mukhtar ya saki dariya yana fad'in
"Ohhhhh na tunafa Imaan tacemin Ayshaa ta koma gida zakabi sawunta kenan ko shine ba neman d'an rakiya?''.
"Damuwa ce banaso kai kuma gaba d'ayanka damuwarce". Ya bashi amsa cikin k'osawa dan ya fara gajiya da shegen surutun Mukhtar d'in.
"Au hakane fa kar inje inyi disturbing d'in lurv bird nagane kag......tsaki yayi ya katse wayar ya maidata charge d'in, yana fad'in
"Ko uwarshi ya kira ya fad'amin shege sarkin surutu". Wani zubin har mamakin Mukhtar yake yadda yake da magana ko gajiya bayayi(kowa ma irinka ne dunkum).
Yana gani wani kiran ya k'ara shigowa ya shareshi dan idan ya biye masa b'ata masa lokaci zaiyi, kuma yau yakeson juyowa, text message ne daya shigo phone d'insa yasa ya duba yaga Daddy ne ya turo masa address d'in gidansu Ayshaa numfashi ya sauke a hankali yana hura iskar bakinshi yaja seat belt ya kafin ya tada motar ya fice dama already maigadi ya bud'e masa gate.
****
Ayshaa na hango kan gadonta, da waya a hannunta tana game tanajin motsin shigowa bedroom d'in tayi saurin cusata k'asan pillow ta janyo blanket ta k'udundune, tsaf Ammi ta ganta saita bata dariya ma murmushi tayi ta k'arasa bakin bed d'in ta yaye blanket d'in tana kallon Ayshaa data wani narke ido tana kallon Ammin.
"Tashi Ayshaa kiyi wanka ki shirya kafin Saifullahin yazo".
"Ammi banida lafiya fa". Tace tana wani shasshakewa ita marar lafiya.
"Toh ya za'ayi dashi kenan idan yazo?''. Ammi ta tambaya tana matse dariyar ta.
"Ammi kawai basai ku gaisa ba ace masa banida lafiya bazai samu ganina ba''.
Tsaki Ammi taja tace
"Dallah malama tashi kije ki shirya tun kafin ranki ya b'aci haka dama marasa lafiyar suke, ko kin zata ban ganki kina danna waya ba dana shigo?".
Ganin Ammi ta ramfo ta yasa ta tashi zaune tana tura baki.
"Oyaa quickly now". Ammi tace tana kallonta.
Saida Ammi taga shigarta bathroom sannan ta fita daga bedroom d'in tana dariyar Ayshaa.
"Wllhy badan Ammi ba da tsofaffin kaya ma zan saka nasan kona sa saina ciresu''. Cikin turo baki tayi maganar tana tsaye gaban wardrobe d'inta tana laluben kayan dazata saka.
Idanunta suka kai kan wata shadda dabata tab'a sawaba dan daf dazata tafi Abuja aka kawo d'inkin dazata tafi kuma bata tafi dasuba.
Light purple ce shaddar doguwar riga ita ta janyo tasa sai faman k'unk'uni take, sosai rigar ta fitar da zubi da k'irar da ubangiji yayi mata saboda ta d'an matse daga sama k'asan kuma ya bud'e sosai.
Simple makeup tayi kamar yadda ta saba, powder da lipstick sai kwalli sai eye shadow data d'an goga saman idonta kalar purple, necklace and earring fashion duk purple tasaka tayi d'aurin ture kaga tsiya ta shafa turare sannan ta zauna gefen gado ta d'auki waya ta shiga dannawa.
Ammi na bedroom salamatu tayi sallama daga bakin k'ofar bedroom d'in tana jiran a bata iznin shiga.
"Shigo mana salamatu". Ammi tace tana kallon bakin k'ofar.
Shiga tayi, ta durk'usa tace
"Barka da hutawa Hajia".
"Barka dai". Ammi ta amsa mata tana kallonta dan jin abinda zata fad'a mata.
"Yawwa dama Ilah mai wankine ya shigo yake sanar da bak'on da zaizo".
"Okay ungo wannan ki kaiwa Ilahn kice ya bud'e masa sitting room ya shiga kafin Ayshaan tazo''. Ta fad'a tana janyo side drower dake kusa da ita ta d'ebo keys guda uku ta mik'awa salamatun.
Hannu biyu tasa ta karb'a ta tashi ta fice dan kaiwa Ilahn makullan.
Tashi Ammi tayi ta nufi bedroom d'in Ayshaa ta bud'e ta shiga.
"Masha ALLAH autata kinga yadda kika fito kuwa", Ammi tace cikin yaba kwalliyar Ayshaan.
Baki kawai ta d'an turo ta kauda kai.
Murmushi Ammi tayi tace
"Taso muje gashi can yazo yana sitting room d'in Abbanku.
B'ata fuska tayi tace
"Kuma Ammi daga zuwanshi sai inje''.
Had'e rai Ammi tayi tace
"Toh me zaki tsaya yi tashi ki wuce kafin ranki ya b'aci''.
Baki ta tura ta d'auki mayafinta light purple dake gefenta ta yafa ta nufi gurin takalmanta ta zura wani fari mai d'an tudu ta fito.
Kitchen Ammi ta nufa tana fad'in
"Zoki tafi da wadannan kayan''.
"Ammi ni zan d'auki ma kayan dan ALLAH salamatu ta kawo mana". Tace harda buga k'afa a k'asa.
A fusace Ammi ta juyo tana harararta tace
"Ke d'in ke zaki kaisu zan b'ata miki yanzun nan wllhy dan iskanci duk abinda akace saikin musawa mutane?, To ki kiyaye ni wllhy zoki wuce''.
Gaba ta wuce Ammi tabi bayanta har zuwa kitchen d'in.
Babban basket ne mai kyau da tsari da aka zuba komi a ciki.
''D'auki ki wuce". Ammi tace fuskarta ba alamun wasa.
Hannu tasa ta d'auka taji da d'an nauyi, kamar zatayi kuka tace
"ALLAH Ammi da nauyi fa d'auki kiji".
Kad'a kai Ammi tayi tace
"Eh, haka nan zaki d'auka aiba gagararki zaiyiba".
Haka Ammi ta k'ara tasota a gaba suka fito Ammi ta zauna itakuma ta nufi k'ofar fita tana zumb'ure zumb'uren baki.
"Saura kuma kije kiyi masa d'iban albarka nasan halinki sarai idan ba tsiya akayi dakeba ba'a shiryawa dake''. Taji muryar Ammi na fad'a daf dazata fice daga parlor'n.
Yana zaune kan d'aya daga cikin k'ayatattun kujerun parlor'n kanshi a k'asa yana danna waya tayi sallama a ciki ciki ta shigo sai haki take, shima d'in a cikin ya amsa mata dan har gara tata ta d'an fita shikam shiyaji amsawar tasa kawai.
"Mayen waya dama nasan ita zan tarar yana dannawa, yanaji kuma Ina sallama bazai amsaba saikace arne". Cikin ranta tayi maganar tana harararshi ta gefen ido.
Gabanshi kawai ta dire basket d'in ta juya ta koma ta zauna kan wata kujerar, bai d'ago ya kalleta ba kuma bai kalli abinda ta aje masa a gabanshi ba.
Cikin tutturo baki tace
"Ina yini''.
Har saidata fidda ran amsawa kafin taji yace
"Lafiya" shima d'in kamar wanda akayiwa dole da k'yar da k'yar ya amsa.
Tun daga nan kowa yaja bakinshi ya tsuke ba wanda yasake ko tari, Ayshaa duk zaman ya isheta gashi bata taho da wayarta ba sai sakin tsaki take cikin ranta tana harararshi ta k'asan Ido, shima d'in ta k'asan Idon yake kallon duk wasu harare harare datake, k'wafa yayi cikin ranshi yace
''Very very soon zai saitawa yarinyar nan zama yaga alamun kanta hayak'i yake inba haka ba shi Matawalle take wa haka?.
Sunfi k'arfin 30minutes a haka Ayshaa jitake kamar ta tashi ta bar wajen.
K'asa k'asa taji yace
"Zubamin abincin''.
Yi tai kamar bataji ba ta juyar da kanta gefe ta d'ora k'afa d'aya kan d'aya tana d'an girgizasu.
''Bakiji bane?''. Yayi maganar a fusace yana ajiye wayar kan cinyarshi, tashi tayi tana kumburo baki ta nufi Inda yake, itafa wannan isar tashi da mulkin ta tsana, a fusace ta k'arasa ta fito da plate d'in da snacks d'in ke cike ta dangwarar dashi a gabanshi ta fito da jug d'in da zo6o yake ciki ta zuba a glass cup din shima ta dangwarar dashi garin haka har yayi fallatsi ya zube ya fallatsar masa kuma a bakin wandon shaddarshi har k'afarshi sai daya d'an tab'a.
Wani huci ya saki yana lumshe ido ya bud'e kafin ya mik'e tsaye a fusace tabbas yarinyar nan saiya tsorata ta abin nata yayi yawa.
Tana shirin d'auko warmer a cikin basket d'in taga ya mik'e tsaye, d'agowa tayi ta kalleshi gabanta ne ya fad'i ganin yadda fuskarshi ta koma, tuni jikinta ya d'au rawa, da sauri ta mik'e ta nufi k'ofa da niyyar guduwa saidai taku biyu yayi ya rigata isa k'ofar ya zura sakata ya tsaya ya kama k'ugunshi da duka hannayenshi yana mata wani irin mugun kallo.
Tuni idon Ayshaa ya raina fata jikinta ya fara shaking sai zaro ido take.
Ganin ya nufota yasa ta fara ja baya, binta ya farayi yana fad'in
"Yau saina koya miki hankali saina fitar miki da duk hayak'in dake kanki", ya cire hularshi ya jefa kan kujera ya fara k'ok'arin cire links d'in hannunshi.
Ido ta k'ara k'walalowa sosai ta shiga girgiza masa kai hannunta rufe da bakinta tana shirin sakin kuka.
Ganin ya fara b'alle button d'in rigarshi yasa ta sakin wani k'aramin ihu ta shiga fad'in
"Wayyo ALLAH na shiga uku Ammi nah kizo ki taimakeni dan girman ALLAH kayi........"Shssshh'' yace yana zare mata ido gamida d'ora yatsanshi manuniya akan bakinshi, shirun tayi kuwa ta cigaba da yin baya baya tana girgiza masa kai ganin yana k'ara nufota gadan gadan ne yasa tace
"Dan Annabi kayi hak'uri wllhy ALLAH niba y'ar iska bace''.
Kai ya dinga kad'awa yana fad'in
"Ban tab'a fad'a miki Ni babban d'an iska bane farkon had'uwarmu?, Tantirine nan da kika ganni daya samu license a ma'aikatar iskanci''.
Cak ta tsaya jin ta k'urewa bango kai ta cigaba da girgiza masa tana kuka, a haka ya tarar da ita yasa hannayenshi duka ya tokare bangon yayi k'asa da kanshi yana kallon yadda take kuka.
Ta k'arfin tsiya ya d'ago kanta ya matse bakinta da hannunshi yana mata wani irin kallo ta k'asan Ido, rufe nata idon tayi hawaye suka gangaro kan fuskarta tsayawa yayi yana k'arewa eye lashes d'inta ido da suka kwanta sukayi zaro zaro saboda hawayen da suka jik'asu.
Bakin ya murd'e sosai cikin tsabar mugunta, ta kuwa saki k'arar azaba.
Cikin k'ank'ance ido yace
"Yaushe nafara wasa dake? Koni abokin wasanki ne? Kai ta girgiza tana ALLAH ALLAH ya sakar mata baki, sai daya k'ara murza lips d'in nata sannan ya saki aikuwa yana saki ta dafeshi tana hawaye.
"Wuce muje''. Ya fad'a cikin tsawa yana nuna mata hanya da kanshi, simi simi ta rab'e ta gefenshi ta wuce binta yayi da kallo yana fad'in
"Stupid girl bata iya komai ba sai rashin kunya".
"Anyi d'in". Tace a ranta tana murgud'a bakinta dayake mata mugun zafi.
Wajen basket d'in ta koma ta zauna ta fara fito da warmers d'in abincin, dawowa yayi ya zauna inda ya tashi ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya yana girgizasu ya shiga maida links d'inshi da button d'in rigarshi.
A nutse ta shiga zuba masa abincin white rice da aka dafata da carrots da green beans...
#Comments.
#Vote.
#Share.
Mrs Salees Mu'az❤️
*DR. SAIF*
@Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No 17.
Shinkafar ta zuba a plate ta zuba miyar hanta akai sai cow slow a gefe ta mik'a masa cikin ranta sai masifa take.
Bai karb'a ba sai daya k'arasa saka links d'inshi sannan ya amsa, tana bashi ta mik'e zata bar wajen cikin isa yace
"Ina zaki?''.
Sai data murgud'a baki dayake ta juya masa baya sannan tace
"Can zan koma".
Kai tsaye yace
"Dawo ki zauna".
Haushi kamar me, tadawo ta zauna tana kallon k'asa tanata maganganu cikin ranta ba damar dai ta fito fili tayi.
Ba'a jimaba taga ya ajiye plate d'in a k'asa kallon plate d'in tayi taga baima wani ci dayawa ba baki kawai ta tab'e.
Saida yayi y'an latse latsenshi a waya sannan ya mik'e tsaye yace
"Muje ki rakani wajen Ammi''. Yana fad'a yayi gaba abinshi tabi bayanshi da harara.
Yana gaba tana biye dashi har k'ofar parlor'n sannan ya dakata ya juyo ya d'an kalleta alamun ta wuce gaba, wucewar tayi yabi bayanta har zuwa cikin parlor'n.
Ba kowa lokacin da suka shiga parlor'n sai TV daketa aiki a tashar MBC Bollywood, kujera ya zauna ya hakimce itakuma ta tsaya gefen kujerar kanta a k'asa ganin batada niyyar kiran Ammin yasa ya kalleta yana wani k'ank'ance ido yace
"Zan samu damar da za'a yiwa Ammi magana?''.
Batayi niyyar amsawa ba ganin yadda ya tsareta da manyan idanunshi yasa ta gyad'a kai ta nufi bedroom d'in Ammin tanata masifa a zuciyarta, da kallo ya bita har ta shige wani corridor numfashi ya sauke tareda lumshe ido a had'uwarsu da yarinyar ya fahimci bata k'aunar a tab'a mata mutuncinta abu d'aya dazai bugi k'irji yace yaga abinda ya burgeshi tattare da yarinyar.
A bakin gado ta samu Ammi tana waya, jikin wardrobe ta tsaya fuskar nan k'iris take jira ta fashe da kuka.
"Yaya dai autar Ammi?''. Ammin ta fad'a bayan gama wayar tata.
"Kizo wai zaku gaisa''.
Cikin fara'a Ammi tace
"Yana parlor ne?''.
Ta amsa da ''Eh".
Mik'ewa Ammi tayi tana harararta tace
"Toh wannan cika da batsewar kuma na meye, wllhy Ayshaa ki kiyaye ni zanyi mugun sab'a miki fa akan lamarin nan ke idan ba'a yimiki tsiya tsiya ba ba'a shiryawa dake''.
Tuni idanunta suka ciko da k'wallah tace
"Wai Ammi sai aita ganin laifina shikuma duk muguntar dayake min ba'a gani''.
"Muguntar uban me yake miki?''. Ammi tace fuskarta a d'aure tana harararta.
"Wllhy ALLAH Ammi mutumin nan da kike gani mugune kum......bazato taji Ammi ta bige mata baki kuka ta fashe dashi Ammi ta cigaba dayi mata fad'a.
"Wuce muje, kuma ki rufemin baki ki share hawayen nan shashasha kawai''. Gaba Ammi ta tasata suka fita bakin nan kamar zai tab'o sama saboda yadda ta turoshi gaba, wani haushin Saif ya k'ara kamata ganin yadda Ammi ke mata fad'a akanshi.
Zama Ammi tayi kan kujera tana masa sannu da zuwa, itakuma hannun kujerar da Ammi take ta zauna ta juya musu baya.
Har k'asa ya sauko ya kwashi gaisuwa gurin Ammi yana wani sussunne kai waishi kunya, ta amsa cikin fara'a tana tambayarshi hanya da yadda ya baro su Mamie da Daddy.
"Hmmm bayan iskanci harda munafurci ashe duk ya iya ji yadda yake wani k'asa da kai kamar wani na ALLAH dama Imaan tace mata a outside yayi karatunshi gaba d'aya bata raba d'ayan biyu acan ya koyo iskanci". A zuciyarta tayi maganar lokacin data juyo ta d'an kalleshi, amma dai koba komai taji dad'in yadda ya girmama mahaifiyarta.
Q'warai mamaki ya kamata yadda taji sunata hira da Ammi duk da dai yanajin kunya shi kanshi baiyi zaton zaiji kunyar Ammi ba amma tunda ya ganta yaji matar tayi masa mugun kwarjini.
Sun d'auki lokaci suna hira kafin yayi mata sallama.
"Ai nayi zaton zaka kwanar mana ne Saifullahi da nan da can ai duk d'ayane". Ammi ta fad'a tana kallonshi.
Kanshi ya shafa yace
"Ammi akwai matar da zan duba gobene Insha ALLAH".
"Toh babu damuwa, ALLAH ya tsare hanya a gaishesu da kyau dan ALLAH".
Amsawa yayi da "Aamin", yana ajiye mata kud'i masu yawa a kusa da ita duk cewar datake ya d'auke abinshi bazata karb'a ba.
"Ammi ki karb'a dan ALLAH addu'arku kawai muke b'ukata dasa albarkarku". Addu'a Ammi ta shiga yimasa yana amsawa cikeda jin dad'i sannan sukayi sallama ya fita fuskarshi d'auke da murmushi wanda kafin ma kaga yayishi aikine.
"Tashi ki bishi kuyi sallama". Ammi ta fad'a tana kallon Ayshaa.
Zatayi magana Ammi ta jefeta da wani mugun kallo ba shiri ta tashi tana kumbura ta fita.
A bakin motarshi ta hangoshi a tsaye ya dafa murfin motar bai kai ga shigaba ya kara waya a kunnenshi da alamu waya yake har ya k'ara d'inke fuskarshi ba kamar yadda ya fito da murmushi saman fuskarshi ba.
Tsaye tayi bayan k'arasawarta wajen sam bai nuna alamun ma ya ganta ba ya cigaba da amsa wayarshi yana wasa da mukullin motarshi da d'aya hannun.
Sun d'anyi nesa shiyasa batajin abinda yake cewa duk da dai dama wayar Saif idan bakayi kusa dashi sosai ba to bazakaji abinda yake fad'a ba saboda yadda yake maganar kamar wanda akeyiwa dole.
Kusan 7min ya d'auka yana wayar kafin ya kashe ya zurata a aljihu batare daya kalleta ba ya shige motar, tsaki taja ta juya tana fad'in
"Aikin banza kawai, shi idan bai wulak'anta mutane ba bayajin dad'i ji yadda dan ALLAH ya nuna kamar ma baisan da wata halittar taba.
Tana ji aka bud'e masa gate ya fice, tana daf da shiga main parlor taji maigadi na tsayar da ita, dakatawa tayi tareda juyowa, k'arasowa yayi ya d'an rissina ya mik'a mata wata jaka, da alamun rashin fahimta take kallonshi tanason taji wannan jakar kuma daga ina.
"Baba ta waye wannan jakar?''.
"Mutumin daya tafi yanzu shine ya bani yace in kawo miki''. Ya bata amsa.
"Okay shikenan". Ta fad'a tana juyawa ta shige parlor'n shikuma ya koma bakin aikinshi.
Da kamar bazata bud'e jakar ba saikuma ta canza shawara, ta zauna kan kujera ta bud'e ta ta zazzago kayan ciki tsadaddun turaruka ne na mata masu matuk'ar k'amshi dasa nutsuwa guda uku sai wata y'ar k'aramar akwati ta bud'e ta awarwaro ne masu kyau da tsari guda hud'u sai zobensu da d'an kunne.
"Woww" ta fad'a cikeda farin ciki tana k'ara dubasu tasan wannan kyautar daga wajen Mamie take duk da bawai ya fad'a mata bane.
Cikin jakar ta maidasu ta d'auka taje ta nunawa Ammi godiya tayi itama sannan ta d'auka ta tafi da ita bedroom d'inta.
Daf da magreebah ya isa cikin garin Abuja, side d'inshi kawai ya wuce lokacin daya isa dan bakowa a parlor'n ba wanda yasan shigowarshi.
Wanka yayi ya d'aura alwalah ya fito ya zura farar jallabiyyah ya fesa turare ya fito zuwa lokacin har anfara kiraye kirayen sallah.
Har lokacin bakowa ya fice ya nufi masjeed.
Mamie na shirin shiga kitchen taga shigowar Saif, da mamaki take kallonshi tace
"A'ah kai kuma shigowar yaushe?''.
Wajen kitchen d'in ya k'arasa yana murmushi yace
"Yanzu Mamie wanka kawai nayi na fita masallachi''.
Kai ta kad'a tace
"Toh duk yaka baro mutanen kanon?''.
"Lafiya k'alau Mamie suna gaisheku''.
"Masha ALLAH, Ina mamana y'ar gudun hijirah?''. Tace cikin y'ar dariya.
"Lafiya Mamie tace a gaisheku keda Imaan".(kaji k'arya mutumin dako maganar arzik'i bata had'ashi da itaba).
Daga haka Mamie ta shige kitchen d'in shikuma ya juya ya koma part d'inshi.
★★★
Friday morning.
Juma'atu babbar rana, kamar ko yaushe idan ranar juma'ah ne ya kanyi k'ok'ari yasaka manyan kaya harda hula duk kuwa da yadda suke takura masa.
Yau d'inma datake juma'ah haka ta kasance ya shirya tsaf cikin manyan kaya dan fita hosp.
Farar shadda ce k'al kamar takarda anyi mata aikin hannu da ash color d'in zare daya zauna sosai jikin shaddar, sai yasa hula kalar aikin agogon hannunshi ma na sark'a ash ne da ash d'in takalmi sawu ciki siririn farin glass na gayu ya manna a idanunshi ya fesa turaruka ya fito.
Dinning ya nufa yaga an shirya komai akai saidai bakowa yana tunanin Mamie ta wuce hospital Mamie babbar likitace a babban asibitin dake Abuja, Imaan ma tawuce school.
Tea kawai ya had'a yasha sai Irish dayaci ya tashi ya fita.
Tun shigarshi asibitin aketa faman yimasa sannu da zuwa kama daga kan ma'aikatan asibitin leburori da sauran mutanen dake ciki.
Hannu kawai yake d'aga musu dan waya ma yake d'ayan hannun kuma zube cikin aljihun rigarshi.
"Woww, yah salaam". Wasu nurses y'an mata biyu daga can gefe d'aya daga cikinsu ta fad'a tana dafo kafad'ar d'ayar data juya baya tana waya, juyowa tayi suka saki baki dukansu suna binshi da kallo harya wuce inda office yake.
Ajiyar zuciya d'ayar ta sauke tareda lumshe idanunta tana dafe k'irjinta da hannayenta tace
"Wllhy Aleeyah Ina masifar son mutumin can wayyo ALLAH zuciyata kamar zata fashe wllhy".
Wadda ke wayar ce tace
"ALLAH Nusaiba kina b'atawa kanki lokacine kin sani kema ya za'ayi wancan Man d'in ya kulaki?''.
"Toh ai Ina sonshi Aleeyah bazaki gane yadda nakeji cikin zuciya taba wllhy Ina mutuwar sonshi". Ta k'arasa maganar tata kamar zatayi kuka.
Baki Aleeyah ta tab'e tace
''Toh nidai shawarar dazan baki wllhy kidawo cikin hankalinki fa da tunaninki tun kafin lokaci ya k'ure miki, ga Auwal nan yanata faman bibiyarki kina wulak'antashi zaki kai kanki inda bakida daraja ko d'aya dan kinsan dai Dr ba aurenki zaiyiba".
Kai ta d'an rausayar tace
"Shikenan zan duba shawarar ki".
"Atoh ya fiye miki dai, zo mutafi". Taja hannunta suka wuce.
Yana shiga office d'in nashi dayasha gyara ko Ina k'al yana tashin k'amshi, kujerar shi ya nufa ya zauna tareda karb'ar jakarshi a wajen masinjan sa daya rakoshi da ita hular kanshi ya cire ya d'ora bisa babban table d'in gabanshi ya ciro pen d'in dazaiyi amfani dashi sannan ya ciro wayarshi ya kunna karatun Alqur'ani mai girma cikin suratul kahf k'asa k'asa karatun ke tashi d'abi'arshi kenan dama indai yazo zai saka karatun Alqur'ani kafin ya fara duba patients yana saurara gefe d'aya kuma yana duba patients d'in.
Cikeda gwanancewa yafara dubasu, marasa lafiya na matuk'ar son Dr Saif ya dubasu saboda yasan takan aikinshi cikin q'udurar ubangiji indai ya duba mutum ya rubuta magani cikin ikon ALLAH ana samun waraka, saidai fa dole sai kayi hak'uri da halinshi na rashin fara'a da sakin fuska ga fad'a kuma dolensu suke hak'urin tunda sune masu nema.
Mutum uku ya duba sai wata matashiyar budurwa data shigo ata hud'u, irin matan nanne giant ga tsayi ga k'iba sosai tasha gayu cikin doguwar abayah black color tayi rolling da gyalen abayahr takalmin k'afarta ma bak'ine sai side bag d'inta itama bak'a ta d'ora bak'in shade a idonta sai zabga daddad'an k'amshi take tamkar dai wadda zataje biki ko wani muhimmin taro saboda yadda taci gayu, ba laifi tanada kyawunta daidai nata haka kuma bata cika hasken fataba amma kuma fatar tata mai kyau ce dagani ba k'ananun kud'ad'e ake kashe mataba.
"Wow,wow,woww" ta fad'a a ranta tana kur'e Dr'n dake gabanta da kallo gabanta yana wani irin fad'uwa lokaci d'aya zuciyarta tayi mugun kamuwa da tsananin so da k'aunar wannan bawan ALLAH dake gabanta duk hurd'ar datake da maza zata iya rantsewa bata tab'a gamo da d'a namijin daya kai wannan cikar zati da haiba da amsa sunan namiji a kowane mataki irin wannan ba lallai ALLAH ya sota daya jefota wannan hospital d'in, ta had'u dashi a lokacin daya dace babu kuma abinda ya isa yayi mata katanga dashi, cikin wani irin taku najan hankali ta isa gaban table d'in taja kujera ta zauna saidai shi wanda ake abin danshi hankalinshi ma gaba d'aya bai wajen bare yasan mi akeyi, wani mugun farin ciki na ratsata tako ina k'urr ta k'ura masa ido tana kallon gefen fuskarshi daya d'an karkatar yana duba labtop lips d'inta ta d'an tsotsa tana sakin ajiyar zuciya.
ZUHRAH kenan.
Tofah! Ga wata wai zuhrah ga kuma Safnah a gefe sunsa dai indo a tsakiya koya zata kaya.
Uzuri please harkar mai iyali.
Mrs Salees Mu'az❤️
*DR. SAIF*
Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
ALLAH ya mana dawowa.
Fatan alkhairi agareku dafatan kowa yayi sallah lapia, ALLAH ya maimaita mana Amin Happy Sallah 2 oll Muslims hop bakuci nama dayawa ba saboda burkicewar ciki kamar yadda na k'awas ya birkice, Ina yiwa kowa fatan alkhairi ubangiji ya datar damu yasa mu cika da imaani.
No 18.
Cike da wani irin salon tafiya da yauk'i ta k'arasa ta zauna idanunta sam sun kasa barin kallon Dr'n dake gabanta.
Shi duk baisan ma bikin datake ba saboda yadda hankalinshi kacokam yake kan labtop yana sarrafata cike da k'warewa.
K'uri tayi masa tana k'ara karanto baiwa da irin kamala da kyawun sufar da ubangiji yayi masa cikin ranta tana ayyana ta yadda zata mallakeshi cikin sauk'i.
Labtop d'in ya rufe ya d'an turata gefe yadawo da hankalinshi kan wadda ke zaune gabanshi, had'uwar idanunsu ya haddasa mata shiga cikin wani yanayi harta nemi nutsuwarta ta rasa d'an lumshe ido tayi ta bud'e akansa taga har ya maida kanshi k'asa yana duba wasu files mamakin yadda ta tasashi tamkar wani TV tana kallonshi yake ya tsani kallo hakan yasa yaja tsaki cikin cinkushasshiyar murya yace
"Ban fiya son kallo ba,kina iya tafiya idan abinda ya kawoki kenan''.
Ajiyar zuciya tasaki gami da d'an dafe k'irjinta saboda amon muryarsa daya ratsa dodon kunnenta sai taji muryar tashi tamkar busar sarewa.
Murmushi tayi cikin karya harshe da taushin murya ta shiga rattabo masa dalilin zuwanta hosp d'in, katin ya janyo ya shiga rubutu akai cikin gwanancewa saida yayi rubutu da d'an yawa sannan ya mik'a mata batare da yace uffan ba, kyakkyawan hannunshi tabi da kallo tana amsar katin, da son samunta ne ta zauna ta cigaba da kallonshi dan komi nashi abin burgewa ne hatta shan k'amshin dayake ma abin tsayawa a kalla ne tasan hakan bamai yiwuwa bane dan dolenta ta tashi tsaye tana rataya k'aramar jakarta swagger ta fice tana d'an waiwayenshi.
Tsaki ya buga bayan fitarta, cikin ranshi ya shiga mitar kallon da yarinyar ta dinga masa dan duk yana lura da ita.
Tafe take cikin motarta tana juya kan sitarin motar cikin k'warewa, kallo d'aya zakayi mata ka fahimci tana cikin tsantsar farin ciki da tarin nishad'i har wata wak'a ta shiga rairawa tana faman kad'a kai alamun duniyar tayi mata dad'i.
Kai tsaye gidansu aminiyarta ta nufa dan dole taji wannan labarin.
A parlor tasamu maman k'awar tata da k'annenta suna kallo gaishe da Maman tayi ta amsa cikin sakin fuska suma k'annen suka gaisheta.
"Mama Zainab fa?''.
Tayi tambayar tana kallon Maman.
"Tana ciki, kinsanta da shegen son zaman d'aki kamar wata maijego".
Dariya kawai tayi ta nufi hanyar da zata kaita bedroom d'in zainab, a bakin gado ta sameta da waya a hannunta tana chatting tana shiga ta cilla jakarta kan sofa da gyalen datayi rolling dashi ta fad'a saman gadon tana dariyar farin ciki.
Dariya itama zainab d'in tayi tareda ajiye wayar a side drower ta juya wajen zuhrah tace
"Ko zan iya sanin daga ina wannan farin cikin yake?''.
Zaune ta tashi gami da janyo pillow ta rungume tana murmushi tace
"Zee na sameshi".
"Waye?''.
Zamanta ta k'ara gyarawa tace
"Kinsan na dad'e inason zuwa hospital kan matsalar nan, to sai yau ALLAH ya kaini wani hosp Premier hospital....shiru tayi tana cigaba da murmushi.
Girgiza kai zainab tayi tana murmushi dan ta fara gano inda k'awar tata ta dosa.
"Kina bani labari".
Ajiyar zuciya zuhrah tasaki ta lumshe ido tana hango fuskar Dr Saif a idanunta tace
"Zee na had'u da namijin daya dace dani na had'u da namijin dana dad'e Ina burin samu, zee na had'u da wanda gani d'aya danayi masa ya tafi da dukkan zuciyata ba kuma zan iya jurar rashinshi ba dole saina aureshi kota halin k'ak'a dan wallahi zan iya komi a kanshi, zee Dr'n daya dubani ya tafi da zuciyata naji inayi masa son da ban tab'a yiwa wani d'a namiji ba a doron k'asa zee ki taimakeni kibani shawarar yadda zan b'illowa al'amarin". A hankali ta k'arasa maganar cikin raunin murya na wadda SO yayiwa kamun kazar kuku.
Numfashi zainab ta sauke cikeda tausayin aminiyar tata tun a sunan asibitin data fad'a ta gano kowaye wanda ya sace zuciyar k'awar tata kuma sam batayi murna ba saboda tasan a wahala kawai zatasa kanta dan Dr Saif dai ba kulata zaiyiba.
Matsawa zee tayi kusa da ita ta dafa cinyarta tace
"K'awata inbaki shawara?''.
"Ina jinki". Zuhrah ta amsa mata tana kallonta.
Cigaba zee tayi da fad'in
''Ina ganin ki rabu da guy d'in nan zuhrah akwai guys dayawa dake crushing akanki sai wanda kika zab'a please ki rabu da maganar Dr Saif".
Da mamaki zuhrah ke kallon zee tace
"Kin sanshi ne? Kuma akan me zakice in rabu dashi?''.
"Zuhrah mutumin nan mugun d'an wulak'anci ne sam mata basa gabanshi, kinsan ai Fateemah cousin sister d'ina tafiki haukacewa akansa lokacin data ganshi ta dinga bibiyarshi k'arshe da suka had'u wllhy idan kinga wulak'ancin dayayi mata saikin tausaya mata yaci mata mutunci, kuma yaja mata dogon gargad'i kan karta k'ara shiga sabgarshi ke cin mutunci dai iri iri to dayake dai tanada tsoro kuma akwai zuciya shinefa ta shafawa kanta lafiya ta k'yaleshi badan tanaso ba kema kuma in har zan baki shawara ki d'auka to ki fita batunshi ALLAH kuwa".
"Ki gane zee matsalar ba daga ni bane daga zuciyata ce, wllhy duk yadda zan miki bayani kan irin son dana kamu dashi na wannan Man d'in bazaki fahimta ba, wai taya ma kika sanshi ne?''
Baki zainab ta d'an tab'e tace
"Ina Zubaida Kabeer wannan k'awar tawa?.
"Yeah na ganeta".
Dr Saif bashida amini sama da yayanta Mukhtar". Zee ta amsata.
"Wow, so happy yanzu ya za'ayi kenan'', zuhrah ta fad'a cikin k'aguwa da son jin mafita.
Kafad'a zee ta d'age tana d'an tab'e baki tace
"Zansan yadda zanyi insa zuby ta samo phone number d'insa a wayar yayanta inbaki sauran aiki kuma ya rage naki tunda kinga zaki iya".
Hannun zee zuhrah ta kamo ta k'ank'ame tana zuba mata godiya kamar wadda tace ta mallaka mata Saif d'in ne gaba d'aya itadai zee kallonta kawai take tana tausaya mata dan abar tausayin ce.
"Toh yanzu yaushe zakije gidansu zubyn?''.
Kai zee ta d'aga tana d'an jujjuya idanu tace
"Next week Insha ALLAH".
Ido zuhrah ta zaro tana fad'in
"Haba mana aminiyar har next week dan ALLAH, kije gobe mana please''.
Kai zee ta girgiza tace
"Kefa bakida hankali,daga yin magana yau gobe kuma sai in d'auki k'afa in tafi''.
"Please, please please", zuhrah ta fad'a kamar zatayi kuka tana k'ara damk'e hannun zee dake cikin nata hannun.
"Mtssw, naji zanje goben banza''. Zee tayi maganar tana hararar zuhrah.
Itakam zuhrah y'ar dariya tayi tareda kai hannun zee bakinta ta sumbata cikin jin dad'i.
Kusan yini tayi a gidan suna hira duk rabi da kwatan hirar kuma akan Saif ne dabai san wainar da ake toyawa a kansa ba(Tofah).
★★★★★★
Kamar yadda zee tayiwa zuhrah alk'awarin zuwa gidansu Zubaida kuwa ta cika dan a washegarin ranar tayiwa gidansu zuby tsinke.
A parlo tasamu zubyn itada Hajia, q'warai zuby tayi murna da ziyarar da k'awar tata takawo mata dan sun kwana biyu basu had'u ba, saida suka gaisa da Hajia sannan suka k'ule bedroom d'in zubyn bayan ta umarci mai aikinsu data kawowa zee abin motsa baki.
Hirar yaushe gamo suka shiga yi kafin zee ta gangaro kan maganar data kawota.
''Nikam zuby girl Ina wannan abokin yayan naki?".
"Wanne daga ciki?''. Zubaida ta mayar mata da tambaya.
"Babban amininshi dai dayafi kusanci dashi".
"Ohooo cemin zakiyi d'an yarfe, yana nan kinsan ni bana shiga harkarshi dan Ina kare mutuncina banson abinda za'a cimin mutunci". Zubaida ta k'arasa maganar tana tab'e baki.
Zama zee ta gyara tace
"Kice bakwa mutunci dashi".
Ido zuby ta zaro tana d'an dafe k'irji kafin tayi wata y'ar dariya tana gyad'a kai tace
''Hmm k'awata bakisan waye wannan guy d'in ba wllhy ba abinda ya shafeni dashi bana shiga shirginshi ko gidan nan yazo farko dai zuciyata taso afkawa cikin kogin k'aunarshi amma dana zauna nayi karatun ta nutsu nayiwa kaina fad'a saina yakicewa kaina, ke ko meyasa kike tambayarshi fatan dai ba sonshi kike ba?''.
Numfashi zee ta sauke tace
"Wllhy zuby k'awata zuhrah ce ta fad'a tana nan duk tabi ta zare data ganshi shine nazo neman taimakonki''.
"Taimako wane iri?''.
Zubaida ta fad'a cikin mamaki tana kallon zee.
"Please zuby girl phone number d'inshi kawai zaki samomin a wayar yayanki dan ALLAH''.
Shiru Zubaida tayi alamar tunani.
"Please k'awata".
"Shikenan zan samo miki''.
"Thanks so much zuby".
Zee ta fad'a tana murmushi gami da kama hannun zubyn alamar godiya.
Sai yammaci sosai sannan zee ta bar gidan su Mukhtar ranta fess.
)))))((((((
Da Magreebah.
Mukhtar daya d'auro alwalah ya fito daga bedroom d'inshi cikin hanzari jin ana shirin tada sallah, Zubaida ya wuce zaune da waya a hannunta kasancewar tana fashin sallah ne.
Daf dazai fita ya tuna bai jona wayarshi a caji ba kuma yana b'ukatar cajin dan baifi saura 20 percent gareshiba, tsayawa yayi ya kira Zubaida tana zuwa ya mik'a mata wayar bayan ya cirota daga aljihu.
''Ki jonamin a charge yanzu''.
Tana karb'a yayi gaba batare da jiran amsar taba.
Murna ta shiga yi ganin abin yazo mata da sauk'i dama tana ta tunanin ta yadda za'ayi harta d'auki wayarshi dan shima d'in bawani sakar musu fuska yakeba bare ta karb'a.
Bedroom d'in nashi ta nufa tana addu'ar ALLAH yasa ba Lock a jiki tasan dai da k'yar ne dan yanzu kowa wayarshi sai an samu lock a jiki, amma ga mamakinta tana yin swipe up wayar ta bud'e ta shiga contacts d'inshi da laluben number Saif d'in.
Mr. Man tagani cikin jerin sunaye dasuka fara da M tuni ta kwafe number a wayarta sanin cewa Saif d'in kawai Mukhtar ke kira da wannan sunan.
Wayar ta jona bayan ta fita daga contact ta koma asalin yadda ya bata sannan ta fito ta janyo k'ofar.
(Hmmm).
Bedroom d'inta ta shige ta kwanta gefen gado ta shiga WhatsApp ta bud'e data, dayake GB WhatsApp ne sai aka nuna mata zee tana kan online nan da nan kuwa ta shiga cikin numberta ta tura mata number Saif, voice message tayi mata tana godiya daga nan suka d'an yi hira har zuwa lokacin da Zubaida taji muryar Hajia na kiranta sallama sukayi da zee ta kashe datar sannan ta jona a charge ta fita kiran Hajia.
★★★★
Kwana biyu kenan Saif yana fama da ciwon mara, har bai samun isasshen barci yanayin daya d'an dad'e bai shigaba shine yadawo masa wato sha'awa ce dai ta tasoshi a gaba.
Ko a lokacin dayake kan ganiyar sha'awar koda yake likita hakan baisa yayi allura ko yasha tablet na kwantar da sha'awa ba, saboda yasan dole akwai edge d'in da za'a kai dabazasu yi amfani ba koda anyisu yafi gane yasha lemon tsami sai kuma azumi dayake yawaita yinsa saboda samun mafita kamar yadda Annabinmu (sallallahu alayhi wasallam) ya koyar.
Yau d'inma tun a hosp yakejin alamun ba daidai ba, k'ananun tsaki ya dinga saki yana lumshe ido shi kanshi yasan yana b'ukatar mace a kusa dashi yakai munzalin da za'ace yanzu akwai wadda yake saukewa b'ukatar shi Ayshaa ce ta fad'o masa cikin rai ya tuno yadda take y'ar siririya ba jikin kirki k'ashinta bai gama k'wari ba zuwa d'aya zaiyi mata ta tashi aiki, koba hakaba kuma bazai iya mu'amalar aure ba da ita dan a yanzun ma tafara rainashi Ina kuma ga ya mu'amalanceta a shimfid'a kai bama zai iyaba sam.
Files d'inshi ya tattara yabar asibitin ya nufi gida, zuwa lokacin ciwon marar tashi ya k'ara tsanani da k'yar ya k'arasa gida ALLAH ya taimakeshi bakowa a parlor'n bare aga halin dayake ciki kai tsaye ya wuce part d'inshi
Toilet ya fara shiga bayan ya cire kayan jikinshi ya watsa ruwa ya fito a daddafe, cikin k'arfin hali ya shirya cikin wando 3qtr bak'i da farar riga mai gajeren hannu ya fesa turare ya wuce kitchen yayi sa'a ya samu lemon tsami yasa wuk'a ya rabashi biyu jin tsayuwar na neman gagararshi saboda yadda ta wani murd'a masa yasa ya koma bedroom d'in ya zauna ya matse lemon tsami nan duka a bakinshi bayan ya rufe ido saboda tsamin daya gauraye bakinshi yana faman yamutsa fuska, bud'e idon dazaiyi yayi arba da Mukhtar tsaye a bakin k'ofar shigowa ya hard'e hannayenshi a k'irjinshi yana kallon Saif fuskarshi d'auke da wani shegen murmushi na shak'iyanci, basarwa Saif yayi yaci d'aci yana wani k'ank'ance ido irin kar ma Mukhtar yace zai kawo masa maganar banza ka makaro Saif dan kuwa Mukhtar bai gani yayi shiru saiya tanka.
Mrs Salees Mu'az❤️
*DR. SAIF*
Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No 19.
Sosai Saif ya tsuke fuska ya shiga latsa waya yana wani cin magani, Mukhtar daya k'araso cikin d'akin yana wata shegiyar dariya ya zube kan gadon kusa da Saif yana cigaba da dariyar shi gami da nuna Saif da hannunshi. Saif daya fara k'uluwa ya cillar da wayar akan gadon a fusace yace
"Wai kai mahaukacin inane zaka shigomin d'aki ba sallama uwarka akayi zaka shigo kanamin dariyar hauka''.
Tsagaitawa Mukhtar yayi da dariyar yace
"Malam kaji da abinda ke damunka tabarmar kunya ce dai kake nad'ewa kace yau ta motsa kenan''.
Cije lips d'inshi Saif yayi yana tsaki dan yarasa abin fad'a shidai ba abin ya musa masa ba ya ganshi k'uru k'uru ya juye lemon tsami a bakinshi.
"Wai uwar mi yakawo kama Mukhtar? Ba d'azun muka rabu ba?''. Saif yace yana jefa masa harara.
Kwanciya Mukhtar ya gyara akan gadon ya d'age kafad'a yace
"Normal kwana biyu bamu gaisa da Mamie ba shine nazo, ashe kai kana nan jaraba na cinka". Ya k'arasa maganar yana k'ara k'yalk'yalewa da wata dariyar.
Baiyi zato ba yaji bammm Saif ya dakar masa baki, tuni yabar dariyar ya dafe bakinshi yana kallon Saif d'in daya maze tamkar bashi ya aikata ba, harararshi Mukhtar yayi yace
"ALLAH ya isana banza mugu, kuma an fad'a d'in jaraba na cinka(Kamar wasu yara).
Banza yayi masa bai kulashi ba saboda yadda marar ta k'ara murd'a masa ya runtse ido yana cije baki saikuma tausayinshi ya kama Mukhtar d'in cikin tausayawa yace
'' I'm sorry Mr Man ALLAH ya kusa yanke maka na rantse ma ni tausayin Ayshaa nake wllhy idan ta shiga hannunka".
Duk da halin da Saif yake ciki saidaya bud'e idonshi dayayi jawur ya antaya masa harara. Baki Mukhtar ya gumtse yana y'ar dariya, tsaki Saif yaja ya maida idanunshi ya k'ara lumshewa yana sakin ajiyar zuciya.
Mukhtar dai yana nan bai tafiba sai dayaga Saif ya koma normal suka d'an fara hira duk da duk rabi fad'a ne dai.
Sai bayan wani lokaci sannan ya mik'e tsaye yana shirin tafiya ganin Saif bashida alamun rakashi yasa yace
"Wai S Matawalle ko rakiya babu?''.
"Nina kawoka? Munafurci kazo yi kuma kayi hankalinka ya kwanta". Yana fad'a ya rufe ido dan wani irin barci keson d'aukeshi.
Murmushi Mukhtar yayi ya fice yana fad'in
"A cigaba da shan lemon tsami Mr Man".
Bai tankashi ba illa kwanciyar shi daya k'ara gyarawa idanunshi a rufe .
★★★★★★
Ba k'aramar murna zuhrah tayiba da samun phone number d'in Saif zee kam tasha godiya. Tun a ranar tafara tura masa text message lokacin yana tsaka da duba patients sak'on ya shigo dan haka baibi ta kanshi ba, sai bayan wani lokaci da akayi kiran wayar tashi bayan yayi picking ya gama maganar da zaiyi yana shirin ajiye wayar idanunshi suka sauka kan text d'in kamar zai ajiye saikuma ya shiga cikin inbox d'inshi dan karantawa.
*_Amincin ALLAH ya tabbata kan hasken idaniyata fatan alkhairi dafatan kana lafiya ya aiki I hope komai normal Ina maka addu'ar samun nasara a duk abinda kasa gaba kamar yadda nake yiwa kaina addu'ar mallakar ka a matsayin mijina na halal, I love you more baby and I miss my beautiful face._*
_*Z M.*_
Abinda sak'on ya k'unsa kenan, tsaki yaja yana tab'e baki yayi deleting d'in text d'in ya maida wayar ya ajiye saman table d'in inda take.
Ba yau aka fara yimasa irin wad'annan sak'onnin ba saidai sam baya bi ta kansu dan daya gani yake gogewa dan basuda amfani a wajenshi baya ga kiran waya da y'an mata ke damunshi dashi shima d'in dai dayayi picking yaji muryar mace yake kashewa shiyasa some times ma bai cika d'aga bak'uwar number ba dan yasan kwanan zancen ya rasama gidan uban dasuke samun number shi zamani yazo mata ba jan aji ba kamun kai.
**★★★**
Tun daga wannan rana saiya zamana kullum ta ALLAH sai an tura masa text's zafafa na soyayya time to time ma sau biyu ko sau uku a rana, bai tab'a bi takai ba hasalima daya gani yake deleting yaita masifa shi kad'ai.
*******
Rayuwa nata shud'awa wataran zuma wataran kuma mad'aci dama haka rayuwar ta gada watarana ayi kuka watarana kuma ayi dariya kamar baza'a dainaba, Lokacin biki yanata k'ara k'aratowa ta kowane b'angare an fara tsara yadda bikin zai kasance amma shi uban gayyar ko a jikinshi kuma tun zuwan da yayi Kano sau d'aya bai k'ara zuwaba kuma baya kiranta a waya, to shikam ya kirata ma yace mata me? Mamie tana yawan tambayarshi suna waya da Ayshaa saidai yace mata Eh suna waya sosai ma (kuji k'arya reader's).
Itama ta b'angaren Ayshaan duk lokacin da sukayi waya da Mamie takan tambayeta suna waya da Saif itama d'in dai duk amsar d'aya ce suna waya dan haka Mamie ta sakankance tafara murnar sun fara saukowa tun kafin akai ga auren(Ayyah Mamie sun kifar dake).
Suna zaune a parlor Mamie ce da Imaan suna kallon wa'azi a tashar Sunnah Tv ya shigo parlor'n bakinshi d'auke da sallama wadda labb'anne kawai suka motsa alamun sallamar, yana sanye ne cikin bak'in jeans da farar riga sai bak'ar jacket daya d'ora akai ya d'ora bak'ar hula mai kamar ta sanyi akan nashi. Tunda ya shigo parlor'n k'amshin shi ya game ko ina duk ya cika parlor'n dama gana fresheners da turaren wuta dake parlor'n saiya had'u yabada wani sassanyan k'amshi mai dad'i.
Bai cika zaman kujera ba indai Mamie na wajen dan haka yau d'inma k'asan carpet ya zauna yana mata sannu da gida ta amsa cikin kulawa, bai iya zaman hiraba shi sam a rayuwarshi dan haka ya tashi yana shirin wucewa sashenshi kiran da Mamie tayi masa yasa yadawo ya zauna kusa da ita.
Kallonta ta d'auke daga kan TV'n tadawo dashi kan Saif tace
"Biki yanata tahowa banji kafara maganar lefe ba babana''.
"Lefe kuma Mamie?''.
Yace yana wani yatsina fuska.
"Eh, lefe kowani zaiyi maka shi ne?''. Mamie ta fad'a tana masa wani irin kallo.
Jujjuya kai ya fara yana faman b'ata fuska
"Kai nake jira naji yadda za'ayi". Mamie ta fad'a ranta a d'an b'ace.
"Shikenan zan dubu d'ari biyar ta account d'inki sai a siyo". Tsakaninshi da ALLAH yayi maganar yana kallon TV, Mamie da haushi ya k'umeta saita rasa abin fad'a tayi shiru da bakinta. Imaan kuwa dake gefe kan kujera ta dafe baki cikin ranta tace
"Kan bala'i 50000 ne zasu isa had'a lefe?.
Jin Mamie batace komiba yasa ya juyo ya kalleta yayi karo da muguwar hararar datake jifanshi da ita.
"Lafiya Mamie?''. Yayi tambayar cikin rashin sanin laifin dayayi.
Saida Mamie ta k'ara zabga masa wata hararar sannan tace
"Ai kasan maman tawa y'ar tsanace da dubu d'ari biyar zasu isa had'a mata lefe.
Kai ya karyar yana b'ata fuska yace
"For God sake Mamie ace 50000 bazasu isa a had'a ba me za'a sa a ciki to?''.
"K'aniyarka za'asa, Mamie tace tana jefa masa dak'uwa.
Baki ya d'an tura yayi k'asa da kanshi, Mamie ta cigaba da fad'in
"Idan jikinka ne aika iya fitar da mak'udan kud'ad'e ka siya sutura ko shine dan rashin mutunci zaka kawomin wata maganar banza to wllhy ka kiyaye ni bansan d'iban albarka kaji ko.......ganin yadda Mamie ta d'auki zafi sai faman sambad'a masa fad'a take yasa yace
"I'm sorry Mamie nawa zan bayar to?''.
"2million zakamin transfer".
Da sauri ya kalleta zaiyi magana yaga fuskar ba alamun wasa sam saiya langab'e kai alamar a tausaya masa yace
"Please Mamie a rage inbada 1.5million".
"Wllhy karki yadda Mamie Aunt Ayshaan mu mai tsadace dan haka yazama dole duk abinda za'a zuba mata yazama mai tsada'', Imaan ce mai maganar cikin ranta tana matse dariyar mugunta.
"Wllhy ko biyar bazan rage ba saika kawosu ai nasan kanada kud'in wato asara kake gani ka bayar asa mata kaya masu kyau ko kuwa. Kwana biyu nabaka inji alert dan zan turawa Hajia Muneerah k'awata dake Dubai ita zata had'a komi saidai a aiko dasu kawai.
"Insha ALLAH".
Haka kawai ya fad'a ya tashi ya bar wajen cikin ranshi yanata mitar kayan da za'a zuba har na 2million(Saif mak'o baka irin na mazan novel ne kai).
Yana barin wajen Imaan tadawo kusa da Mamie ta zauna tana fad'in
"Yawwa Mamie wllhy gara da kikayi masa haka yama za'ayi ace 50000 ta had'a lefe''.
"Ai barni dashi kawai maganinsa zanyi''. Mamie ta amsa mata tana mik'ewa tsaye dan barin parlor'n.
Tun a washegarin ma da Mamie tayi masa maganar saiga alert taji ya turo mata kud'in dariya tayi lokacin data gani tace "wato da yana dasu d'in yake neman zamewa tana sane tayi masa hakan dan da farko ma Daddy ne yace zai d'auki nauyin yin lefen Mamie tace a,a a barshi yayi kayansa tafiso ya jigatu lokacin bikin yafi ganin matar da mutunci (Mamie akwai hana ruwa gudu wai tafiso ya jigatu).
A take tayiwa Hajia Muneerah transfer d'in kud'in sannan ta kirata sukayi magana ta fad'a mata yadda take so lefen ya kasance.
Ba'a d'auki dogon lokaci ba kuwa aka had'a har ankawo kaya ma set biyu na akwatina kai da ganin akwatinan da kayan dake shak'e a cikinta kasan naira tayi kuka kayane masu matuk'ar kyau da tsada na zamani.
A ranar da kayan suka iso da daddare duk suna parlor an baje kayan anata kallo harda Aunt Aisha datazo ranar sai yabawa suke dan kayane duk bana banza ga kalolin ma duk masu kyau ne.
Mukhtar ne ya fara shigowa da sallama kafin Saif yabiyo bayanshi shima da sallamar kamar yadda ya saba a ciki ciki. Ganin kayan yasa Mukhtar washe baki ya k'arasa wajen ya zauna yana fad'in
"Masha ALLAH Mamie kayan sun k'araso kenan?''.
Y'ar dariya Mamie tayi tace
"Aikuwa dai Mukhtar d'azun nan aka kawosu". Saida suka gaisa da Mamie da Aunt Aisha Imaan ta gaisheshi sannan ya shiga duba kayan yana yabawa.
Ogan kuwa dama tun shigowarshi ya hakimce kan kujera ya shiga sana'ar tashi ta latsa waya ko inda kayan suke bai duba ba sai Aunt Aisha ce tace
"Wai Saifu bakaga kaya bane? Kazo kagani mana". Mamie kam dama kota kanshi batabi ba ta cigaba da hidimar ta na ganin kaya.
Kanshi a k'asa batare daya d'ago ba yace
"Sunyi".
Daga haka yaja bakinshi ya tsuke, kai Aunt Aisha ta girgiza tana tab'e baki Mukhtar kam da k'arfi yace
"ALLAH ka shirya mana bawannan naka".
"Ubanka nayi?''.
Saif ya fad'a kanshi tsaye yana hararar Mukhtar da baisan ma yanayi ba dan kanshi a k'asa yake.
"Oho maka". Mukhtar d'in ya amsa masa.
Dariya su Mamie sukayi dramar Saif da Mukhtar akwai abin dariya dan mafa Saif d'in bai cika biye masa bane da abinda zasu dingayi ai saiyafi haka.
Tashi ma yayi gaba d'aya yabar suka bishi da kallo gaba d'ayansu Aunt Aisha ce da Mamie suka had'a baki wajen fad'in
" ALLAH ya shirya ".
Murmushi Mukhtar yayi yace
"Mamie sai hak'uri halinne haka''.
"ALLAH ya kyauta to".
Da Amin suka amsa suna mammaida kayayyakin cikin akwatinan dan sun gama gani Aunt Aisha ma mijinta ya mata waya kan gashi yazo ta fito sallama tayi musu ta sab'a k'aramin yaronta datake goyo sauran yaran suna gida badasu tazoba Imaan ta d'aukar mata jakarta suka fita danyi mata rakiya.
A bedroom d'inshi Mukhtar ya sameshi zaune kan sofa ya mik'e k'afafunshi kan d'an k'aramin center table da labtop akan cinyarshi yana dubawa sai fresh milk dake cike a cikin dogon glass cup dayake d'an sha jefi jefi. Mukhtar na k'arasawa ya amshe cup d'in ya kafa kai (Mukhtar ka shiga uku da d'aukan magana).
Tankau Saif bai tankaba bai kuma d'ago yabar abinda yake ba dan yasan neman magana ne kawai so yake suyi rigimar tasu da suka saba shikuma yanzu baijin zai biye masa.
Zama Mukhtar d'in yayi a gefen gado yana fad'in
"Wllhy S Matawalle kaji tsoron ALLAH ka daina munafunci".
Jin kalmar munafunci yasa Saif d'agowa yana kallon Mukhtar kallon rashin fahimta.
"Eh, mana inba munafunci ba dama ashe haka kakeson babyn nan amma kake mana wani alaye kai ala dole matsa maka akayi ko? ALLAH ya toni asirinka to". Ya ida maganar yana dire cup d'in daya shanye milk d'in a side drawer.
"ALLAH ya baka lafiya". Abinda Saif yace kawai ya maida kanshi kan system d'in.
Basirar ta tsaya cak mu had'u gobe ko jibi insha ALLAHU
Mrs Salees Mu'az❤️
*DR. SAIF*
Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No 20.
Harara Mukhtar ya zuba masa yace
"Da nayi me".
"Kai ka sani''.
Saif yace kanshi a k'asa.
Tsaki Mukhtar yayi yace
"ALLAH Mr Man kanason Ayshaa ji uban kayan lefen daka had'a mata fa".
D'agowa Saif yayi ya kafe Mukhtar da idanunshi kamar zaiyi magana saikuma ya fasa ya maida kanshi k'asa yana cigaba da danne danne a laptop d'in.
Dariya Mukhtar yayi tareda da cewa
"Ka rasa ta cewa ko? Dama ai nasan bakada damar musu saboda gaskiya na fad'a".
"Bani da lokacin ka".
Amsar da Saif ya bashi kenan, Mukhtar kuma ya cigaba da zuba masa surutu batare daya kulashi ba.
**★**★**★
Zuhrah ce keta faman kaida kawo a bedroom d'inta ta kasa tsaye ta kasa zaune, tunda labarin bikin Saif ya sameta ta bakin Zee da Zubaida take fad'a mata ta kasa nutsuwa ta k'ulla ta kwance yafi sau d'ari tana tunanin mafita a gareta.
"Wace yarinya ce wannan?''.
Tambayar data dinga nanatawa kenan cikin ranta, wace yarinya ce tayi mata kutse cikin rayuwarta. Lallai ta shiga uku kuwa koma wacece zata auri Saif d'inta saita gwammace bata tab'a sanin ma mai kama da Saif d'in ba saita b'atar da ita daga doron k'asa kafin ta dawo kan shi uban gayyar dan taga alamun taurin kai gareshi.
Bakin bed ta zauna tana sauke numfashi idanunta sunyi ja a yadda take bala'in son Saif bazata tab'a bari wata d'iya mace ta rab'eshi ba amma kuma a yanzun dole sai anyi auren sannan zata samu hanyar cimma burinta dan a yanzun idan tace zata nemi yarinyar batasan ta ina zata faraba. Kai ta shiga girgizawa na yarda da shawarar da zuciyarta tabata.
(Toh ga Safnah ga zuhrah kuma duk sun d'auki aniyar sai bayan auren zasu d'auki mataki kowani matakin zasu d'auka bayan auren).
Kwana biyar da kawo kayan lefen aka kaisu, dayake kaiwar mazane bisa jagorancin Kabeer mijin Aunt Salma.
Anyi musu tarba ta musamman da kyakkyawar karramawa da sukayi matuk'ar jin dad'i anyi abu na mutunci da mutunta juna.
Kowa ya yaba da lefen duk da lamarin na mazane hakan bai hana gidan cika da mataba y'an uwa da abokan arzik'i.
Ayshaa kam ficewarta tayi ta tafi gidansu k'awar ta Hannah da sukayi candy tare dayake unguwa d'ayace dan a k'asa ma ana zuwa driver ne ya kaita tun safe can ta yini sai yamma lik'is sannan driver'n gidansu Hannah yadawo da ita tareda Hannahn lokacin duk an tattafi daga Aunt Fateemah yayarta dake aure anan kanon sai Aunt Rahmah autar su Ammi da itama auren ya kawota garin na kano.
Gabanta ne ya fad'i lokacin da suka shiga parlor'n taci karo da jerin had'add'un akwatinan dake jibge cikin parlor'n, baki ta d'an tab'e ta k'arasa kusa da Aunt Rahmah ta zauna tana karb'ar yarinyar datake goyo y'ar three months Ayrah tasha kwalliya cikin riga da wando na kanti masu kyau sai k'amshi take tanason yara sosai a rayuwarta kodan basu garesu ba.
Hannah kam k'asa ta zauna kusa da k'afafun Ammi tana gaishesu gamida fara kallon kayan da suke a bubbud'e batare data kalli kayan ba ta mik'e sab'e da Ayrah a kafad'arta ta shige bedroom d'inta jitake tamkar ta fasa ihu harga ALLAH bata k'aunar wannan auren musamman idan ta tuna wanda zata aura d'in sai taji duk komi ma ya fice mata a rai. Akan gadonta ta kwantar da Ayrah itama ta kwanta gefen ta ta kishingid'a ta kamo hannunta tana mata wasa ji tayi kawai an fad'o kanta cikin ihun murna har yarinyar ta tsorata tasa kuka, da sauri ta tashi tana d'aukar yarinyar ta fara jijjigata tana kallon Hannah tareda jefa mata harara tace
"Dallah malama meye haka kin wani fad'omin akai gashi nan har kin tsorata Ayrah''.
Dariya Hannah tayi tace
"Wayyo M Thabit (yawancin y'an class d'insu da sukayi candy haka suke kiranta), Congrats na tayaki murna q'warai da gaske ALLAH ya bamu itaku, irin wannan uban lefe haka saifa tasowa nayi ban gama ganiba".
Tsaki Ayshaa taja tace
"Banza akan wannan kikazo kinamin ihu akai".
"Toh ba doleba, kinga uban kayan kuwa? ALLAH dai yabada zaman lapia''.
Tsaki Ayshaa ta k'ara ja tana kwantar da Ayrah datayi barci saboda jijjigatan datake. "Wai M Thabit meyake damunki ne nagafa ko d'aukin auren nan bakyayi?''.
Hannah tayi maganar tana k'urawa Ayshaa ido.
Sai data janyo pillow tasa a bayanta ta jingina a jiki sannan tace
"Basai kanason mutum ba sannan zakai d'okin aurenshi harma kayi d'okin zama dashi".
Da mamaki Hannah take kallonta dan basu tab'a maganar ba lokuta da dama dai takanyi tunanin kodai Ayshaa batason auren idan taga irin acting d'in datake akan auren da yadda bataso taji anyi maganar bikin, saidai kuma takan alak'anta hakan da jimami da alhinin barin gidane dazatayi da kuma shiga sabuwar rayuwar dabata saba ba.
A hankali Hannah ta sauke numfashi tace
"Kina nufin kicemin AUREN HAD'I ne za'ayi miki?''.
Kai Ayshaa ta kad'a mata alamun 'Eh, hakane'. Kafin Hannah tasamu zarafin yin magana Ayshaa ta shiga labarta mata tun farkon had'uwarsu da had'uwarsu a Mall da abinda yayi mata da kuma Daddynshi da aka kaiwa tsegumi har yace dolenshi saiya aureta.
Wani k'ayataccen murmushi Hannah tasaki tana fad'in
"Wow, gamida clapping hand dinta, "Wato had'uwar takuma dawani sabon salo tazo, nifa a d'an story d'in nan da kika bani ma na fad'an nan da kuke sai nake ganin kamar son juna ma kuke batare da d'ayanku ya saniba".
Pillow'n kusa da ita ta d'auka ta jefawa Hannah tana harararta tace
"A,a kin manta abinda yafi son juna muke mtwss". Pillow'n Hannah ta cab'e tana dariya tace
'' ALLAH kuwa zakice no a fad'a miki da bakinki zakizo ki dinga fad'amin irin soyayyar da kukesha dashi".
Wayarta ta janyo tana cewa
"Bakida hankali yarinya, ALLAH ya tsareni inyi soyayya da mugu wllhy mugune Doctor d'in nan".
Ido Hannah ta kashe tace
"Duk cikin soyayya ne k'awata''.
Idanun Ayshaa akan waya ta tab'e baki da fad'in
"Banida lokacinki".
Nan Hannah ta zauna ta shiga tsara yadda zasu gudanar da hidimar idan lokacin yayi, Ayshaa bata k'ara tofa tata ba tayi mata banza tana sauraron ta saidai lokaci zuwa lokaci tayi tsaki tace ta dameta.
@@@@@@
Gyara sosai aka shiga yiwa gidan su Saif duk da dai bawai b'ukatar gyaran yakeba dan komi fes yake amma saboda bikin da za'ayi yasa ake masa kwaskwarima. Musamman part d'in Saif d'in da akafi gyarawa sosai inda Ayshaan zata fara zama zuwa lokacin da zai gama nashi gidan dan bazai yiwu ace angama har an tare a ciki shiyasa Daddy yace masa yafara zama anan d'in zuwa lokacin dazai gama nashi saisu koma.
Falone madaidaici a sashen nashi sai bedroom guda biyu a ciki kowanne da toilet a ciki sai kitchen had'e da store duk a cikin parlor'n. Akwai y'ar k'aramar baranda da ake shiga ta bayan d'akunan an k'awata wajen da shuke shuke irin na tukwanen k'asa d'in nan sai kujeru masu kyau da aka zuba guda hud'u da table a tsakiyarsu, daga wajen kana hango swimming pool d'in gidan. Part d'in dai bashida wani girma amma kuma ya tsaru sosai bedroom d'in guda biyu an zuba musu sabbin furnitures masu matuk'ar kyau parlor'n ma an k'awatashi da kujeru da duk wasu kayayyakin k'awa da ake sawa a parlor kitchen d'inma an zuba komi na amfani wanda zata b'ukata da kayan electric duk dai bama dad'ewa zasuyi a nan d'inba. Duk aikin Daddy ne wannan.
Biki dai yanata k'ara matsowa dan yau saura kwana goma a shiga hidimar bikin shirye shirye aketayi ta b'angarorin guda biyu Saif ma dai ganin ba sarki sai ALLAH abin dai da gaske ne yasa dolenshi ya fara shirye shirye musamman na kayan dazaiyi amfani dasu da bikin.
Mukhtar kuwa tamkar shine angon ma tsabar d'oki sai faman zirga zirga yake bashi nan bashi can da kanshi ma yasa aka buga invitations ya rabawa abokansu na kusa na nesa kuma ya tura musu ta waya duk da dai Saif d'in bawani biyawa ta kansu yakeba amma sun d'auki alk'awarin halartar d'aurin aure idan mai kowa mai komi ya kaimu lokacin dan duk abokan karatunsu saida ya gayyacesu. Q'warai Mamie da Daddy kejin dad'in yadda Mukhtar ya tsaya kan komi yayi da jikinshi yayi kuma da aljihunshi, suna son Mukhtar dan yadda yake musu tamkar su suka haifeshi hakan yana musu dad'i musamman daya kasance mutum mai faran faran da barkwanci da mutane duk y'an gidan sunyi sabo dashi dan wanda bai saniba ma saiyace Mukhtar shine d'an gidan Saif kuma abokin dan yadda yake shiga cikinsu ayi wasa da dariya Saif bayayi inama yasaki fuskar.
Shak'uwar da Mukhtar da Imaan sukayi harta fara rikid'ewa ta fara zama soyayya ba wanda ya kula da hakan cikin y'an gidan.
**********
La'asar sakaliya Saif da Mukhtar suka shigo gidansu Saif d'in. Mamie kawai suka samu a gidan a parlor da paper da biro a hannunta tana yin list d'in wasu abubuwa da za'a siyo mata, Imaan driver ya kaita wajen telansu takai masa d'inkunansu itada Mamie.
Dukansu k'asa suka zauna bayan shigarsu shi Mukhtar ya zauna daga gefen k'afafun Mamie shikuma Saif k'asan kujerar dake facing d'in ta Mamie. Da kulawa take dubansu tana amsa sallamar su fuskarta da murmushi saida sukayi mata barka da hutawa kafin Mukhtar yace
"Mamie k'ara nakawo miki fa wllhy''.
Mamie da har lokacin fuskarta da murmushi tace
"Tohh k'arar wa kuma ka kawo Mukhtar?''.
"Wancan mutumin mana". Yace yana nuna Saif daya had'a girar sama data k'asa idanunshi akan TV (Ina daga gefe nace 'Uhmm anyi abin kai yau ba'a d'auki wayar ta k'aida ba).
Kallon Saif tayi kafin ta maida kallon ta kan Mukhtar tace
'"Meya had'a yakasa rabawa''. Tana y'ar dariya.
Saidaya gyara zama kafin yace
"Mamie gani nayi tunda hidimar nan ta taho ya kamata ace munje can Kano mun zauna da Ayshaan da k'awayenta munji tsare tsarensu da abubuwan da zasu b'ukata koba hakaba Mamie?''. Ya k'are maganar yana kallon Mamie da sigar tambaya.
''Gaskiya ne''. Mamie ta fad'a tana jinjina kai.
Sai daya kalli Saif daya zuba masa ido yana jiran yaji abinda zaice fuska a tamke murmushi ya sakar masa na mugunta ya cigaba da cewa
''Toh Mamie nayi masa maganar yace in k'yaleshi kusan 1week Ina masa maganar yace wai ba inda zashi idan na k'ara yimasa maganar ma sai yaci ubana''. Ya idar maganar yana d'an yin k'asa da kai kamar irin wanda ya fad'i gaskiyar nan.
Saif da mamaki yagama cikashi na jin k'aryar da Mukhtar ya sharo, dukafa yau kwana biyu dayi masa maganar ranar kuma dama a cike yake saboda yadda patients suka tara masa gajiya a hospital tunda yaje bai hutaba saida k'yar yasamu ya kub'uto yadawo gida yazo ya d'an huta kuma yazo ya dameshi da maganar wai yaushe zasuje Kano gurin Ayshaa shikuma dama a kusa yake ya d'udd'ura masa zagi yace karya dameshi, fushi ma yayi ya tafi a ranar yana fad'in zaiga abinda zaiyi akai, ya bishi da fad'in "ya dad'e baiyi abinda zaiyin ba, wato shine yazo ya had'a masa k'arya kenan?.
A fusace yace
"A gidan uwarka mukayi haka dakai''.
''Ka rantse baka zageni ba akan nayi maka maganar?''.
Ganin yadda Mamie ta kafeshi da ido tana masa kallon tuhuma yasa yace
"ALLAH Mamie k'arya yake dukafa yau two days dayayi min maganar ''. Ya k'arasa maganar yana jefawa Mukhtar myguwar harara, Ido kawai Mukhtar ya kashe masa gamida gwalo kasancewar yaba Mamie baya yasa batasan meyakewa Saif d'inba.
Zamanta ta gyara tace
"Da yayi maka maganar saikace masa me?''.
Shiru yayi yana sosa kai gefe d'aya kuma yana hararar Mukhtar d'in.
Tasan bashida amsar fad'a hakan yasa ta girgiza kai ta maida kallonta kan Mukhtar tace
"Rabu da Abbana Mukhtar na fuskanci kafin ayi hidimar nan a k'are saina b'ata masa rai yadda baya zato, duk wani d'acin rai dai bazai hana a d'aura ba. kasamu wani cikin abokanku kuje tare sai kuyi magana dasu".
"Zan samu Dr Sooraj muje tare naga tasu tazo d'aya da mutumin shima yanada juriyar zama da Mr Man''.
Murmushi Mamie tayi tace
"Toh madallah kuje d'in ku tabbatar dai an musu duk abinda sukeso''.
''Insha ALLAH Mamie''.
Daga haka ya mik'e yayiwa Mamie sallama ya fice yana gumtse dariyar shi dan bazai yarda ma su had'u da Saif ba a yanzun dan yaga yadda ya shak'a ba k'aramin aikinsa bane ya bubbugeshi.
Mamie ma paper'n ta ta d'auko ta cigaba da rubutun da take akai, ganin haka yasa ya tashi ya nufi sashenshi. Ta bishi da kallo a fili ta furta 'ALLAH ya had'a mamana da aiki'.
¢¢¢¢¢¢¢¢¢¢¢¢
A ranar da daddare Mamie tasa Imaan ta turawa Mukhtar phone number d'in Ayshaa da address d'in gidansu. Da daddaren ya kira Dr Sooraj ya sanar dashi tafiyar da zasuyi yace ba matsala insha ALLAH ya sanar dashi duk ranar da tafiyar ta kama sai suje d'in ayi masa kara dai badan halinshi ba.
Sai a washegari Mukhtar ya kira Ayshaa da yamma, da kamar ma bazatayi picking ba dataga new number saikuma ta canza shawara tunda batasan waye mai kiran ba.
Sallama sukayi a tare sannan suka amsawa juna tare, Mukhtar yace
''ALLAH yaja da ran amaryar mu barka da yammaci''.
Bata d'au murya ba tunda dama had'uwarsu d'aya dashi, cikin rashin fahimta tace
''Barka dai waye ne?''.
"Kina tare da babban aminin angonki Dr Saif''. Yace cikeda zolaya.
Tsaki taja a ranta tana d'an tab'e baki 'Wai wani angona kota Ina yazama angon nawa'. (Zai zama ne Hajia Ayshaa).
Cikin basarwa tace
''Ina yini Ina gajiya ya gida?''.
Amsawa yayi suka gaisa sannan yayi mata maganar zuwan da zasuyi su zauna akan tsare tsaren bikin.
Wayar ta cire daga kunnenta ta maka mata harara ta mayar tana gatsina baki tace
"Aini badani zakayi magana ba zan turo maka number Hannah k'awata sai kuyi magana da ita''.
''Okay no probs kimin sending d'in number saimu tattauna''.
''Okay''.
Tace tana shirin kashe wayar ya tsayar da ita wai bata tambayeshi angonta ba. K'aramin tsaki taja a ranta itafa bak'in ciki takeji idan yace wai angonta. Ganin yana shirin tsaidata da surutu yasa tace masa 'Ammi na kiranta, da haka tasamu sukayi sallama ta aje wayar tana tura baki da k'unk'uni.
Mrs Salees Mu'az❤️
*DR. SAIF*
Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No 21.
Kamar bazata tura masa number Hannahn ba ko tunanin metayi kuma oho tayi masa sending d'in number.
Yana ganin number kuwa ya kira. Bayan sun gaisa yayi mata bayanin waye shi sukayi magana tare da tsaida ranar da zasuzo saida suka d'an tab'a hira sannan sukayi sallama.
***
After two days.
Su Mukhtar sunzo garin Kano shida Dr Sooraj kyakkyawar tarba suka samu daga wajen Ammi tuni aka cika musu gabansu da abin ci dana sha. Ayshaa har mamakin Mukhtar ta dingayi ganin yadda ya sake da Ammi suketa shan hira ba irin y'ar alkunyar nan da rashin sabo ganin ranar ne zuwanshi na farko gidan.
Saida suka ci suka sha daga abinda Ammi ta tanadar musu sannan suka koma sitting room da zama Hannah ce k'awarta sai Amirah da Husnah y'ay'an yayan Abba kasancewar ita Ammi ba y'ar Kano bace fulanin gombe ne yasa ba danginta ko d'aya.
Ayshaa da farko ma k'in binsu sitting room d'in tayi saida suka takura mata sannan suka tafi tare. Koda taje d'inma zamanta kawai tayi tana latsa waya batare data tofa tata ko d'aya ba, Dama tun farko Abba yace baya son wad'annan partys partys d'in dan haka ta sanar dasu Hannah suka fad'a musu. Abinda zasuyi dai bridal shower a day one waleemah and Arabian nights a day two iya abinda zasuyi kenan sudai daga b'angaren Ayshaan kud'i suka basu masu yawa wanda zai isheshu hidimarsu sukace kuma idan da wani abu da suke b'ukata suyi magana. Ayshaa data gaji da jin magana akan bikin ta tashi tsam ta fice, sukam saida suka sha hira musamman sarakan surutun Mukhtar da Hannah sai Amirah dake bin bayansu Dr Sooraj da Husnah kuwa basu cika magana ba.
Saida suka koma sukayiwa Ammi sallama Ayshaa ma tazo sukayi sallama sannan suka tafi bayan sunyi exchanging numbers a tsakaninsu.
)(()())()()()()(
Sosai Ammi ta dage da bawa Ayshaa magungunan sanyi da wad'anda zasu taimakawa jikinta da lafiyar ta da tsiya take shan magungunan sai Ammi ta mata kaca kaca ta nuna mata b'acin ranta sannan zatasha wataran har kuka take saidai sam Ammi bata biyeta.
Ana saura sati d'aya biki Ayshaa ta koma gidan Aunt Rahmah dazama saboda mak'ociyar Aunt Rahmahn kuma k'awarta mutuniyar maiduguri ce kuma sana'ar tace gyaran jikin amare dan haka Aunt Rahmah tasaki kud'i sosai domin gyaran d'iyar y'ar uwar tata. Duk wannan gyaran da ake mutuniyar taku bawai dason ranta akeba ganinta gyaran me za'ayi mata bayan ba son mijin take ba shima kuma ba sonta yakeba wani tym d'in da tsiya ake gyaran dan ma dai ita Fannah ba wasa jan Ido take mata dolenta ta tsaya amma sai anta fama da ita wajen shiga ruwan lalle da tsugunno kan turarukan k'amshi ana gyaran tana faman k'unk'uni da tura baki Fannah kam batabi ta kanta gyaranta kawai take sadidan da iya gaskiyar ta. Cikin kwana biyu da zuwanta kuwa tayi mugun canzawa dama abinka ga y'ar hutu ya had'u da gyara, ga wani fitinannen k'amshi mai mugun dad'i da sanya nutsuwa daya kama jikinta ta inda duk inda ta zauna saitabar tsarabarshi a gurin.
★****★****★
Su Mukhtar ba zama yadda kasan shine angon saboda yadda yake faman kaida kawo. Suma abokansu sun shigo ciki anata hidimar dasu duk da sunce saidai suyi dan ALLAH badan halinshi ba kamar yadda Dr Sooraj ya fad'a. Saboda shi sam bai cika kulawa dasuba haka kuma bai cika shiga shirginsu ba ko hidimarsu, su wajen shida ne suke tsaye kan al'amarin, Mukhtar, Dr Sooraj, Muhseen, Sabeer sai Mahfooz d'an yayar Mamie sai Basheer dayake kamar d'a a gurin Daddy, duk sa'anni suke da Saif d'in tun ana saura kwana uku sukayiwa garin na Abuja tsinke Saif daya gansu ma sai cewa yayi wai uban me yakawosu tun yanzu. Dayake ya had'u da daidai shi suka had'a baki kuwa wajen fad'in ubanshi ne ya kawosu anyi 1 1 kenan.
Tun zuwansu suka jone dasu Mukhtar suka cigaba da shirye shiryen tare ba abinda ya dameshi dasu duk wanda ya sakashi a ciki ma yanzun nan ya zageshi tas shiyasa sukayi uwar watsi dashi suka cigaba da sabgarsu batare da sun nemeshi ba.
Gida fa yafara d'aukar harami dan bak'i na nesa duk sun hallara dangin Mamie dana Daddyn anata shirye shirye da tanadar abinciccikan da za'aci wajen taron, Mamie da Daddy kam kana kallonsu kasan suna cikin tsantsar farin ciki da jin dad'i na ganin auren yaron nasu bayan tsayin shekarun daya d'auka baiyi aurenba.Imaan dad'i ya cikata ganin mutane a gidansu dan bata saba gani ba dayake maison mutane ce tuni ta shige cikin y'an uwa sa'anninta anata hidima da ita.
***
Safnah tana can damuwa da bak'in ciki kamar sa karta dan da farko ma batayi niyyar zuwa bikin ba k'awarta Mansurah da mahaifiyarta Hajia Safeenah su suka tilasta mata ta fara shirin zuwa itada Mansurahr (Kuji gayyar sod'i).
Fitowarshi wanka kenan wayarshi tafara ringing yasan Mamie ce dan ringtone d'in daya sa musu itada Daddy special ring ne, bakin gado ya zauna yana cigaba da goge sumarshi da k'aramin towel yayi picking call d'in tare da sallama daga can b'angaren Mamie ta amsa sallamar ta d'ora da fad'in yazo tana nemanshi da 'Toh' ya amsa mata sannan ya ajiye wayar ya cigaba da shirinshi.
Black jeans da black shirt yasa ya d'ora white jacket yasa farin takalmi sawu ciki sai bak'in agogon fata daya d'aura a tsintsiyar hannunshi mai cike da kwantattun gargasa ya manna bak'in glass ya fesa turaruka ya fita yaja k'ofar ya rufe ya tafi kiran Mamien.
Gaba d'aya idanun jama'ar dake parlor'n suka dawo kanshi lokacin daya shiga, ya tsani kallo hakan yasa dama yasaka glass d'in sama sama ya gaishesu ya wuce bedroom d'in Mamie. duk suka bishi da kallo wata dattijuwa ta tab'e baki tace
"Oh oh oh wannan yaro anyi kafirin miskili dunkum dunkum dai ba magana".
Ta gefenta ce tace
"Uhm ai kya gaji da gani indai Saifullahi ne Bilkisun (Mamie) ma hak'uri take dashi ai wannan amaryar ta shiga uku". Dariya sauran y'an parlor'n sukayi suna cigaba da gulmar Saif da baisan sunayi ba.
Knocking yayi a bakin k'ofar bedroom d'in tabashi iznin shiga ya kama handle d'in k'ofar ya bud'e ya shiga.
Mamien ce kawai a d'akin sai wata yarinya da batafi shekara shidda ba dake barci kan bed Mamien tana tsaye gaban wardrobe tana saka wasu kaya a ciki, bakin gadon ya zauna daga inda Mamien take tsaye yana mata sannu da aiki ta amsa cikin kulawa.
"Mamie gani".
Saida tasa wani had'add'en lace a wardrobe d'in ta rufe sannan ta zauna kusa dashi tana fad'in
"Abbana yanaga ka fara ramewa ne?''
An sosa masa inda yake masa k'aik'ayi dan haka ya wani shagwab'e murya yace
''Ba doleba Mamie sam yanzu fa banida hutu Mamie''. Kanshi ta shafa tana murmushi tace
"Ai auren kenan babana danma su Mukhtar suna tsaye akan komai ai da abinda zakayi saiyafi haka ALLAH dai yabada zaman lapia".
Tasan bazai amsaba shiyasa ta d'ora da fad'in
"Key d'in part d'inka zaka bani dan bazai yiwu ace kun cigaba da zama a cikiba".
"Why Mamie''. Yace da rashin fahimta.
"So kake a b'ata mata part d'inta? No rufeshi za'ayi sai ranar da za'a kawota saidai idan kana b'ukatar d'aukar wani abun saika bud'e''.
Kai ya shiga mirginawa kamar wani k'aramin yaro yana b'ata fuska yake fad'in
''Haba Mamie for God sake ya za'ayi min haka nida part d'ina kuma a hanani shiga''.
''Yanzu ai yatashi daga naka kai kad'ai yakoma naku ku biyu''. Mamie ta amsa masa tana dariyar yadda yake wani tura baki.
"Toh Mamie Ina ni zan koma?''.
"Ga part d'in waje can ku koma duk abinda yake dai anan akwai acan d'in , kai dan bakada kunya ma saikazo kana tsattsallake mutane kana shigewa ana hidimar taka''. Ta k'are maganar tana d'an tallafe masa k'eya. Wajen ya dafe yana b'ata fuska Mamie tayi dariya tana mik'ewa tsaye dolenshi ya ciro key d'in daga jikin makullan motarshi ya mik'a mata ya fice tana masa ALLAH ya kiyaye.
Yana fitowa parlor'n wata abokiyar wasanshi tafara tsokanarshi bai kulata yayi ficewarshi yana wani k'ara tamke fuska da ciro wayarshi daga aljihun jeans d'inshi yasan dai bazai wuce wad'annan mayun ba(su Mukhtar). Dariya duk y'an parlor'n sukasa mata ganin yadda ya kunyatata, wata matashiyar matace tace
"Kema dai Kareemah meya kaiki? Kinsan halin d'an yarfin nan sarai ya dizga mutum ba wuya yake masaba, shiyasa ni bana shiga sabgarshi wllhy''.
''Ai kin huta nima d'in rabon zai yarfani d'inne d'an banza da jajayen kunnuwa". Gaba d'aya sukasa dariya suka cigaba da hirarsu.
********
Sai ana gobe kamu sannan Ayshaa ta dawo gida. 'Masha ALLAH' itace kalmar dana ambata lokacin dana ganta gaba d'ayanta ta canza kamanni ta k'ara wani irin mugun kyau mai tafiya da hankali tamkar wadda aka fito da ita daga inji sai wani glowing skin d'inta take da wani irin santsi da laushi da fatar take, ga k'amshin nan mai dad'i daya manne mata a jiki kowani abun ta tab'a yanzu zai hau irin k'amshin, Tabarakallah amarya dai ta fito rad'au da ita masha ALLAH.
Suma gidan nasu yafara d'inkewa da jama'a y'an uwan Ammi duk sunzo sai wanda ba'a rasaba wad'anda zasuzo washegari da kuma ranar d'aurin aure.
Washegari.
Tun wuri suka tafi wajen saloon da k'unshi itada tsirarun k'awayenta da kuma y'anmata y'an uwansu. Sai bayan la'asar suka dawo, suna dawowa kuma aka fara shirye shiryen kamun.
Amarya tayi kyau har tagaji sai walwali take tana haskawa kowa ya kalleta saiya yaba irin kwayun datayi hannu da k'afarta da sukasha zanen lalle bak'i da ja ya zauna rad'au kan farar fatarta k'unshin yayi kyau sosai dan k'wararriya ce tayi musu musamman da hannayen suka sha adon warwaraye da zobba da kuma agogo abindai sai wanda yagani Ina hango y'an team Saif suna lek'en Ayshaa ana tutturesu amma dan naci saida suka san yadda sukayi suka shige gaba gaba bazan kama suna ba dai.
An gabatar da kamu a harabar gidan inda aka k'awata harabar da had'add'en dacoration
Anyi kamu lafiya an rarraba abubuwan da aka tanada irin wanda ake rabawa wajen kamu, sai daf da magreebah sannan aka tashi.
Washegari kuma akayi waleemah inda aka gayyaci malamai mata har su uku suka gabatar da nasihohi akan zamantakewar aure sannan akaci aka sha aka rarraba Alqur'anai da dardumai da harda carbina masu kyau da sauran abubuwa dai na rabo.
A ranar da daddare kuma sukayi Arabian nights sukayi shigar dogayen riguna iya y'an matane kawai amma kasancewar a gidanne yasa iyaye ma saida suka fiffito sukasha kallo, abin ya k'ayatar sosai amarya tanata d'aukan wanka yadda ya kamata anata cancarewa. K'arfe goman kuma masallachin kusa da gidansu da Abba yayi magana da limamin masallachin suka fara musaffah wato kwanan karatu inda zasu kwana suna karatun Alqur'ani mai girma abinci mai kyau da ruwan roba da lemuka aka kai masallachin saboda masu karatun. Abin dai ba bidi'a.
Toh ALLAH dai yabada zaman lapia malam Saifu.
Washegari asabar aka tashi da hidimar d'aurin aure, Ayshaa jiki yafara la'asar kawai kallon mutane take suna hidimarsu ba abinda ya shafesu itakuwa tsorone fall cikin ranta k'arfin hali kawai take, abokan wasa sai tsokanarta suke bata mayarwa da ada ne kam kafin kakai maganar tabaka amsa tamkar tana jira.
Tuni garin Kano yafara d'aukar d'imbin jama'a y'an d'aurin auren tako Ina galla gallan motoci ne ke b'ullowa hidima ce ta fitattu kuma sanannu a fad'in Nigeria da wajen cikinta.
Angwaye ma sun kusa k'arasowa da tawagarshi fad'ar irin kyawun da ango yayi ma b'ata bakine kunsan dai mutumin naku da iya d'aukar wanka bare kuma a yau datake rana ta musamman duk da shidai bai d'auki ranar da wani muhimmanci ba a cewar shi amma.
Motocine sunfi guda ashirin tsala tsala sukayo jeran gwano kan titin wadda yake a ciki ce a tsakiya Mahfooz ne mai tuk'in sai Auwal wani d'an uwansu dake gefenshi back seat d'in kuma Saif ne da Sabeer kawai banda k'amshin kalolin turaruka ba abinda ke tashi a motar, Saif yayi relaxing sosai a jikin kujerar kanshi a sama idanunshi na kallon saman motar ganin abin yake tamkar a mafarki wai shine yau ake d'aurawa aure, auren ma da Ayshaa wadda bai tab'a tunanin aurenta ba a hankali daki daki ya shiga tariyo farkon had'uwarsu da yayarta takaita hospital tana zazzab'i da yadda suka cigaba da had'uwa a gurare daban daban.
Sanye yake cikin wata fitinanniyar farar shadda k'al kamar takarda y'ar ciki da wando da babbar riga tasha wani uban aiki mai masifar kyau da akayi da kalar ash d'in zare, saiya kafa hula zanna bukar data hau sosai da kalar zaren takalmin k'afarshi ma ash d'inne na zallar fata sai agogon daya mak'ala a tsintsiyar hannunshi wadda sark'ar agogon ta kasance ash. An daidaita sumar kanshi tasha uban gyara fuskar ma ta k'ara fayau ta kuma k'ara kyau saboda gyaran da sajenshi da zagayayyen gashin bakinshi quarter million yasha, fuskar dai gata nan ne dai kawai dan mutum bai isa ya fassara yanayin dayake cikiba na farin ciki ko akasin haka. Fatabarakallahu ahsanul khaleek'in. Kyau dai ansha shi kam har ba'a magana.
Sabeer sai janshi yake da hira yamasa bakam kamar badashi yakeba Mahfooz ma juyowa yayi yacewa Sabeer d'in 'Ya k'yaleshi yasan dai halin Man d'in nan ba kulashi zaiyiba tsabar iskanci da iya shege ranar d'aurin aurenshi ma bazai saki fuska yayi fara'a ba yagama iskancin nashi dai bashi zai hana d'aura auren ba maybe ma nan da nine months suna yagama lalube d'iyar mutane'. Shidai ci kanka baice ba saisu Auwal ne da suketa faman dariya.
Kai tsaye gidan su Ayshaa suka tafi dan lokacin d'aurin auren ma ya kusa.
K'arfe 11am da y'an mintuna d'aruruwan al'umma suka tabbatar suka kuma shaida d'aurin auren
SAIFULLAHI SADEEQ MATAWALLE da amaryar shi AYSHAA MOHAMMAD THABIT akan sadaki dubu d'ari lakadan ba ajalan ba.
Duk wanda ka gani a wajen nan farin ciki yake musamman Daddy da Abba da nasu ya zarta na kowa, Saif kam dolenshi ya d'an saki fuskar saboda mutane da yadda Daddy ya dinga jefa masa wani irin kallo dayasan ma'anar shi, haka dai ya dinga gaggaisawa da mutane yana faman zuba yak'e.
A cikin gida kam tunda Ayshaa taji wata marok'iya ta shigo tanata gud'a taji gidan ya k'ara kacamewa da hayaniya da gud'a alamun an d'aura auren tasaki kuka harda shasshek'a har taso b'ata kwalliyar tata saida wata k'anwar Abba tayita rarrashinta da bata baki sannan tayi shiru tana jan ajiyar zuciya gaba d'aya tagama sarewa da al'amarin bare dataji ana maganar a ranar za'a kaita ai saita k'ara rikicewa da k'yar dai aka lallab'ata. Dama kuma da k'yar Aunt Rahmah ta lallab'ata tayi wanka aka shiryata cikin farar shadda riga da zani datasha aikin stone work da jajayen duwatsu saiya zamana duk abinda tayi kwalliya dashi red color ne kama daga kan necklace da earrings da agogo dasu awarwaro da zobuna mayafi ma ja ne da takalmi da k'aramar jakarta, da k'yar ta yarda akayi mata y'ar madaidaiciyar kwalliya dan saida aka kirawo goggo haleema yayar Ammi da suke jin tsoronta saboda d'an banzan fad'a datake dashi.
Bayan d'aurin auren angwaye suka shiga gaida iyaye, bayan an gaggaisa suka fito aka yiyyi hotuna daga nan suka rankaya suka tafi Taheer guest palace inda sukayi wani d'an k'aramin party a ciki kafin su huce Abuja.
Mrs Salees Mu'az❤️
*DR. SAIF*
Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No 22.
_*Dan ALLAH masu bina private suna so daga farko suyi hakuri please book din nan yafara nisa su dinga nema a groups din dasuke ba za'a rasaba.
Nagode sosai da kulawa luv u oll.
Ayshaa fa tak'ara karaya ganin abin da gaske ne dai zata tafi tabar Amminta.
Haka aka cigaba da shan shagalin biki jikin Ayshaa duk a sanyaye yake ita kad'ai tasan metake ji.
Wasu dafa cikin abokan ne suka tsaya dan taho da amarya ciki harda Mukhtar da Mahfooz, Saif kam tuni sukayi gaba su da sauran tawagar.
Bayan sallahr zuhr aka fara shirye shiryen tafiya, ankai Ayshaa wajen Abbanta da wasu daga cikin y'an uwanshi dabasu tafiba suke zaune a sitting room, nasiha mai ratsa jiki sukayi mata kowa ya tofa albarkacin bakinshi kuka kawai take tana sakin ajiyar zuciya. Daga nan yayan Abba wanda ya karb'i auren nata ya damk'a mata sadakinta a hannunta ai saita k'ara b'arke musu da kuka haka dai aka kamota aka fito da ita kud'in ma sai wata goggon Ammi ce ta ta d'aukesu dan k'asa ta ajiyesu. Daga nan kuma aka koma cikin gida wajen iyaye mata dan su tofa nasu albarkacin bakin.
Ammi kam bata wani yi magana ba sosai saboda duk wata nasiha da jan kunne ta riga datayi mata tun tuni saidai tishi akan wanda tayin.
D'ai d'ai ne basuyi k'wallah ba cikin mutanen d'akin lokacin da akazo fita da ita tabi ta cacume Ammi tana gunjin kuka tana fad'in ita ba inda zata. Ammin kanta dauriya ce kawai take amma duk da haka saida idanunta suka ciko da k'wallah shikenan mai d'ebe mata kewar ta tafi tafiya ta har abada da ba'a fatan dawowarta indai ba zuwan kawo ziyara ba. Addu'a ta dinga mata ta zaman lapia da mijinta da samun kyakkyawar zuri'ah dhayyibah saleehah wadda wadda MANZO sallallahu alayhi wasallam zaiyi alfahari da ita ranar Alqiyamah.
Duk yadda aka d'auki abin ya wuce haka dan Ayshaa firr tak'i sakin Ammi har saida Abba yazo da lallashi da ban baki ya samu ya rabata da jikin Ammi ya rungumeta a b'arin jikinshi suka fita. Da kanshi yasata a mota yana binta da kyawawan addu'o'e shi kanshi Abban k'arfin hali ne kawai irin na maza amma yanajin rabuwa da y'ar autarsu har cikin ranshi har motarsu ta d'aga yana binta da addu'a (Toh Mrs Saif ALLAH ya bada zaman lapia da fahimtar juna).
Ko a cikin motar ma bakinta baiyi shiruba ta cigaba da raira kukanta tun ana rarrashinta har aka gaji aka k'yaleta ganin abin nata bana k'are bane tana lafe jikin Aunt Rahmah tun tana kukan da k'arfi harta koma yi k'asa k'asa daga k'arshe ma akaji shiru sai ajiyar zuciya datake ta faman saukewa alamun barci ne ya d'auketa.
Suna komawa yaso shigewa part d'in da Mamie ta koroshi su Sabeer suka hanashi suka tasa k'eyarshi cikin gidan dayake dank'am da mutane anata shan shagali. saida suka d'auko masa babbar rigarshi yasa daya cireta tun shigarshi mota. Suna shiga aka fara sakin gud'a gidan ya k'ara kacamewa da hayaniyar mata, shidai yak'e kawai yake dan a matuk'ar gajiye yake ga wani irin ciwon kai dake d'awainiya dashi.
Sai daya lalubo Mamien shi aikuwa kasa b'oye farin cikinta tayi ta rungumeshi tana dariyar farin ciki shima d'in saiya tsinci kansa da sakin lallausan murmushi. Yana matuk'ar murna da jin dad'i idan yaga iyayenshi na cikin farin ciki, d'agoshi tayi ta kama damtsen hannunshi tana kallonshi fuskar ta d'auke da mad'aukakin murmushi yayin da k'wallah suka fara cika idanunta bazata iya misalta irin tsantsar farin cikin datake ciki a yau d'in nan ba yau ALLAH ya cika mata burinta na auren yaronta. Ido ya d'an zaro kad'an ganin k'wallahr idonta kai ya shiga jijjigawa yana b'ata fuska yace
''Mamieeeee yaja sunan, please ki daina mana banaso''. Ya ida maganar yana saka hannu yana share mata idon nata.
''ALHAMDULILLAH, nagodewa ALLAH daya kaini wannan lokacin yarona ya girma ya shiga sawun manya ubangiji ya baka ikon d'aukar amanar da aka baka babana ALLAH yayi maka albarka yarona yayi riq'o da hannunka''. Da 'Ameen' ya amsa yana hugging d'inta saikuma yafara marairaice mata shifa yagaji wllhy, ko bai fad'a ba tasan yagajin dan haka tace masa yaje ya zauna ya d'an huta dan zuwa dare ma akwai dinner ta musamman da aka shirya. Shi baima san da dinner ba ya karyar da kai yace
"Again dai Mamie?''.
"Yes, dole mu nuna farin cikinmu babana''.
Saida aka yi hotuna sosai a cikin gidan duk da yadda yaso samfewa.
Hidima ta cigaba da gudana cikin nutsuwa da kwanciyar hankali kamar yadda Mamien take fata. Abinciccika gasu nan kala kala da wanda akayi a gidan da wanda kuma aka bayar ayi a waje sai wanda mutum ya zab'a lemuka da ruwan roba gasu nan sai kalar da mutum keso. Safnah da Mansurah kam ko gidan bikin basu zoba suna gidan Hajjah sun mak'ale kamar ma ba bikin sukazo ba, duk da dai tana kwad'ayin ganin jinin jikin nata Saif amma batason abinda zai d'aga mata hankali dan haka tayi zamanta sai dinner da akace za'ayi yau da Mansurah ta matsa mata kan cewa lallai sai sun halarta dan bazai yiwu ace sunzo biki ba kuma sun lik'e a gida basu fitaba.
¢¢¢¢¢¢¢¢¢
¢¢€€€€€€€€€€€€€€€€€€
¢¢¢¢¢¢¢¢¢
Y'an kawo amarya sun k'araso, Ayshaa da saida aka shigo garin Abuja sannan ta farka barcinta tasha sosai abinta. Tana farkawa kuma ta d'ora daga inda ta tsaya saidai k'asa k'asa take kukan dan ita kanta ta gaji.
Kyakkyawar karb'a suka samu daga wajen Mamie da danginta nan parlor'n Mamien aka zauna aka damk'a amanar Ayshaa wajenta ta karb'a kuwa da hannu bibbiyu ita ganinta ma har sai anbata amanar Ayshaa? Ita ai matsayin y'a take kallon Ayshaa har cikin zuciyarta kuwa.
An cika musu gabansu da abinci kala kala da lemuka, amaryar ma Mamie bedroom d'inta ta jata danta lura kamar batada lafiya, hakanne kuwa dan wani mugun zazzab'i da ciwon kaine suka dirar mata lokaci d'aya saboda kukan datasha, jikin harya d'auki zafi.
Abinci tasa aka kawo mata tafara lallab'ata taci, da k'yar taci kad'an saboda zafin da jikinta yayi ta bata magani tasha shima saidatayi fama dan ba k'aunarshi take ba. Tanasha ta kwanta ta lullub'a mata wani k'aton blanket mai taushi(Amarya zazzab'i yayi kaye).
Saida barci ya d'auketa sannan Mamie taja mata k'ofar ta fita ta koma wajen y'an uwan Ayshaa da aka kaisu wani babban d'aki mai kyau dansu huta.
Barcinta tasha hankali kwance, lokacin data tashi shida ta wuce sosai garin harya d'an fara duhu. Sosai tajj dad'in jikinta dan zazzab'in ya sauka gaba d'aya ciwon kan ma ya daina sai lokaci zuwa lokaci dayake d'an sara mata saidai jikinta da batajinshi daidai ga rashin k'warin jikin.
Mamie da tunda ta kwanta take lek'ota akai akai taga kota farka sai taga tanata barcinta saita koma, wannan zuwan kam tana bud'e d'akin ta ganta zaune kan gadon da saurinta ta k'arasa tana fad'in
"Mamana kin tashi?''.
Kai ta d'aga mata a hankali cikeda kunya.
Bakin gadon ta zauna tana kamo hannunta tace. "Sannu mamana zazzab'in ya sauka ko?.
"Eh, Mamie''.
"Alhamdulillah sannu ALLAH ya sauke, ai zaki iya zuwa dinner da za'ayi ko?''.
Kai kawai ta d'aga, amma ita cikin ranta ma bataso wannan dinner ba dan tasan dole saita had'u da mutumin nan.
"Masha ALLAH, bari in had'a miki ruwa mai d'umi kiyi wanka zakiji dad'in jikinki sosai''. Bata jira amsarta ba ta shige bathroom itadai da kallo ta bita kawai tanajin k'aunar matar har cikin zuciyarta.
Bata jimaba ta fito tace taje tayi wankan tana zuwa zata dawo. Ta fita tareda jan k'ofar.
Sai data rage kayan jikinta sannan ta shiga toilet d'in tasamu ta had'a mata ruwa masu d'umi sosai da turarukan wanka masu dad'in k'amshi.
Tunda magreebah ta gabato aka shiga shirye shiryen tafiya wajen dinner a wani babban Hall da aka kama, kowa kagani da abinda yake dan harda iyaye mata.
Ta dad'e cikin ruwan tana lumshe ido kamar maison komawa barcin kafin daga bisani tayi wankan ta d'aura alwalah ta fito.
Mutum uku tasamu a d'akin Aunt Rahmah da wata da zasuyi sa'a da Aunt Rahmahn kamarsu d'aya da Mamie saidai Mamien ta nuna mata manyanta saikuma wata matashiyar mata, wannan mai kama da Mamien ce ta tarota tana fad'in
"Sannu maman mu ya jikin Aunt Bilki tace bakijin dad'i''.
''Naji sauk'i''. Tace a hankali kan stool d'in mirror ta zaunar da ita Aunt Rahmah nayi mata sannu.
"Tom makeup artist zoki fara aikinki''. Wannan mai kama da Mamien ta fad'a tana dariya gamida kallon d'aya matar.
Dariya itama d'in tayi tace
''Toh Aunt Maryam yanzu kuwa''.
Jin makeup za'ayi mata yasa ta marairaicewa tana kallon Aunt Rahmah tace
''Please Aunt Rahmah nifa banson makeup d'in nan wllhy''.
Haka nan zaki hak'ura ai ba heavy za'ayi miki ba''. Aunt Rahmah ce tayi maganar tana k'ara turata gaban mirror'n.
Itadai harga ALLAH bason kwalliyar nan take ba amma ba yadda ta iya dole ta tsaya aka fara mata kwalliyar ganin yadda Aunt Maryam da Aunt Rahmah suka kasa suka tsare.
A can part d'in da angwaye ma suke sai shirye shiryen tafiya dinner ake kowa da irin shirin dayake ga wani cool music dake tashi a hankali cikin d'akin.
Gogan naku kam yana kwance daga bakin gado ya tada kanshi da pillow ya d'ago kanshi sosai ya hard'e k'afa tareda d'ora laptop akan ruwan cikinshi yana danne danne a ciki bak'in wandone 3qrt a jikinshi sai k'aramar riga blue mara hannu. Duk hidimar da sukeyi baibi ta kansu ba hankalinshi kacokam yana kan abinda yake.
Mukhtar ne ya k'araso inda yake yana gyara karin hularshi yace
"Dallah malam katashi ka shirya karka b'ata mana lokaci''.
Batare daya d'auke idanunshi daga kan laptop d'inba yace
"Idan nak'i fa?''.
''Yo wani abune a ciki? Mugun duka kawai zakasha mu d'aureka kuma saimun wanke ka tas yaro''.
Kamar bazaiyi magana ba saikuma ya juyo ya kalli Mukhtar d'in yace
"Dayake gaku tantiran y'an iska ko.
K'wafa Mukhtar yayi yana y'ar dariya yace
"Dan ALLAH S Matawalle karka tashi ka shirya kaga yadda zamuci ubanka a d'akin nan, k'aryar iskanci kake wllhy''.
"Banza d'an iska''. Saif yace tareda jan tsaki ya juya ya maida idanunshi kan laptop d'in.
Gaba Mukhtar yayi ya nufi wajen mirror yana fad'in
''Y'an iskan ai dayawa kaine babban mu".
Mukhtar na barin wajen Basheer ya shigo hannunshi da wata jaka mai d'an girma ya ajiye kan side drawer dake kusa da kan Saif yace
"Gashi nan wai su zaka sa idan zaka shiya''.
''Bazan saba, dallah d'auke abarka''.
Harara Basheer ya maka masa yace
Malam bafa nina kawo nace kasaba zakamin k'ananun iskancin daka saba''.
''K'yaleshi Basheer ALLAH yau inajin sai munci uban gayen nan naga wani take taken rashin mutunci yakeji''. Mahfooz ne yayi maganar yana d'aura agogo a hannunshi.
Duk zagin da suke masa ko gezau bai tankaba bai kuma bar abinda yake ba. Sai dayaga dama sannan ya rufe laptop d'in ya d'orata kan side drawer ya shiga wanka lokacin duk kusan sun gama shiryawa sai mabambantan k'amshi ke tashi masu dad'i da k'amshi da kuma k'amshin gezner's kala kala dake jikunansu.
Sai daya gama nuk'u nuk'unshi a bathroom d'in sannan ya fito ya shiga shiryawa lokacin suna ta shan selfie.
Jakar ya bud'e ya fito da kayan ciki, wata rantsattsiyar shaddace peach color sai faman shek'i da walwali take tana zuba maik'o, riga da wandone harda babbar riga sai takalmi peach da agogo da hula duk kalar kayan.
Yasan duk aikin Mamie ne wannan.
''Oh my God Mamieeee''. Yace murya a narke yana kallon babbar rigar shifa wllhy yagaji da babbar rigar nan bala'in takura masa take shifa da k'ananun kaya ma zai saka(saboda bakada man kai inji billyn abdoul).
Duk Ido suka zuba masa lokacin daya gama shiryawa saboda tsabar kyau da yayi kayan sun matuk'ar haskashi sai wani annurin kyau yake fitarwa zanso kuga Saif a lokacin kuga irin yadda ya zuba kyau na d'aukar magana.
''Malamai kallon ya isheku haka karku cinyeni d'anye''. Yace yana wani tsuke fuska gamida bud'e wani had'add'en turare ya fara fesawa.
Nan kowa ya fara fad'ar albarkacin bakinshi suna yaba kyawun dayayi har Auwal na fad'in 'zai gigita d'iyar mutane da wannan salon gayun nashi'.
Baice k'ala ba ya wuce wajen mirror yana k'ara daidaita zaman hularshi.
Duk yadda ya dinga zamewa saida suka yiyyi hotuna dashi ba laifi dai ya saki fuskar ba kamar yadda aka santaba.
Mamie ce takawo wasu kaya doguwar rigace har k'asa ta wani material mai rawa, d'inkin mutunci ne sosai dan dogon hannu ne ma ya rufe mata ko Ina amma d'inkin yayi matuk'ar yin kyau peach color ne kalar kayan Saif duk abinda akayi mata amfani dasu na ado kalar peach d'inne haka takalminta mai uban tsini mai mad'auri da purse d'inta peach ne anzuba ruwan 2mach gsky masu karatu bazan tsaya dai misalta muku irin had'uwar da Ayshaa tayiba Masha ALLAH ku k'iyasta da kanku k'amshi kuwa ba'a magana kamar wadda tayi wanka da ruwan turaren gaba d'aya. Fuskar ta ba wata fara'a sai wani cika da batsewa take saida Aunt Rahmah tayi mata alamun tasaki fuskarta sannan ta d'an saki tana d'an tura baki.
Cike harabar gidan take da mutane da motoci anata tafiya.
Lokacin da Mamie ta shigo ta ganta bayan angama shiryata tasbihi ta shiga yi cikin farin ciki tana yaba kyawun datayi, k'asa tayi da kanta tana murmushi cikin kunya.
Aunt Rahmah da Aunt Maryam da suka jone tun had'uwarsu su suka fito da ita harabar gidan inda zasu tafi duk an tattafi sai tsirarun mutane da suke shirin tafiya.
Gaban wata dank'areriyar k'atuwar farar motar suka tsaya Aunt Maryam ta bud'e mata tace
''Toh my daughter bismillah''.
Fuska ta narke tace
"Aunt Maryam ba daku zan tafi ba?.
Dariya tayi tace
"Ina kika tab'a gani anyi haka? Da mijinki zaki tafi''.
Baki ta turo zatayi magana Aunt Rahmah tace
''Oyaa maza ki shiga ana jiranki". Tayi maganar tana turata cikin motar. Tana shiga suka rufe suka bar wajen, inda motar Aunt Maryam take suka k'arasa dama da wasu a back seat Aunt Rahmah ta shiga front seat Aunt Maryam tajasu suka tafi.
Yadda yake a can k'arshen motar itama data shigan saita zauna daga bakin motar bata matsa can ba, yana zaune da waya a kunnenshi alamun waya yake duk da dai bawai magana yakeba sai zuwa can taji ya furta 'Amin' kamar wani mai ciwon hak'ori ya sauke wayar ya rik'eta a hannunshi yadda bai kalli inda take ba haka itama bata kalli inda yake ba ta gefen ido dai ta d'an saci kallonshi taga yadda ya wani had'e rai yana wani cin d'aci, baki ta d'an tab'e kawai ta maida kallonta kan purse d'in hannunta.
Shima d'in da munafukin kallon nan nashi na k'asan Ido yake k'are mata kallo, harga ALLAH kwalliyar ta tafi dashi da imaninshi ga wata muguwar kasala data lullub'eshi tun shigowarta saboda wani irin kalar turare dayaji a jikinta dayasa kuzarinshi ya k'ara k'asa sosai. Musamman daya had'u da nashi k'amshin da sanyin A.c ya cakud'e yabada wani kalar k'amshin mai saukar da nutsuwa da kwanciyar hankali. K'aramar ajiyar zuciya ya sauke yana lumshe ido gamida cije lips d'inshi yana k'ara relaxing kan kujerar saboda yanayin shi dake son canzawa.
Dayake Babu wani nisan kirki nan da nan suka isa k'aton Hall d'in daya gaji da had'uwa.
Su Aunt Rahmah ma sun rigasu isa wajen ko dan Auwal daya tuk'a motar a hankali ya tafi da da ita yana wani slow kamar baya son tuk'in.
Suna yin parking Aunt Rahmah da Aunt Maryam sukazo suka bud'e murafan motar, suna bud'ewa kuwa Ayshaa ta fito shikam saida ya tsaya fi'ilin tsiya dan k'in fitowar yayi saida Aunt Maryam tace
''Wai ko saina kira su Mahfooz ne sun fito dakai nikam''. Sai a sannan ya fito yana gyara babbar rigarshi yana wani basarwa.
Baiyi aune ba yaji an damk'i hannunshi an had'a dana Ayshaa, Aunt Maryam ce da wannan aikin murya ya narke yace
"Aunt Maryaaaam......"Malam haka ake naga alamun saina zaunar dakai na maka special lecture akan mace''. Ta katseshi tare da barin wajen ta kama hannun Aunt Rahmah sukayi gaba suna dariya.
Dukansu saida suka saki ajiyar zuciya saboda laushin hannun junansu daya ratsasu shikam saidaya d'an rumtse ido yana cije baki saboda yanayin daya shiga.
Y'an mata da samari ne da yawa wasu a gabansu wasu a bayansu suka fara takawa a hankali zuwa cikin ainihin Hall d'in dayake ta walwali da kala kalar fitilu. Baisan ya akayi ba ya tsinci kansa da sake damk'e hannunta sosai har ta d'anji zafi ta waigo ta kalleshi shima daidai lokacin da shima d'in ya waigo idanunsu suka had'u dana juna.
Mrs Salees Mu'az❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu (Ummee).
*DR. SAIF*
Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No 23.
Cikeda basarwa yayi saurin d'auke kanshi yana wani k'ara tsuke fuska, itama d'in kauda kai tayi tana d'an tab'e baki. Sunci gaba da tafiya a hankali hannayensu mak'ale dana juna, tuni Hall d'in ya k'ara hargitsewa saboda shigowarsu akasa wata tattausar wak'a ta ango da amarya.
Gurin dayafi ko Ina kyau da ado da aka tanada dansu suka k'arasa suka zauna sai a lokacin ya sakar mata hannun. Addu'a aka fara bud'e wajen da ita kafin a kira babban aminin ango Mukhtar yazo ya d'an bada tak'aitaccen tarihin ango, saikuma Hannah data bada na amarya.
Tunda ango da amarya suka zauna Mansurah ta tsurawa Saif idanu tanason tantancewa shin shine ko ba shibane, exactly shine babu ko tantama dama shine Saif d'in da Safnah ta matowa? Lokaci yayi, lokacin da zata d'auki fansar abinda yayi mata yazo saiyayi dana sanin zuwa duniya ta dalilinta (Kuji ikon ALLAH kenan dawani abu a tsakaninsu, shin Saif d'in ma ya santa kuwa wata sabuwa inji y'an caca).
Safnah da zuciyarta ke wani irin mugun tuk'uk'i tun zaman ta wajen bare kuma dasu Saif suka shigo dan ta gefenta suka wuce ji take tamkar tayita tsala ihu ko zata samu sauk'in rad'ad'in da zuciyarta keyi mata. Ido ta k'ura musu lokacin da suka zauna tana k'are musu kallo taga yadda Saif d'in yayi masifar yin kyau kayan sun hau sun kuma zauna sosai a jikinsa fuskarshi sai wani annuri take fitarwa duk da dai a tamke take amma ya d'an saketa ba kamar yadda suka shigo ba saita ganshi tamkar wanda aka k'arawa kyau akan nada. Ta maida kallonta gefenshi kan Ayshaa ta runtse ido na takaici ganin ba abinda zata nunawa Ayshaan to ta inama zata had'a kanta da Ayshaa? Kyawun fuska,surar jiki da k'uruciya duk Ayshaan ta fita amma hakan fa bashi zaisa ta karaya ba sai inda k'arfin ta ya k'are akan Saif bazata tab'a bar mata shiba Saif natane ita kad'ai zatayi duk yadda zatayi taga ta mallakeshi ko ana ha maza ha mata muje zuwa dai wai mahaukaci ya hau kura, cikin dabara tasa hannu ta d'auke y'ar k'wallahr data fara zubowa daga idonta tanajin wata tsanar Ayshaa a ranta duk da taji labarin ba da son ranshi zai aureta ba.
Can d'aya gefen ma 3 Z ne zaune, wato Zubaida, Zainab da Zuhrah. Sun samu zuwane ta hanyar Zubaida da Zee ta matsa mata lallai sunaso su halarci wajen dinner.
Yadda zuciyar Safnah ke cikin k'unci hakama zuhrahn ganin Saif d'in ya k'ara tada mata wata muguwar k'aunarshi tanata k'iyasta yadda zata raba Saif da Ayshaa ta d'auki ALWASHI kuma saita tabbatar dashi, Ayshaan zata fara kawarwa kafin ta dawo kan Saif d'in itama d'in dai hakan taji ta tsani Ayshaa ta yadda da zata samu dama a lokacin da zata iya caka mata wuk'a ta kasheta har lahira(Abin naki azimun ne zuhrah kinfi k'arfina).
An kira ango da amarya domin su yanka cake, ba wanda ya motsa a cikinsu saida Mc ya k'ara maimaitawa sannan Saif ya mik'a mata tafin hannunshi alamun ta sako nata kallonshi ta d'anyi taga idanunshi a kanta ya cukule fuska saita nuna tamkar ma bata gane abinda yake nufiba tana shirin juyar da kai taji muryarshi a cunkushe yace
''Idanun mutane yana kanmu ya kamata ki kiyaye''. Baki ta d'an gatsina kad'an sannan takai hannunta kan nashi tamkar wadda zata d'ora akan wuta tana sawa kuwa ya damk'e tare da mik'ewa itama ta mik'e suka nufi wajen yanka cake d'in. A hankali suka fara sauka daga kan step d'in last step d'in da zasu sauka tayi wata irin zamewa saboda yadda jikinta yake ba k'wari ga hill shoes dake k'afarta ga kuma wani sabon zazzab'in dake son rufeta. Da wani irin mugun hanzari dashi kanshi yayi mamaki ya tarota ta fad'a k'irjinshi yasa duka hannayenshi ya zagaye waist d'inta, wata y'ar ajiyar zuciya tasaki saboda yadda ta gama saddak'arwa sai takai k'asa tuni Hall d'in ya d'auki sowa da tafi especially rukunin inda su Mukhtar ke zaune dasu Mahfooz da sauran abokansu har tsaye suka mik'e suna d'aga hannaye sama suna ihu dan sosai abin ya k'ayatar dasu. kafin yayi wani yunk'urin rabata da jikinshi har an fara d'aukarsu hotuna sai hasken flashers dake haskesu tako Ina, Ido ya d'an lumshe had'i da jan k'aramin tsaki cikin ranshi ya bud'e kan camera's dake ta haskasu harda masu yin video dukansu kunya ce ta kamasu ganin akwai iyaye a wajen, mazewa yayi kawai a hankali cikin nutsuwa ya d'agata sai dayaga ta daidaita sosai ta yadda ko ya saketa bazata fad'i ba sannan ya saketa.
''Lazy girl kawai''. Ta tsinci muryarshi ya fad'a a hankali kusada kunnenta lokacin da suke k'arasa sauka, ga wanda baisani bama saiya iya cewa wata maganar soyayyar yake fad'a mata.
(Zuhrah da Safnah kam saida zuciyarsu tayi zillo lokacin da Ayshaa ta fad'a k'irjin Saif suka d'an zabura tareda komawa su zauna kowacce tana jan tsaki, saidai muce muku sorryn ku).
Shiya fara yanka cake d'in d'an k'arami yasa mata a baki akayi tafi sannan itama ta d'auki knife ta fara yanka wanda zata bashi, gargad'i ya shiga yimata ta cikin idanunshi kan ta rage wanda ta yanko d'in dan babba ta yanko saidai ta nuna masa bata gane meyake nufiba takai masa bakinshi tana d'an wani murmushi da bansan ma'anar shiba. Sai daya d'an harareta ya cije baki sannan ya bud'e bakin, kad'an yayi niyyar gutsura saidai kafin ya ankara ta tura masa shi duka bakinshi da k'yar ya had'iyeshi har yana b'ata masa k'asan bakinshi kan zagayayyen gemunshi dayasha gyara, nan ma dai tafin akayi wasu na dariyar abinda tayi masa wasu kam haushi ne ya k'umesu irin su o,o.
Ya matuk'ar bata dariya ganin yadda ya tamke fuska yana wani tsuke baki duk gurin ma dariyar yabasu saboda yadda yayi, dariyar ta ta matse dan harga ALLAH yabata dariyar. Tissue ya yago yana goge bakinshi yana faman zuba mata wani irin kallo mai kamada harara.
Daga nan suka koma wajen zamansu sai cika da batsewa yake.
Saida aka fara ciye ciye da shaye shaye sannan aka shiga filin rawa aka fara gwangwajewa, ansha rawa kam wad'anda ma sukayi cin over sun zazzage sukam dai tsaye sukai lokacin da aka basu filin rawar dansu taka sai lik'i da akayita zuba musu musamman abokanshi dan suma d'in indai hidimarsu tazo duk da dai ba komai yake zuwa ba amma indai ansamu yaje d'in to yana taka rawar gani yana musu bajinta.
Da wuri aka tashi dan ko sha d'aya da rabi bata k'arasa ba, Aunt Salma daga nan ta wuce gidanta itada wasu daga cikin y'an uwansu sai washegari zasu koma in ALLAH ya kaimu.
Ayshaa zazzab'in tane yadawo sosai ko a motar ma takurewa tayi saboda sanyin datake ji dama dai tafiyar kurame ce dan babu mai magana sai Auwal ne da wani d'an uwansu suketa hirarsu basu sako Saif a cikiba dan sun san ba tanka musu zaiyiba a haka suka k'arasa gidan.
Suna parking tayi k'ok'arin bud'ewa ta fita saidai k'ofar tak'i bud'uwa alamun lock akasa mata, tamkar zata fasa ihu tsabar takaici su Auwal kuwa dama tuni sun fice sun kama nasu wuri. Juyawa tayi ta kalli side d'in dayake yana zaune abinshi ya hard'e k'afa da waya a hannunshi yadda ya nunama tamkar babu wata halitta a wajen saishi kad'ai, ji tayi kawai hawaye sun tarar mata a Ido dan wulak'anci ya nuna kamar ma baisan da zamanta a wajen ba, burinta kawai tajita a kwance cikin bargo a lokacin kwantar da kanta tayi a bayan kujerar ta runtse idanunta saboda yadda take jin jikinta.
Sai dayaga dama dan kanshi sannan ya bud'e k'arar bud'e motar yasa ta bud'e idonta ta kalleshi lokacin harya fice sai bayanshi data gani ta kuwa dallawa bayan nashi harara da baisan ma tanayi ba, k'wafa tayi ta fito daga motar, can ta hangeshi kusa da wata k'aramar bishiya harya fige babbar rigar tana rataye a kafad'arshi (kai wannan ango) hannunshi d'aya a aljihun rigar d'ayan kuma ya rik'e waya ya mak'ala ta a kunnenshi da alamu waya yake. Sai data harari inga yake sannan ta wuce inda su Hannah suke suka shige parlor'n tare.
Tana shiga bedroom d'in Mamie ba kowa a d'akin abinda ya danganci su sark'a da abin hannu kawai ta cire ta kwanta ta shige bargo tana rawar sanyi.
Mamie ce ta shigo bedroom d'in da sallama dan su sunma d'an dad'e da dawowa, bayanta Imaan ce hannunta d'auke da food flak's da plate da spoon a cikin plate d'in.
Da sauri Mamie ta k'arasa gaban gadon ta yaye blanket d'in tana fad'in
"Subhanallahi mamana zazzab'in ne dai?''. Daga kwancen ta d'aga mata kai idanunta a rufe.
"Yaa salaam". Mamie ta ambata tana zama a gefen gadon duk tabi ta damu, Imaan ta ajiye kayan hannunta ta k'araso wajen tana mata sannu. Hannu Mamie ta d'ora a kanta tace
"Mamana zazzab'in nan naki dole sai anyi allura''. Da sauri ta tashi zaune tana girgiza kai tace
''Dan ALLAH Mamie kar ayi min please naji sauk'i''. Idanunta har sun fara kawo ruwan hawaye.
''Ahhh tab'ara". Imaan tayi maganar tana y'ar dariya gamida kama bakinta.
"Ungo naki nan Imaan, Mamie ta sakar mata dak'uwa, wai zaman me kikemin nema anan ficemin dagani''. Ta ida tana nuna mata k'ofar fita, sum sum ta wuce saida taje bakin k'ofar sannan ta juyo tace
"ALLAH Mamie ki kira Yah Saifu kawai yayi mata allurar. Yin da Mamie tayi kamar zata tashi yasa Imaan ta gudu tana dariya. "Mamie dan ALLAH". Ta tsinci muryar Ayshaa ta fad'a kamar zatayi kuka.
Murmushi Mamien tayi tace
"To ya isa haka, yanzu dai fara cin abincin kinga d'azun baki wani ci na kirki ba''.
Kai ta d'aga mata alamun 'Toh'.
Fried rice and chicken ta zuba mata, saboda kar ayi allurar yasa ta daure taci abincin da d'an yawa tasha ruwa ta koma ta kwanta har lokacin jikinta yana y'ar rawa.
Mamie saidata fita daga d'akin sannan abinda Imaan ta fad'a ya dawo mata na cewar a kira Saifu yayi mata, Bari ta kirashi kawai dan maganin zazzab'in nan kawai allura maganin bai cika yiba.
Tana fita kuwa ta kira wayarshi, lokacin yana shirin shiga wanka dan har ya cire rigar daga shi sai wandon shaddar da singlet fara k'al, ya d'aga kiran yana zama kan sofa Mamie tace
''Babana matarka fa ba lafiya ya kamata kazo kaga jikinta da alamu kuma bason allura take ba kaine zaka iya da ita''.
Marairaicewa yayi sosai yana k'ara kwanciya kan kujerar tareda shafa sumar kanshi yace
"Mamie ALLAH nagaji sosai fa''.
"Toh gajiyar dakayi ce zata hanaka zuwa dubata? Haka nan zaka daure kazo ka dubata''.
Kamar zaice wani abu saikuma ya fasa ya amsa da 'Toh' amma banida allura a wajena.
"Kazo akwai a wajena'' Mamie tace batare da jiran amsar shiba ta kashe wayar.
Lumshe idanunshi yayi yana dafe goshinshi, a matuk'ar gajiye yake yanada b'ukatar hutu, Dole kuma ya amsa kiran Mamie yayi kuma abinda ta umarceshi daya yin.
Tashi yayi ya maida rigar shaddar ya fice dama shi kad'ai ne a bedroom d'in sauran duk suna parlor.
Ba wanda ya kula ya fita. Suma d'in kowa ya maida hankali kan abinda yake ne wasu chatting wasu kuma waya suke da y'an matansu wasu kam a laptop suke latse latse.
Haka ya ratsa parlor'n da wasu dayawa sukayi barci sai d'ai d'aiku ne ke zaune suna kallo.
Bedroom d'in ya shiga ya maida k'ofar ya rufe bakowa a ciki har A.c ma duk an kashe alamar ba'a b'ukatar sanyin a cikin d'akin.
Bakin gadon ya k'arasa ya tsaya akanta tare da k'urawa fuskar ta Ido dama kantane kawai a bud'e, idanunshi suka sauka kan ruwan allura da syringe a side drawer wayarshi ya ajiye kan sofa ya d'auki allurar ya fara k'ok'arin had'awa, Ayshaa da barcinta baiyi nisan kirki ba jin kamar da mutum a wajen yasa ta bud'e idonta a hankali aikuwa suka sauka kan Saif dake had'a allura.
Zabura tayi ta tashi zaune gabanta na fad'uwa tana k'ara jan bargon jikinta ta bar iya kanta kallonshi take tana d'an tab'e baki kamar wadda zata fara kuka, shikam baisan ma tanayi ba saida yagama had'awa sannan ya kalleta fuska a tamke yace
''Cire abin nan''.
Tuni idanunta suka kawo k'wallah har sun fara zubowa tace
"Wai me zakayi min?''.sai k'ara jan bargon take tana zazzare Ido.
Gaban gadon ya k'ara matsawa sosai itama ta k'ara ja baya tana girgiza masa kai.
Cike da k'osawa yace
''Kina b'ata min lokaci''.
"Ni ba'a min allura''. Cikin tura baki tayi maganar tana k'ara k'udundunewa cikin blanket.
Syringe d'in ya ajiye yakama k'ugunshi da hannu d'aya d'ayan kuma ya shafo k'eyarshi zuwa wuyanshi yana mata wani kallon k'asan Idanu ya k'ara tsuke fuska sosai yace
''Na tab'a dukan ki?.
"Yo a wane dalilin zaka dakeni?''. Tace k'asa k'asa tana tura baki gamida matse ido.
Sarai yaji abinda ta fad'a a ranshi yace 'bakin dai bazai mutuba kuwa tana fama da kanta yaga alamun saiya birkice mata yanzun nan dan yaga taurin kan tsiya gareta.
Cikin tsawa yace
"Yaushe wai nafara wasa dake, bazaki tasoba''.
Duk data tsorata da tsawar hakan baisa ta sauko d'in ba saima wani kukan shagwab'a data saki tana marmara ido tace
"Na rantse ba za'ayi min ba''.
A fusace yana k'ank'ance ido yace
"Dawa kika rantse?''.
Banza tayi masa ta cigaba da k'unk'uni tana share k'wallah, tsaki ya saki ganin yadda take ja masa lokaci gashi shi d'inma a gajiyen yake kanshi har sarawa yake.
''Toh bari in karya rantsuwar taki ta yadda kaffara zata hau kanki, yayi maganar yana cire links d'in hannun rigarshi ya jefa kan sofa ya shiga tattare hannun rigar kamar wanda zaiyi kokawa da wani k'aton gardi ya d'auki allurar ya hau gadon a zafafe.
Mrs Salees Mu'az❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu (Ummee).
*DR. SAIF*
Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
Alhamdulillah! Ina mik'a d'inbin godiyata gareku reader's bisa yadda kuke k'aunar book din nan da addu'arku gareni Rabbi yabar zumunchi da k'aunar juna luv u so much.
Saif a canza hali ko za'a samu team masu yawa.
No 24.
Yana hawa gadon ya fincike bargon ya wurgashi k'asa, tana niyyar sauka daga gadon taji ya fincikota ya matse a jikinshi k'ok'arin k'wacewa ta shiga yi tana kuka nan suka shiga kokawa (Ayshaa kokawa da Saif). Ita a lallai saiya saketa shikuma ya rik'eta gam, shi dariya ma tabashi ganin yadda ta daddage lallai saita k'waci kanta a gurinshi ganin tana k'ara b'ata masa lokaci yasa ya murd'e mata hannayen da suke tuttureshi d'in ya matseta gam a k'irjinshi sannan ya tsira mata allurar a inda ya kamata yayi d'in, kuka ta sakar masa sosai harda shasshek'a, yana gamawa ya tureta daga jikinshi, ya tashi ya sauka ya ajiye allurar kan side drawer ruf da ciki tayi ta cigaba da kukanta cikin kukan tace
"Na rantse bazan tab'a yafewa ba''.
Yana shirin d'aukar links d'inshi ya maida yaji ta fad'i haka, ai saiya fasa ya nufo gurinta yaga alamun yarinyar nan idan ba saita masa zama yayi ba raini yana shirin shiga tsakaninsu.
Da k'arfi ya birkitota ta dawo rigingine kafin tayi tunanin abinda zaimata taji ya rank'wafo kanta ya zura bakinshi cikin nata bayan ya had'e hannayenta ya matse cikin nashi.
Wani irin mugun zazzafan kiss yake aika mata cikin mugunta gaba d'aya ya hard'e harshenta cikin nashi yana gana mata azaba duk yadda taso ta k'waci kanta hakan ya gagara dan rik'o yayi mata bana wasaba hawaye kawai take tsiyayarwa saboda azabar zafi saitaji yafi wanda yayi mata ma shopping mall ALLAH ya isa kawai take faman jera masa cikin ranta. Y'an k'afafun nata ma datake shure shure dasu yasa yasa tashi k'afar guda d'aya ya dannesu dan mugunta
Imaan da Mamie ta aikota taga anyi allurar kuwa, tazo ta bud'e k'ofar dayake k'ofar ma ba k'ara yasa sam basu jitaba, abinda idonta yagani ne yasa ta saurin juyawa ta janyo k'ofar tana zaro ido gamida jingina jikin k'ofar ta dafe bakinta da hannayenta cikin ranta take fad'in 'Na rantse Yah Saifun nan mugun d'an pretending ne dubi yadda ya dinga wani zazzamewa bayason auren nan amma kalli yadda yazo yasa yarinyar mutane a lungu daga allura. Wajen tabari tana murmushi tana tunanin abinda zata fad'awa Mamie idan ta koma.
Sai daya wajigata son ranshi tayi lak'was sannan ya sakar mata bakinta ya mik'e tsaye yana sakin numfashi gamida shafa kanshi yana lumshe ido kamar mashayi ya juya zai fice, har yakai k'ofa ya tuna bai d'auki wayarshi ba ya dawo ya d'auka saidaya kalli inda take sannan ya juya ya fice yana cije lips.
Kamar jira take yafita tasaka wani uban kuka tana kama bakinta dake mata azabar zafi yanzu ta k'ara tabbatarwa wannan Dr'n mugune number one ya iya salon mugunta tuni jikin nata ma ya k'ara zafi a fili cikin kuka tace 'Wllhy ALLAH saiya sakamin mamugunci kawai'.
Imaan data koma Mamie ta tambayeta anyi allurar? Cewa tayi 'Eh anyi', Mamie nagama abinda take kuwa ta nufo d'akin Imaan na biye da ita a baya tana addu'ar ALLAH yasa Yah Saifun yabar d'akin tanaso ta tsaida Mamien batasan kuma abinda zatace mataba.
Ajiyar zuciya Imaan ta saki lokacin da suka shiga d'akin taga ya fita, cikin sauri Mamie ta k'arasa wajen Ayshaa dake kuka tsakaninta da ALLAH hannunta akan bakinta.
''OH mamana allurar akewa wannan kukan haka? Ta k'arasa maganar tana d'ago kanta, Imaan dai tasan bawai allurar take yiwa wannan uban kukan hakaba ta saci kallon bakin Ayshaan data cire hannunta a lokacin taga yadda yayi jajawur dashi ya kuma tasa kad'an gaba d'aya jambakin da akasa babu shi duk saitaji d'an tausayin ta ya kamata a ranta tace
"ALLAH sarki Aunt Ayshaa ji yadda tayi wujiga wujiga da ita iya kiss kawai inaga anzo mai gaba d'ayan tab akwai jan aiki.
Rarrashi Mamie ta shigayi har tayi shiru tana sauke jerin ajiyar zuciya, Mamie dai tanata jinjina irin yadda Ayshaan ke k'in allura ganin irin kukan datasha, Mamie sam hankalinta baikai kan bakin Ayshaa ba k'ila da sai ta tambayi inda jambakin mamanta ya shige.
Saida barci ya kwasheta sannan Mamie ta fita taja k'ofar dama ita Imaan tuni ta fita.
Lokacin daya fita parlor'n Mamie duk sunyi barci sai TV da akabari take ta aiki.
Kai tsaye ya wuce part d'in da suke, yana shiga yaga ba wanda yayi barci a cikinsu kowa da abinda yake yana shiga suka zubo masa Ido dukansu tuni aka shiga k'us k'us sai wannan yayi magana da wannan ta Ido sai a shek'e da dariya har da masu tafawa, wani haushi ne ya kamasa ganin abinda suke masa kamar sunga wani mahaukaci dama ga abinda ya janyowa kanshi sakamakon hukuncin dayayi.
A hasale yace
"Likitan k'wak'walwa ya kamata a kira muku tunda duk kun haukace''.
Cikin dariya Mahfooz yace
''Malam bazaka hanamu dariya ba wllhy mu mukaga abinda muka gani dan haka ka k'yalemu mu dara". Ya k'arasa yana sakin wata dariyar.
Auwal ne yace
''Saboda ALLAH Yah Saifullahi daka bari ankai maka ita amma wannan abu ai da kunya''. Ya ida maganar yana wani sunkuyar dakai yana shafa k'eya (dayake haka yake cemasa Yaya saboda ya girmeshi).
Baki ya cije yana kallon Auwal yace
''Dan ubanka abokin wasanka ne ni?''.
Mukhtar ne yace
''Kai bawani Ido dazaka bud'e mana fa kaje kagama lalube d'iyar mutane dan ubanka kaji tsoron ALLAH wllhy.
Tsaki kawai yaja ya nufi hanyar bedroom yaji Mukhtar yace
''Kun ganshi nan ba irin tsiyar da baiyiba akan wannan auren shi bayaso meye meye shi takura masa akayi amma kunga daga kawo baiwar ALLAH d'an banzan ya lallab'a yana latse musu yarinyar''.
Dariya suka saka gaba d'ayansu suna tafawa Basheer yace
"Shegen ba a haka kamar ustazu irin wanda bai damu da lamarin mataba tsabar shi tantirine ma a d'akin Aunt Bilki''.
Mukhtar ne ya zaro ido yace
"Wa? Wllhy S Matawalle mugun jarababbe ne dakake ganinshi haka kawai dai ya iya takunshi ne kuma abinda yake k'ara burgeni dashi duk da wannan matsalar dayake da ita baya kula matan banza wllhy na kirkin ma basa gabanshi na rantse shiyasa nake tausayin yarinyar nan dan wllhy duk ranar da S Matawalle ya damk'eta sai anyi aika aika yanzu yana can nasan saiya had'a da shan lemon tsami''. Nan ma dariyar suka k'ara shek'ewa da ita kamar wasu tab'abb'u.
Yana jinsu sunata iskancinsu har Mukhtar na basu labarin had'uwarshi da Ayshaa da kiss d'in dayayi mata a Mall, cikin dariya Basheer yace
"Shegen sama, wato yaji dad'i abinshi yayi pretend kan cewa punishing yayi kenan.
Shidai baibi ta kansu ba dan yana cikin damuwa, saidaya shiga ya kula da abinda yasa suke masa iskancin akai danshi sam hankalinshi baikai kaiba saboda irin mood d'in dayake ciki, na farko dai shaddar jikinshi ta had'a uban squeezing saboda kokawar da sukasha da Ayshaa a fili yace
''Banzaye akan wannan suke wannan iskancin''.
Rigar ya cire ya cilla kan bed yana shirin juyawa yaga wani uban jambaki a rigar daidai k'irjinshi, "Oh my God" yace cikin jan tsaki yana d'an dukan goshinshi yasan Mukhtar kuma yasamu abinyi gara su Mahfooz tafiya zasuyi. Tsakin ya k'ara saki ya shiga toilet ya sakarwa kanshi shawa ruwan ya shiga zuba a jikinshi idanunshi a rufe ba abinda yake hangowa sai irin abinda yaji lokacin dayake kissing d'inta duk da yayine bisa hukunci amma hakan baisa ya kasa shiga wani yanayiba amma yayi alk'awarin wannan abin bazai k'ara faruwa ba kar yaje garin hukunci yarinya ta rainashi ta d'auka da wata manufa yake mata hakan.
Sai daya wanke jikinshi sosai sannan ya saka bathrobe ya fito da k'aramin towel a kanshi yana goge sumarshi, gaban mirror ya tsaya ya gama goge kanshi sannan ya shirya cikin pyjamas ruwan k'asa masu kauri ya fesa turare ya nemi gurin kwanciya duk da yunwar dake k'wak'ular cikinshi kuwa sai yakejin kamar bazai iya sawa cikinshi komi ba, waya ya d'auka ya d'an shiga yanar gizo yaga abinda duniya ke ciki sannan yayi addu'ar barci har lokacin yana jiyo hayaniyar su Mukhtar kamar ma basuda shirin kwanciya.
Aradu yau saidai kuyi hakuri ba yawa wani uzurin yasha kaina♀️
Saura inji wani yace yayi kadan.
Mrs Salees Mu'az❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu (Ummee).
*DR. SAIF*
Oum Hanan.
Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No 25.
Washegari.
Da k'yar Ayshaa ta tashi tayi sallahr asubah saboda gajiyar biki data fara tambayarta dan ba k'arya sunsha yawo tun kafin bikin. Tana idarwa kuwa ta k'ara komawa wani barcin.
Sai 10:24@m sannan ta farka bathroom ta shiga danyin wanka gaban mirror'n bathroom d'in ta tsaya tana k'arewa bakinta kallo da har lokacin bai gama komawa daidai ba ga rad'ad'in dayake mata har yanzun, hannu takai kai kamar zatayi kuka tace
"Wllhy mutumin nan mugune na k'arshe shi idan baisha bakin mutane ba bayajin dad'i da guntuwar muguntar shi ta motsa saiya kama tsotse bakin mutum ya fake da cewa hukunci itadai ALLAH ya isanta wllhy, inka ganshi kamar bazai aikataba yayita wani kallon mutane ta k'asan Ido na rashin mutunci yadda yake mata kiss d'in tamkar wanda zai tsige mata harshe ko kuma ya cire mata bakin ma gaba d'aya ke mugun bata takaici.
Haka tayi wankan tana ta mitar abinda yayi mata jiya, tana fitowa tasamu Imaan tana ajiye kayan breakfast a saman k'aramin center table dake kusa da sofa.
"Gud morning Aunt Ayshaa''.
"Morning Imaan ya gajiya?''. Tayi maganar tana zama bakin gado.
"Lapia k'alau Aunt Ayshaa ya jikin naki?''
"Alhamdulillah''.
Zama Imaan tayi kan stool d'in mirror tana fad'in
"Tun d'azu Mamie take ta lek'owa baki tashi ba''.
Tsaki Ayshaa ta d'anyi tace
"Wllhy nagaji ne Imaan over yanzun ma kamar kar in tashi, please mik'o lotion d'in nan''.
Mik'a mata Imaan tayi tana satar kallon bakin Ayshaa taga har lokacin bai daidaice ba cikin ranta tace
'Gaskiya Aunt Ayshaa ba k'aramin jin maza tayiba'. Tashi tayi ta fita tana cemata ga break nan tayi.
Tun kafin tagama shafa man su Aunt Salma Aunt Aisha da Aunt Maryam suka shigo bedroom d'in kowanne fuskarshi a sake gaishesu tayi Aunt Aisha ta bata wasu kaya atamface riga da zani mara ado kalarta pink da ash sai fari ta shirya cikinsu kayan sun mata d'as a jikinta ta yafa mayafi kalar pink da aka had'o tareda atamfar,duk yadda taso gocewa saida Aunt Salma tayi mata makeup sama sama ta kuwa yi kyau sosai sai k'yallin amarci take nan kowa ya shiga yimata hotuna a wayoyinsu, fita sukayi suka bar Aunt Salma kawai a d'akin kayan breakfast d'in ta janyo mata tace tazo tayi, kad'an ta tsakura tace ta k'oshi saida Aunt Salma ta takura mata sannan ta k'ara.
Narke fuska tayi ta kalli Aunt Salma tace
"Dan ALLAH Aunt Salma mutafi gidanki tare ALLAH ni nan.....shiru tayi tana turo baki saboda irin kallon da Aunt Salman dake k'ok'arin had'e kayan breakfast d'in ta watsa mata.
"Ai kinsan a garin gab'a gab'a muke dole in tafi dake gidana''.
Dama zuciyar a kusa take dantaji ance duk yau wad'anda suka kawota zasu tafi kawai saigani Aunt Salma tayi ta fara hawaye. Kai Aunt Salma ta girgiza tana d'an murmushi tabar abinda take tadawo kusa da ita ta zauna tareda dafa kafad'arta tace
"Meye kuma na kuka little sis? Yanzufa kin girma Ayshaa kin shiga sawun manya uhm share hawayenki kinji autar Ammi. Ta ida maganar tana share mata hawayen.
"Aunt Salma nifa bana son zama dashi wllhy''. Cikin shagwab'a tayi maganar tana kamo hannun Aunt Salma.
''Why Ayshaa?''.
Zama ta gyara tace
"ALLAH mugune kuma d'an isk.....kafin ta k'arasa Aunt Salma ta buge mata baki tana harararta tace
"Banason shashanci mana Ayshaa, mijin naki kikicewa d'an iska saboda bakida hankali''.
"Aunt Salma kunsan meyayi min to?'' tace kamar zata saki kuka.
''Koma meyayi miki ba mijinki bane nasan dai kinsan abinda aure yake nufi zakimin sakarci''. Baki ta tura tace
''To ba tun kafin ayi auren ba yayimin''.
Da sauri Aunt Salma ta zaro ido gabanta na fad'uwa tace
"Bangane me kike nufiba''.
"Aunt Salma fad'a mikine fa banyiba amma ranar dana tab'a zuwa shopping mall nadawo Ina kuka ban siyo komaiba dashi fa muka had'u daga munyi karo nayi tsaki nace kamar makaho kawai ya kamani yayi kissing d'ina, kuma ranar daya fara zuwa wajena fa saida yace wai zaimin abinda yafi kiss". Murmushi Aunt Salma tayi tana sakin ajiyar zuciya dan harta tsorata da taji Ayshaan tace wai tun kafin aure yayi mata.
"Bakinki keja miki Ayshaa, na tabbatar yana hukuntaki ne ta hakan ki daina masa rashin kunya inba haka ba zakita shan wuya, kiyi hak'uri ki zauna da mijinki lafiya kiyi masa biyayya dan ALLAH Ayshaa karki bamu kunya kinji gashi kin had'u da suruka mai mutunci da karamchi matar nan ta had'u wllhy Ayshaa tasan k'imar mutane kuma karki sake koda wasa ki nuna k'iyayyar shi a gaban idonta hakan zai rage son datake miki kar kiga tana biye miki kiyi tunanin ko bata sonshi ne kokuma batajin zafin abinda kike nuna masa, kiyi hak'uri insha ALLAHU nan gaba zaki soshi ta yadda ke kanki sai kinyi mamakin hakan.....sosai Aunt Salma ta yiwa Ayshaa nasiha mai ratsa jiki da wasu dabarun na zama da miji da kuma y'an uwanshi.
Daga nan Aunt Salma ta rakata wani bedroom d'in inda Mamie take ta gaisheta, harga ALLAH tanajin dad'in yadda Mamien ke nuna mata soyayya da kulawa itama kuma tanajin matar cikin ranta.
A ranar y'an biki suka fara kama gabansu dan wasu tun jiyama sun tattafi, kuka tasha sosai lokacin da y'an uwanta zasu tafi bayan an bud'e musu part d'inta sun gani sun sa albarka Aunt Salma ita tana nan sai zuwa yamma zata wuce.
B'angaren angwaye ma duk kowa ya kama gabansa duk rashin maganar shi sai daya bud'e baki yayi musu godiya sosai ya nuna jin dad'inshi bisa karar da sukayi masa
Baima shigo gidan ba duk safiyar yau d'in dan shifa haka ALLAH yayishi baya k'aunar a kalleshi musamman taron mata duk da dai matan ma saura kad'an yayar Mamie ce kawai maman Mahfooz sai Mum d'in Auwal, Aunt Maryam da wasu y'an uwan dabasufi mutum uku ba suma anjima zasu wuce dasu Mahfooz d'in.
********
****
Zuwa yamma gidan ya koma ba kowa sai masu gidan an gyara ko Ina da aka b'abb'ata saikuma Aunt Salma da Mamie ta bud'e mata part d'in Ayshaa tace ta duba ko akwai y'an gyare gyaren dazatayi, Aunt Salma ta yaba k'warai da kyan part d'in kuma komai neat baya b'ukatar gyaran komi sai tashin k'amshin sabon fenti dana sabbin kayan furniture's dake tashi part d'in ya matuk'ar burgeta gashi dai d'an k'arami amma an tsarashi sosai saidai fatan zaman lapia dawwamamme tsakanin ma'auratan.
Ayshaa tasha kuka lokacin da Aunt Salma zata tafi, Mamie dai rarrashinta ta dingayi tana nuna mata karta d'aga hankalinta nan d'inma ai gidane kuma duk lokacin dataso zuwa zatasa Saif ya kaita gidan da wannan tasamu tayi shiru saidai har lokacin ta kasa sakin jikinta, duk a d'arare take ganin abin take kamar a mafarki wai itace a gidan aure a matsayin matar Saif.
Mukhtar yana nane da Saif saiyaga k'wal uwar daka, yana zaune Saif d'in ya fito daga wanka farar bathrobe ce a jikinshi sai k'aramin towel daya gama tsane ruwan kanshi ya ratayashi a kafad'arshi. Sama sama ya shafa mai ya bud'e trolley d'in daya zuba kayanshi lokacin bikin dazai dawo nan part d'in waje, suit ya d'auko ruwan zuma da black shirt ya nufi bathroom danya shirya Mukhtar ya d'ago ya ganshi da sauri ya tashi ya tari gabanshi.
Kallon rashin fahimta Saif yayi masa tare da cewa
"Malam lafiya?''.
"Ita takawo haka bani suit d'in nan manyan kaya zakasa".
Wani mugun kallo ya watsa masa yace
"Dallah malam matsamin a hanya Ina ruwanka da kayan dazan saka''.
Kayan Mukhtar ya warce yana fad'in
Da ruwana kuwa, kai saboda bakada kai daga tashin bikin zaka wani samana suit kai ga bature ko''. Hannu yasa ya shafo kanshi tareda mik'a masa d'ayan hannun yace
''Bani kayana Mukhtar banason iskanci''.
Wajen akwatin ya nufa yana fad'in
"ALLAH bazaka saka ba''. Yana zuwa ya maidasu cikin akwatin ya ciro wata sabuwar shadda ruwan hanta ya mik'a masa harda hula kalar kayan. K'in karb'a yayi ya zagayeshi yaje ya d'auko wasu kayan bak'in jeans da fara T.shirt baiyi auneba yaji Mukhtar d'in ya k'ara warcesu yana dariya. Ido ya lumshe ya kama k'ugunshi da hannu d'aya d'ayan kuma ya murza goshinshi sannan ya zube cikin sofa.
Yace "Na rantse Mukhtar zan maka rashin mutuncin da bakayi zatoba''.
''Ka dad'e bakayi rashin mutuncin ba dan ubanka,ko rabin kayan daka d'inka da biki baka sakaba shine zaka d'auko wasu k'ananu dan iskanci''.
''Mukhtaaar kana takuramin fa''.
''Nina sani Mr Man''. Mukhtar ya fad'a cikin dariya.
Tsaki yayi yace
"Dan ALLAH ka tattara ka tafi banga zaman uban da kakeba angode da hidima''.
''Ko baka fad'a ba tafiya zanyi ai, kaji dad'in saka y'ar mutane a loko ko''.
" D'an iska maganar ka kenan''. Ya warci shaddar hannun Mukhtar ya shige toilet yana zaginshi.
"Oho dai, sai kasa dai''.
Koda ya fito k'in kula Mukhtar yayi shikuma ya samu abinyi nan ya dinga tsokanarshi shidai kanzil baice masaba.
★★★★
Bayan sallahr Esha'e Mamie tasa Ayshaa ta k'ara yin wani wankan da ruwan turare mai matuk'ar k'amshi bayan ta fito ta bata lace cikin kayanta na biki data d'inka silver ne mai manyan flowers da k'ananun duwatsu da suketa k'yalli riga da zani ne fitted ce rigar data d'an kamata tasa agogo silver da abin hannu sai fashion d'an kunne shima silver tayi matuk'ar yin kyau sai zuba k'amshi take. Mamie ta kira Saif tana b'ukatar ganinshi, lokacin basu dad'e da rabuwa da Mukhtar ba sai daya kulle part d'in gaba d'aya sannan ya nufo kiran Mamien.
Imaan ce kawai a parlor'n tana kallon wani shiri a MBC Bollywood da suke haskawa mayyar Indian films ce bata gajiya da kallonsu.
Ita dariya ma yabata wllhy ganin yadda yake wani cin d'aci yana muzurai shi a dole bayason raini saita tuno abinda taga yanayi jiya a bedroom d'in Mamie, k'asa tayi da kanta tana matse dariyarta. Baisan ma tanayi ba ya wuce upstairs kai tsaye.
Saida yayi knocking tabashi iznin shiga sannan ya shiga da mak'alalliyar sallamar shi daya saba yinta a ciki. Mamie tana zaune kan kujera Ayshaa na gefe k'asan k'afafunta kanta a k'asa tana wasa da zoben hannunta.
''K'araso nan''. Mamie ta fad'a tana nuna masa d'aya gefen nata ganin yana shirin zama a k'asan bed, ganin ba alamun wasa sam a tattare da fuskar Mamie yasa ya k'arasa d'in ya zauna kamar yadda ta b'ukata har gwiwoyinsu na gugar na juna shida Ayshaa shima kanshi ya saddar yana sauraron Mamie.
Saida tayi bismillah sannan ta fara da fad'in
"Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah!, Bansan irin d'inbin godiyar da zanyiwa ubangiji ALLAH ba daya kawomu wannan rana hak'ik'a farin cikina bazai misaltu ba duk wanda ya kalleni kuma zai tabbatar da hakan.
Saifullahi, jin yadda Mamien ta ambaci sunanshi yasa ya d'ago ya kalleta dan yasan al'amarin babbane ya manta rabon da Mamien ta kirashi da sunanshi na asali saidai tace babana ko Abbana saboda sunan k'anin mahaifinta ne daya rik'eta saboda rashin haihuwa da ALLAH bai bashi ba sai aka bashi ita, shiya aurar da ita bayan auren natane da y'an watanni ALLAH yayi masa rasuwa.
''Na'am Mamie". Yace a sanyaye yana k'ara sunkuyar dakai k'asa.
Ga mamana nan dan ALLAH ka rik'eta rik'on gaskiya da amana banaso inji wani abu marar dad'i ya fito daga wajenka kayi koyi da kyawawan halayen MANZON RAHMAH (S.A.W) kayi koyi da yadda yake zama da iyalinshi cikin aminci da salama, dan ALLAH Saifu karka bamu kunya kayi iya yinka wajen rik'e amanar da aka baka dan ALLAH Saifu''. Sai yaji tamkar yasaka kuka saboda irin yadda take had'ashi da ALLAH sai yakejin kamar wasu kayane Mamien take aza masa a kanshi, Idonshi ya runtse da suka d'anyi ja yace
''Insha ALLAH Mamie''.
Murmushi tayi ta shafa kanshi tace
"ALLAH yayi maka albarka yasa ka gama da duniya lafiya yarona ubangiji ya baka wuyar d'aukar amanar nan yabaka ikon sauke hak'k'in da ubangiji ya d'ora maka''.
Lumshe ido yayi tareda sakin ajiyar zuciya yana mugun son yaji Mamien shi tanayi masa addu'a, hannunta dake kanshi ya kamo ya sumbata ya damk'e cikin nashi hannun yanajin tsananin k'aunar mahaifiyar tashi.
Hannunta ta zame ta rik'o hannun Ayshaa ta had'a da nashin tace
"Mamana ga yarona nan ki kulamin dashi kiyi masa ladabi da biyayya ki sauke duk wani hak'k'i da ALLAH ya d'ora miki a kanshi Ina fad'a miki hakane ba'a matsayina na mamar mijinki ba ki d'auka Amminki ce take miki wannan nasihar dan ALLAH mamana ki zauna lafiya da mijinki kar inji kar in gani zaman aure rabi da kwatanshi duk hak'uri ne sai ana kai zuciya nesa ki rik'e sirrin mijinki karki bari kowa yasan matsalar ki dashi idan yayi miki abinda bakiji dad'in shiba ki zauna kuyi magana ta fahimta tsakaninki dashi idan kuma har abin babbane wanda bama fatan haka kizo ki sameni ki sanar dani zan bincika idan kece mai laifin to bafa zan d'aga miki k'afa ba saina sab'a miki kamar yadda idan nayi bincike naga shine bashi da gaskiya zan sab'a masa har bulala zan samu in zaneshi ciki da bai''. Ta ida maganar cikin sigar zolaya tana dariya. Murmushi ne ya sub'ucewa Ayshaa jin abinda Mamie ta fad'a karaf idanunsu suka shige cikin na juna lokacin da take murmushin ya kuwa gallah mata harara yana tsuke baki wanda daga had'uwarsu zuwa yanzun ta fahimci hakan d'abi'arshi ce, haushin hararar dayayi mata yasa itama ta harareshin harda k'arin murgud'a baki, baki ya cije wanda shima tana yawan ganin yana yin hakan ya d'an kad'a kai, Mamie batasan bikin da sukeba dan duk kansu a k'asa yake. Nagartattun addu'o'e ta shigayi musu tana sa musu albarka daga nan tace su tashi su tafi Ayshaa harda k'wallah kamar wadda zatabar gidan ko garin gaba d'aya.
Saida ta rakosu har parlor ba kowa Imaan ta shiga bedroom d'inta lokacin suka shige part d'in nasu.
Yana gaba tana biye dashi har k'ofar dazasu shiga parlor'n yasa key ya bud'e kafin ya shiga ta fara shigewa ya bita a baya kafin takai tsakiyar parlor'n taji an finciko hannunta an dawo da ita baya irin yadda omer dai yakewa zehrah kafin tayi wani yunk'uri ya turata jikin bango ya matseta yana binta da wani kalar kallo data kasa fassarashi.
I'm sorry reader's naso yin typing yafi haka wlhi nayi bakuwa babbar aminiyata dake auren nesa takawo min ziyara sai zuwa gobe insha ALLAHU Inkuma bansamu yi goben ba sai jibi da yardar ALLAH, luv u wujiga wujiga guys.
Mrs Salees Mu'az❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu (Ummee).
Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
*DR. SAIF*
Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No 26.
★★★
Wani irin kallo yake mata cikin k'ank'ance ido da tsuke fuska, itama d'in k'wal k'wal tayi da Ido tana kallonshi cikin ranta tana ayyana shikenan ta banu kuma yanzu yace zaiyi d'an banzan hukuncin nan nashi na zalunci tasamu bakin ya daina zafi.
"Wa kika harara d'azu?''. Ya jefo mata tambayar yana k'ara tamke fuska.
"Kai mafa ka harareni ne". Tayi maganar kamar zata sakar masa kuka
"Sa'anki ne ni?''.
Baki ta cuno batayi magana ba.
"Ko wasa nake dake?''.
Nan d'inma shirun tayi tana k'ara b'ata fuska zatayi kuka. Baki ya cije a hankali kuma ya shiga kusantar da fuskarshi kusa da tata numfashinsu na k'ara gauraya hakama k'amshin turarukansu na sake cakud'uwa waje d'aya, ba abinda gabanta yake sai fad'uwa, gam ta runtse Ido tana jiran jin bakinshi cikin nata dan tasan abinda zaiyi d'in kenan.
''Kina jiran kiss ko?''.
Taji muryar shi ya fad'a k'asa k'asa tamkar wani mai rad'a.
Da azama ta bud'e Ido tana warosu waje tace
"What?''.
Gira ya d'age mata yana mata wani kallon k'asan Ido tamkar wanda yakejin barci.
Sub'ul da baka tayi ta saki tsaki tana d'an tab'e baki, Ido yad'an zaro yace
"Tsaki again?''. Ganin yadda yasha mur yasata k'ara tsorata ta shiga girgiza masa kai tanason yin kuka ganin yadda ya matso da bakinshi daf da nata har lips d'inshi na tab'a nata yana shirin zura bakinshi a nata wayarshi dake aljihun gaban rigarshi tafara neman agaji, k'aramin tsaki ya saki yana lumshe ido ya matsa daga kusa da ita yana k'ok'arin ciro wayar.
Ajiyar zuciya ta saki cikin ranta tana shiwa wanda ya kira wayar nan albarka tasan da yanzu tana nan tana shan azaba da sunan kiss, mayen kiss kawai. Tunda tasamu yabar wajen ta shige bedroom d'in kusa da ita.
"Mukhtar kuma'' ya fad'a a ranshi cikin mamaki lokacin dayaga sunan mai kiran nashi a waya.
Picking yayi yanajan tsaki yace
"Meye kuma yanzun?''.
"Ka fito Ina jiranka a waje". Mukhtar ya fad'a daga b'angarenshi.
Goshinshi ya dafe tareda fad'in
" OH my God,Wllhy Mukhtar da mayene kai idan ka kama mutum saika tasheshi aiki hankalinka zai kwanta uban me kadawo yi yanzu?''.
"Mallam ka fito kawai sak'o zan baka''. Mukhtar d'in ya fad'a yana katse wayar.
Tsaki yaja ya fice daga parlor'n da tunanin sak'on uban me yakawo masa.
Har lokacin Imaan tana nan tana kallonta ya wuceta ya fice. "Ko Ina kuma zashi yanzun? kai ALLAH ya kyautawa mutumin nan'', Imaan ce tayi maganar tana bin bayanshi da kallo.
A harabar gidan ya hango Mukhtar tsaye jikin motarshi hannunshi rik'e da leda, k'arasawa yayi yana faman cika da batsewa ya tsaya gabanshi ya zura hannunshi d'aya a aljihun wandonshi d'ayan kuma ya dafe wuyanshi yana kallon Mukhtar d'in dake masa wani irin kallon shegantaka.
''Wace uwa kadawo yi?''.
"Kaza nakawo maka angon Ayshaa''.
"Uwarka zanyi da kaza Mukhtar?, Ya fad'a a hasale cikeda jin haushin tasoshi d'in dayayi.
Dariya Mukhtar yayi yace
"A,ah yada zagi haka Mr.Man?.
Harara ya b'alla masa yace
''To dan ubanka cemaka akayi inada b'ukatar kaza".
"Kaga malam bakai na kawowa ba nasan ba hankali garekaba kad'an daga cikin shika shikan iskancinka ka shigar mata haka zik'au d'inka ko bakaso a baka had'in kaine?''. Takaici yahana Saif magana sai kai daya juyar yana fesar da iskar bakinshi.
''Karb'i malam sauri nake inje kai hak'ark'arina k'asa ko naji dad'i''. Mukhtar ya fad'a yana mik'a masa ledar hannunshi. ''Bazan karb'a ba ALLAH Mukhtar so kake in.......kafin ya k'arasa Mukhtar ya tareshi da fad'in
"Na rantse Matawalle saika karb'a dan ubanka bazanyi wahalar banzaba harna kusa k'arasawa gida na tuna nadawo na siya sanin halinka danayi kaida ba'a maka abin arzik'i kuma wllhy idan baka karb'a ba yanzun nan zanyiwa Mamie waya in fad'a mata''. Ya ida maganar yana k'wak'ular hannunshi yasa masa ledar a ciki, jin yasako Mamie yasa ya rik'e ledar yana harararshi.
Cikin matse dariya Mukhtar yace
"Wai bangane bama Matawalle ko harka fara sha'ani na tasoka ne''.
K'wafa Saif yayi yace
"Sha'anin ubanka nafara wllhy Mukhtar ko, bai k'arasa ba sai jiggiga kai dayayi alamun zai sani.
Cikeda tsokana Mukhtar yace
"Ah to gani nayi idonka yayi ja, nidai nasihar da zan maka kabi yarinyar nan a hankali kaga dai yarinyace shataf just nineteen years old ALLAH ya had'ata da k'aton tuzuru irinka kaga.....ganin Saif ya dunk'ule hannu zai kaimasa naushi yasa yayi saurin shigewa motarshi yana masa dariya da fad'in 'Asha amarci lafiya'.
Baki ya cije yana sakin k'wafa yabi motar Mukhtar da kallo wadda harta kusa ficewa daga gidan. ALLAH ya had'a jininshi dans Mukhtar shi kad'ai ke iyayi masa duk iskancin dayaga dama batare daya d'aga kai ya kallaba koya damu ya maidashi kamar wani abokin wasanshi kuma duk yanayine dan yasashi magana, murmushi ya d'an saki kad'an ya juya ya koma cikin gidan.
Tunda ta shiga bedroom d'in take binshi da kallo tsarin d'akin da kayan ciki sun matuk'ar burgeta komi na ciki sky blue ne da fari daga kan furniture , curtains da rug d'in dake shimfid'e a k'asan d'akin zuwa flowers d'in da akayi adon d'akin, sosai yayi mata kyau ta dinga binshi da kallo sam babu tarkace a d'akin.
Har zai wuce saikuma ya tsaya ya juyo yana kallon Imaan da gaba d'aya attention d'inta yana kan TV tayi nisa a kallon datake.
"Ke mekike bakije kin kwanta ba?''. Ya fad'a murya a dakushe yana mata wani irin kallo.
''Dama wannan series d'in nakeson ingama gani''. Cikin in Ina tayi maganar tana wasa da yatsun hannunta cikin ranta addu'a take ALLAH yasa kar yace ta tashi dan wani zazzafan Indian series ne akeyi ba'a dad'e da farashi ba baya wuceta saboda yadda take sonshi.
Addu'ar tata dai bata ciba dan kuwa haka yace
" inace next week zaku fara exams shine shine zakizo ki tasa TV a gaba bazakije kiyi karatu ba,get out kafin in sameki gurin nan''. Da sauri ta mik'e ta nufi hanyar bedroom d'inta kamar zata saki kuka ALLAH nagani taso k'arasa ganin yadda abin zai kasance yazo ya wani tasheta, masifaffe.
Socket d'in ya kashe ya shige part d'inshi ya maida k'ofar ya rufe, bai sameta parlor'n ba baiyi kuma tunanin inda ta shigaba ya wuce bedroom d'inshi kai tsaye, tsaye yayi yana kallonta gaban wani frame mai zanen flowers masu kyau dake jikin bango ta juya baya, jin an shigo yasata juyowa ta kalleshi ta wani b'ata rai tana tunanin abinda ya kawoshi d'akinta, a cukule yace
''Zaki iya fitarmin a bedroom?''.
Idanunta ta d'an juya tana tab'e baki, 'Oh dama bedroom d'inshi ne wannan? No wonder ta ganshi baiyi kama dana mata ba saitayi zaton tsarin d'akin ne kawai haka, hanyar fita ta nufa shikuma yana k'ok'arin shigewa ciki, har takai bakin k'ofar fita taji yace
"Tafi da ledar nan''.
Kamar bazata kulashi ba saikuma ta dawo takai dubanta kan ledar dake a jiye a k'asan couch, d'auka tayi tace
"Me za'ayi da ita?''.
Kai tsaye yace
''Ki zubar''. Yana k'ok'arin cire agogon hannunshi kamar bama shi yayi maganar ba. Ta gefen ido ta harareshi sannan ta fice a ranta tana fad'in ' Waishi nan bak'ar magana.
K'ofofi biyu tagani a jere tafara bud'e ta farkon taga ba komi a ciki ta janyota ta bud'e ta biyun had'add'en kitchen ya bayyana ta tura k'ofar ta shiga tanabin kitchen d'in da kallo ya gama tafiya da imaninta an tsarashi iya tsaruwa yaji kayan electronics na zamani komi an ajeshi a inda ya dace.
Ledar ta bud'e taga kaji guda uku manya sunji vegetables a freezer tasaka su dan batada b'ukatar cin komi a halin yanzu dan Mamie gaba tasata saida taci abinci kafin tayi wanka.
Fitowa tayi ta rufo k'ofar ta nufi d'ayan bedroom d'in dake kallon nashi ta bud'e ta shiga 'Wow' abinda ta ambata kenan lokacin datake shiga cikin d'akin ya matuk'ar yin kyau ainun shikuma kalarshi pink da farine an k'awata d'akin sosai komai an ajiyeshi a mazauninshi masha ALLAH. Mayafinta ta cire ta rage kayan jikinta ta shiga bathroom danyin wanka, shima d'in dai an k'awatashi da kayan zamani na amfanin toilet, wanka tayi ta d'auro towel ta fito bayan ta d'aura alwalah. Sama sama ta shafa cream tasa night dress riga da wando masu kauri ash color ta nemi hijab cikin wardrobe cikin sa'a kuwa tasamu tasa ta kabbara sallah, raka'a hud'u tayi kyawawa tayi addu'o'en ta ta tashi ta cire hijab d'in ta ninke rug prayer d'in ta haye gado abinta tana karanto addu'ar kwanciya barci, kasancewar a gajiye take yasa bata da'u wani dogon lokaci ba barci yayi awon gaba da ita.
Shima a nashi b'angaren wankan yayi yasa pyjamas ruwan makuba ya fesa turare ya kwanta, haka nan yake jinshi cikin wani irin yanayi daya kasa fassarashi a haka ya karanto addu'o'e barci yayi gaba dashi.
Kiran sallahr farko akan kunnenta akayi shi, tashi tayi bakinta d'auke da addu'a ta shiga bathroom tayi alwalah ta fito ta gabatar da raka'atanil fajr bayan ta idar ta cigaba da azkhar d'inta. Bayan tashinshi shima yayi alwalahr ya zura jallabiyyah milk color ya fesa turare ya mak'ala counter a hannunshi ya fito. Har zai fita saikuma ya juya ya nufi bedroom d'inta dan yanzu hakk'inshi ne hakan, handle d'in k'ofar ya kama ya bud'e tun kafin ya gama shiga ya hangota zaune kan pray mat kanta a k'asa sai kawai ya juya ya koma tareda jan k'ofar ya fice.
Bayan idar da sallahr ta fara karatun Alqur'ani a wayarta tunda bataga Alqur'ani a d'akin ba gashi ta riga tayi sabo da hakan duk bayan sallahr asubah saitayi take jin dad'i. Bayan ta karanta abinda ya sawwak'a tayi wani azkhar d'in ta rufe da addu'o'e ta tashi ta k'ara komawa kan gadon ta koma wani barcin.
Sai kusan k'arfe 10:45@m sannan ta tashi tayi wanka ta shirya cikin material riga da siket light blue sun mata cif kayan kamar a jikinta aka hallicesu simple kwalliya tayi kamar yadda ta saba tabi jikinta da kalolin turaruka ta d'aura k'aramin vail akanta kalar kayan. Gyaran d'akin ta fara daga nan ta fito parlor'n ta shiga gyaranshi duk da bawai dattine dashi ba sai a lokacin ta k'arewa parlor'n kallo shima dai masha ALLAH yaji royal cushion kalar dark blue da tattausan center carpet kalar kujerun sai b'angaren dinning table daban ga faskekiyar plasma da sauran kayan amfaninta ba abinda yafi d'aukar hankalinta irin k'atuwar show glass d'in da aka cika da kayan k'amshin gida dana jiki aka kuma k'awata ta da ado flowers masu kyau jiya duk bata kula da itaba dan tana shigowa wannan Mr hukuncin ya matseta, tsaf ta gyara ko Ina ta kunna burners ko Ina tana shirin shiga kitchen taji ana knocking door ta k'arasa ta bud'e, y'ar aikin Mamie ce suka gaisa ta mik'a mata basket d'in hannunta tace inji Mamie tace a kawo mata. Karb'a tayi ta juya ta tafi itakuma ta maida k'ofar ta rufe tadawo, dinning ta nufa ta jera kayan zama tayi, tayi breakfast d'inta bayan ta gama ta koma kan kujera ta kwanta ta hau online dan ta jima rabon data hau d'in.
Tun kafin ya k'arasa fitowa k'amshin shi mai masifar dad'i ya fara yiwa parlor'n sallama k'amshin ya mata bala'in dad'i ta k'ara bud'e k'ofofin hanci tana zuk'arshi, a hankali kuma cikin takun nutsuwa da mazantaka ya fito daga bedroom d'in nashi yayi shirinshi tsaf cikin blue black jeans da round neck shirt white color mai dogayen hannuwa k'afafunshi sanye cikin fararen takalma ya sakaya idanunshi cikin siririn farin glass, gashi dai shigar tashi so simple amma sai tsabar kyau dayayi hannunshi d'aya rik'e da waya akan kunnenshi alamun waya dai yake d'ayan kuma ya cusashi cikin aljihun jeans d'inshi. Kujerar dake facing bedroom d'inshi take kwance dan haka yana fitowa idanunshi suka sauka cikin nata da sauri kowa ya janye nashi idanun tsaye yayi cak kusa da show glass yana cigaba da wayar da itadai bataji yace uffan ba sai daga bisani taji a hankali cikin sweet voice d'inshi yace
"Okay I'm coming".
'Mutumin nan ya cika sanabe da fi'ilin tsiya wllhy yaita wani yanga kamar mace. A ranta tayi maganar tana satar kallonshi ta wutsiyar idonta lokacin da yake dosowa inda take, da alamu dinning zai nufa, kamar bazata kulashi ba saikuma dai taga hakan bai daceba duk tsiya dai yanzu a matsayin mijinta yake kuma ubangiji ba ruwanshi da wani bata sonshi tunda dai har ya zama mijinta dole zata girmamashi duk da taga alamun shi ba'a iya masa.
''Ina kwana''. Ta fad'a a hankali.
Jin bai amsaba yasa tayi tunanin ko baiji bane dan haka ta k'ara maimaitawa da d'an k'arfi, cak ya tsaya tareda juyowa cikin fad'a yace
"Kurma ne ni dazaki dinga min shouting aka''.
''Oh Yaa ALLAH wannan mutumi wannan mutumi ALLAH ya shirya shi daga gaisuwa saikuma fad'a?.
Cikin k'unk'uni tace
''Waya sani?, Bambancinka da kurman ai kad'an ne''.
Yajita sarai, kamar zai tanka mata saikuma yayi gaba yana taune lips yaga alamun had'a bakin dayake da ita kamar ma wani rainin yake k'ara janyo masa.
Sama sama yayi breakfast d'in ya taso har lokacin tana kwance tana duba wani hadith datayi searching d'inshi.
"Tashi muje mu gaida Mamie''. Ta tsinkayi muryar shi saman kanta, da sauri kuwa ta tashi dan dama tagaji da wannan zaman shirun.
Bedroom d'inta takoma ta d'auko mayafi white color ta yafa ta fito lokacin harya fita waje, ta janyo k'ofar gaba yayi abinshi tabi bayanshi tana kallon tafiyar shi a ranta take ayyana cewa 'Da ganin mutumin nan mugun k'arfi zaiyi ji takun nashi ma na k'arfafan mazaje da suka horu da motsa jiki.
Ba kowa parlor'n don Imaan ma tuni ta wuce school Mamie kam dutyn yamma take Daddy kuwa tun kwana biyu da d'aurin aure yayi tafiya zuwa Lagos kamfaninshi dake can na sarrafa fata suka nemeshi har zuwa yau d'in kuma bai dawoba.
Suna shiga Mamien tana saukowa daga upstairs, tuni fuskarta ta washe da fara'a tasha kwalliyarta cikin wani dank'areran lace bak'i kasancewar ta fara yasa ya haskata q'warai.
"Maraba da ango da amarya". Ta fad'a cikin zolaya lokacin data k'arasa saukowa downstair tana shirin zama kan kujera, Ayshaa tayi k'asa da kanta cikin jin kunya shikam ya wani maze yana gaida Mamie, itama Ayshaan har k'asa ta durk'usa ta gaida Mamien ta kasa d'ago Ido ta kalli Mamien wani irin nauyinta take ji jinta take tamkar a d'add'aure.
"Zonan mamana". Mamie ta fad'a tana mik'a mata hannu, a kunyace ta tashi ta isa gareta tana shirin tsugunawa Mamien ta kamota ta zaunar da ita kusa da ita tareda dafo kafad'arta tace
''Kin tashi lafiya?. ''Lafiya k'alau Mamie''.
"Masha ALLAH, komai lafiya dai ko kunyi breakfast d'in?'' kai ta d'aga mata, Saif ya mik'e tsaye yana fad'in
''Mamie zanje hospital''.
Hararar shi tayi tace
"Baka d'auki hutu bane?''.
Kanshi ya shafa yace
''Mamie wani important abune zai kaini ba dad'ewa zanyi ba''.
''Okay, toh ALLAH ya kiyaye yabada sa'a''.
Ya amsa da 'Amin' yana yin gaba ta d'ago tana k'ok'arin cemasa a dawo lafiya ganin ga Mamie a wajen taga harya fice daga parlor'n.
Nan dai Mamie ta dinga janta da hira cikin hikima kuma irin tasu ta manya tana k'ara nusar da ita yadda zata dinga kysutatawa mijinta da dabarun zama da miji ta yadda zai kasance bawata d'iya mace dayake kallo a gabanshi face KE.
@@@@@@@@
Kwance zuhrah take tayi nisa cikin tunanin mafita da yadda zata b'ullowa al'amarin gaba d'aya duk wata basira tata da tunaninta sun tsaya cak ta sak'a ta kwance ta k'ulla ta kwance yafi a k'irga sai tayi kamar zata hak'ura da Saif d'in saitaji inaa bazata iyaba kamar ma wani bala'in ake k'ara mata na SO da k'aunar shi, kamar wadda aka tsikara ta tashi zumbur gamida janyo wayarta dake gefenta ta shiga contacts d'inta tana fara laluben number datake son samu tana addu'ar ALLAH yasa akwai number har yanzu cikin wayar. Cikin sa'a kuwa tasamu murmushin farin ciki ta saki lokaci d'aya kuma tana dialling number harta katse ba'ayi picking ba ta k'ara kira sai data kusa katsewa sannan aka d'aga, ''Hello". Ta fad'a cikin k'aguwar son jin muryar wanda ta kira d'in.
''Waye?''. Aka fad'a daga d'ayan b'angaren cikin muryar maye.
"Alhamdulillah, ZUMA nice''. Ta fad'a tana y'ar dariya.
''Ke wa?''. Ya k'ara fad'a a cikin muryar mayen da tsantsar duniyanci.
"Zuma zuhrah ce fa baka ganeni bane?''.
''Oh ayyah hajjaju kwana dayawa''.
Dariya tayi tace
"Wllhy kuwa yanzu ma wani aikine zakamin akan wata yarinya nayi maka alk'awarin kud'ad'e masu yawa idan aikin ya kammala''.
"No probalem hajjaju ki d'auka kamar anyi an gama ne''.
"Yawwa mutumina ai dama nasanka aikinka ba wasa anjima kamar 4pm mu had'u a gidan gonar Dad mu tattauna in nuna maka hotan yarinyar''.
"Karki damu hajjaju zaki ganni''. Da haka sukayi sallama ta katse wayar tana dariyar farin ciki ta yadda komai zaizo mata cikin sauk'i.
*******
Gidan Gona at 4:34pm.
Babban table ne d'auke da kwalaban lemuka iri iri da ruwa, da kofuna. Zuhrah ce zaune kan kujera sanye cikin d'inkin atamfa na zamani riga da siket duk ya bayyanar da surar jikinta taci uban makeup ga tulin attachment data bazoshi har gadon bayanta sai zuba k'amshi take idanunshi b'oye cikin bak'in google sai taunar chewing gum take. Sai kujerar dake facing tata wani matashine kallo d'aya zakayi masa ka bashi sunan tantiri daga kan kayan jikinshi zuwa kan askin dake kanshi zai tabbatar maka da hakan.
Sai daya kurb'i lemon dake cike cikin glass cup sannan cikin irin maganar su ta y'an iska yace
"Ina jinki hajjaju'.
Glass d'inta ta cire ta d'ora shi kan table d'in tana wasa dashi kafin tace
''Aiki zan baka Zuma banaso a samu matsala please''. Kai kawai ya kad'a mata baice komiba, wayarta ta d'auko ta shiga gallery tafara neman pic d'in Ayshaa data d'auketa ranar dinner lokacin da y'an uwa da abokan arzik'i ke d'aukarsu hotuna.
Zooming d'inshi tayi ta mik'a masa wayar yasa hannu ya karb'a yana bin screen d'in wayar da kallo inda hotan Ayshaa ya fito b'aro b'aro a kai.
"Nagani me kikeso ayi mata?''.
"Kasheta zakuyi''..
Ayi hak'urin rashin jina da ba'ayi ba two days
Mrs Salees Mu'az❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu
(Ummee).
HASKE WRITER'S ASSOCIATION
(Home of expert & perfect writer's).
*DR. SAIF*
Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No 27.
Kai tsaye zuhrah tayi maganar tana k'ara had'e fuska, kallonta zuma yayi sosai kafin yace
"Bakida matsala hajjaju, nawa zaki biyani ladan aiki?''.
Hand bag d'inta ta zuge ta ciro kud'ad'e masu yawa ta cilla masa tana fad'in
"Ga kafin alk'alami nan kafin aiki ya kammala''.
Kud'in yakai bakinsa ya sumbata ya karkace ya zurasu cikin aljihun wandonshi sannan ya d'ago yana kallonta yace
''Ki turamin address d'in gidan da picture d'inta''.
"Okay, amma nifa Zuma inajin tsoro, taya har zaku iya shiga gidan nasu?".
Dariya ya shek'e da ita yace
''Karki damu da hakan akwai Mufee ita zatayi mana wannan aiki na shiga gidan''.
Murmushi ta saki tana jinjina kai tace
"Very good Zuma aikinka na kyau, fatana kar a samu matsala''.
Saida ya cije baki yana mata wani irin kallo sannan yace
"Matsala bata cikin aikinmu a kodayaushe nasara mukasa gaba''.
Saida suka k'ara tattaunawa sosai kafin sukayi sallama kowa yayi nashi waje.
@@@@@@
Saif bai dad'e a hospital d'inba yagama uzurin daya kaishi ya fito, kai tsaye wani k'ayataccen wajen hutawa yaje na manyan mutane. Can inda ba hayaniya ya ware kanshi aka kawo masa abin motsa baki yayita danne dannenshi a laptop yana k'ara wasu binciken akan harkar lafiya da sauran abubuwa dai da suka shafi aikinshi na likita.
Sai bayan la'asar sannan yabar wajen ya nufi gida, gaba d'aya yama manta da wata aba wai Ayshaa.
Lokacin daya shiga compound d'in gidan Mamie tana shirin shiga mota zata wuce wajen aiki, saidaya daidaita parking sannan ya fito ya nufo gurinta da itama ganinshi yasa ta dakata da shiga motar.
Daf da ita ya tsaya yana fad'in
"Mamie zaki fitane?''.
Tuhumammen kallon data bishi dashi yasa yasha jinin jikinshi yasan laifinshi bazai wuce na dad'ewar dayayi a wajeba, k'asa yayi da kai yana sosa k'eya ya bud'e baki zaiyi magana yaji ta damk'i kunnenshi da hannunta y'ar k'ara yasaki tareda dafe hannunta dake kan kunnen yana b'ata fuska yace
"I'm sorry Mamie please''.
Fuskarta ba fara'a tace
"A ina ka tab'a ganin ango yayi haka kabar yarinyar nan tun safe shine sai yanzu kaga damar dawowa gidan ko,wato so kake ka nunawa duniya cewa bakason auren nan ko babana?''.
"I'm sorry Mamie''. K'wafa tayi ta cire hannunta bayan ta k'ara murd'e masa kunnen.
"Ouchh Mamie da zafi fa''.
"Ai gara kaji zafin dan mai garinku haka akeyi, tun safe kayi ficewarka wai sunan kuma kabar amarya a gida fisabilillahi''. Shidai baice komiba sai kallon Mamie daya keyi yana b'ata fuska.
''Wuce ka shiga gida kuma saura in k'ara ganin y'ar k'afarka a waje saina sab'a maka kaji nagaya maka dan kad'an daga aikinka kace zakayi wanka ka k'ara ficewa da da yanzu ba d'aya bane dole tana b'ukatar kulawarka". Juyawa yayi yana mata ALLAH ya kiyaye hanya itakuma ta shiga motarta ta fice a ranta tana k'ara yimusu fatan alkhairi da zaman lapia mai d'orewa.
Ayshaa tana kwance kan 3sitter da waya a hannunta tana puzzles game, tayi kwalliyarta cikin exclusive atamfa purple color d'inkin doguwar riga data kamata sosai ta bayyanar da kyakkyawar surar jikinta ta fito da k'irjinta sosai rigar, gashinta dayasha gyara yaketa zuba k'amshi da k'yalli ta d'aureshi da purple ribbon a tsakiyar kai, k'aramin d'an kunne tasa mai had'e da zobe da agogonshi kalar purple d'in fuskarta dai simple kwalliyar data saba yice bakin nan sai shinning yake na lipglosses data shafa sai baza k'amshin khumrah take masha ALLAH tayi matuk'ar kyau har ba'a magana, bata dad'e ma da dawowa daga wajen Mamie ba tayi wanka tazo ta kwanta, k'aramin vail d'in data d'aura a kanta ma duk ya zame hakan yasa gashin nata ya bayyana sosai.
Da k'yar ya motsa bakinshi yayi sallama lokacin daya shigo parlor'n dan ita harga ALLAH ma bataji sallamar tashiba(dama sababbe ne ai).
Wani irin bugawa k'irjinshi yayi lokacin da yayi tozali da ita, matuk'a gaya kwalliyar ta tafi da imaninshi musamman da idanunshi suka fad'a kan k'irjinta tuni bugun gabanshi ya k'ara tsananta, wai yarinyar nan keda irin wannan surar, muk'ut ya had'iye wani irin yawu daya tsaya masa a mak'oshi ta gabanta yazo zai wuce yana wani basarwa ka rantse da ALLAH baiga wani abu daya tada masa hankali ba. Zaune ta tashi tana k'ok'arin janyo vail d'in dake kan hannun kujera, sannu da zuwan ma datayi masa bai amsa ba ya shige bedroom d'inshi ya rufo k'ofar da k'arfi. Baki ta kama, a fili tace
''Wannan mutumi inajin sai anyi masa ruk'iyya da alamu jinnu sun tab'ashi, k'aramin tsaki kawai ta saki takoma tayi kwanciyar ta ta cigaba da game d'inta can k'asan ranta kuma tana mamakin halayyar abokin rayuwar tata da ALLAH ya had'ata dashi mutum banda nunkufurci da bak'in rai ba abinda ya iya ALLAH ya kyauta masa dan damuwashi ce ba tata ba.
Yana shiga bedroom d'in ya cilla key da wayoyinshi kan bed yabi bayansu, iya jikinshi ne kawai akan gadon k'afafunshi na k'asa ko takalmin k'afarshi bai samu damar cirewa ba ya tallabe kanshi da hannayenshi duka yana kallon Pop d'in saman d'akin, maganar gaskiya yagaji da wannan wahalar yana b'ukatar kasancewa da d'iya mace a matsayinshi na Dr yasan irin illar da hakan ke haifarwa shidai abu d'aya ya sani bazai tab'a neman abu gurin y'ar yarinyar can ba to mema zatayi masa? A yadda yakejin k'arfin nan idan ya kasance da ita zai iya illatata ma wllhy yadda bata dawani qualityn kirkin nan bazata iya dashi ba sam mai iyawa dashi sai macen data kai mace ta amsa sunanta na mace, tsaki ya saki tareda tashi zaune kanshi ya kulle gaba d'aya ya rasa ta inda zai b'ullowa al'amarin ma wllhy, amma dai dole ya takawa yarinyar nan birki ta daina zamar masa haka dan yana zaman zamanshi bazata tada masa hankali ba ta barshi cikin matsala gara ya cigaba da gungurawa a haka har zuwa lokacin da ALLAH zai kawo masa mafita, dole ta dinga zama da hijabi kuwa. Takalmin k'afarshi ya cire ya cire wrist watch d'inshi ya ajiye ya tashi ya fita parlor. Har lokacin tana kwance abinta.
"Ke tashi kije ki saka hijab". Taji maganar kamar daga sama, tashi tayi zaune tana kallonshi cikin rashin fahimta a ranta tana fad'in 'Ji wata masifa kuma dan ALLAH Ina ruwanshi da ita zaice wani taje tasaka hijabi shi idan bai nemi bala'i da mutane ba bayajin dad'i.
''Bakyaji ne''. Yayi maganar yana k'ara had'e girar sama data k'asa.
Baki ta tura tace
"Toh wai akan me zansa hijabi ni ban iya zama da hijabi a jikina bafa.
"Dole ki koya". Ya fad'a yana bud'e mata ido.
K'asa k'asa tace
"Wllhy ba dole''.
"Bazaki bi dokar tawaba kenan''.
Cikin k'unk'uni tace
"Toh dokar ALLAH ce''.
Kanta yayo a harzuk'e ta zabura ta mik'e tsaye tana shirin guduwa bakin kuma bai mutuba dan fad'i take 'Toh wai haka nan saikace insa wani hijabi'. Taku biyu yayi yai ram da ita ta fasa ihu kuwa tana k'ok'arin zillewa dan bata shiryawa wannan shegen kiss d'in nashiba mai shegen azaba ba a halin yanzun, 1sitter dake kusa dashi ya watsata tasaki y'ar k'ara tana runtse Ido saboda yadda bayanta ya bugu, bisa kanta ya rank'wafa sosai tareda d'ora k'afarshi d'aya kan kujerar yana mata wani kallon k'asan Ido ya k'ara had'e face kafin yace
''Me kike d'aukar kanki ne?.
A marairaice tace
"Dan ALLAH menayi to? Kaifa kafara tsokanata, kawai sai kace insa hijab a gida bawani waje zanjeba''.
"Gidana ne kuma inada ikon dazansa ko in hanaki a cikinsa''.
"Au dama gidanka be?''. Tayi maganar cikeda rainin wayo. Hakan daya gano yasa ya k'ara shan mur yana jifanta da harara, k'irjin nan dai dasuka tsone masa Ido, yakai idanunshi kai. ''OMG". Ya furta cikin ranshi yana wani d'an girgiza kai kamar irin wanda ya fice a hankalinshi na wucin gadi, cikin sauri ta d'auke idonshi daga kai ya maida kan fuskarta dake a marairaice kamar zata saki kuka. Ba zato taji ya damk'i tsintsiyar hannunta yana k'ara k'ank'ance ido yace
''Dole kibi duk abinda na fad'a idan ba hakaba zakisha wuya, zan fito miki a true color d'ina na ainahin Saifullahi a yanzu Dr Saif kika sani nan gaba zaki san waye Saifullahi Matawalle idan har kina k'etare maganata ko kinamin rashin kunya, be careful ki saita bakinki akaina''. Itadai kallonshi kawai take idanunta sun tara ruwan hawaye saboda zafin da hannunta yake mata inda ya rik'e d'in.
"Please ka sakeni dan ALLAH''. Ta fad'a hawayen da suka taru suka fara zubowa.
Sai daya k'ara matsewa sannan ya saki, kafin ya mik'e ma tabi ta k'asanshi ta shige bedroom d'inta da gudu saida ta tabbatar ta shiga sannan ta lek'o da kanta ta kalleshi Ido cikin Ido bayan ya zauna kan kujera. "Wllhy ALLAH bazan yafe cin zalina dakayi ba sai ALLAH ya sakamin''. Crossing legs yayi yana girgizasu yace
''Ni kike fad'awa haka ko?''.
''Eh, d'in kuma har Mamie saina fad'awa mugunta kakemin''.
Sumarshi ya shiga shafawa yana k'are mata kallo yace
''Zakimin bayanin rashin kunyar nan duk ranar dana kamaki ALLAH saikin fad'awa y'an garinku''.
"Ai nasan abinda zakai min bai wuce kiss ba, mayen baki kawai''. Kai ya jijjiga yana cije lips yace
''Duk ni kad'ai ko?''
"Eh, d'in, tace tareda murgud'a baki, yunk'urin tashi yayi ta rufo k'ofar da k'arfi, komawa yayi ya zauna yana tsaki mamakin kanshi ma yake yadda ya biyewa k'aramar yarinyan nan haka, sai rashin kunya ga kuma shegen tsoro yanzu dazai rutsata kuma ta iya shasshake fuska tana marairaicewa amma yanzu dayake daga nesa ne ji yadda take fad'a masa magana son ranta.....Ya jima zaune a wajen sannan ya tashi ya wuce bedroom d'inshi zaiyi wanka.
Sai dataji shigarshi bedroom sannan ta bud'e k'ofar a hankali ta fito sad'af sad'af ta d'auki wayarta dake kan kujerar data kwanta d'azun tayi saurin komawa dan bazata bari su had'u ba wllhy.
Tun daga ranar suka fara wasan b'uya da Saif sam bata bari su had'u saitaji fitarshi dan tuni ya koma bakin aiki saboda yadda hospital d'in keda b'ukatar shi. wani tym d'inma wajensu Mamie take breakfast d'inta, magreebah nayi kuma zata shige bedroom d'inta ta kulle saikuma wata safiyar. Shi dariya ma abin yake bashi na shirmen datake ganinta hakan datake yasa har yanzun basu had'u ba batasan cewa niyyar kamatan ne kawai baiyiba. A haka har sukayi kwanaki biyar ko tukunya bata tab'a d'orawa ba da sunan girki, a kwana na shida ne Mamie tayi masa maganar ya kamata a ajiyewa Ayshaa kayan abinci saboda tafara girki kar a tauye mata hakk'inta karya zamana abinda suka dafa bashi takeson ciba. Hakan kuwa akayi dan a ranar aka lodo mata kayan abinci da duk wasu nau'ikan kayan girke girke ba abinda ba'a ajiye mataba duk abinda akasan zata nema. Satinta d'aya tafara girki da kanta kuma har lokacin bata yadda su had'u da Saif daga shi sai ita saidai su had'u wajen Mamie tasan dai duk rashin M d'inshi bazai tab'ata a gaban idon Mamie ba, sun k'ara shak'uwa da Mamie sosai duk kunyar nan datake ji ta rageta sosai, Imaan kuwa bama su cika had'uwa ba kullum tana school saboda exams dazasu fara kota dawo d'inma bata cika zaman parlor ba tana bedroom d'inta tana karatu.
________
★★★★★★★
Ta b'angaren zuhrah kuwa tana can sunata k'ok'arin yadda zasu gudanar da aikinsu akan Ayshaa cikin sauk'i kullum sai sunyi waya da Zuma yana fad'a mata tsare tsarensu. Yau d'inma tafe take a mota zataje inda zuma yake shida yaranshi saboda nemanta dayayi batasan dai dalilin kiranba, wayarta dake front seat tayi k'ara alamar kira hannu ta mik'a ta d'auko taga sunan k'awarta Aneesah d'an fulani tayi picking tareda karawa a kunnenta tace
''Hello Anee ya kike''.
Daga d'aya b'angaren akace
"Lafiya k'alau mutuniyar kina inane na k'ara samo miki wani abufa ta yadda zaki shigar da kanki gurin Man d'in nan idan kin aika da wannan shegiyar matar tashi lahira''. Dariya zuhrah tayi cikeda jin dad'i tace
''Kin ganni yanzu haka Ina kan hanyar zuwa wajensu Zuma yana nemana bansan dai neman dayake min ba idan na dawo zan biyo ta nan d'in''.
"Owk Ina jiranki ta Dr Saif kinci dubu sai ceto''.
Dariyar ta k'ara yi cikin tsananin farin ciki tana k'ara hango kanta a matsayin matarshi da yadda zata dinga juyashi duk wannan shegen girman kan nashi da jan ajin nan duk saiya saukesu yayi mata biyayya. Hang up d'in wayar tayi ta maidata inda take, juyowar dazatayi taganta daf da wata babbar motar d'auko kaya kafin tayi wani yunk'urin tsaida tata motar tayi gefe wannan babbar motar ta daki motarta, motar tayi wani irin hantsilawa kafin ta fara kamawa da wuta, tuni jama'ar wajen suka tattaso da sauran masu wucewa aka tsattsaya domin kawo mata d'auki anyi nasarar cirota duk da wutar tafara tab'ata sosai koda aka cirota d'inma bata numfashi wasu sukace a hanzarta tafiya da ita asibiti ko dogon suma tayi a ceto rayuwar ta wani likita daya tsaya shima ganin accident d'in ya dubata ya sanar musu data rasu ai gaba d'aya gurin ya hargitse masu saurin kuka kuwa tuni sun fara nan aka shiga laluben wayarta dan kiran y'an uwanta ba'a samu wayarba, wani saurayi ne d'an unguwar su daya tabbatar da zuhrahn ce ya kira yayanta abokinshi ne ya sanar dashi abinda ke faruwa. Ba'a d'auki dogon lokaci ba kuwa suka k'araso wajen hankali tashe suna faman koke koke suka d'auki gawarta suka nufi gida domin yimata sutura.
Shikuma direban babbar motar nan police ne suka tafi dashi station d'insu dan alamu sun nuna guduwa yakeson yayi.
*_NOTE :_* *Wannan wata gab'a ce dazanyi jan hankali wasu reader's din zasuce meyasa aka kashe zuhrah tunda wuri haka? Ku sani nasa zuhrah cikin wannan labarinne don akwai mutane da yawa dazaka samesu basuda aiki sai kulle kullen yadda zasu cutar da y'an uwansu musulmai kun sani akwai mutane da dama cikin wannan al'ummar tamu, ya kamata muyi karatun ta nutsu musani cewa ita mutuwa lokaci d'aya idan tazo second ba za'a kara makaba wllhy ba kuma ji zakayi a jikinkaba cewa na kusa mutuwa, ba tambari ake bugawa mutum a goshinshi ba na k'aratowar mutuwarshi katsam saidai ka wayi gari kajika cikin k'abarinka, ubangiji ba ruwanshi da cewa wai aikin kirki nake ko kuma aikin assha nake idan lokacin da aka k'ayyade maka na tafiya yayi za'a d'auki rayuwar kane, To meya kamata muyi? Saimu kasance kullum cikin kyautata mu'amalarmu da mahaliccinmu mu daina yunk'urin cutar da y'an uwanmu kar abin duniya ya rufe mana ido, ga dai zuhrah nan tunda ta d'ora idanunta akan Dr Saif taji nan duniya ba wanda takeso sai shi dataji labarin zaiyi aure tun kafin taga wadda zai aura d'in ta tsaneta tafara shirya yadda zata cutar da ita daga k'arshe ta yanke shawarar rabata da duniyar baki daya k'arshe meya faru da ita, bata tab'a kawowa a ranta zatabar duniya a lokacin ba to ita mutuwa haka take lokacin da kai kake ganin yanzu zaka fara jin dad'in duniyar shikuma ubangiji a lokacin yakeda b'ukatar ka koma gareshi shiyasa akeso mutum ya kasance kullum yana aikata aikin alkhairi ka daina kwana dawasu a cikin zuciyarka because bakasan tym din da mutuwa zata riskeka ba saboda a kullum muna k'ara kusantar kaburburanmu batareda mun saniba shikenan kuma daka mutu an shafe babinka ssika aikata aikin alkhairi nema za'a d'an dinga tunawa dakai ana maka addu'a, zuhrah tun kafin tagama aiwatar da nufinta ma ALLAH ya d'auki rayuwar ta to tana iya faruwa a kaina a kanki a kansu akan kowa ma ubangiji ALLAH yasa mufi k'arfin zukatanmu ya rabamu da sharrin shaytan dan komi yana faruwa ne ta silarshi, ALLAH kasa mu cika da imaani ka k'ara gyara mana zuciyoyinmu ya kasance sharri na fita alkhairi na shiga ALLAH yayi mana gafara badan halinmu ko aikinmu ba Yaa zuljalali wal Ikraam, Ajibda'awatuna Yaa ALLAH.*
Kufara da wannan insha ALLAH zuwa anjima idan na samu tym zaku kara jina.
Mrs Salees Mu'az❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu
(Ummee)
HASKE WRITER'S ASSOCIATION
(Home of expert & perfect writer's).
*DR. SAIF*
Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No 28.
Mutuwa akwai tambari indai anyita to nan da nan zata karad'e ko ina hakan ce ta faru da rasuwar zuhrah nan da nan zancen mutuwarta ya baza gari, kowa yaji rasuwar saiyayi mamaki, daga wanda zaice gama wayarsu kenan sai wanda zaice yanzun nan fa yaganta ta shiga mota ko tana shirin shiga mota (Hmm mutuwa kenan, ba'a mamaki da lamarin ubangiji yanzun nan zaka rabu da mutum anjima kad'an ace maka babu shi haka zakai tajin mutuwoyi kala kala kafin kaima aji taka, shin wane tanadi kayiwa wannan rana daka tabbatar wajib saitazo gareka duk daren dad'ewa?,yiwa kanka hisabi tun kafin ranar da za'ayi maka munada aiki a gabanmu baizoba bai kuma wuceba ALLAH ya datar damu ubangiji ALLAH yasa mu dace mu rabauta duniya da lahira).
Ba wanda jikinshi baiyi sanyiba a cikinsu zuma lokacin da labarin mutuwar zuhrah ya riskesu, musamman Zuma dayafi saninta tun a lokacin wasu suka fara nadamar irin abinda suke aikatawa yayin da wasu kam wanda ALLAH bai nufa da shiriyar ba kuma zuciyarsu ko gezau.
Aneesah da Zee sunfi kowa jin rasuwar zuhrah a cikin k'awayenta sunyi kuka kamar me jikin Aneesah yayi matuk'ar yin sanyi tanata jinjina wannan al'amarin gashi tasan k'awar tata ta tafi da mugun nufi a cikin zuciyarta saidai ALLAH yayi mata gafara kawai amma ita tasan wacece zuhrah tasan sirrinta da duk irin abinda take aikatawa. Zee kuwa duk abinda zuhrah take shirin yi batada masaniya akai saboda indai zatayi abu tasan abin bashida kyau bata tunkarar zee d'in saboda tasan hanata zatayi ta shiga yimata wa'azi yanzu tata ta k'are an rufe babinta tana can zata girbi abinda ta shuka, saidai fatan ALLAH yaji k'anta yayi mata gafara.
★★★ Friday ★★★
Tun barcin data koma bayan tayi sallahr asubah bata tashi ba sai fin sha biyu na rana batasan wane irin barci tayi hakaba. Cikin sauri ta gyara ko Ina ta kunna burners k'amshi ya cika ko ina wanka tayi ta shirya cikin dogon skirt black color da farar riga body hug mai dogon hannu tayi rolling da black Vail turaruka kawai ta fesa batareda ta tsaya yin wata kwalliya ba saboda yunwar dake k'wak'ular cikinta tasa farin slipper mai taushi ta wuce kitchen dan samun abinda zatasa a cikinta, tea ta dafa dayaji kayan k'amshi da na'a na'a ta juye a tea flaks sai indomie dazata dafa tayi blending uban attaruhu ta had'a komai a pot ta kunna gas, tana tsaye gaban gas d'in tana jira ta k'arasa dahuwa yawun bakinta har tsinkewa yake saboda yadda k'amshin attaruhun ke dukan hancinta d'an banzan cin yaji gareta kamar me Ammi tayi fad'an harta gaji ko a gida haka take wani tym d'inma girkinta daban takeyi yadda zata cika yaji son ranta. Haka nan jikinta ya bata kamar ana kallonta ga kuma bak'on k'amshi daya ziyarci kitchen d'in daya bambanta da nata a hankali ta juyo takai dubanta bakin k'ofar kitchen d'in da sauri tayi baya har hannunta na tankwab'ar wani glass cup dake ajiye ya fad'o ya fashe, Saif ne tsaye ya jingina da bango yayi crossing legs d'inshi hannayenshi zube cikin aljihun wandonshi sanye yake cikin farin wando k'al da farar riga mai gajeren hannu takalmin k'afarshi ma farine sawu ciki sai bak'ar jacket dake rataye a kafad'arshi black P.Cap ce akanshi ya sauko da ita sosai ta rufe idanunshi bakinshi kawai ake gani mai zagaye da kwantaccen gashi sai dogon hancinshi daya kasa b'oyuwa. Sai hakan ya zama kamar sun tsara sa kayan nasu ne saboda kowanne black and white ne a jikinshi.
Tsaye tayi tana kallonshi har zuwa lokacin yana a yadda yake tasan yau ta kad'e har ganyenta dan bazata manta last had'uwarsu ba da irin rashin kunyar datayi masa ba.
A hankali yasa hannu yayi sama da P.Cap d'in idanunshi suka bayyana, kanta ya zubesu yana mata wani irin kallo data fassarashi dana cin k'aniyarta dazaiyi kamar tsohuwar munafuka tayi k'asa da kai sai k'ikk'ifta ido take tana rarrabasu hannunta a gefen wuyanta kana ganinta kaga marar gaskiya.
Shi sai tabashi dariya ma ganin yadda take kamar ba itabace tagama masa rashin kunya ba ranar nan yanzu dayake taga tazo hannu ji yadda tayi tsamo tsamo kamar an tsamota daga ruwa.
Dawowarshi kenan daga hospital yazo yin shirin masjeed yaji tashin k'amshi a kitchen ya tabbatar tana ciki shiyasa ya shigo yaga yadda zatayi idan ta ganshi.
Harya fara takowa zuwa wajenta kuma ko me ya tuna ya juya da sauri ya bar kitchen d'in.
Ajiyar zuciya ta saki tareda dafe k'irjinta tana lumshe ido tace
"Alhamdulillah''. Ta juya zata kashe gas d'in glass cup d'in daya fashe ya yanki gefen k'afarta dan sam ta manta da wani cup ya fashe a gurin, k'ara tasaki da k'arfi ta durk'ushe a wajen tana kuka. Yana shirin shiga bedroom d'inshi yaji k'arar tata kamar zai share saikuma yaga hakan bai daceba koba komi a k'ark'ashin kulawarshi take a yanzun dan haka ya juya ya koma kitchen d'in bayan ya bud'e bedroom d'in ya cilla jacket d'in kan couch.
Kanta a k'asa tana kallon yankewar tana faman ihu especially dataga jini yana zuba duk saita k'ara rud'ewa, sai daya kashe gas d'in ya duba k'afar tata yaga yankan, ba laifi yankan da d'an girmanshi amma baici ace tana masa wannan uban kwaroroton ba duk tabi ta cika masa kunne da k'ara ga muryar shegen zak'i, k'aramin tsaki ya d'an ja yana kama k'ugunshi da duka hannayenshi biyun murya a dakushe yace
"Stand up".
"Ni bazan iyaba''. Tace cikin kuka tana yarfe hannu.
Mamaki ne ya kamashi d'an wannan yankar take cewa bazata iya tashiba eh lallai yarinyar nan muguwar shagwab'abb'iya ce.
''Ke ki tashi ki wuce muje in miki dressing ciwon''. Kafad'a ta mak'ale masa tana turo baki.
Tsaki yaja da k'arfi yayi mata d'aukar amarya saiji tayi anyi sama da ita aikuwa ta tsorata dan batayi tsammanin d'aukan ba hakan yasa ta k'ank'ameshi a tsorace, wata siririyar ajiyar zuciya yasaki dashi kad'ai yaji abarsa. K'amshin turaren jikinshi ne yayi mata masifar dad'i hakan yasa batasan lokacin data k'ara cusa kanta a k'irjinshi ba, da k'afa ya tura k'ofar bedroom d'in ta bud'e ya shiga tsakiyar bed d'inshi ya sauketa ya cire P.Cap d'in kanshi ya cilla kusa da ita ya cire takalmin k'afarshi sannan ya isa gaban wardrobe d'inshi ya bud'e ya ciro first aid kit ya nufo bed d'in tana zaune sai k'ananun koke koke take tana yayyarfe hannuwa, Shima hawan yayi kusa da ita ya zauna tareda tank'washe k'afafunshi ya bud'e kit d'in tana tozali da abubuwan dake ciki ta k'ara volume d'in kukanta a fusace ya d'ago ya jefa mata harara yace
"Shut up your mouth, stupid d'in yarinya kawai, kan wannan d'an ciwon zaki cikamin kunne da d'an banzan muryarki nan kamar ta aljanu''. Kukan ta rage tana d'an turo baki a ranta take fad'in
"Mutumin nan wala Imani ko tausayinta bayaji yake mata fad'a.
K'afar ya kamo ya d'ora kan cinyarshi yafara dubawa ko glass d'in ya shiga yadda yake duddubawar ne yasata fara zame k'afar saboda zafi, wani mugun kallo ya d'ago ya jefa mata saita tura baki, k'wafa ya saki ya maida kanshi kan abinda yake dole saiya wanke mata. Tunda taga alamun abinda zaiyi jikinta ya d'an fara rawa ta shiga girgiza masa kai shi baisan ma hidimar datake ba yafara k'ok'arin wankewa tunda yafara tasaki k'arar da saida ya runtse idanunshi saboda yadda ta ratsa dodon kunnenshi hannunshi ta dafe dake kan ciwon tana fad'in
"Na shiga uku dan ALLAH dan ANNABI Dr kayi hak'uri please na tuba wllhy".
Shi saiya rasa abinda zaice mata ma wllhy ji abinda take dan ALLAH kamar wadda ake shirin yankawa.
Saidaya had'e girar sama data k'asa yasha mur sosai yace
"Remove your hand''. K'in d'aukewar tayi sai shasshek'a take tana fad'in 'Please yayi hak'uri'
"I said remove your hand''. Cikin tsawa yayi maganar yana zare mata ido da sauri kuwa ta cire tana cigaba da zuba masa raki. "Kika k'ara sa hannu a nan saina mareki ki gwada kuma kigani, ki kuma nutsu ki dainamin mutsu mutsun nan ko in caccaka miki scissors yanzu a cikin ciwon Yaja tsaki ya cigaba da aikinshi, Ido ta zaro tana kama bakinta da hannayenta tsaf fa zai iya aikata abinda yace dan zubin mutumin nan na marasa Imani ne gaba d'aya. Bakin ta toshe ta cigaba da kukanta a haka batareda ta k'ara yunk'urin kai hannu ba.
Kuyi hakuri da kadan wllh mura ce tamin mugun kamu sak'onnin ku daketa riskata ma yasa nayi k'ok'arin yin wannan d'in, need ur prayers
Mrs Salees Mu'az❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu
(Ummee).
Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's ).
*DR. SAIF*
Writer: Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No. 29
"Dan ALLAH kayimin a hankali please Dr".
Ayshaa ta fad'a cikin kuka jin azaba ta isheta.
"Bakin dai bazai min shiru ba ko? Ko zaki koyamin aikina ne?". Ya fad'a yana jefa mata harara. Kai kawai ta girgiza tare da sa hannu ta share hawayen daya zubo mata a ranta take jinjina rashin imanin shi yana ganinta cikin wannan halin bazai tausaya mata ba masifaffen.
Sai daya gama tsaf ya d'aga Ido ya kalleta yayi matuk'ar bashi dariya ganin yadda fuskarta tayi uban ja tayi jage jage da hawaye hardasu majina, Ido ya d'an waro yana nunata da hannu yace
"Akan wannan d'an ciwon kika zama haka?".
"Wannan ne d'an ciwo saboda ALLAH". Saita k'ara b'arke masa dawani kukan har dasa vail d'inta daya kusa zamewa daga kan nata ta rufe idanunta.
"Ke meyake damunki hakane? ALLAH koki rufamin baki ko inyi maganinshi yanzun nan".
Sanin abinda zaiyi d'in yasata yin shirun ta bud'e idon tanata faman murzarshi da hannunta tana tura baki. Kai kawai ya girgiza yana d'an tab'e baki ya had'e abubuwan dayayi amfani dasu ya maida cikin box d'in ya sauka daga kan gadon ya maida box d'in ma'ajiyarshi.
Zamanta ta gyara sosai akan bed d'in tana k'ara kallon d'akin.
"Yunwa nakeji". Tace a shagwab'e tana kallonshi lokacin yana gaban wardrobe da alamu kayan da zai saka yake zab'owa.
"Yunwa?". Ya maimaita yana kallonta.
Kai ta d'aga cikin tura baki tace
"Eh, banyi breakfast fa".
"Why?". Ya tambayeta cikin had'e rai.
"Barci nayi". Tabashi amsa kai tsaye, tsaki ya saki tareda rufe wardrobe d'in ya fita daga bedroom d'in, tabi bayanshi da harara tana k'ara kumbura baki dan gani take harda mugunta ya had'a mata wajen yin dressing d'in.
Bai jimaba sosai taga ya shigo hannunshi d'auke da mug ya mik'a mata mug d'in ta kalla kafin ta maida kallonta gurinshi tace
"Nifa indomie zanci ba tea ba".
"Bazaki ci indomien ba, bakida hankali ne wancan uban peppe d'in da kika zuba fa".
K'wal k'wal tayi da Ido tana kallonshi tace
"Please dan ALLAH ka bani indomien".
"ALLAH bazaki ciba kinji ma na rantse karb'i wannan kisha".
Kai ta juyar tana zumb'ura baki tace
"Ni bazan shaba".
"Ke Ina wasa dake ne? Juyo ki karb'a ki shanye ko kiga yadda zanyi dake yanzun nan ko dan kinga Ina lallab'aki". Murya ba alamun wasa yayi maganar yana k'ara had'e fuska.
Juyowar tayi tana share k'wallah, ya mik'a mata mug d'in ganin irin kallon dayake mata yasa ta karb'a ta shiga jujjuya cokalin ciki batare data sha d'in ba.
"Cewa nayi kisha ba jujjuyawa ba". D'agowa tayi ta kalleshi wani mugun haushinshi takeji dan harga ALLAH ta k'wallafa ranta akan indomien nan ko Ina ruwanshi zaice wani ta cika yaji to wai taya ma yasan yaji yayi yawa a ciki, kawai dai fin k'arfi yayi mata kuma ALLAH zai saka mata.
Kamar magani haka ta d'ebo tea d'in takai bakinta, hannu taga ya mik'o mata bata gane abinda yake nufiba dan haka tayi masa alamu da idonta na bata ganeba, shima d'in da Ido yayi mata nuni da spoon d'in hannunta a fusace ta mik'a masa tana harararshi ta gefen ido karb'a yayi batare dayayi magana ba ya k'ara yimata alamu da hannunshi na ta kafa kai.
'Ikon ALLAH, yau kuma kurame ne akan nashi kenan da alamu dai yanzu suka sauka tunda d'azu ai yayi magana (ALLAH ya shiryaki Ayshaa ). Baki ta tab'e ta kafa kan saidata shanye ta sauke tareda mik'a masa cup d'in ya karb'a ya fita.
Kwanciyar ta ta gyara tana lumshe ido, koda yadawo kaya ya d'auka a wardrobe ya shiga toilet. Bayan wani lokaci ya fito ya shirya tsaf cikin farar shadda wajen mirror ya tsaya yana fesa turare ta cikin mirror'n yake kallon yadda tawani bararraje masa a bed saikace nata, bak'in takalmi yasa na fata yayi ficewarsa daga bedroom d'in. Ayshaa kam wani barcin ne ya k'ara figarta dan sama sama ma taji fitarshi a d'akin.
Mamie ke tambayarshi Ayshaa lafiya kuwa duk yau bata lek'o ba? Nan yake fad'a mata abinda ya faru, duk saita rud'e ta shiga tambayar shi ya jikin nata.
"Mamie bafa wani ciwone mai yawaba fa".
Harararshi Mamie tayi tace
"Banson shirmen banza ciwo dai ai duk sunanshi ciwo ko kuma lafiyar jikinta aka tab'a". Shidai baice komiba yayi mata sallama ya fita dan zuwa masallachi.
Sai bayan sallahr zuhr sannan ta tashi da k'yar ta sauka daga gadon ta taka k'afar a hankali datayi mata nauyi ta fita daga bedroom d'in taja masa k'ofar.
Nata bedroom d'in ta koma tayi sallah ta fito cikinta banda kiran yunwa ba abinda yake, kitchen ta shiga tasamu indomien ta na nan a cikin pot dad'i taji sosai ta zubo tadawo parlor ta zauna ta ci abarta.
Da yamma Mamie da Imaan suka shigo suka dubata sun dad'e sosai suna hira sannan Mamie ta tafi tabar Imaan tana tayata hira.
Ranar ko girki batayi ba Mamie ce ta aiko musu dashi, itadai bata k'ara sashi a idonta bama dan da wuri tayi barci bakuma tasan lokacin daya shigo ba.
★★★
Safnah ce zaune gaban mamanta Hajia Binta tana k'ara tuna mata maganar Saif, shiru tayi na y'an mintuna kafin yace
"Safnah,nifa Ina ganin mu hak'ura kawai da wannan maganar ALLAH yayi ba mijin aurenki bane ki rungumi k'addarah kawai".
Cike da mamaki take kallonta jin abinda take fad'a, ya za'ayi tace mata wani wai tayi hak'uri da Saif bayan shine cikar muradinta kuma ta sakankance da abinda tace zatayi bayan bikin?.
Cikin b'acin rai take fad'in
"Haba Momy kefa kikace zakiyi wani abu akan lamarin nan bayan biki kuma yanzu kice wai in hak'ura dashi inbar maganar?"
"Gaskiya ne da kam nayi niyyar yin abu akai amma yanzu nafasa kiyi hak'uri safnah ga Naseer nan (d'an yayan babanta) yanata faman son samun dama daga wajenki kink'i bashi fuska".
"Nidai Momy ba Naseer nakeso ba Yah Saifu nakeso kuma zanyi duk abinda zanyi ganin na mallakeshi". Ta tashi fuuu tabar parlor'n ta shige bedroom d'inta.
Sai gata ta fito da mayafi da hand bag da car key a hannunta, uwar tana mata magana tayi ficewarta alamun fushi.
Kaita girgiza tana fad'in
"ALLAH ya shirya, batasan meyasa ba haka nan kawai taji bazata iya cutar dasuba a baya kam ba irin mugayen nufin da bata dinga k'ullawa akansu ba (Kunsan wani lokacin haka al'amarin ALLAH yake gashi dai mutum zaita kitsa mugun nufi akan wani saikuma ubangiji yak'i bashi damar dazai aiwatar da nufin nashi ya kasa katab'us ya tsare wancan d'in da ake hari musamman idan ya rik'e addu'a,Ina jan hankalinmu a nan mudage da addu'o'e dan bakasan wanda keson cutar dakaiba wani ma wllhy d'an uwanka ne da kake tunanin idan yaga abinda zai cutar dakai sai inda k'arfinshi ya k'are batare dakasan shine mai son cutar dakai d'in ba, wani baya k'aunar ci gabanka a rayuwa ALLAH yasa mu dace mufi k'arfin zuciyoyinmu ya rabamu da aikin dana sani).
Tana fita ta shiga mota kai tsaye gidan Mansurah ta wuce dan tana ganin itace zata share mata hawayenta.
Kallonta Mansurah tayi tace
"Meyake damunki ne k'awata naganki a haka?".
Tsaki safnah taja tace
"Nida Momy mana, waifa tayimin alk'awarin bayan bikin nan zatasan abinda zatayi akan Yah Saifu da shegiyar matar nan tashi yanzu kuma nataso da maganar tace wani wai inyi hak'uri meye meye ga Naseer nan in bashi dama".
Murmushi Mansurah tayi cikin zuciyarta tace 'Anzo wajen'.
A fili tace
"Amma dake mukayi maganar nan nace kibar komi a hannuna ko bansan meyasa ma kika yiwa Momy maganar ba".
''To yanzu meye shawarar ki akai dan ALLAH na matsufa in ganni na mallakeshi meya kamata ayiwa matar tashi".
"Eh to akwai abubuwan yi mana sosai, saidai ban saniba ko zaki iya bin hanyar dan ganin kin cimma burin rayuwar ki".
"Wllhy ko meye zanyi akan Saifu, Mansurah bakisan waye Saif a cikin zuciyata ba".
"Zaki iya zuwa wajen boka???.
Kai tsaye babu alamun tsoro tace
"Zan iya Mansurah". (Wa'iyazubillah, dan ALLAH abin duniya ya daina rud'ar mu muna kai kanmu ga halaka zuwa wajen boka bashine maslaha ba idan ma kina cikin damuwa ne kiyi addu'a ki tashi kiyi tsayuwar dare ki fad'awa ubangiji b'ukatunki saikiga ALLAH ya amsa miki yawancin mu mata indai akan zancen kishiya ne ba abinda bazamu iya yiba shige shigen malamai da y'an tsubbu duk akan duniya yakamata dai muyi karatun ta nutsu ALLAH ya k'ara karemu masu yi kuma ubangiji ya shiryasu).
Dariya Mansurah tayi sosai kafin yace
"Bakida damuwa cikin abu uku dole ki zab'i d'aya wanda za'ayi mata da zamu fad'awa boka".
''Kamar me da me kenan?" Safnah ta b'ukata.
Zama Mansurah ta gyara tace
"Na farko ko a kasheta har lahira ko kuma a salwantar miki da ita ta shiga duniya ko kuma asata cikin yanayi na rayuwa da mutuwa".
"Kamar yafa, meye rayuwa da mutuwa?".
"Ina nufin a nak'asta duk wani abu mai amfani a jikinta ya zamana gata dai da ranta amma kuma kamar matacciyace dan bazata iya tsinanawa kanta komiba harta d'an yatsan hannunta bazata iya motsashi ba wanne kika zab'a a ciki?".
Tsai tayi da ranta tana tunanin wanda za'ayiwa Ayshaa, zuwa can tace
"Ina tunanin kawai ayi mata wanda za'a nak'asta ta tazama batada wata mamora inaga hakan zaifi".
"Done, ki d'auka kamar anyi angama aikine daga yanzu ki dinga hangota a kwance bata ko motsi daga nan kuma sai mu koma ayi miki aiki a kanshi dan shima ba haka zamu barshi ba dan naga alamun mugun taurin kai zaiyi".
Hannu safnah ta bata suka tafa suna shek'a dariyar jin dad'i, daga nan suka fara shirya yadda zasu gudanar da aikinsu da ranar dazasu ziyarci bokan dazai musu aikin.
Safnah ta dad'e a gidan kafin suyi sallama ta tafi ranta fari k'al.
Baki Mansurah ta cije tana k'ank'ance ido tace
"Gani nan Saif, zan d'auki fansar abinda kayi min da irin cin mutuncin dakayi min, wllhy saikayi dana sanin sanina a rayuwarka saikayi bak'in ciki ka zubar da hawayen ka muje zuwa.......
Wai shin me Saif yayiwa Mansurah ne haka? Me kuma take shirin aikatawa a kanshi? Shin asirin zai kama Ayshaa ko kuwa dai wani abu daban ne zai faru?.
Ayi hak'uri da kad'an
Mrs Salees Mu'az ❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu
(Ummee).
Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's ).
Writer: Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No. 30.
Tun daga yanayin driving d'in dayake zakasan cewa a gajiye yake ko kuma akwai wani abu dake damunshi saboda yadda yake yinshi a kasalance yana wani irin slow kamar dai bayason yin tuk'in ne. A haka ya k'araso gidan yayi horn aka bud'e masa gate ya kutsa da motar tashi cikin compound yayi parking, koda yayi parking d'inma bai fitoba sai relaxing daya k'arayi sosai bisa seat d'in yana lumshe idanunshi da suka d'anyi ja. A matuk'ar gajiye yake tun safe daya fita bai hutaba ga yanayin dayake jinshi a ciki har lokacin kuma ya kasa nemawa kanshi mafita.
Ya dad'e a haka sannan ya fito ya kulle motar black jeans ne a jikinshi da long sleeve shirt white color sai bak'in rufaffen takalmi sanye a k'afarshi, hannu kawai ya d'agawa maigadi dayake masa barka da zuwa bayan ya fito daga motar ya wuce ciki.
Bai samu kowa a parlor'n ba sai TV daketa aiki a tashar MBC Bollywood da aka saka wata wak'a mai masifar dad'i yanayin sound music d'in da yadda wak'ar ke tafiya duk a slow Ajiyar zuciya ya sauke ya wuce side d'insu yakai kai zai shiga itakuma zata fito ba wanda yasan da tahowar d'an uwanshi dan haka suka bangaji juna kanta ya daki k'irjinshi.
"Ouchh". Tace a shagwab'e tana dafe goshinta tareda kai kallonta kanshi daya tsaya k'ik'am yana mata wani irin kallo baki ta tura tana murza goshinta, sosai ya bud'e Ido yana k'are mata kallo sanye take cikin bak'ar abayah dataji adon duwatsu daga sama har k'asa masu mugun k'yalli da d'aukar ido ta d'an kamata rigar hakan yasa ta fidda tsarin halittarta sosai da cikar k'irjinta, tayi rolling da gyalen abayahr fuskarta fayau ba wata kwalliya sai powder da lipstick da gazar datasa wani masifaffen k'amshi ne ke fita daga jikinta na had'add'un turaruka magana ta ALLAH ya yaba da kwalliyar sosai cikin ranshi tayi masa mugun kyau saita koma masa tamkar irin y'anmatan Arab d'innan amma jin kai bazai barshi ya nunaba sai yatsina fuska dayayi yana harararta yace
"Makauniyar inace ke?".
Baki ta tura tana wasa da yatsun hannunta tace
"Nima baka bigeni ba, kuma naji zafi".
"Zakimin rashin kunya ne?". Yace cikin had'e face yana d'age mata gira gamida nufar inda take tsaye. Baya ta fara ja cikin marairaice fuska kamar zata sakar masa kuka a ranta take fad'in 'Yan jarabar a kusa suke amma in banda neman fitina yasani fa sarai bata ganshi bane kuma itama ai wannan k'aton k'irjin nashi mai kama dana y'an dambe ya bugeta kuma taji zafi ai saishi dayake da bakin magana zai wani cemata makauniya.
Jikin bango ta jingina kusa da wata flower duk a cikin parlor'n, hannayenshi yasa duka biyun ya tokare bangon datake tsaye yayi mata rumfa yayi k'asa da kanshi sosai ta yadda har yake zuk'ar numfashinta itama take zuk'ar nashi k'amshin turaren jikinshi danata na k'ara had'uwa tareda bada wani salon k'amshin na daban k'asa yayi sosai da murya tamkar wanda yake mata rad'a yace
"I said zakimin rashin kunyar dakika sabane".
Ita dai yau tana ganin ikon ALLAH, mutumin nan d'an neman bala'ine wllhy inba neman fitina ba meye laifinta a nan zaizo yawani matseta a bango, rawa jikinta ya farayi kad'an saboda yadda kusancin nasu yayi yawa over bawani gap a tsakaninsu ta shiga motsa bakinta batare da tasan abinda zata fad'a d'in ba, lips d'in nata ya k'urawa Ido yana kallon yadda suke motsawa gashi dama yaji lipstick sai uban shinning yake Ido ya runtse gam tareda had'iyar wani yawu dayazo masa a bazata yana sauke numfashi a hankali yayin da yanayinshi ya fara k'ok'arin sauyawa ga wak'ar dake tashi daga TV har lokacin basu cireta ba ta k'ara taimakawa sosai wajen canza mood d'in nashi sai yake jinshi cikin wata duniya irin ta daban, har lokacin idanunshi nakan lip's d'inta yana wani kallonsu ta k'asan idanunshi da suka canza launi yana ayyana abubuwa da dama akansu. Ganin yadda yake kallon bakin nata tasha jinin jikinta tana addu'ar ALLAH yasa dai ba muguntar ce ta motsaba, ita bama wannan ne damuwarta ba a halin yanzu damuwarta d'aya kar Mamie ta fito ta gansu a haka data shiga uku kuwa dan kunya. Ganin ya fara daidaita nashi lips d'in kan nata yasa ta marairaice sosai kamar mai shirin sakin kuka tace
"Please doctor a parlor'n Mamie fa muke dan ALLAH kabari I'm sorry indai dan na bigeka ne bazan k'ara ba please". Ta k'arasa maganar tana d'an had'e hannayenta alamun rok'o, shidai kanzil baice mataba sai kanta daya rik'o da hannayenshi harda wani karkatar da kan nata yadda zaifi jin dad'in kissing d'in itadai Ido ta rufe gam lokacin dataji saukar soft lips d'inshi akan nata tareda zura harshenshi cikin bakinta ya kamo nata harshen, ji take tamkar tasaki kuka saboda takaici fisabilillahi wani irin kallo Mamie zatayi mata idan ta fito tagansu a wannan yanayin salon dayazo mata dashi yau yasha bambam da irin kissing d'in dayake mata a baya na mugunta dan yau d'in da wani irin style mai k'ayatarwa ya shiga bata French kissing daya saka jikinta rawa especially idan ta tuna cewa a koda yaushe Mamie tana iya fitowa kuma ko giyar wake tasha tasan bazata iya tureshi ba ta gudu yadda yake tsaye kyam kan k'afafunshi cikeda mazantaka to ina taga k'arfin hakan ma, Saif dai tuni ya fara hawa network shima jikin nashi rawar yafara idanunshi a rufe da alamu yafara manta inda yake.
Imaan data kawo kai zata shigo parlor'n kenan dan dama ita ta kunna TV'n takamo favorite channels d'inta ta koma bedroom zata d'auko phone d'inta ta ganowa idonta su cikin wannan yanayin da sauri tayi baya tana dafe bakinta tareda d'an waro Ido waje.
Y'ar dariya tasaki tana rufe bakinta a ranta tace
"WOW that's very nice su Yah Saifu yau kuma anan ake baje kolin making love d'in,abin fa yabada ginger sosai sad'af sad'af ta koma da baya cikin ranta take fad'in 'Kai namiji bashida kunya wllhy yanzu shi ko tunanin Mamie zata fito bayayi, yanzu saiya gama yazo yana wani shan kunu yana muzurai shi a dole bayason raini kashi biyu kenan tana ganinshi yana saka y'ar mutane a loko , bedroom d'inta ta koma ta kwanta tana addu'ar ALLAH yasa kar Mamie tazo ta katse musu jin dad'insu.
Saida yayi son ranshi sannan ya saketa yana yana maida numfashi a hankali ya k'ura mata ido da munafukin kallon nan nashi na k'asan idanu, idanun nashi sun kad'a sunyi red color sosai sai faman lumshe mata su yake tamkar wanda yasha kayan maye, itama d'in kallon nashi take ta b'ata fuska sai motsa baki take tana gunguni ita kad'ai tasan abinda take fad'a bakin nan a d'ane kamar zata saki kuka.
Jin kamar ana saukowa downstair yasata waro Ido waje tana kallonshi, kafin tayi wani yunk'uri taji ya fisgeta yana fad'in
"Muje ki fad'amin ma'anar gungunin nan da dalilin yinshi".
Turjewa taso yi ya nuna mata k'arfi suna zuwa parlor'nsu ya jefata kan doguwar kujera yabi ya danne ya sake mata nauyinshi gaba d'aya (Aradu wasa wasa Saif d'in nan mugun d'an air ne banda iskanci kaita latse yarinya da wayo da wayo kuma kana mata muzurai ba gara ka fito mata a mutum sak ba Sofia galadanchi kiyi masa fad'a yasin inba haka ba tamm d'inshi Ayshaa baiwar ALLAH ☹️).
Da k'yar take numfashi saboda yadda ya sakar mata jikinshi gaba d'aya yana mata wani irin kallo, kuma yak'i sakin fuskar a tamke take tam, cikin nishi da son yin kuka tace
"Wayyo ALLAH nah Mamie ki ceceni I'm sorry doctor ka d'agani dan ALLAH wayyo nauyi na tuba wllhy".
Wani malalacin kallo yake mata kafin yace
"Bari ki k'ara jin kalar nauyin nawa ki k'ara tabbatarwa. Ya k'are maganar yana k'ara aza mata dukkan jikinshi tareda kai kanshi kan wuyanta ya fara shinshinar k'amshin turarenta daya k'ara kasalantar dashi, a wahalce take sakin nishi tafara shasshek'a kamar zatayi kuka ba zato ta k'ara jin ya maida lip's d'inshi kan nata, yaa salaam itadai yau ta shiga uku da wannan mutumin waishi kam baya gajiya ne da kiss a rayuwarshi? K'wallah ce ta taru cikin idanunta ta rufe idanun gam hakan yabasu damar zubowa.
Ayshaa sai hak'uri ALLAH ya had'aki da mayen leb'e.
Afwan dai.
Mrs Salees Mu'az ❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu
(Ummee)
[8/27, 17:43] UmmAsghar: Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
*DR. SAIF*
Writer: Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No.31
Wani irin passionate kisses yake mata wanda cikin lokacin k'ank'ani jikinta ya mutu tayi lak'was idanunta rufe batada k'arfin ma dazata k'waci kanta a gurinshi, saida yayi mai isarsa sannan ya cire bakinshi daga nata sai faman sakin numfashi yake a jajjere itama numfashin take saukewa har lokacin bata bud'e idonta ba. Kamar wanda aka tsikara ya tashi da sauri yabar wajen ya shige bedroom d'inshi.
Zaune ta tashi tabi k'ofar bedroom d'in da harara meyasa mutumin nan yake mata hakane? ALLAH ita tagaji da wannan shegen kiss d'in nashi, mutum bashida aiki sai cin leb'e, daga yanzu ta daina tsayawa ma saidai duk abinda zaiyi yayi. Tsaki taja ta lalubi mayafin datayi rolling dashi wanda tuni yayi nashi waje ta yafa ta wuce bedroom d'inta tana faman mita.
Yana shiga ya fara cire kayan jikinsa boxer da singlet kawai ya bari ya fad'a bathroom a hakan ya sakarwa kanshi shawa ruwan ya shiga zuba kanshi, idanunshi a rufe yana sauke ajiyar zuciya a jajjere wannan kissing d'in dayayi ba k'aramin kunno masa wuta yayi ba dama gashi yau d'in a kusa yake shi yarasa ta yadda zai b'ullowa al'amarin ma wllhy yagaji da bawa kanshi wannan horon(kaga zaka iya ne ). Ya dad'e tsaye cikin ruwan sannan ya cire underwear d'in yasaka bathrobe ya fito yana goge sumar kanshi da k'aramin towel riga da wando yasa silk marasa nauyi ya shafa cream sama sama da turare ya kwanta, so yake ya huce gajiyar daya kwaso amma Ina matsalar dayake ciki tak'i barinshi lallai dole ma yayi wani abu akai dole ya nemowa kanshi mafita amma shi kanshi baisan ta inaba.
Tsaki yaja kawai ya lalubi wayarshi ya fara danne danne. Ba wanda ya k'ara jin d'uriyar wani a cikinsu.
Washegari.
Saturday's morning.
Bayan ta gyara ko Ina tayi wanka ta shirya cikin material mai rawa red color doguwar riga data matseta daga sama sosai daga k'asan kuma ya bud'e shima sosai, black vail tayi rolling dashi ta fesa turaruka ta fito tayi breakfast. Tazo shiga bedroom kenan ta hangi k'ofar baya da aka fitar alamun an bud'eta sai yau tayi sha'awar shiga wajen itadai tana ganin k'ofa amma bata tab'a gwada bud'ewa ba dan haka batasan abinda ke wajen ba sai yanzu kam data shiga taga y'ar farfajiya ce da aka k'awata da furanni masu kyau da k'amshi da kujerun zama sai tebur dake tsakiyar kujerun.
"WOW so beautiful". Tace cikin murmushi tareda cirar flower daga jikin wata bishiya takai hancinta ta shak'i k'amshinta ta lumshe ido tana sakin ajiyar zuciya ta bud'e idon tana cigaba da kallon shuke shuken wajen tana murmushi a fili tace
"Yanzu dama akwai wannan wajen shine wannan d'an black stomach d'in bai tab'a fad'amin ba? Ya barni da kewa idan Mamie da Imaan basa nan, zamu gamu dashine wllhy".(kunji fa mutuniyar wai zasu gamu dashi).
Sosai gurin yayi mata dad'i musamman dayake iskar safiya na kad'awa data had'u data weather d'in sanyi daya fara shigowa kwanannan.
Selfie ta shiga yi style kala kala saidata gaji dan kanta sannan ta zauna tana kallon pictures d'in data d'add'auka tana murmushi, Kamar ance d'ago kanki ta k'ara hango wata k'ofa dai again daga gefenta wadda bata kula da itaba tym d'in data shigo wajen.
"Can kuma ko meye?, Ta fad'a a fili tareda tashi ta nufi inda k'ofar take, ga mamakinta tana murd'a handle d'in k'ofar saitaga ta bud'e a hankali ta zura kanta ciki nan taga ashe gymnastics room ne ga abubuwan motsa jiki nan kala kala shigewa tayi gaba d'aya tana k'arewa kayan wajen kallo bi da bi wani takai hannu ta tab'a wani kuma ta hangoshi daga nesa dayake room d'in babbane.
A hankali ta fara takawa da shirin barin d'akin
"Stop, come here". Taji amon muryarsa cikin d'akin, Cak ta tsaya a tsorace tana zaro ido mamaki ya kamata,dama wai yana cikin room d'innan? A hankali kamar munafuka ta juya tabi inda sautin maganar tashi ta fito dayake akwai wani babban abu da batasan ko meyeba daya kareshi kuma d'akin ma dai bai cika haskeba yana zaune kan wata kujera dawani k'arfe a hannunshi yana d'agawa. a hankali ta taka ta nufi wajen gefenshi ta tsaya kanta a k'asa tana wasa da wayar hannunta.
Bai kalleta ba kuma bai fasa d'aga k'arfen ba da sauri sauri saidaya mula dan kanshi harta fara gajiya da tsayuwar sannan taji yace
"Meya kawoki nan?". Shiru tayi kawai batayi magana ba.
"Bakya jine?". Ya fad'a yana ajiye k'arfen ya tashi ya tsaya kusa da ita ya rik'e k'ugunshi da hannu d'aya d'ayan kuma ya shiga goge fuskarshi da k'aramin towel d'in daya d'auko kan kujerar daya tashi.
Yana sanye da farin wando 3qtr da red color d'in riga mara hannu sai wata farar hula daya d'ora saman kanshi mai kama data sanyi da tambarin Nike a gaban hular da white slipper sanye a k'afarshi
"Bafa komai, kawai dai na fitone shine naga nan shinefa na shigo". Cikin rarraba kalmomin tayi maganar har lokacin bata kalleshi ba.
"Gulma kikazo nasani ai". Ya fad'a kanshi tsaye. Da sauri ta d'ago ta kalleshi saida gabanta ya fad'i saboda k'irar jikinshi data gani gashi rigar ba hannu cikakkun damtsenshi sun fito sosai da duk wata halitta da ALLAH yayi masa bata tab'a ganinshi a hakaba dan haka duk saitaji wani irin tsoro ya kamata.
K'asa k'asa tace
"Ni bawata gulma danazo yi".
Towel d'in ya jefa kan kujera yana k'ara matsawa daf da ita yana shafa sajenshi yace
"Okay, duk da haka kin kawo kanki definitely yau d'in nan saikin motsa jikinki".
"Kamar ya motsa jiki?" Ta fad'a cikin rashin fahimta tana masa kallon tsoro.
Kanshi ya wani rausayar yana d'an tab'e baki gami da d'age kafad'unshi bai daiyi magana ba.
Idonshi ta faka tayi hanyar fita da gudu tana fad'in
"Ni wllhy bawani motsa jiki da zanyi".
duka taku biyu lafiyayyu yayi ram da ita ta fasa k'ara tana son k'wacewa ya matseta gam a jikinshi a haka ya k'arasa k'ofar ya murza key ya cire ya jefashi cikin aljihun wandonshi, sakinta yayi tareda yimata nuni da hannunshi alamun ta wuce.
Baki ta zumb'ura ta wuce tana tunanin ta yadda zai sata abinda batayi niyyar yiba?.
Wajen wani gym machine ya jawota ita harta wuce gaba ma, da kanshi yayi mata nuni ta hau, kafad'a ta nok'e tana tura baki tace
"ALLAH ni bazan hauba, wai haka akeyi ne kawai kace...... maganarta ta katse lokacin da taji ya sureta ya d'ora kan machine d'in k'ara ta fasa masa tana fad'in
"Please doctor dan ALLAH ka saukeni ALLAH bazan k'ara shigowa ba".
Murmushi ya saki yana cije lips baice komai ba yasa hannu ya kunna machine d'in ya fara gudu da ita, yasamu kujera ya zauna yana kallonta yana murmushin mugunta.
"Wayyo ALLAH Yah Saifu dan ALLAH kazo ka saukeni ALLAH ban tab'a hawaba please kaji, cikin ihu take maganar tana kakkama abun da k'arfi, crossing legs yayi daga zaunen fuskarshi d'auke da murmushi jinshi yake cikin nishad'i da farin ciki.
Saida aka d'auki y'an mintuna sannan ya tashi ya isa wajen har lokacin bata daina ihu ba tana masa magiyar ya sauketa duk ta had'a uban gumi da hawaye shab'e shab'e a fuskar. Hannu yasa yayi off machine d'in ya tsaya cak yana tsayawa kuwa jiri ya kwasheta tayi luuu zata fad'i yayi hanzarin tarota ta fad'a kanshi, cak ya d'auketa ya nufi wata doguwar kujera ya kwantar da ita sai faman kuka take tana saukar da numfashi wani stool ya janyo ya zauna daf da ita ya rank'wafar da kanshi wajen fuskarta ya d'age gira k'asa k'asa yace
"Yaa tsegumi yayi dad'i ko?". Wani kukan ta k'ara fashewa dashi tsakaninta da ALLAH take kukan tana ja masa ALLAH ya isa cikin ranta wllhy mutumin nan mugune ba iya karatun likitanci yayiba maybe saidaya farayi akan mugunta.
"Shut up malama", yace yana sunkuyowa daf da fuskarta har tanajin hucin numfashinshi da k'amshin mouth fresheners d'in bakinshi, idan rashin kunya ne da tsiwa ba wanda yafiki amma ji yadda kika koma daga hawa gym machine village girl kawai".
Shiru tayi sai jan majina datake har lokacin bata gama dawowa normal ba ga kanta dake sara mata itadai tsakaninta dashi saidai sakayyar ALLAH, tashi yayi ya d'auko k'aramin towel d'in dake kan kujera ya dawo ya k'ara zama yakai towel d'in fuskarta da nufin goge mata gumi da hawayen da suka b'ata ta, hannu takai zata amshi towel d'in ya sakar mata harara tare da yimata sign da idonshi alamun ta d'auke hannun nata. Baki ta cuno ta matsar da hannun, a hankali yafara goge mata yana kallon cikin idanunta ya tuno yadda d'azu ta dinga zarosu tana ihu a bazata kawai taga ya saki dariya har fararen teeth d'inshi na bayyana.
"Yaa Rabb! Tace k'asa k'asa a fili tana zaro ido na mamakin dariyar dayayi zata iya rantsewa bata tab'a ganin yayi dariya ba murmushin ma saita k'ure yakeyi to ita duka ma sau nawa taga yayi murmushin tun had'uwarsu? Amma yau dariya yake? Inama ya dinga dariya ya daina had'e fuskar nan daya taimakawa kanshi dan wani irin mugun kyau ya k'ara lokacin dayayi kamar yasan tunanin datake nan da nan ya k'ara d'inke fuskar ya maidata asalin yadda take yace
"Daina kallona". Baki ta tura ta kauda kanta data tuna dalilin dariyar tashi ma tasan muguntar dayayi mata ce itadai bazata yafeba.
"Kuma saina fad'awa Mamie abinda kayimin". Ya tsinkayi muryarta ta fad'a tana turo baki.
"Really?". Yace yana d'age mata gira gamida d'allar bakinta data turo d'in, bakin ta dafe tana b'ata fuska da sonyin kuka
"Kina bud'e min baki Ina cinyeshi". Yace yana mik'ewa tsaye.
"Basai ka cinye d'in ba". Tace k'asa k'asa tana harararshi ta gefen idonta.
"Oya stand up". Yace yana yimata alama da hannunshi na ta mik'e tsaye.
Zaune ta tashi ta gyara rolling d'inta sannan ta mik'e tsaye, tana mik'ewa kuwa jirin ya k'ara kwasarta yayi hanzarin kamata tsaki yaja yace
"Raguwar inace ke wai?" Bata tankashi ba dan haushin shi takeji, k'ugunta ya kamo ya rab'ata gefenshi suka nufi k'ofa.
Tayi zaton ta k'ofar baya zasubi ta inda ta fito saikuma taga sun zagaya sun nufi k'ofar parlor'n Mamie suna zuwa bakin k'ofar ya saketa ALLAH dai ya taimaketa bataji jirin irin na d'azu ba, k'ofar ya tura suka shiga Mamie hisnul Muslim ne a hannunta itakuma Imaan wayace a hannunta, dukansu suka juyo lokacin da suka shiga tuni fuskar Mamie ta washe da fara'a ganin yanayin Ayshaa yasa ta ajiye littafin tana fad'in
"A'ah mamana lafiya kuwa!".
Wajen Mamie ta k'arasa ta zauna kusa da ita tana b'ata fuska kamar zatayi kuka, Imaan ma dawowa tayi kusa da kujerar su Mamien ta zauna duk suka maida hankalinsu kanta, shikam dama tun shigowarsu ya wuce dinning area ya bud'e fridge d'in dake wajen ya d'auko k'aramar robar faro yadawo kusada k'afafun Mamie ya zauna ya bud'e yafara sha.
"Kinyi shiru mamana fad'amin abinda yake damunki mana ko Abbana ne?". Kai ta d'aga tana share k'wallah.
"Meyayi miki?". Mamie ta tambayeta.
"Mamie kan gym machine ya d'orani har yanzu jiri nakeji". Dariya Imaan ta fashe da ita Mamie ta jefa mata harara, saita k'unshe bakinta tana murmushi, ALLAH Aunt Ayshaa tabata dariya sosai.
"Meye dalilinka na d'orata?" Mamie ta tambaya fuskarta ba fara'a.
Robar ruwan dake bakinshi ya sauke yace
"Mamie training nefa ta motsa jikine".
"Gidanku kaida motsa jikin, ALLAH ka kiyayeni fa banason mugunta". Ta k'arasa maganar tana sakin k'wafa gamida juyawa wajen Ayshaa tace
"I'm sorry mamana kinji k'yaleshi saina b'ata masa rai". Kai ta d'aga mata.
Murmushi Mamie tayi tace
"Yawwa d'iyar albarka kwanta ki huta kinji", tashi tayi ta gyara mata pillow'n dake kan kujerar ta kwanta, ganin irin kallon da Mamie take masa yasa ya d'anyi murmushi yana shafa kanshi yace
"Yanzu Mamie nayi laifi kenan?".
"Babba ma kuwa, kuma ka k'ara gwadawa kaga yadda zan sab'a maka, Ina aka tab'a haka saboda ALLAH? Kai dakaga zaka iya sai kaitayi ka k'yaleta ko ana dolene".
Bai daice komaiba yatashi yabar wajen.
Yana barin wajen Imaan ta shek'e da dariya Ayshaa ta maka mata harara Mamien ma dak'uwa tayi mata d'auki pillow ta jefa mata, da gudu ta tashi ta bar wajen tana cigaba da dariyar ta.
Hira Mamie ta d'an dinga janta da ita, ba'a dad'e sosai ba ya k'ara fitowa tsaf cikin shirinshi na manyan kaya, plain yadine lallausa ruwan zuma da kad'an rigar ta wuce masa gwiwa bak'in takalmi yasa da bak'in agogon daya d'aura wanda ya haska farar fatarshi, sallama yayiwa Mamie yace zaije wajen Mukhtar tayi masa ALLAH ya kiyaye Ayshaa kuwa idon Mamie ta faka ta murgud'a masa baki, kanshi ya kad'a tareda yimata alamun zai kamata ne daga nan ya fice daga parlor'n fuskarshi d'auke da murmushi, haka nan idan ya tuna yadda ta dingayi d'azun da tsoratar datayi saiyayi murmushi ko a bathroom ma yana wanka yana murmushi tayi matuk'ar bashi dariya kam d'azu.
Ranar nan ta yini wajen Mamie suna hira sai yamma ta koma part d'inta har lokacin kuma bai dawo gidan ba.
★★★
Two days after.
Su safnah sunyi shirinsu tsaf na zuwa wajen boka dake can jihar Delta, k'arya tayiwa Momy da cewa daga wajen aikinsu ne aka turasu.
Sai yamma lik'is sannan suka isa dayake bokan bama cikin garin Deltan yakeba can wani k'auyene hakan yasa suka k'ara mik'ar wata hanyar da zata sadasu da inda yake......
Toh gadai su safnah a hanyar zuwa wajen boka, ko asirin zaici?.
❤️Jummah Kareem❤️
Mrs Salees Mu'az ❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu
(Ummee).
[8/29, 13:19] UmmAsghar: Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
*DR. SAIF*
Writer: Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No.32.
Can wani mugun k'auyene inda bokan yake mota bata shiga hanyar saidai mashin kuma shima akwai iya inda yake tsayawa saidai mutum ya k'arasa a k'afa, bayan saukarsu a mashinan suka fara takawa a k'afa saida sukayi tafiya mai nisa sannan suka k'arasa inda yake can kan wani dutse da k'yar suka hau dutsen suna faman haki da nishi mutane ne birjik saman dutsen masu jiran layi nan suma sukabi sahun masu jira.
(ALLAH ubangiji ka k'ara tsare mana imaninmu da zuciyarmu).
Saida suka dad'e sosai kafin layi yazo kansu, suka shiga cikin bukkar dayake, k'ato ne bak'ikk'irin dashi yana zaune saman fatar damisa wani d'an bante ne kawai a jikinshi sai tarin guraye da layoyi dake ko Ina na jikin nashi ga kayan tsubbace tsubbacenshi nan a ko Ina na d'akin.
Gabanshi suka zube sukayi gurfane suna mik'a gaisuwa, da kallo kawai ya dinga binsu da jajayen idanunshi masu ban tsoro, safnah duk a tsorace take sai rawar jiki take kasancewar wannan shine zuwanta na farko gurin sab'anin Mansurah da dama gurin zuwan tane.
Nuni yayi musu da hannu alamun su zauna sosai, nan suka zauna Mansurah ta bud'e baki zata fara bayani ya daka mata wata irin tsawar data firgitasu gaba d'ayansu cikin k'atuwar muryarshi da amonta ba dad'i yace
"Karki k'ara gigin fad'a mana abinda yake tafe daku, tuni an riga an sanar mana da zuwanku da kuma abinda ya kawoku dan haka zab'i kawai zaku bayar na abinda kukeso ayi mata". Ya ida maganar yana shek'ewa da wata mahaukaciyar dariyar dakkan wajen saidaya amsa.
Kallon juna Mansurah da safnah sukayi, kafin Mansurah tace
"Toh safnah ki fad'i abinda za'ayi mata shawara takice yanzu".
Cikin rawar murya safnah tace
"Boka sonake a nakasta ta a maida ita tsakanin mutuwa da rayuwa ta yadda bazata amfani rayuwar taba ya zamana komi sai anyi ma......."dakata, ya dakatar da ita da k'arfi yana d'aga mata hannu, zabura tayi tayi shirun tana zazzare Ido.
"Mun san mezaki fad'a b'ukatarki zata biya".
"Godiya muke boka". Mansurah ta fad'a tana d'an risinawa daga zaunen.
Mak'udan kud'ad'e masu yawa suka aje masa sannan suka tashi zasu fito Mansurah dayake tasan takan sharad'in fitar da baya baya tafara tafiya ganin hakan yasa itama safnahr ta shiga tafiya da bayan har suka fito. Da k'yar suka samu mashinan da suka fitar dasu zuwa cikin gari dan dare yayi lokacin daga nan suka kama wani lodge suka kwana, da sassafe Mansurah tacewa safnah tayi mantuwa itama akwai aikin dazai mata dan haka zata koma wajenshi haushi taba safnah ta shiga yimata masifar dan meyasa jiyan bata fad'a ba sai yanzu da suka riga suka baro wajen itakam saidai ts jirata anan taje tadawo, bata damuba dan dama bata b'ukatar safnah a wajen, haka tabar safnah a lodge d'in ta tafi sai wajen azahar sannan tadawo suka kamo hanya kowanne zuciyarshi cikeda farin ciki da fatan cikar burikansu.
★★★. ★★★. ★★★.
After three days.
Tunda garin ALLAH ya waye Ayshaa take jinta ba daidai ba ita kanta bazata iya tantance abinda ke damuntaba kawai dai taji jikinta ba k'arfi ga yawan fad'uwar gaba datake sai tashiga maimaita kalmar innalillahi cikin ranta. Gyaran data saba yiwa part d'in tayi jikinta duk a sanyaye sannan tayi wanka ta shiga kitchen ta had'a breakfast, kad'an ta iya ci ma tabarshi.
Tadawo nan cikin parlor'n ta kwanta, data ga nan d'in bazai mataba ta tashi ta koma bedroom tana shirin hawa kan bed ta hango motar Saif datake ganin yana yawan fita da ita a cikin compound ta labulen d'akin dayake net curtains ne saita fasa hawa gadon taje bakin window'n ta tsaya tareda yaye labulen a fili tace 'Yau Mr arrogant yana gida kenan? To mai zaisa hakan bayan ba weekend bane, d'an zaman nan dasukayi ta fahimci mutum ne shi mai k'wazon aiki garin ALLAH yana wayewa yake fita sam baya wasa da aikinshi duk da ba ganinshi take ba saidai taji tashin motarshi to yau kuma ko me ya hanashi fita, ko kuma da wata motar daban ya fitane? Baki kawai ta tab'e tana ganin meye na wani damun kanta da tunanin abinda yake faruwa.
Bed d'in takoma ta kwanta saidai duk yadda taso kawar da tunaninshi cikin ranta hakan ya gagara ta rasa meke damunta haka, kasa kwanciyar tayi ta tashi ta saka k'aramin hijab mai hannu kan riga da siket d'in dake jikinta na atamfa ta fita ta nufi bedroom d'inshi gabanta na fad'uwa da tunanin yanzu idan tasamu bai fitaba ya rutsata da tambayar ba'asin abinda ya kawota me zatace masa? Koma dai meye zataje, dan haka nan takejin tamkar ana janta zuwa d'akin ne.
Tayi sa'a tana murd'a handle d'in k'ofar ya bud'e a hankali ta zura kanta ciki kafin gangar jikinta tabi baya, dund'um d'akin yake fitilu duk a kashe sannan curtains d'in d'akin duk an sassakesu kuma masu duhune hakan yasa ba'a ganin komi.
Makunni ta laluba da hannunta ta kunna k'wayayen d'akin ta juya ta kalli inda bed yake abinda ta ganine yayi matuk'ar girgizata tareda fad'uwar gaba mai tsanani, a hankali ta shiga tunkararshi tana nunashi da yatsanta bakinta na rawa ta gaza furta ko kalma d'ayane saboda yadda bakin nata yayi mugun nauyi, a haka harta k'arasa bakin gadon ta durk'ushe k'asa tana kallonshi, Saif ne kwance samb'el dashi ba inda yake motsi a jikinshi ta kalli idanunshi da hawaye ke kwaranyowa ga wasu duk a bushe ga dukkan alamu ya dad'e yana kukan sama kawai yake kallo hawaye na zuba har suna shiga cikin kunnuwanshi.
"Innalillahi wa Inna ilaihi rajioun, hasbunallahu wa ni'imal wakeel, ta fad'a cikin rawar murya yayin da idanunta suka cika da ruwan hawaye.
"Yah Saifu lafiya kake kuwa meya faru kake kuka me ya faru dakai?".
Ba magana sai hawayenshi dasuka k'ara yawa, maganar ma babu kenan? Wani irin kuka ta saki mai tsuma zuciyar mai sauraro ta kife kanta gefenshi tareda kamo hannayenshi ta d'ora bisa fuskarta tana shasshek'a cikin kukan take fad'in
"Yah Saifu meya faru dakai please kayimin magana mana dan ALLAH kace wani abu Yah Saifu please". Ta ida maganar tana k'ara fashewa da wani irin kuka, kuka take sosai tana rik'e da hannunshi gaba d'aya kanta ya kulle ta rasa abinda ma zatayi masa ko meye ma ya faru dashi da daddare ne dan jiya tana d'aki taji shigowarshi.
Sai daga baya dabarar kiran Mamie yazo mata dan ta tabbatar yanzu ta fita asibiti, da hanzari ta tashi ta fita daga bedroom d'in jikinta har rawa yake, ta shiga nata bedroom d'in ta lalubi wayarta dake kan bed ta fara neman number Mamie da k'yar ta nemo number saboda tsabar rud'ewa datayi tayi calling har tagama ringing ta katse ba'a d'aga ba tana shirin k'ara wani kiran, Kiran Mamie ya shigo da sauri tayi picking ta kara a kunnenta batayi magana ba sai kuka data fashe dashi tana toshe bakinta nan da nan hankalin Mamie ya tashi ta shiga tambayar ta lafiya meyake faruwa ne kasa magana tayi sai kukan data cigaba dayi, hakan ya k'ara tada hankalin Mamie ta shiga lallashinta kan ta fad'a mata meyake faruwa da ita,da k'yar cikin kuka tace
"Mamie kizo dan ALLAH Yah Saifu ne".
Cikin fad'uwar gaba Mamie tace
"Mamana me baban nawa yayi miki?".
Cikin kuka tace
"Kizo kawai Mamie muna b'ukatarki Mamie kizo dan ALLAH". Ta k'arasa maganar tana k'ara fashewa da kuka gamida katse wayar batareda ta jira jin abinda Mamien take fad'a ba.
D'akin ta k'ara komawa tana addu'ar ALLAH yasa ta sameshi ya tashi saidai tana shiga ta ganshi yadda ta barshi, jingina tayi da bango tana kallonshi ta d'aga kanta sama hawaye na tsiyaya ta rasa ta yadda zata fassara wannan al'amarin mai kama da almara. Komawa tayi bakin gadon ta durk'usa tareda kamo hannunshi har yanzu hawayen fuskar ta sunk'i tsayawa.
Mamie kam ikon ALLAH ne kawai ya kawota gidan lafiya saboda yadda hankalinta yayi matuk'ar tashi tanaji a jikinta wani gagarimin al'amari ne mai girma daya faru.
Kai tsaye part d'insu tawuce harta nufi bedroom d'in Ayshaa taji kamar sautin kuka daga bedroom d'in Saif dan haka ta nufi can d'in da sauri k'ofar ma a bud'e take dan haka ta kutsa kai ciki.
Ayshaa najin shigowarta ta tashi da gudu ta k'arasa wajen Mamie ta rungumeta tana k'ara sakin wani kukan itama Mamien rungumota tayi sosai jikinta tana fad'in
"Mamana meyake faruwa ne fad'amin mana".
Gadon da Saif ke kwance ta nuna mata tana fad'in
"Mamie Yah Saifu ne kije ki ganshi kiga halin dayake ciki....cikin sassarfa Mamie ta k'arasa gaban gadon Ayshaa tabi bayanta birki taci tana k'are masa kallo kafin a hankali cikin rawar jiki ta k'arasa gaban gadon ta rank'wafa kanshi tareda kai hannu ta dafa goshinshi cikin rawar murya tace
"Abbana". Idanu kawai ya zuba mata wasu sabbin hawayen suna kwaranyowa.
"Mamie baya motsi baya magana, dan ALLAH Mamie kice yatashi kice yayi magana Mamie". Ayshaa tayi maganar cikin matsanancin kuka.
Mamie da taji kanta yayi mugun sarawa jiri na neman d'ibanta tayi hanzarin zama bakin gadon Ayshaa ta k'arasa gabanta ta durk'usa tana kamo hannunta.
"Tun yaushe hakan mamana?". Mamie ta tambaya idanunta fal k'wallah.
"Koma meye Mamie cikin dare ya sameshi,danaji banji fitarshi ba shine na lek'o naganshi cikin wannan yanayin".
Kai Mamie ta dafe tana ambatar
"Innalillahi wa Inna ilaihi rajioun, Allahumma ajirni min musibati wa aklifni khairan minha".
Juyawa tayi wajen Saif ta kamo hannunshi tace
"Babana meya faru dakai haka kayi mana magana please", hawaye suka zubo mata shima hawayen nashi ne suka k'ara yawa jinshi yake tamkar bashiba tun cikin barci yake jinshi wani iri baya iya motsi bai k'ara tabbatar da hakan ba saida aka kira sallahr asubah yazo tashi yaji ko Ina na jikinshi ba inda yake motsi kamar an d'aure duk wata jijiya ta jikinshi ne hankalinshi yayi matuk'ar tashi duk wani k'ok'arin dayayi ganin ya tashi a banza ko d'an yatsanshi bai iya d'agawa ba tun lokacin yake hawaye tareda karanto duk addu'ar datazo bakinshi.
Number Daddy Mamie ta nema wanda yau two days da dawowarshi gidan, bayan ya d'aga tace yazo gida akwai matsala, daga nan ta kira Mukhtar shima ta fad'a masa yazo gida akwai abinda yake faruwa da abokinshi, nan suka zauna kusa dashi suna kallonshi Ayshaa har lokacin kuka take Mamie kam idon ya bushe wani tashin hankalin yafi gaban ayi masa kuka, wani lokacin ma kukan rahma ne ga mutum so take tayi kukan amma ta kasa sai zuciyarta dake mata wani irin zafi.
Hankali tashe Daddy da Mukhtar kowanne ya nufo gidan kusan tare suka iso dan motar Daddy na shigowa ko rufe gate d'in maigadi baiyiba motar Mukhtar ta danno kai, shi kanshi maigadin gabanshi fad'uwa yake yana tunanin akwai muhimmin abu dayake faruwa a gidan koma meye ba mai dad'i bane ganin yadda Mamie ta shigo da motarta a firgice ko parking d'in kirki batayi ba ta fito ta nufi cikin gidan da sauri yanzu ga maigidan da Mukhtar suma sun shigo kuma daga ganinsu hankalinsu tashe yake.
Sunayin parking kowa ya fito daga motarshi sai a lokacin Daddy yaga Mukhtar tare suka jera suka shiga cikin gidan Mukhtar yana fad'awa Daddy Mamie ceta kirashi yazo wani abu yafaru da Saifu, Daddyn yace shima haka su shiga dai koma meye zasu gani.
Afwan reader's zan fitane kuyi hakuri da kad'an .
Mrs Salees Mu'az ❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu
(Ummee).
[8/31, 17:09] UmmAsghar: Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
*DR. SAIF*
Writer: Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No.33.
Ba k'aramin girgizasu al'amarin yayiba lokacin da suka shiga hankalinsu yayi bala'in tashi sukayi tsaye kanshi kowanne zuciyarshi rawa take, Daddy kanshi ya dafe tareda runtse Ido saboda yadda kan nashi yayi mugun sarawa. Mukhtar kam duk yadda yaso yayi jarumta yazama namiji hakan ya gagara dan zubewa yayi gaban gadon tareda kamo hannayen Saif ya d'ora kan fuskarshi yana fashewa da wani irin kuka mai ban tausayi, shima Saif d'in ganin Mukhtar yasa hawayen dayake k'aruwa Mamie kam ta kasa magana tana zaune kawai ta k'urawa waje d'aya Ido sai ajiyar zuciya take saki, Ayshaa har lokacin kuka take ta jingina da jikin mirror kanta a k'asa.
A hankali Daddy da shima k'arfin haline yake ya d'ago Mukhtar yana fad'in
"I'm sorry Mukhtar be a man mana, insha ALLAHU zai tashi yanzu hospital yakamata muje duk wannan koke koken bashi bane".
Cikin zubar hawaye Mukhtar yace
"Daddy kana kallon halin dayake ciki fa kalleshi fa kagani ba inda yake motsi a jikinshi me hakan yake nufi".
Kai Daddy ya girgiza cikin rawar murya yace
"Insha ALLAH zai tashi bari muje asibiti".
Wajenshi Mukhtar ya koma ya durk'usa a bakin bed d'in cikin kuka yace
"Ka kwantar da hankalinka abokina, da yardar ALLAH zaka mik'e ka taka da k'afafunka kamar yadda kake ada, zakayi magana da bakinka tamkar yadda kake ada". Saiya kife kanshi kusada Saif d'in, jiyake tamkar zuciyarshi zata fasa k'irjinshi ta fito tsabar yadda take masa zafi.
Ganin basai an canza masa kayaba yasa Daddy fara k'ok'arin d'aukarshi Mukhtar ya dakatar dashi, shi kad'ai ya d'aukeshi saboda shima Mukhtar d'in ALLAH yayi masa halittar k'arfi kusan zubinsu d'aya da Saif dan yafi Saif jiki ma. Haka ya d'aukeshi ya fita dashi sukabi bayanshi a motarshi yasashi a back seat Ayshaa ta shiga gaban motar suka fita, Mamie da Daddy kuma suka shiga motar Daddyn suka rufa musu baya, maigadi kanshi hankalinshi saida ya tashi lokacin dayaga anfito da Saif cikin wannan hali, har k'wallah saida yayi yana tunanin rayuwar nan mai cikeda k'alubale masu tarin yawa da yadda d'an Adam yake ba'a bakin komiba.
Kai tsaye hospital d'in Saif suka nufa dashi, ba k'aramin tashin hankali ma'aikatan asibitin suka shiga ba dama sauran masu jinya cikin asibitin a yadda sukaga an shigo da mai asibitin da yadda ya koma, wani special room aka shiga dashi Dr Sooraj, Dr Kabeer da Dr Mahmoud sune manyan doctor's d'in da ake jidasu bayan Saif d'in su suka rufu kanshi da gwaje gwaje dan gano inda matsalar take. Kowa kagani cikin asibitin jikinshi a sanyaye yake kuma kowa mamakin wannan al'amarin yake na tafar d'aya dan kowa yasan Saif lafiyar shi k'alau bashida wata matsala kuma, ko jiya ya dad'e yana duba patients dan harya wuce lokacin tashinshi aiki. saidai al'amarin ubangiji yafi gaban haka kowa addu'a yake masa ta samun sauk'i gurin ubangiji ALLAH.
Su Mamie ma na nan zaune suna jiran fitowar su, kowa ka kalli Idonshi zaka hangi tsantsar tashin hankali da rashin kwanciyar hankali, Ayshaa tayi wani zuru zuru idanun nan sunyi jawur saboda kukan datake sha duk rarrashinta da Mamie keyi a banza tak'i yin shiru kawai tuno d'an zaman nan da sukayi na kwanaki take.
Cikin k'warewa da sanin makamar aiki likitocin suka duk'ufa kanshi da aune aune dan gano abinda ya haddasa matsalar saidai kuma abinfa ya gagara dan duk wasu gwaje gwajensu ya nuna Saif bashida wata matsala a cikin k'ashinsa da jijiyoyinsa abin yayi matuk'ar d'aure musu kai da basu mamaki.
Kusan awa biyu da rabi suka d'auka a kanshi kafin suka fito, yanata bacci saboda allurar bacci da akayi masa.
A matuk'ar sanyaye suka fito daga room d'in kowanne idonshi ya kad'a yayi ja. Cikin hanzari su Daddy suka taresu dan son jin k'arin bayani daga gurinsu.
Office d'in Saif aka bud'e saboda yafi kowanne girma, nan suka shiga suka zazzauna tunda babu wani bare a cikinsu, Dr Mahmood kuwa bai iya zama ba dan mutum ne shi mai raunin zuciya fita yayi ya koma nashi office d'in cikin jimami, ya rage daga Dr Sooraj sai Dr Kabeer, bayan kowa ya zauna Dr Sooraj ya fara bayani cikin sanyin murya da fad'in
"Munyi iya k'ok'arinmu mugano daga inda matsalar take dan musan irin taimakon dazamu bashi saidai kuma komai yana nuna mana normal Dr bashida wata matsala a dukkan jikinshi".
"Innalillahi wa Inna ilaihi rajioun". Mamie da Daddy suka had'a baki wajen fad'a, Mukhtar hannu yasa ya d'auke k'wallahr data taho masa, wai Saifunshi ne a haka?, Ayshaa ma hijabinta tasa ta rufe idanunta tana hawaye.
Handkerchief Dr Mahmood yasa ya share fuskarsa kafin yace
"Amm....dan ALLAH Daddy ku kwantar da hankalinku Insha ALLAH Doctor zai tashi akwai abokin aikinmu Dr Habeeb masani ne akan irin wannan matsalar, shima yanada asibitin shi nashi na k'ashin kanshi a yanzu haka dai baya k'asar yana Cyprus yaje wani aiki munasa ran dawowarshi nanda two days masu zuwa insha ALLAHU za'a samu waraka bi'iznillah ta'ala". Duk sunji dad'in bayanin Dr Kabeer, nan likitocin suka shiga k'ara kwantar musu da hankali da basu tabbacin za'a samu sauk'i insha ALLAH.
Imaan dabatan abinda yake faruwa ba, kasancewar tana skull saidata dawone take samun labari gurin maigadi da shima har lokacin hankalinshi yak'i kwanciya.
Cikin tashin hankali tana kuka tasa driver ya kaita asibitin,sai ganinta sukayi kawai, rungume juna sukayi da Ayshaa suka saki wani sabon kukan da k'yar Mamie ta rarrashesu sukayi shiru. Ba jimawa asibitin yafara cika da y'an uwa na kusa Hajjah ma tazo da Aunt Aisha, kowa yaji abinda yasamu Saif saiya tausaya masa kowa kagani cikin alhini da rashin nutsuwa. Har yamma suna nan saidai suyi sallah sudawo ko takan abinda zasu saka a cikinsu ba wanda yabi to inama hankalin ya kwanta?.
Hajiyar Mukhtar cema data tashi zuwa tayi abinci ta taho dashi duk yadda Mamie ta matsawa su Ayshaa da Imaan kan suci abincin ko kad'an ne hakan ya gagara fur sukace sun k'oshi dole ta k'yalesu dan data matsa ma Ayshaan saita fashe da kuka dama da k'yar aka samu tayi shirun zuciyar a kusa take. Ba wanda ya k'ara ganinshi tun lokacin da aka kawoshi.
Bayan sallahr Esha'e aka maida Hajjah gida hajiyan Mukhtar ma ta tafi Aunt Aisha ma mijinta yazo yayiwa su Mamie ya jiki sannan suka wuce tare.
Mamie tace Ayshaa da Imaan sutafi gida ita zata kwana dashi, da k'yar da k'yar Ayshaa ta amince dan da farko cewa tayi ba inda zata it's zata kwana dashi saida Daddy yasa baki sannan Mukhtar ya tafi dasu zai ajiyesu a gida. Dukansu tausayin Ayshaa suke k'asan ransu kuma mamakine fal saboda sun san dai ba soyayya a tsakaninta da Saif amma dubi yadda ta nuna tsantsar damuwarta da alhinin halin dayake ciki, tuni soyayyarta ta k'ara nunkuwa cikin zuciyoyinsu gamida k'ara samun babban matsayi a gurinsu. Koda suka koma gidan ma kukan suka d'ora daga inda suka tsaya bamai rarrashin wani haka suka kwana ba barci safiya nayi kuwa suka nufo asibitin.
Allurar tanada mugun k'arfi hakan yasa sam bai farkaba a ranar sai washegari, lokacin su Dr Sooraj suna d'akin tunda ya farka yake hawaye ba bakin magana jinshi yake duk a d'add'aure yarasa meya faru dashi haka duk yadda yaso fassara al'amarin ya kasa. Su suka dinga bashi baki kafin Mamie tazo ta d'ora da nata.
Su Ayshaa ma dasukazo da Imaan suka shiga d'akin Ido kawai ya zuba mata yanaso yayi magana ba dama, alamun hakan data ganine yasa zuciyarta karyewa,taso rik'e kukan daya taho mata amma ta kasa ficewa tayi da sauri tana toshe bakinta. Kai kawai Mamie ta girgiza itama k'wallah ta cika mata Ido tausayi yarinyar take bata wllhy.
A gurguje please.
Bayan kwana biyu Dr Habeeb ya sauka a k'asar 9ja, batare da wani jinkiri ba aka maida Saif asibitin shi, shima d'in dai ya jinjina al'amarin zuciyarshi tayi rawa ya k'ara tsorata da lamarin duniyar nan wai yau doctor Saifullahi Sadeeq Matawalle ne kwance haka ko d'an yatsanshi baya iya motsawa? Abin akwai ban tsoro da al'ajabi.
Shima dai Dr Habeeb d'in duk iya bincikenshi da wasu aune aunenshi baisamu abinda yakeso ba dan duk results d'aya yake nunawa da gwaje gwajen su Dr Sooraj abin yayi masifar d'aure musu kai saboda duk wani gwaji da sukayi saiya nuna musu komi normal komai yake kuma dole sai sunsan daga inda matsalar take kafin sufara masa abinda ya dace dan haka Dr Habeeb yayi magana da Daddy kan gara a fita dashi kawai zaiyi musu hanyar wani babban hospital dake k'asar Spain idan da rabo sai a warke da iznin ALLAH. Kullum cikin barci yake saboda irin alluran da ake masa na bacci saboda halin dayake shiga idan idanunshi biyu.
Afwan da kad'an .
Mrs Salees Mu'az ❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu
(Ummee).
*Mg's skin care*
Hi sister's
Nasan kunsan da labarin mg's skincare toh kusaurara dakyau
Kaman yanda kukasani sunada sabulun gyaranjiki fitacce Kuma ingantacce Wanda yake mayarda tsohuwa yarinyasanin kankune dukme wani matsalan fata walau pimples,black spot,black head, acne,sunburn,tattarewan fata dama sauran tsaiko/matsalan fata daya ke dmn fata yahana mata rawan gaban hantsi nasan kunsan cewa iya mg's herbal whitening black soap yawadaceku zaikawar da dukkan wadannan dama sauran matsalolin gamasu nankarwa ( stretch mark)duk wnd yy using mg's yasan yanarageshi sosai regular use of it ma zainemeshine yarasa Kuma wani abinma koda mutum bashida komai zaiyi anfani da sabulun inda zaikara gogema mutum fata yasa fatar tayi fresh kuzama kalar hutu jikinku yayi smooth kuyita kyalli kamar saban madubi jikinku zedinga glowing fiye da tsammaninku toh hajiyata mekike jirane♀️ kinsan fa mata da gyara akasanmu Kuma duk kyanka akace kakara da wanka bama cika Baki duk wnd yajaraba mg's zaitabbatar da kanshi cewa nadabannekoda yaushe mg's sai sanbarka inamai sanardaku kuzo ayidaku Kar abarku abaya domin duk macen da ta amsa sunanta da anganta zaa tabbatar da hakankugarzayo adama daku mg's akoda yaushe burinsu shine fatarku tayi fresh luwai luwai tazama wanke hannu ataba
Maiso should chat
08062991549
Call 08064532391
Sannan albishirinku ayanzu akwai complete set nagyaranjiki Wanda baa magana wnd yajarabane kadai zaigane zancen soap kadai yy wadancan aikin inakuma ga set☺️ hohoho kunsan abun nayine maza maiso yarugo aguje yy placing ordernshi via 08062991549
Call 08064532391
Note:soap akwaisu available buh for the set zezama available within 2weeks insha Allah gawanda baida halin siyan set soap din yawadatarba tsaurarawa amare Kuna inaaa kunsan da kyn mg's Baku bukatar wani gyaranjiki Dan ynd fatanku zemurje dawuya ango zaigane amarya just gv it a try nd ur skin will definitely nd forever thank you
Note:pls kayanmu bn bleaching bn organic ne basa bleaching zaifiddo ma mutum da ainihin natural beauty dinshine living the skin so lovely
Soap price:3k
For the set:13k
What are you guys waiting forhurry nd grb urs DNT be left behind
We can't wait to be part of ur beauty story❤️
[9/1, 17:16] UmmAsghar: Haske writer's association
Home of expert & perfect writer's.
*DR SAIF*
Writer: Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No.34.
Hankalin Safnah yayi mugun tashi lokacin da labarin abinda yasamu Saif yaje musu, tunanin taya reshe ya juye da mujiya take tarasa ta yadda zata fassara wannan rikitaccen al'amarin itadai tasan sunan Ayshaa suka kai wajen boka amma ya akai abin ya koma kan Saif? Tambayar data dinga nanatawa kenan cikin ranta tana hawaye. Ba shiri ta d'auki key d'in motarta ta wuce gidan Mansurah dan fad'a mata yadda abin ya kasance.
A parlor ta sameta zaune kan kujera tana kallo da waya kuma a hannunta tana chatting,sai juice dake cike cikin glass cup tana korawa, kusa da ita ta zube tana kuka sosai, murmushi Mansurah tayi tana ajiye cup d'in a k'aramin center table d'in gabanta ko bata fad'a bata fad'a ba tasan dalilin kukan nata kuma tayi alk'awarin bazata rufe mata komiba zata fad'a mata gaskiya koma meye zai faru saidai ya faru.
"Wai k'awata lafiyarki kuwa kin shigo kinata koke koke what wrong with you ehmm?".
Hannunta ta kamo cikin kuka tace
"Na shiga uku Mansurah aikin da aka yiwa Ayshaa bai kamata ba kan Yah Saifu ya fad'a d'azu akayiwa Momy waya ake fad'a mata yana can ko motsa d'an yatsanshi baya iyayi why Mansurah meyasa hakan tafaru?".
"Nice sila". Ta amsa mata kai tsaye tana wani k'ank'ance ido cikin tsabar rashin Imani.
Da sauri Safnah tasaki hannunta ta d'an ja baya tana mata kallon tsoro da mamaki ta shiga nunata da hannu bakinta na motsawa alamun magana take son tayi amma ta kasa.
"Yeah nice nan sanadi, ninasa aka maida aikin kan Saif wannan komawar danayi nace za'ayi min aiki akan wani ba kowa bane face Saif".
Tamkar gunki haka Safnah ta kasa motsi ta k'urawa Mansurah Ido cikeda d'imbin mamakin kalaman da suke fitowa daga bakinta ta dad'e tana kallonta kafin tayi k'arfin halin cewa
"Kinsan me kike fad'a kuwa Mansurah?".
Baki ta d'an tab'e tace
"Sanin kanki ne duk iskancina bana shan kayan maye bare kice ba cikin hankalina nakeba".
"Amma meyasa Mansurah? Meyasa zaki aikatawa masoyina haka? Meyayi miki da zafi haka Mansurah daya cancanci irin wannan sakayyar? Why Mansurah why?.... Ta k'arasa maganar cikin k'araji da matsanancin kuka tana cakumo wuyan rigar Mansurah.
Hannu yasa ta fincike rigarta ta mik'e tsaye tace
"Lokacin dazakiji abinda ya had'amu dashi da irin wulak'ancin dayayi min baiyiba ki jira lokaci zakiji komai".
"Muguwa azzaluma, wllhy sai ALLAH ya saka mana wannan cutarwar da kikayi mana shaid'aniya kawai.......musayar yawu suka shiga yi sukai kaca kaca duk da hak'urin da Madeenah k'anwar Mansurahr take basu kamar tiri, da k'yar ta lallab'a Safnah ta fita tana kuka tanajin tamkar zuciyarta zata fashe saboda yadda take mata zafi.
Tana tuk'i tana sharar k'wallah, kawai idan ta tuno irin cin amanar da Mansurah tayi mata ta nakasta mata masoyinta ALLAH ya isanta bazata tab'a yafewa Mansurah ba wllhy, tun kafin aje ko Ina tafara nadamar zuwa wajen boka ita wadda taje ayiwa d'in ALLAH ubangiji ya tsallakar da ita meyasa wai idanunta suka rufe nema ta kasa sanin cewa dama can ALLAH yayi Saif ba mijinta bane? Yanzu gashi garin neman gira anrasa Ido, wata irin nadama ce ta shigeta lokaci d'aya a ranta take rayawa yanzu fa da ace Ayshaan akayiwa takoma hakan duk wani alhaki yana kanta kenan to yanzu ita ya matsayinta kenan meye makomarta?.
Tunda taje gida take kuka, Momy tayita rarrashi da k'yar Safnah tayi shiru ta fad'a mata abinda ya faru, hankalin Hajia Binta yayi matuk'ar tashi fad'a sosai ta shiga yimata ta d'ora dayi mata nasiha mai ratsa jiki sosai jikin Safnah yayi mugun sanyi ta godewa ALLAH daya ganar da ita tunda wuri dama haka abin yake in ALLAH yasoka da rahmarsa saiyayi gaggawar fahimtar dakai abinda kake ba daidaiba kasamu damar dazaka tuba ALLAH yasa mu dace ya ganar damu gaskiya yabamu ikon binta aduk inda take.
Lamarin yayi matuk'ar tsayawa Safnah cikin ranta kwana tayi ba barci kawai tuno yadda Saif yake, idan ta tuna yana can komai sai anyi masa bata sanin lokacin datake fashewa da kuka tana neman gafarar ubangiji (ALLAH kabamu ikon gyara kura kurenmu tun kafin lokaci ya k'ure mana).
★★★★★★★★
Tuni shirye shiryen tafiya yafara kankama Daddy da Mukhtar suke tsaye kan komai, kasancewar abu na manya yasa komi ya kammala cikin lokaci k'ank'ani. Mukhtar kam yazama busy yanzu wajen aikin nashi ma saidai ya lek'a kawai lokacin da tafiyar tazo kuwa takarda ya rubuta ta neman hutu dan yayi alk'awarin k'afarshi k'afar Saif bazai taho ya barshi a can ba saiyaga abinda hali yayi.
Duk wanda yazo duba Saif saiyayi kuka, masu k'arfin haline ma saidai k'wallah ta cika idanunsu kowa yana mamakin rashin lafiyar nan ta Saif kuma duk cikinsu ba wanda yayi tunanin aikin asirine yake d'awainiya dashi ba wanda yakawo hakan. Su Abba da Ammi ma sunzo dubashi, a ranar suka juya cike da tausayin sirikin nasu da addu'ar samun lafiya gareshi.
Mamie, Daddy, Hajjah, Mukhtar, Ayshaa da Imaan saikuma marar lafiyar, gaba d'aya aka d'unguma zuwa k'asar Spain da fatan ALLAH ya bada sa'ar abinda akaje nema.
Kwanansu d'aya Daddy da Mukhtar suka samu ganawa da babban likitan asibitin,suka bashi kuma results d'in duk wasu gwaje gwajen da akayi acan 9ja ya duba yace suma zasuyi nasu aune aunen.
Babban hospital ne, daya amsa sunansa ya kuma k'ware kan duba marasa lafiya irin Saif.
Hankalinsu Daddy yayi matuk'ar tashi lokacin da likitocin suka gama gwaje gwajensu da d'auke d'auke hotunansu sukace basu ga komaiba, komai na jikinshi lafiya yake nunawa, amma zasu sanyashi cikin wani glass za'a jona masa wasu injina na tsawon wata biyu idan har bai tashiba tofa saidai ayi hak'uri dan haka zai k'are rayuwar shi dan indai sukasa mutum cikin injin nan bai tashiba to saidai ayi hak'uri, wannan bayani ba k'aramin dugunzuma hankulan wannan ahali yayiba amma ba yadda suka iya da hukuncin ubangiji duk abinda ya sameshi da saninshi kuma gareshi zasu mik'a kukansu suna masu sakankancewa da tawassuli da sunayenshi tsarkaka ya biya musu b'ukatarsu.
Kwana biyu da zuwansu aka shigar da Saif cikin inda sukace zasu sashi, su Mamie suka bishi da addu'o'en samun waraka.
Washegari su Mamie da Daddy da Imaan suka baro k'asar Mukhtar da Hajjah zasu zauna dashi sai Ayshaa da aka kad'a aka raya tace ba inda zata zata zauna tareda su Hajjah dolensu suka barta d'in su suka tafi.
Koda suka dawo d'in kullum cikin addu'a suke da rok'on ALLAH ya bashi lapia kullum sai anyi sadaqa wa mabuk'ata da almajirai da masu neman taimako.
Daga b'angaren Saif likitocin suna iya bakin k'ok'arin su wajen kula dashi, tunda aka shiga dashi d'akin ba wanda ya sake ganinshi saboda ba'a shiga iya doctor's d'in ne kawai ke shiga, saidai idan sunzo su lek'a su ganshi ta jikin glass d'in d'akin. Ayshaa gaba d'aya ta canza tazama so silent ta rame saboda rashin cin abinci da kwanciyar hankali batada aiki sai kuka dan ma Hajjah tsaye take kanta kullum cikin rarrashinta take tana k'ara kwantar mata da hankali da nuna mata Saif addu'a yake b'ukata yanzu hakan yasa ta dage da k'iyamullayl da karatun Alqur'ani mai girma tana fad'awa ALLAH b'ukatunta akoda yaushe.
@@@@@@@@
Safnah tunda abin nan yafaru batada kwanciyar hankali da nutsuwa gani take duk itace sanadin shigar Saif cikin wannan halin ta maida hankali sosai kan neman gafarar ALLAH yanzu duk tayi sanyi, tsanar Mansurah cikeda zuciyarta tana dana sanin k'awance da ita da biye mata d'in datayi harta rinjayeta sukaje wajen boka. Tana fatan ALLAH ya karb'i tubanta yasa wannan shine na farko kuma na k'arshe.
@@@@@@@@@
Kwanaki sunata tafiya yayin da rayuwar take ta k'ara gangarawa da dad'i ba dad'i, Saif har lokacin yana cikin wannan glass d'in ko iya na'urorin da aka jajjona masa ya ishi mai rai tsoron ALLAH gashi dai a raye amma bambancinsu da matacce kad'an ne. A haka kwanakin da suka d'ibar masa suka kusa k'arewa su Mamie suna yawan zuwa akai akai Mukhtar ma yaje gida sau biyu. Saif yana shan addu'o'e sosai daga bakunan mutane da dama.
Ana gobe za'a cireshi su Mamie suka sauka a k'asar harda Abban Ayshaa.
Washegari da safe duk sun hallara a asibitin jiran sakamako kowa ka kalla zuciyarshi cikeda tararrabi da zullumin yadda zata kasance.
Bayan anyi duk abinda ya dace aka fito dashi daga room d'in kwance kan gadon marasa lafiya sai barcinshi yake cikin wasu riga da wando na yadi farare harda hula itama fara, ta gabansu aka wuce dashi wani d'aki na musamman saiya farka za'a san aikin yayi ko baiyiba.
Har dare bai farkaba ba kuma wanda ya d'ara nan da can a cikinsu kowa burinshi ya farka aga abinda yake ciki, kowa addu'ar fatan nasara yake.
Sai kusan k'arfe 1:00 na dare sannan ya tashi, likitocin dama suna kusa dashi, jikinsu yayi bala'in sanyi ganin bawani cigaba da aka samu yana nan dai a yadda yake bawani canji.
Daga yadda doctor's d'in suka fito daga d'akin yafara sanyayar musu da jikinsu,nan suka nemi ganin wasu daga cikinsu, Daddy da Abba da Mukhtar ne sukabi Dr Mac babban likitan asibitin office d'inshi.
"Innalillahi wa Inna ilaihi rajioun" sune kalmomin da suka dinga tashi a cikin office d'in sakamakon abinda Dr'n ya sanar dasu, cewar bazai tashiba sudai a gurinsu saboda da wuya suyi irin wannan aikin mutum bai tashiba saidai ayi hak'uri amma zasu iya gwada wani hospital d'in idan sunada b'ukatar hakan.
Kallo d'aya su Mamie sukayi musu bayan fitowarsu daga office d'in suka tabbatar da babu nasara koda basuyi magana ba fuskarsu ta nuna hakan,bata nemi ma wani k'arin bayani ba ta sadda kanta k'asa saboda hawayen da suka cika idanunta. Hajjah ceta taresu da tambayar abinda likitan yace musu, Daddy kasa magana yayi sai Abba ne yayi k'arfin halin fad'in
"Hajjah muyi masa addu'a kawai ita yake b'ukata a gurinmu". Fad'ar hakan yasa Hajjah fashewa da kuka dan tasan inda zancen ya dosa. Matsanancin kuka Ayshaa ta saki ta sulale jikin bangon datake tsaye ta durk'ushe k'asa, wani irin kuka take mai ban tausayi da ratsa zuciyar mai sauraro. wani mugun tausayinta ne yakama duk y'an wajen Mamie ce ta d'agota ta rungumeta tana tapping bayanta alamun rarrashi duk da itama hawayen take hakan yasa ko kalma d'aya ta kasa furtawa. Mukhtar ma zaune yayi kan wata kujera dake kusa dashi ya sunkuyar dakai tareda dafe kanshi yana hawaye, gaba d'aya ya gama saddak'arwa idan aka fito da Saif zai samu lafiya ya tashi saikuma suji wannan mummunan labarin? Ana nufin a haka abokinshi zai k'arasa rayuwar shi kenan? Hasbunallahu wa ni'imal wakeel ubangiji ka dubemu ka tashi wannan bawan naka Yaa ALLAH .
Ba wanda ya iya runtsawa a ranar wayake ta maganar bacci ma hankali ba'a kwance ba? A yadda Daddy ya tsara k'asar India yayi niyyar wucewa dashi Hajjah tace a,a sukoma gida da alamu wannan ciwon nashi bana asibiti bane. Yaso fahimtar da ita Abba ya nuna masa yabi shawarar Hajjahn kawai su koma d'in kawai a fara yimasa na Islamic ko ALLAH zaisa a dace. Haka suka d'ungumo washegari suka baro k'asar kowa zuciya ba dad'i.
Su Saif anzama maridai
Bari mugani idan katashi zaka cigaba da tafka rashin M d'in naka ko kuwa?.
Mrs Salees Mu'az ❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu
(Ummee).
.*Mg's skincare*
Hi sister's
Nasan kunsan da labarin mg's skincare toh kusaurara dakyau
Kaman yanda kukasani sunada sabulun gyaranjiki fitacce Kuma ingantacce Wanda yake mayarda tsohuwa yarinyasanin kankune dukme wani matsalan fata walau pimples,black spot,black head, acne,sunburn,tattarewan fata dama sauran tsaiko/matsalan fata daya ke dmn fata yahana mata rawan gaban hantsi nasan kunsan cewa iya mg's herbal whitening black soap yawadaceku zaikawar da dukkan wadannan dama sauran matsalolin gamasu nankarwa ( stretch mark)duk wnd yy using mg's yasan yanarageshi sosai regular use of it ma zainemeshine yarasa Kuma wani abinma koda mutum bashida komai zaiyi anfani da sabulun inda zaikara gogema mutum fata yasa fatar tayi fresh kuzama kalar hutu jikinku yayi smooth kuyita kyalli kamar saban madubi jikinku zedinga glowing fiye da tsammaninku toh hajiyata mekike jirane♀️ kinsan fa mata da gyara akasanmu Kuma duk kyanka akace kakara da wanka bama cika Baki duk wnd yajaraba mg's zaitabbatar da kanshi cewa nadabannekoda yaushe mg's sai sanbarka inamai sanardaku kuzo ayidaku Kar abarku abaya domin duk macen da ta amsa sunanta da anganta zaa tabbatar da hakankugarzayo adama daku mg's akoda yaushe burinsu shine fatarku tayi fresh luwai luwai tazama wanke hannu ataba
Maiso should chat
08062991549
Call 08064532391
Sannan albishirinku ayanzu akwai complete set nagyaranjiki Wanda baa magana wnd yajarabane kadai zaigane zancen soap kadai yy wadancan aikin inakuma ga set☺️ hohoho kunsan abun nayine maza maiso yarugo aguje yy placing ordernshi via 08062991549
Call 08064532391
Note:soap akwaisu available buh for the set zezama available within 2weeks insha Allah gawanda baida halin siyan set soap din yawadatarba tsaurarawa amare Kuna inaaa kunsan da kyn mg's Baku bukatar wani gyaranjiki Dan ynd fatanku zemurje dawuya ango zaigane amarya just gv it a try nd ur skin will definitely nd forever thank you
Note:pls kayanmu bn bleaching bn organic ne basa bleaching zaifiddo ma mutum da ainihin natural beauty dinshine living the skin so lovely
Soap price:3k
For the set:13k
What are you guys waiting forhurry nd grb urs DNT be left behind
We can't wait to be part of ur beauty story❤️
[9/3, 18:13] UmmAsghar: Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
*DR. SAIF*
Writer: Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No.35
★★. ★★. ★★.
Kai tsaye part d'insu aka wuce dashi bayan dawowarsu, har lokacin alluran barcin dayasha basu gama sakinsa ba dan daya bud'e Ido kafin k'iftawa da bismillah saiya mayar ya rufe ya cigaba da barcinshi.
Mukhtar ne ya kwana dashi kasancewar sai bayan sallahr Esha'e flight d'insu yayi landing saida safe ya wuce gida bayan ya gama kimtsashi. Ranar yini akayi ana karb'ar bak'i y'an zuwa dubiya, na jiki jiki nema suke samun ganinshi wasu kam saidai suyiwa Mamie da Hajjah ya mai jiki su tafi har yamma kuma har lokacin bai tashiba hakan yasa duk suka tashi hankulansu saida Dr Sooraj dayazo gidanne ya kwantar musu da hankali da nuna musu hakan ba wata matsala bace.
Bini bini Ayshaa ta lek'a taga koya farka saita ganshi yana nan dai yadda yake yana barcinshi, yanzun ma shigowarta kenan bedroom d'in ta tsaya saman kanshi tareda k'ura masa Ido tana kallon kyakkyawar fuskarshi wannan jinyar daya kwanta ma saiyaga tamkar wani kyau aka k'ara masa na musamman saboda yadda fuskar tayi wani fayau ta k'ara haske pink lips d'inshi kamar an k'ara turasu da pink jambaki gashi dama Mukhtar ya gyara masa sajenshi, y'ar ramar dayayi saita k'ara masa wani kyawun. mugun tausayinshi ne dank'are cikin zuciyarta, gaskiya mutum yaji tsoron ALLAH lallai ta k'ara yarda d'an Adam ba'a bakin komi yakeba ji yadda ubangiji ya maidashi haka lokaci d'aya mutum mai jida lafiya ilmi, kyau, kud'i gayu da sauran abubuwa na jin dad'in rayuwa ya taka duk wasu matakai najin dad'in rayuwa amma dubi yadda yake kwance a halin yanzu baya iya yiwa kanshi komai yadda za'a juya jaririn dayazo duniya yau shima haka za'a juyashi ta kuma k'ara yarda da cewa ba duka abu bane kud'i suke bayarwa, saboda irin kud'ad'en da aka kashe fitar nan da akayi dashi ALLAH kad'ai yasan yawansu amma gashi nan yadda dai aka kaishi haka aka dawo dashi bawani cigaba.
Ajiyar zuciya ta saki tana d'an d'auke k'wallahr data taho mata a fili cikin rawar murya tace
‘‘Yah ubangijin kursiyyu da al'arshi ya ubangijin sammai da k'assai kabawa bawan nan naka lafiya Ina tawassuli da tsarkakan sunayenka ALLAH katashi kafad'unshi dan alfarmar ANNABI MUHAMMAD.
tana shirin juyawa taga kamar ya bud'e ido, da sauri ta juyo tana kallonshi da gaske ya bud'e idanun nashi. Ido ya k'ura mata yana kallonta itama d'in durk'usawa tayi a gabanshi tana kallonshi yayin da wata k'wallahr ta k'ara cika mata Ido.
"Yah Saif how are you feeling now?, Ka kwantar da hankalinka insha ALLAHU zaka samu lafiya kaji". Ido kawai ya zuba mata yarinyar tabashi mamaki q'warai bai tab'a tunanin zata damu har haka da rashin lafiyar shiba ko addu'ar data gamayi yanzu yana jinta ya tashi lokacin idonshi ne kawai a rufe.
"Yanzu nasan kanajin yunwa ko?". Shidai idone nashi sai yanayin fuskarshi daya canza alamun yanajin dad'in zamanta a gurin.
"Please Yah Saifu". Tace a shagwab'e tana marairaice murya. Saita bashi dariya saboda yanayin yadda tayi maganar baisan lokacin daya saki murmushi ba.
"Woww, yaushe rabon da inga murmushi saman fuskarka? Koda yake dama bakayi". Ta k'arasa maganar tana d'an tura baki, fuska ya b'ata yana kallonta. Murmushi kawai tayi ta mik'e tana fad'in ' I'm coming' ta fice da sauri ya bita da kallo tareda sakin wani murmushin.
Su Mamie ta fad'awa ya farka, dukansu suka nufo d'akin, Hajjah ta taimakawa Mamie suka dag'ashi aka jingina masa pillow a bayanshi saboda gajiya dayayi da kwanciyar.
Ayshaa da dama kitchen ta nufa bayan ta fad'awa su Mamie tashinsa, ta had'o masa tea mai kauri dayaji kayan k'amshi sai pepper soup na kayan ciki data zubo a plate, sallama tayi ta shiga bedroom d'in ganinsu Mamie yasa taji kunya duk ta kamata saitai k'asa da kai ita bata k'arasa cikiba kuma bata juya ta fitaba.
Murmushi Mamie tayi tace
"Taho mana mamana, ai yana b'ukatar yasa wani abu a cikinshi dama".
A hankali ta taka zuwa bakin gadon ta ajiye cup da plate d'in akan bedside drawer tayi tsaye kanta a k'asa tana wasa da hannunta, tunda ta shigo idanunshi na kanta kallon nan nashi dai daya saba ta k'asan idanu yake binta dashi. dariya Hajjah tayi tace
"Kunga Bilkisu kutashi mu fita tabawa mijinta kulawa naga alamun kunya takeji".
Duk tashi sukayi kuwa suka fita Imaan harda yimata signa da ido ta banka mata harara kuwa. Saidata rufe k'ofar sannan ta dawo ta hau gadon ta zauna kusa dashi bayan ta d'auko plate da cup d'in. Cup d'in takai bakinshi yawani marairaice fuska yana kallonta, saita had'e rai irin ba wasan nan tace
"Saifa ka shanye tea d'in nan, nima tym din danaji ciwo haka kayimin, ka tuna?". Ta ida maganar tana murmushi gami da d'age gira.
Ido ya lumshe ya bud'e alamun ya tuna, dan yanzu ta cikin idanunshi ake gane amsarshi.
"Good, open ur mouth now". A hankali ya bud'e bakin ta kafa masa cup d'in ya shiga sha bata d'aukeba saidaya shanye sannan ta sauke cup d'in ta janyo plate d'in ta shiga bashi farfesun kad'an kad'an sai surutu take zuba masa shidai sai binta yake da kallo yana d'an murmushi. Tunda yasamu lalurar nan bai tab'a jin zuciyarshi tayi masa sanyi irin na yauba.
Baisha wani maiyawa ba ya nuna mata ya k'oshi, tissue ta yago ta goge masa bakinshi ta sauke kwanukan k'asa lokacin anata kiraye kirayen sallahr magreebah, tunanin yadda zata taimaka masa yayi alwalah take saiga Mukhtar yayi sallama ya shigo. Cike da jin dad'i ya k'arasa ya zauna bakin gadon yana kallon Saif yace
"Masha ALLAH mutumina ya jikin naka?". Amsar daya saba bayarwa da Ido yabashi.
"ALLAH zaibaka lafiya Matawalle insha ALLAHU zaka k'ara takawa da k'afafunka".
Gaisawa sukayi da Ayshaa tace
"Dama zaiyi sallah ne".
"Owk bari in taimaka masa".
Fita tayi daga bedroom d'in dan zuwa tayi tata sallahr.
Ta d'auki dogon lokaci tana addu'o'e kafin ta shafa ta fito parlor'n kenan Mukhtar ya fito daga d'akin yace takoma wajenshi zai fita, ta amsa da'Toh'ta shige bedroom d'in shikuma ya fita.
Yana zaune inda yake tayi sallama ta shiga, ba kayan d'azu bane a jikinshi plain trouser ne purple da k'aramar riga white color da aka rubuta PERFECT da purple fenti, yayi matuk'ar yin kyau abinshi sai k'amshi yake zubawa.
Zama tayi gefen gadon tana fad'in
"Ya kamata muyi karatun Alqur'ani ko?".
Cikeda jin dad'i ya lumshe Ido ya bud'esu a kanta, tsaye ta tashi tana cewa
"A Ina Alqur'anin yake?".
Idanunshi ya maida can wani guri ya tsura masa Ido, saitabi gurin da kallo itama wata k'aramar drawer ce ita sam bata kula da ita bama, ta fahimci dai anan suke dan haka ta k'arasa ta bud'e Alqur'anai ne dayawa da sauran littattafan addini, ta d'auko ta dawo ta hau gadon ta zauna kusa dashi.
"Wace surah zamu fara?". Ta fad'a tana kallonshi.
K'uri yayi mata da Ido kawai, hakan yasa tayi d'an murmushi tace
"Bari mufara da suratul baqrah ko?". A hankali ya lumshe mata Ido alamun 'Eh'.
Zamanta ta gyara ta bud'e suratul baqrahn cikin siririyar muryar ta tayi A'uziyyah da basmala sannan ta karanto suratul fatihatul kitab daga nan ta shiga cikin surar.
Amon sautin karatun nata da yadda take bawa kowani harafi hakk'inshi da yadda karatun nata yayi masa mugun dad'i ya saukar masa da wata irin nutsuwa da kwanciyar hankali zuciyarshi tayi wani irin sanyi daya dad'e rabon dayaji irinshi, ta dad'e tana karatun ganin yanata lumshe Ido kamar zaiyi barci yasa ta rufe Alqur'anin tana fad'in
"Kar kayi barci kabari kayi sallahr Esha naji anfara kira". Sauka tayi ta maida Alqur'anin tadawo tace masa
"Bari inje nima inyi sallahr".
Sanin ba amsa yasa ta fita taja masa k'ofar yabita da kallo jiyake tamkar karta fita ta barshi ya gabatar da farali ya cigaba da zama har lokacin data dawo ta cigaba da karatun k'arshe dai a hakan yayi barcin daga zaune karatun ta dakatar ta gyara masa kwanciyar shi ta k'ara d'orawa daga inda ta tsaya. Sai datayi izif biyu sannan tayi addu'o'en ta ta shafa.
Tunda suka dawo Ayshaa ke hidima da Saif gaba d'aya duk wani lokaci nata akanshi yake k'arewa batada aiki da zance sai nashi, yanzu kam ko gaban waye bata kunyar tabashi kulawa, matsayi da kima da darajarta sun d'agu fiyeda zaton mai karatu a wajen familyn gidan nan kullum cikin sanya mata albarka suke saboda yadda take kula dashi duk wata d'awainiyar shi tana kanta abinda ya shafi wanka ne dai da sauran wasu uzurirrikan saidai Mukhtar ko Daddy.
Four days da dawowarsu Safnah da Momy sukazo dubashi, Safnah tunda ta ganshi take kuka tunaninta d'aya yanzu hanyar dazatabi a karya asirin nan. Anan Momy kebawa Mamie shawarar ya kamata su nemar masa maganin sammu Mamie tace insha ALLAH zasuyi magana da Daddy zasu san abinyi akai. A ranar suka juya kaduna.
Kwana biyu da komawar su tayi shiri ta koma wajen bokan nan tayi masa bayanin tanaso a karya sihirin nan da Mansurah tadawo akayi mata akan mutumin nan sharad'in daya gindaya matane yasa hankalinta yayi mugun tashi dan cewa yayi saidai rauhanin dayayi aikin ya sadu da ita ta hakane kawai asirin zai karye kokuma makarin asirin da akabawa Mansurahr wanda yake hannunta a yanzu. Masifar tashin hankali ta shigeshi a ranar haka ta juyo tana kuka tadawo ko gida bata jeba ta wuce gidan Mansurah cikin rashin sa'a tasamu batanan k'anwar Mansurahr Madeenah take fad'a mata tayi tafiya tun 2wks da suka wuce bata kuma san ranar dawowarta ba, cikin dabara tacewa Madeenahn akwai ajiyarta a d'akin Mansurahr tanaso tayi amfani da ita bari ta duba d'akin. Bata kawo komai ba tabata key d'in d'akin ta bud'e ta shiga ta maida k'ofar ta kulle, cikin sauri ta shiga dube dube tayiwa d'akin filla filla amma bataga komaiba ba inda bata dubaba amma ba abinda tagani haka ta fito ta rufo d'akin taba Madeenah key d'in ta fita. Sai datasha kukanta a mota sannan taja ta koma gida tana tunanin abinda zatayi next.
An cigaba da addu'a da sadaqa da saukar Alqur'ani mai girma da Daddy ya bayar masallatai akeyi, jikin dai gashi nan ne dai kawai, har lokacin bawani cigaba da aka samu yanzu a wheelchair ake zaunar dashi saidai idan yagaji a saukeshi, Ayshaa bata tab'a nuna gajiyawarta ba kan hidimar datake masa musamman dayake Ammi na yawan kiranta tana k'ara kwantar mata da hankali da nuna mata cewa ibadah take tayi hak'uri ta jure insha ALLAHU mijinta zai tashi tanajin dad'i sosai kuma tayi alk'awarin ko shekara nawa zai d'auka a haka bazata tab'a rabuwa dashiba ba kuma zata nuna gajiyawarta ba tasan aikin ALLAH take dan jinyar miji akwai falala da tarin lada a ciki, fatanta da addu'arta akoda yaushe ALLAH ya tashi kafad'un mijinta yabashi lafiya.
Mukhtar amini ne nagari dan tunda ALLAH yasa lalurar nan tasamu Saif shima bai tab'a nuna gazawarshi ba kullum cikin yimasa hidima yake kuma ko a fuska bai tab'a nuna ya gaji da abinda yake ba. ALLAH ya had'amu da abokan zama nagari.
A yau ne y'an uwan Mamie sukazo daga garinsu duba Saif wad'anda basu samu zuwa ba, mota biyu ce maza da mata bayan an gaggaisa anyi masa ya jiki Baffahn Mamie da sukazo tare ya nemi ganin su Mamie.
Daddy da Mamie ne zaune a inda suka keb'e da Baffah Musa a nan yake shaida musu tunda yaga Saif yaga sihiri a jikinshi dayake malamine sosai, sunyi mamaki sosai suka shiga tunanin waye wannan wanda zaimasa asiri? Iya saninsu dai yaronsu bashida abokin adawa to shi inama ya shiga harkar mutanen? Meyayi kuma da zafi da har za'ayi masa irin wannan cutarwar an dankwafar da rayuwar shi tsawon wannan lokacin? Hankalinsu yayi k'ololuwar tashi a lokacin dayake gaya musu.
A nan ya kwantar musu da hankali yace insha ALLAHU zasusan abinyi akwai abubuwan da za'ayi wanda jikinshi zaifara motsawa koda bai tashi gaba d'aya ba har zuwa lokacin da ALLAH zai karya alkadarin abin gaba d'aya, sunyi matuk'ar jin dad'i sosai, tun a lokacin ya fad'i wasu abubuwa yace a nemosu a Islamic center.batareda b'ata lokaci ba Daddy ya kira Mukhtar ya fad'a masa abinda za'a siyo d'in.
Cikin lokaci k'ank'ani kuwa saiga Mukhtar harya siyo ya kawo, anan Baffah Musa ya harhad'a wasu, wasu kuma zai tafi dasu mahad'in dazai had'asu suna can ruwa yace a kawo masa yayi tofi a ciki yace yafara shanshi kafin ya aiko dawani ba k'aramin farin ciki su Mamie sukayi ba sukaita zuba masa godiya da fatan gamawa lafiya.
Aikuwa su Mamie suka bada himma wajen magungunan ba wasa gefe kuma ga addu'o'en dasukeyi da saukar Alqur'ani da aka duk'ufa anayi.
Kwana uku da komawar su Baffah Musa ya aiko da wasu magungunan masu yawa dana sha dana turare dakuma na shafawa a jiki.
Wata muguwar shak'uwa ce ta shiga tsakanin Saif da Ayshaa, wadda tafara rikid'ewa ta koma soyayya, gaba d'aya Saif ya canza amma dai har yanzu bai cika sakin fuskar ba saidai ya d'an ragu ba kamar da ba.
Sosai aka maida hankali gurin magungunan da Baffah Musa yake had'awa,kafin su k'are ma Daddy zai aika driver ya amso wasu kuma Alhamdulillah ana ganin fa'idar abin hakan yasa aka k'ara dagewa sosai. Kashi biyu Safnah na komawa gidan Mansurah sai Madeenah tace mata har yanzun bata dawoba tarasa inda taje gashi idan an kira wayarta bata shiga, abin duniya duk ya taru yayi mata yawa.
★★★
One month after.
Cikin k'udurar ALLAH da buwayarsa saiga Saif a hankali a hankali ya fara motsa jikinshi, gaskiya ne da akace ba abinda addu'a tabari tafi tafi dai bakin nashi ma ya bud'e fad'ar irin farin cikin da wannan ahali suka shiga bazai fasaltu ba kowa kagani baki bud'e saboda murna ALLAH maji rok'on bayinsa ya amsa addu'ar su anfara samun waraka ta hanyar bawanshi Baffah Musa. Yanzu haka yana iya motsa duk sassan jikinshi tafiya ce dai har lokacin bayayi.
Tunda ALLAH yasa yafara jin sauk'in nan ya hana Ayshaa sakat, kullum yafiso yajita mak'ale a jikinshi. Yauma bayan ta fito wanka tayi shirinta tsaf cikin doguwar riga ta material black color mai k'yalk'yali bata d'aura dankwalin ba sai k'aramin mayafi data d'aura ta fesa turaruka ta nufi bedroom d'inshi tayi sallama ta shiga.
Yana zaune kan wheelchair d'inshi kanshi a k'asa yana latsa waya, sabuwar jallabiyyah ce a jikinshi ash color sai k'amshi yake.
Ido ya k'ura mata yana mata wani irin narkakken kallo itama irin kallon take masa.
"Come here". Yace k'asa k'asa kamar mai rad'a yana mik'a mata hannu. A hankali ta shiga takowa harta isa gabanshi ta tsaya, hannu yasa ya janyota ta fad'a kanshi kanta ya bugi k'irjinshi tasaki k'arar shagwab'a tana fad'in
"Wayyo ALLAH Mamie". Ta ida maganar tana tunzuro baki gaba, bakin yakama ya matse da d'an k'arfi ta k'ara sakin wata k'arar tanason k'wace bakinta.
Bakin ya saki yasa kanshi a wuyanta yana shinshinar k'amshinta kafin kuma a hankali ya lalubi bakinta ya shigar da nashi ya shiga kissing d'inta.
❤️Jummah Kareem❤️
Mrs Salees Mu'az ❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu
(Ummee).
Hi lovelies
Shin Ina matan suke
Kumarmazo kuji wani sirri maiban mamaki
Inamai gayamuku indai gyaran fata kikeso hajiya kigarzaya @mg's skincare kiga yanda fatarki zata koma lukui lukui abun burgewa ga ke kanki ma ballantana mutane duk masu fama da matsalan fata abundaya danganci pimples,acne,spot, sunburn, stretch mark, black head,eye glass, knuckles, wrinkles, matsalan cream reaction toh mg's skincare is the solutions to all ur prblms inagayamuku karkudauka mgnn for granted sannan results d zakusamu zakusan cewa konawa kukasiya aikinshi m yafi haka wnd sukayi bleaching ma yabatamusu fata mg's skincare sunada product da zaigyaramuku jikinku yadawo daidai Uwargida da amarya Kai harma da yanmata kunemi mg's kusha mamaki da yardar Allah indai fannin gyarajiki ne ko mutum baida komai akwai soap dazaikara gyarama mutum jiki fiye d tsammaninku jiki yy kyau yadinga walwali wani abun sewanda yajaraba shine zaitabbatar inamai tabbatar kuhanzarta kugarzayo adama daku domin mata dagyara akasanmu☺️Kuma duk macen data amsa sunanta da tsabta akasanta sister gani yakori ji Kuma siyan nagari maida kudi gida adade anayi sai gaskiya
Kayanmu % natural, organic ne bn bleaching bn nagyaranjiki ne wnd zaa yk.gyarajiki yasa fata tafita daban tagoge tadinga haskawa tana kyalli d daukar Ido
Maiso should chat 08062991549
Call 08064532391
Soap price:3k
Set:13k
Pls serious buyers only
We deliver Nationwide buh delivery is not free
Hurry nd grb ursdnt be left behind
Team glow skin♀️
Dm
[9/4, 18:40] UmmAsghar: Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
*DR. SAIF*
Writer: Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
Masoya book din nan godiya a gareku kunyi nagani baki bazai iya fad'a ba haka alk'alamina bazai iya rubutawa, nagode sosai ALLAH yabar zaman tare I love u so much my dearest friends ❣️❣️❣️.
Nagode .
No.36.
Cikin wani irin salo mai tafiyar da hankali yake sumbatar ta, for the first time dataji yanayinta yafara sauyawa aduk sauran kisses d'in dayayi mata a baya duk da sauran dai na mugunta ne amma ai bayan haka akwai wad'anda yayi cikin nutsuwa. Shiru tayi, tai lak'was tana accepting d'in sak'on bata hanashi ba haka kuma bata tayashi ba, cikin wani irin yanayi ya shiga k'ok'arin zura hannu cikin rigarta ai tuni ta farga tadawo hankalinta ta rik'e hannun nashi gam tanason k'wace bakinta yana saki kuwa ta tashi kafin yayi yunk'urin kamata tabar wajen da gudu ta tsaya jikin mirror tana kallonshi gaba d'aya idanunshi sun canza kala sai numfarfashi yake saki yana d'an lumshe ido. Hannu ya k'ara mik'a mata alamun tazo ta mak'ale kafad'a tana tura baki gami da wasa da yatsun hannunta.
"Please". Yace a hankali cikin shak'akk'iyar murya yana wani langab'ar dakai irin a tausaya masa d'in nan.
"Uhm uhm, tace tana k'ara mak'e kafad'a.
"Nine fa". Ya k'ara fad'a yana marairaice fuska.
Y'ar dariya tasaki tace
"Eh, naganka ai".
Fuska ya had'e yasha mur sosai yace
"Ke wai sa'anki ne ni? Ko wasa nake dake? Ina nanfa a Saifuna da kika sani ban canzaba".
"Ina ruwana to". Tace cikin dariya tana masa gwalo. Hannu yakai kanshi ya shafo sumarshi yana mata kallon k'asan Ido yace
"Kinsan idan naso zan iya kamaki ko?".
Baki ta d'an tab'e tana d'age kafad'u gamida wara hannayenta cikin jujjuya idanu tace
"Ta yaya gurgun Mamie?".
"Ta haka". Ya fad'a yana cije lips d'inshi gamida danna wani abu dake gefe da gefen wheelchair d'in kawai sai ganinshi tayi a gabanta, baki ta bud'e ta waro Ido waje kafin tayi yunk'urin barin wajen yasa hannu ya fincikota ta fad'a kanshi ta saki k'aramar k'arar shagwab'a kuwa kamar zata sakar masa kuka.
Kan cinyarshi ya d'orata ya zagayo da hannuwanshi kan ruwan cikinta ya matseta gam ya cusa kanshi kan dokin wuyanta yana goga mata gemunshi, gam ta rufe idanunta saboda yadda tsigar jikinta ya tashi mutsu mutsu tafara tanason k'wacewa ya k'ara matseta yana sauke mata numfarfashi a wuyanta yayin da yakai bakinshi kunnenta cikin rad'a yace
"Yaa, kinga aikin d'an gurgu ko".
A shagwab'e tace
"Please Yah Saif ka sakeni su Mamie fa zasu iya shigowa".
"So what?". Yace kanshi tsaye yana k'ara cusa kanshi saboda yadda k'amshin khumrahr datayi amfani da ita tayi masa masifar dad'i.
Ido kawai ta lumshe tanajin yadda yake k'ara rud'a mata jiki da salonshi, Kamar a mafarki taji hannayenshi kan k'irjinta gabanta ne yayi mugun bugawa tayi wata zabura zata mik'e ya k'ara dawo da ita a tsorace kamar mai shirin sakin kuka tace
"Dan ALLAH Yah Saif ka sakeni please".
Kafin yace wani abu sukaji an tab'a k'ofar d'akin kamar za'a bud'e cikin azama ta b'anb'are hannuwanshi daya rik'eta ta tashi ta matsa can d'an nesa dashi ta tsaya tana zare ido. Mukhtar ne yayi sallama ya shigo a hankali ta amsa sallamar tana satar kallon Saif dayake maida numfashi yana d'an rurrufe Ido kamar mai shirin yin barci.
Bisa sofas Mukhtar ya zauna yana kallon Saif kallon iya shege shikuma ya wani maze ya had'e gabas da yamma yana wani basarwa.
A diririce suka gaisa da Mukhtar ta fice kanta a k'asa duk ta tsargu gani take kamar Mukhtar ya gansu.
Bedroom d'inta ta shige ta fad'a kan bed tareda sakin ajiyar zuciya, wani irin tsamm taji lokacin data tuna abinda yayi mata d'azu maganar gaskiya Saif bashida kunya ji dan ALLAH yadda yawani tab'a mata k'irji ko kunya bayaji, har lokacin gabanta wani irin fat fat yake yana bugawa, fitinannen majinyaci ne kawai wannan.
Bayan fitarta Mukhtar yace
"Mr.Man ya jikin naka?".
Murya a shak'e yace
"Alhamdulillah".
Dariya Mukhtar ya shek'e da ita yana kallon Saif.
Tsaki Saif yayi yace
"Ba tun yauba nasan kanka da motsi Mukhtar, inba haka ba taya zaka tasani kana dariya?".
Cikin dariya Mukhtar yace
"Koma mezaka fad'a ka fad'a shegen sama inacan Ina tausayinka kai kana nan kana lobewarka ko? Good hakan yayi very soon ma za'ayi mai gaba d'ayan a wuce wajen koya kace?". Wani shegen murmushi ya saki yana shafa sajenshi yace
"Ya ranka? Kana bak'in cikine?".
Ido Mukhtar ya d'an zaro yana fad'in
"Ina ni Ina bak'in cikin angwancewar abokina kaidai ALLAH yakai damo ga harawa".
"Koda bai ciba zaiyi birgima". Saif ya k'arasa masa maganar aikuwa Mukhtar ya fashe da dariya tareda bashi hannu suka kashe.
"Mukhtar inaso in k'ara yimaka godiya akan hidimar dakayi min daga lokacin da lalurar nan ta sameni zuwa yanzun, alkhairinka mai tarin yawane a gareni Mukhtar bazan tab'a manta abinda kayimin ba a tarihin rayuwata ba ALLAH ya saka maka da mafificin alkhairi ya biya maka b'ukatunka na alkhairi thanks very very much my friend".
Murmushi Mukhtar yayi ya k'ara matsowa kusa da Saif sosai yace
''Karka damu Matawalle ba godiya tsakanina dakai nidai fatana yanzu da addu'ata Inga ka tashi ka koma kamar yadda kake a da".
"Insha ALLAH very soon zan tashi inaji a jikina na kusa mik'ewa bi'iznillah".
"ALLAH yasa, amma abokina in tambayeka mana".
Ido kawai Saif ya k'ura masa alamun yana jinshi.
"Nace baka fara jin wani abuba game da Ayshaa ba a cikin zuciyarka?". Kallon rashin fahimta yake masa batareda yayi magana ba, haka yasa Mukhtar yace
"I mean wani abu haka daya danganci soyayya ko makamancin haka?".
Wani kallo Saif yayi masa yace
"Tun yaushe kuma? Zauna nan".
"Dan girman ALLAH, bani story Matawalle". Mukhtar yace cikin farin ciki yana waro idanu waje.
"Mukhtar bazan b'oye maka ba daf da abin nan zai sameni nafara jin zuciyata na sauyawa gameda al'amarin yarinyar nan saidai nak'i bari zuciyata ta yadda da hakan saboda gani nake kamar duk shirme ne, saidai a yanzu na tabbatar da hakan banida tantama gameda hakan".
"Woww I'm very very happy abokina, kace ka zurma ciki kawai".
"Wllhy na zurma Mukhtar,duk kaucewar danake yarinyar nan saidata sacemin zuciya".
Dariya Mukhtar yayi yace
"Saika daina wannan shegen nuk'u nuk'un naka ka fito ka fad'a mata".
"Dolena". Abinda yace kenan ya maida kanshi kan wayar hannunshi.
Ayshaa dai bata k'ara shigowa d'akin ba, duk tsoronshi ya kamata gani take kamar data shigo zai k'ara yimata abin d'azu barcine ma ya kwasheta a haka.
@★@★@★@★@★
Washegarin da Mansurah tadawo daga tafiyar datayi tana zaune kan kujera a parlor Madeenah ta fito daga bedroom ta zauna kusa da ita tace
"Aunt Surrey, please wannan doguwar rigar taki sabuwar nan zaki aramin zan d'an fita".
Harara Mansurah ta jefa mata tace
"Banson iskanci Madeenah duk kayanki kirasa wanda zakisa saina baki rigar dana siya mai tsada kuma ko sawa ban tab'a yiba".
"Please Aunt Surrey Ina dawowa zan cire miki wllhy".
Tsaki Mansurah tayi tace
"Sai kije ki d'auka tana cikin trolleyn dake kan wardrobe".
Cikin murna Madeenah ta tashi ta nufi bedroom d'in Mansurah tana fad'in ta gode.
Kai tsaye wardrobe d'in ta nufa ta taka wani stool mai tsayi ta janyo akwatin zata sauko da ita tana sauketa wani abu ya biyo bayan akwatin ya fadi ya fad'i k'asa jikake tusshh.....
Babu dai yawa yasin ☹️ ku kuka matsamin saura inji wanj yace yayi kadan
Mrs Salees Mu'az ❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu
(Ummee).
Hi lovelies
Shin Ina matan suke
Kumarmazo kuji wani sirri maiban mamaki
Inamai gayamuku indai gyaran fata kikeso hajiya kigarzaya @mg's skincare kiga yanda fatarki zata koma lukui lukui abun burgewa ga ke kanki ma ballantana mutane duk masu fama da matsalan fata abundaya danganci pimples,acne,spot, sunburn, stretch mark, black head,eye glass, knuckles, wrinkles, matsalan cream reaction toh mg's skincare is the solutions to all ur prblms inagayamuku karkudauka mgnn for granted sannan results d zakusamu zakusan cewa konawa kukasiya aikinshi m yafi haka wnd sukayi bleaching ma yabatamusu fata mg's skincare sunada product da zaigyaramuku jikinku yadawo daidai Uwargida da amarya Kai harma da yanmata kunemi mg's kusha mamaki da yardar Allah indai fannin gyarajiki ne ko mutum baida komai akwai soap dazaikara gyarama mutum jiki fiye d tsammaninku jiki yy kyau yadinga walwali wani abun sewanda yajaraba shine zaitabbatar inamai tabbatar kuhanzarta kugarzayo adama daku domin mata dagyara akasanmu☺️Kuma duk macen data amsa sunanta da tsabta akasanta sister gani yakori ji Kuma siyan nagari maida kudi gida adade anayi sai gaskiya
Kayanmu % natural, organic ne bn bleaching bn nagyaranjiki ne wnd zaa yk.gyarajiki yasa fata tafita daban tagoge tadinga haskawa tana kyalli d daukar Ido
Maiso should chat 08062991549
Call 08064532391
Soap price:3k
Set:13k
Pls serious buyers only
We deliver Nationwide buh delivery is not free
Hurry nd grb ursdnt be left behind
Team glow skin♀️
Dm
Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
*DR. SAIF*
Writer: Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
Kyautar shafi ga duk wani masoyin book din nan ALLAH yabar zumunchi da k'aunar juna ONE LUV.
No. 37.
Da sauri Madeenah ta kalli k'asan dan ganin abinda ya fad'o tayi arba da wata y'ar k'aramar tukunyar k'asa data farfashe dawani jan k'yalle dake gefenta sai wani irin hayak'i ke tashi mai uban k'auri, akwatin tasaki a kan gadon ta sauko k'asa cikin fad'uwar gaba ta shiga bin wajen da kallo jikinta sai rawa yake kamar daga sama taji Mansurah ta k'wala wata uwar k'ara cikin azama ta fita parlor'n da gudu nan tasamu Mansurah sai ihu take tana mummurza idanunta duk tayi fatali da wayarta da dankwalin kanta ta hargitsa gashin kanta rik'ota Madeenah tayi tana fad'in
"Innalillahi wa Inna ilaihi rajioun, Aunt Surrey meya faru haka meye ya sameki?".
Cikin ihu take fad'in
"Madeenah bana ganinki wllhy Madeenah duhu kawai nake gani bana ganin komai wayyo ALLAH na shiga uku".
Cikin tsananin tashin hankali Madeenah ke jijjiga Mansurah tana fad'in
"Meya samu idonki, meye a cikin tukunyar can data fad'o daga saman wardrobe?"
"Shikenan kin kasheni Madeenah shegiya y'ar iska ke kika fad'o da makarin asirin da akayiwa Saif kin takaitani Madeenah ALLAH ya tsine miki albarka ALLAH yasa kema ki daina gani". Ta k'arasa tana cakumo wuyan Madeenah ta shak'eta tanata zuba uban surutai marasa kan gado, da k'yar Mansurah ta k'waci kanta ta shige bedroom ta kulle tana kuka ta shiga ukunta me Aunt Surrey taje ta aikata haka abu yazo ya dawo kanta? Tuni take nusar da ita illar bin bokaye da malaman tsubbu abune mara kyau tsantsar jahilcine da rashin sanin ciwon kai gashi nan tana zaune k'alau tajawa kanta makanta ga surutan datake tayi da k'yar idan brain d'inta baisamu matsala ba, yanzu wa zata kira ta fad'awa matsalar ta? Iyayensu sun mutu dama wajen kawunsu suke tunda Mansurah kuma taga takawo k'arfi ta kama gida sukabar gidan kasancewar talakane tayi mugun rainashi bai isa ya fad'i abu tayi shiba har kawo yau d'in nan da ake ciki ko game da biye biyen mazan datake ba irin nasihar da baiyi mataba amma bataji kamar ma yana k'ara zugata ne ganin haka yasa ya tattarata ya watsar sai Madeenah dake satar hanya taje gidan batareda sanin Mansurah ba dan ta hanata zuwa inda yake. Wani kukan ta k'ara fashewa dashi jin surutan da Mansurah keyi da buge buge gashi tana tunanin da wayarta ta fita d'azun, cikin ikon ALLAH kuma tana juyawa ta hangi wayar tata akan gado hamdala tayi ta k'arasa ta d'auki wayar tafara neman number kawun dan shaida masa halin dayake ciki.
A daidai wannan lokacin Saif yana kwance yana barci, yaji kamar ana jijjigashi jikinshi yafara rawa haka k'afafunshi yaji kamar ana tsikararsu tashi yayi bakinshi d'auke da addu'a kanshi ya dafe dayaji yana d'an Sara masa kamar wanda aka umarta dayayi tafiya ya zuro k'afafunshi ya sauko daga kan bed d'in ya tashi tsaye kamar wasa ya gwada taka k'afar yaga ta taku saiya shiga tattakawa cikeda mamakin wannan al'amarin wani irin farin cikine ke fisgar zuciyarshi ashe da rabon zai k'ara takawa da k'afafunshi nan bisa carpet ya zube yayi sujudush shukr yana mik'a godiyar shi gurin ubangiji ALLAH daya nufeshi da k'ara takawa bayan wasu watanni daya d'iba a zaune.
Yana mik'ewa Ayshaa ta shigo bedroom d'in tsaye tayi tana kallonshi cikin tsananin mamaki da al'ajabi shima d'in cikin tsananin farin ciki yake kallon nata kafin daga bisani ya ware mata hannayenshi alamun tazo gareshi ganin ta tsaya bata taho d'in ba yasa ya k'ara yimata alamu da kanshi fuskarshi d'auke da mad'aukakin murmushi yayin da idanunshi suka cika da k'wallahr farin ciki. Cikin sassarfa ta k'araso ta shige jikinshi ya maida hannuwanshi ya matseta a k'irjinshi idanunshi a lumshe ya d'ora kanshi akan nata yana sauke ajiyar zuciya tsahon minti hud'u suka d'auka a haka kafin ya d'ago kanta ya rik'e fuskarta yana kallon cikin idanunta itama Idonta cikeda k'wallah ta tsura masa su cikin rawar murya tace
"Tun yaushe hakan Yah Saifu?"
"Yanzun nan nima na tashi najini a haka".
"ALHAMDULILLAH, Ina matuk'ar farin ciki da tashinka Yah Saifu Alhamdulillahillazi bi Ni'imatih tatimus saleehat congrats Doctor Saifullahi Sadeeq Matawalle".
Ido ya lumshe a hankali yakai bakinshi yayi kissing d'in forehead nata ya gangaro kan tsinin hancinta nan ma ya sumbata ya dire kan labb'anta ya basu wani dogon kiss da saida tsigar jikinta ta tashi ya k'ara maida kanta k'irjinshi a hankali kamar mai tsoron magana ya furta
"I love you My Ayshaat, I really love u so much with all my heart". (Finally Ayshaa tayi winning d'inka Mr hukunci).
Gam ta rufe idanunta gabanta na wani irin fad'uwa, zuciyarta na kai kawo wai yau Saif ke furta mata kalmar SO? To meya kamata tayi? Kamata yayi kawai ta rungumi mijinta suyi zaman aure na hak'ik'a ta manta da baya koda can fa Saif baya wulak'antata barshi da nuna isa da wannan miskilancin da bak'in rai dayake d'awainiya dashi wanda tasan a jininshi abin yake kuma kowa hak'uri yake dashi dan bazata manta ba watarana tana wajen Mamie ya shigo duk maganar da Mamie tayi masa saidai ya bata amsa da kai saida tayi masa tsiya tsiya sannan yayi magana to shi haka ALLAH yayishi magana tana masa matuk'ar wahala. A hankali cikin rawar murya itama tace
"I love u too, I really love u with all my ❣️".
Tsam ya k'ara matseta tamkar zaisata cikin k'irjin nashi tasaki y'ar k'ara saboda matsar dataji.
"Zafi ne?". Yace a hankali yana shafa bayanta. Kai ta d'aga tana marairaice fuska.
"OH I'm sorry My Ayshaat". Yace yana sassauta rik'on dayayi mata, Ido ta lumshe saboda jin dad'in sunanta a bakinshi saitace bata tab'a jin wanda ya fad'i sunanta yayi mata masifar dad'i irinshi ba saboda yadda yake fad'arshi da wani irin salo mai k'ayatarwa ko kuma dan bai tab'a fad'ar bane taji oho.
Jikinshi ya raba danata yana mata wani irin kallo yace
"Muje ki tayani wanka". Ido ta d'an zaro tayi saurin juyawa tana fad'in
"Tom bari in dawo". Hannu yasa ya dawo da ita ba zato taji yayi sama da ita k'afafu ta fara jefawa tana masa magiyar ya sauketa baibi ta kantaba ya wuce bathroom ya tura k'ofar da k'afarshi ya shiga ya maida k'ofar ya rufe. Cikin bathtub ya ajiyeta ya tsaya a bakin jacuzzi tub d'in yana kallon yadda take a tsorace sai zare ido take tana b'ata fuska.
A marairaice tace
"Dan ALLAH Yah Saif ka bud'e min in fita nifa yanzu nayi wanka ma wllhy".
"Eh, ai nima bance kiyiba ni zaki taimakawa". Ya fad'a hankalinshi kwance yana k'ok'arin cire jeans d'in jikinshi.
"Na shiga uku". Tace cikin ranta kamar ta fasa ihu, jeans d'in ya cire da T.shirt d'in jikinshi ya zama dagashi sai farin boxer, boxer'n yakama kamar zai cireshi ta fasa k'ara tana durk'ushewa cikin tub d'in ta rufe idanunta ruf gabanta na dukan uku uku, murmushi yayi yana cije baki ya shiga cikin bathtub d'in hannu yasa ya d'agota yana fad'in
"Tashi kigani". Tashin tayi amma har lokacin bata bud'e idonta ba jikinta sai rawa yake.
"Open ur eye, wannan rawar jikin na meye?". Kamar mai shirin kuka tace
"In kana yiwa ALLAH ka maida kayanka Yah Saif please".
Tsaki ya d'an ja yace
"Ke banason k'auyanci bud'e idonki ko kuma in miki irin hukuncin dana saba". A hankali ta bud'e idon taga ashe bai cire boxer'n ba k'aramar ajiyar zuciya ta saki tare dayin hamdala a cikin zuciyarta duk da dai ganinshi a hakan ma wata damuwarce.
"Bak'auya kawai, cire kayan ki kema ki k'ara wani wankan". Yace yana saka hannu a bayanta ya kama zip d'in doguwar rigar material d'in dake jikinta mara nauyi.
"Dan ALLAH Yah Saifu karka ciremin kaya". Ta fad'a tana marairaicewa gamida damk'e rigar.
"Malama sai kinyi wankan nan fa". Yace lokacin daya fara zipping d'in rigar, cikin rawar murya tace
"To naji zanyi wankan amma please kabarni inyi da kayana".
Zuge zip d'in yayi yana fad'in
"A garinku kika tab'a gani anyi wanka da kaya". K'ok'arin rik'e rigar take amma Ina har takai k'asa, k'asa tayi da kanta tana k'ank'ame k'irjinta bak'in wandone mai kama jiki sosai da kad'an ya wuce cinyoyinta sai half vest mai kamar bra itama black mai net tayi matuk'ar haska farar fatarta.
Lumshe ido yayi, ya bud'esu ya zubesu kan k'irjinta wani gwauron numfashi ya saki lokaci d'aya yana kamota ya sakata cikin k'irjinshi tareda kai hannu ya kunna musu shawer ruwa ya fara sauka a kansu. Cikin ruwan ya dinga rud'a mata jiki da wasu zafafan salo daya kusa haukatata dasu, ganin abin take tamkar mafarki ko almara wai dama haka Man d'in nan yake abinda mamaki kam......
Managed .
Naje gaisuwar mutuwa ne ku sashi cikin addu'arku please .
Ubangiji ALLAH yaji k'an wad'anda suka rigamu gidan gaskiya ya kyautata namu k'arshen idan tamu tazo .
Mrs Salees Mu'az ❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu
(Ummee).
Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
*DR. SAIF*
Writer: Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No.38.
Saida suka d'auki lokaci mai tsayi cikin ruwan yana k'ara rud'a mata jiki da salonshi mai matuk'ar tsayawa a rai, da k'yar yabari sukayi wankan suka fito gab'a d'aya Ayshaa a takure take ga kunya dake damunta shikam taga alamunshi d'an kai tsaye ne ba abinda ya dameshi.
"Abani kaya Madam". Yace lokacin dayake taje sumar kanshi a gaban mirror. Clothes d'in ta k'arasa ta fara duddubawa kayane gasu nan birjik tamkar ba'a so shaddoji, voile, suit da sauran k'ananun kaya kaloli daban daban duk saita daburce tarasa wanne ma zata d'auka ne, idanunta suka kai kan wata shadda sky blue takai hannu ta d'aukota ta nufoshi da ita. B'ata fuska yayi dayaga kayan data d'auko masa yace
"Please A'esh kibani k'ananu nafijin dad'insu".
Sakato tayi tana kallonshi jin sunan daya kirata dashi ya matuk'ar burgeta ya kuma yi mata dad'i ainun yaufa Man d'in nan yana bata mamaki dayawa.
"Kinji". Ta tsinkayi muryar shi na fad'a.
Baki ta d'an tura tace
"Gaskiya A'ah Yah Saif manya zakasa gara ka fitarwa su Mamie da mutunci da kamalarka hakane?". Kafad'a ya d'age yana d'an tab'e baki. Nan ya shirya cikin kayan sunyi masa matuk'ar kyau duk yadda taso tasaka hula k'i yayi wai ciwon kai take sashi dole ta k'yaleshi, Arabian perfumes ta feffesa masa daga nan suka nufi bedroom d'inta itama ta shirya cikin atamfa kalar kayanshi sky blue da ratsin fari tasa mayafi kalar kayan tana shirin fita taji ya janyota ya had'e fuskarsu ya kashe musu selfie (Ah lallai abun na dakta azimun ne). Saida yayi musu selfie fin kala goma style's daban daban sannan ya kama hannunta suka fita.
Imaan ce kawai a parlor'n da waya a kunnenta da alamu waya take kamar ance ta d'ago kanta suka had'a Ido da Saif da Ayshaa Ido ta zaro tareda ajiye wayar data manta ma da cewar waya take gaba d'aya ta manta da wani tsoronshi datake ji a da ta tafi da gudu ta fad'a k'irjinshi cikin tsananin murna da farin ciki hannu yasa shima ya rungumeta fuskarshi d'auke da murmushi, Ayshaa ma murmushin take tana kallonsu a hankali ta d'ago kanta tace
"Yah Saifu ka warke fa, yaushe kafara tafiya?".
"D'azu ne little,Ina Mamie fa?".
Sakinshi tayi ta tafi da gudu tana fad'in
"Bari in kirata". Da gudu gudu ta haye stairs d'in tun daga nan take k'walawa Mamie kira, kallon Ayshaa yayi wadda tabi bayan Imaan da kallo tana murmushi batayi zatoba taji ya rik'o k'ugunta da hannu biyu ya matso da ita jikinshi, fuskarshi ya had'a da tata har tsinin hancinshi na tab'a nata.
"Please Yah Saif meye hakane Mamie fa zata fito yanzu dan ALLAH ka sakeni".
Yana shirin yin magana sukaji k'arar takalma alamun ana saukowa tuni tayi hanzarin raba jikinta da nashi dan kar ayi abin kunya.
Kafin Mamie ta k'araso shiya k'arasa ya rungumeta sosai a jikinshi itama d'in cikin matsanancin farin ciki mara misaltuwa ta k'ara shigar dashi jikinta bakinta d'auke da godiyar ALLAH daya nuna musu tashin yaronsu. Da ka tayiwa Ayshaa alamun itama tazo, a kunyace ta tako inda suke tana zuwa kuwa ta had'asu gaba d'aya ta rungume Imaan ma cikin shagwab'a tana tura baki ganin ba'a nemetaba ta k'arasa tayi joining d'insu. Zama sukayi bayan sun saki juna Mamie na k'ara jaddada godiyarta ga ALLAH subhanahu wa ta'ala. Kasa hak'uri tayi saidata kira Daddy ta fad'a masa wannan abin farin cikin aikuwa Daddy tamkar yayi tsuntsuwa yadawo gidan ya gasgata labarin da aka bashi, Imaan ma sai a lokacin ta tuna waya fa suke da Mukhtar lokacin dasu Saif suka shigo hakan yasa ta d'auki wayar ta shige bedroom ta kirashi yana d'auka yafara yimata k'orafin ta aje masa waya basu gama magana ba anan take fad'a masa dalilin dayasa cikin murna shima yace gashi nan zuwa gidan.
Daddy na shigowa shima Mukhtar ya shigo kowa saidaya rungumeshi suna masa murnar tashi da k'afafunshi. Nan da nan y'an uwa na kusa da abokan arzik'i suka cika gidan aka had'a y'ar k'warya k'waryar liyafa akaci aka sha Daddy ya dinga raba kyaututtuka duk dan ya nuna irin farin cikin dayake ciki a wannan rana.
Sai bayan sallahr Esha sannan kowa ya watse akabar masu gidan kawai.
Zaune suke a dinning suna dinner Mamie ce da Saif sai Ayshaa da Imaan shi Daddy ya fita ganawa da wani abokin kasuwancinsa.
Gaba d'aya Ayshaa ta fara canzawa duk tayi sanyi lokaci d'aya abincin ma spoon kawai take juyawa a ciki bawani cin kirki take ba hakan yasa Mamie tambayar ta ko lafiya? Ta amsa da babu komai.
Tissue Saif ya yago ya goge bakinshi yana kallon Ayshaa datake tawani marairaice fuska saita bashi dariya ma murmushi ya d'anyi yace
"Tashi muje dare yafara yi".
Kallonshi tayi ta kalli Mamie tace
"Mamie dan ALLAH zan kwana a wajenki".
"Wajena kuma mamana?". Mamie ta fad'a cikin mamaki tana kallonta, kai ta d'aga alamun Eh.
"Why?". Mamie ta tambaya tana murmushi tareda kallon Saif dayayi tamkar baima ji maganar da akeyiba.
A marairaice tace
"Haka nan Mamie kawai inason kwana a wajenki ne".
"No my daughter kije kibawa mijinki kulawa bakiga yau yatashi bane uhm".
Tsaye ya mik'e ya tura kujerar dayake kai baya ya fita ya fita yana fad'in
"Rabu da ita Mamie rigima ce kawai irin tata saikace da d'in anan take kwana".
"Ba ruwanka, tashi kuje mamana ALLAH yayi muku albarka".
Tashi tayi ta kalli Imaan tace
"Toh Mamie muje da Imaan ta tayani kwana?". Baisan lokacin daya maka musu hararaba itada Imaan d'in, itadai Mamie dariya kawai take k'asan zuciyarta kuma dank'are yake da farin ciki dan taga alamun sun shirya tsakaninsu dan daga d'azun zuwa yanzun taga alamomi masu yawan gaske wanda ko ba'a fad'a maka ba zaka tabbatar da hakan.
Sallama sukayi musu Mamie ta bisu da addu'a.
Har suka shiga part d'insu ba wanda yayi magana bedroom d'inta tayi niyyar wucewa ya jata suka nufi nashi ganin ba alamun wasa a fuskarshi yasa batayi gardama ba tabishi saidai banda fad'uwa ba abinda gabanta yake gaba d'ayanta a tsorace take dashi.
Suna shiga yafara rage kayan jikinshi ya rage daga shi sai singlet da boxer itadai tana zaune kanta a k'asa gurinta ya matso ya kama hannunta ya mik'ar da ita tsaye ya cire mayafin ya jefashi kan couch ya kama zip d'in rigar zai zuge d'agowa tayi ta kalleshi tayi narai rai da Ido bai kulata ba ya zuge ya cire rigar ya cire zanin ya d'auketa ya nufi bathroom da ita duk yadda take zillewa hakan baisa ya sauketa ba har cikin bathtub k'in yadda tayi ya cire mata underwear d'inta dole sai a haka sukayi wankan suka d'aura alwalah suka fito da kanshi yaje bedroom d'inta ya d'auko mata kayan barci riga da wando masu kauri kalar light purple da hijab yakawo mata saida ta koma bathroom tasaka ta fito ta sameshi ya shirya cikin jallabiyyah milk color sai uban k'amshi yake zabgawa mai dad'in gaske k'atuwar darduma ya shimfid'a musu ya jasu sallah, raka'a biyu sukayi, bayan sun idar ya shiga jero addu'o'e cikin harshen larabci sakato tayi tana kallonshi cikin mamaki itafa wllhy duk zatonta bashida wani ilmin addini na kirki amma ji yadda yake kwararo addu'a da larabci ya d'auki lokaci mai tsayi yanayi sannan ya shafa itama shafawar tayi kanta a k'asa. Hannu yakai kan goshinta ya dafa ya shiga karanto addu'ar da ANNABI MUHAMMAD (S.A.W.) ya umarci miji yayi akan matarshi
Tsam ya tashi bayan sun shafa ya fita daga bedroom d'in, Ayshaa tabi bayanshi da kallo gabanta sai fad'uwa yake anya ba guduwa zatayi ba kuwa kafin ya dawo to inta gudu ma taje Ina? Ta tabbatar yanada spare key d'in bedroom d'inta a tsorace take dan tagani a cikin idanunshi ba d'aga k'afa.
Tana nan zaune yadawo hannunshi d'auke da glass cup da fresh milk madaidaicin kwali,
Har lokacin bata motsaba kanta a k'asa tana wasa da gefen hijabinta, kusa da ita ya zauna ya bud'e kwalin ya cika cup d'in ya mik'a mata.
"Na k'oshi". Ta fad'a a hankali tana girgiza masa kai. Shima kan ya girgiza mata yana k'ara mik'a mata cup d'in.
"ALLAH na k'oshi Yah Saif". Tace cikin marairaice murya daji kasan k'iris take jira ta saki kuka.
"Ban tab'a fad'a miki banason gardama ba". Yace cikin tsare gida yana wani k'ank'ance mata ido, baki ta d'an tura a ranta take fad'in 'Koma iya rarrashin mace baiyiba'. Hannu yasa ta karb'a takai baki ko rabi bata shaba ta mik'a masa cup d'in.
"Shanyewa zakiyi". Ya fad'a cikin bada umarni. Kai itadai ta shiga uku da wannan mutumin tace ta k'oshi bazai k'yaleta ba dan mugunta.cikin ranta tayi maganar tana kyab'e fuska kamar zatayi kuka.
"ALLAH Yah Saifu na.......shiru tayi saboda irin kallon dayayi mata gashi ya had'e fuskar bawani alamu na wasa samanta, dolenta ta maida cup d'in bakinta ta kafa kai saidata shanye ta mik'a masa cup d'in karb'a yayi shima ya zuba ya shanye sannan ya tashi ya fita tabi bayanshi da harara, bathroom ta shiga tayi brush tadawo ta k'ara zama inda take, tana zama ya shigo d'akin kai tsaye ya wuce toilet shima d'in brush yayi ya fesa mouth freshener ya fito.
Tana ganin fitowarshi ta mik'e tsaye ta nufi inda yake ajiye Alqur'anai, tsaye yayi ya kama k'ugunshi da duka hannayenshi yana kallonta soyake yaga iya gudun ruwanta, Alqur'ani d'aya ta d'auko k'arami ta juyo tayi tsaye tana kallonshi.
"What are u doing?". Ya fad'a yana shafa sumar kanshi. Da iya gaskiyar ta tace
"Karatu zanyi fa". Kamar zaiyi dariya saikuma ya maze hannu d'aya ya zura cikin aljihun jallabiyyahr d'ayan kuma ya shafo bayan kanshi zuwa gaban yana kallonta ta k'asan Idanu kafin ya fara takowa wajenta yana fad'in
"Okay good girl, but bari in fara d'ora miki nawa karatun kafin kiyi wannan right?".
Kai tashiga girgiza masa kamar zatayi kuka tace
"ALLAH Yah Saif kullum kafin in kwanta sainayi karatu ka tambaya kaji".
"Nima ai bance baza kiyiba taya zan hanaki samun lada amma bari in fara biya miki kalar nawa karatun yarinyar kirki". Yace lokacin daya k'arasa inda take yasa hannu ya amshi Alqur'anin ya maidashi ma'ajiyarshi, cak ya d'auketa in a bridal style ya nufi bed da ita.
"Wayyo ALLAH dan ALLAH Yah Saifu kayi hak'uri dan ALLAH". Tayi maganar cikeda rauni tana cusa kanta a k'irjinshi.
Kunnenta ya sumbata yana fad'in
"Tun kafin in fara komai".
"Na rok'eka kaji Yah Saifu". Tace cikin kuka.
Bakinshi yakai kan kunnenta cikin rad'a yace
"I'm sorry Mrs Saif". Saidaya kashe k'wayayen d'akin ya kunna dump light purple dake kan bedside drawer sannan ya hau gadon da ita ya kwantar da ita ya zare hijabin ya jefar a nutse cikin wani irin salo ya shiga romance d'inta ta ko Ina yake aika mata da hot kisses da duk inda yaci karo dashi a jikinta saikuma tayi lak'was ta daina turje turjen datake alamun ta fara accepting d'in sak'onnin nashi saidaya tabbatar daya gama kashe mata jiki da salonshi tayi sanyi sannan ya nemi gabatar da kanshi gareta ganin ya canza salon wasan nashine yasa ta fara girgiza masa kai tana fad'in
"Dan girman ALLAH Yah Saifu kayi hak'uri kayimin rai wllhy na tuba dan ALLAH kaji tausayina".
Cikin rawar murya yace
"I'm sorry My Easha ki taimakeni please".
Cikin muryar kuka tace
"Ni zaka taimaka Yah Saifu na rantse da ALLAH bazan k'ara yimaka rashin kunya ba wllhy duk abinda kace zanyi na daina yimaka musu". Ganin tana b'ata masa lokaci yasa ya cigaba da k'ok'arin samarwa kanshi nutsuwa gaba d'aya jikinshi rawa yake itama haka, addu'ar da ANNABI ya koyar ta saduwa da iyali ya karanto cikin rawar murya ya fara gabatar da kanshi. Wata uwar k'ara Ayshaa ta k'walla tareda kama damtsen hannunshi ta rik'e gam tana cije baki lokacin daya fara ratsata yayi hanzarin toshe mata bakin da nashi.
Tunda tasamu ya sakar mata bakin ta shiga raira kuka da masa magiyar yayi hak'uri dan ALLAH ya k'yaleta amma dayake bawai yana cikin hankalinshi bane sai sam baya jinta burinshi kawai a lokacin yasamu nutsuwa ya juye abinda yayi shekara da shekaru yana tarawa.
ALLAH sarki Ayshaa kin had'u da tsohon tuzuru .
Duk irin magiyar data dinga antaya masa baisa ya sarara mataba ya zamar mata wani kurman k'arfi da yaji a lokacin ya manta da yarinya yake tare duk sunan dayazo bakinta fad'a take sunan Mamie da Ammi kuwa da suna yana k'arewa danasu ya k'are a wannan ranar saboda yadda ta dinga antaya musu uban kira tana cewa suzo su ceceta Yah Saifu zaiyi kisan kai, har ALLAH ya isa tayi masa batareda tasan tayi d'in ba harda cewa har duniya ta nad'e bazata tab'a yafewa ba.
(Yasin Saif bakada imaani).
Haka Saif ya cigaba da jigata ta har zuwa lokacin da ALLAH ya k'waceta a hannunshi yasamu nutsuwa zuwa lokacin ko d'an yatsanta bata iya d'agawa tsabar wahala kukan ma ta dainashi ga uban gumi dama da suka had'a gaba d'ayansu saiya had'u da hawaye harda majina duk ya b'ata mata fuska idanun nan nata sunyi ja sosai sun k'ank'ance samansu kuma ya kumbura tsabar wuya ko iya bud'esu batayi sosai.
Wani irin matseta yayi a k'irjinshi idanunshi a rufe k'ara tasaki saboda matsar dayayi mata amma saboda muryar tata datake a dashe yasa sam baijita ba wata soyayyarta ce ke fisgarshi tana ratsa duk wasu b'argo da jinin jikinshi jiyake tamkar ya bud'e k'irjinshi yasata ciki, wani irin shauk'i ke ratsashi dabai tab'a tsintar kanshi a cikiba sai ajiyar zuciya yake saki akai kai yau Ayshaa tayi masa maganin damuwarshi ta kaishi wata duniya ta daban ta jiyar dashi dad'i ta sanyashi cikin farin ciki da annashuwa saidai yasan ya bata wahala shi kanshi yasani yaso kuma ya tausaya duba da irin shekarunta saidai kuma hakan ya gagara dan wani irin maganad'isu ne ya dinga fisgarshi gareta tamkar mayen k'arfe haka ya lik'e mata ya kasa raba jikinshi da nata.
Cikin tataccen speech ya shiga fad'a mata wasu special words da sama sama ta dinga jinsu saboda wani wahalallen barci dake shirin d'auketa, Ashe labarin first night take ji saiyau ta tabbatar bata tab'a sanin Saif yasan takan salon mugunta ba saiyau dataji a jikinta wllhy indai hakane wajen Mamie zata dinga guduwa da dare bazata zauna ya kasheta ba wannan azabar wuya haka lallai duk macen data zubar da mutuncinta a waje batasan da sunan dazata kirata ba.
Gaba d'ayansu barcin yayi gaba dasu ita na wahala yayin dashi kuma yayishi cikin jin dad'i da farin ciki mara misaltuwa.
Mrs Salees Mu'az ❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu
(Ummee).
*Mg's skincare*
Hi my people♀️
Ina gaisuwa
Toh albishirinkuku karkade kunnuwanku kuji inamai sanarmaku cewa set dinmu ayanzu yazama available maiso yarugo aguje karya tsaya Sanya ayi babushi☺️kundaisan kayan *mg's* dabanne ba karya indai tafannin gyaran jikine kunsan yanda sabulun mg's herbal whitening black soap kemaida fata tazama Babu kuraje, pimples, acne,eczema, stretch mark, knuckles,black head,spot,dama duk wani matsala daya danganci fata duk wnd yayi anfani dashi yasan yanda yake maida jiki yazama abun burgewa abun kwatance, fata tadinga haskawa tana walwali duk inda kikashiga sai anyaba toh Inaga wannan zazzafan set Mai maida tsohuwa yarinya☺️Uwargida Takoma amarya amarya Takoma tamkar yanmata❤️yanmata Kuma sudawo Yan Sha shida fata tadinga walwali tana daukan Ido wani abun ba'a magana shiru akeyi sai Wanda yajaraba shine zai karasbama cika Baki duk wnd yagwada shine zaifadi ynd product din mg's yake❤️Kuma munakara Fadi cewa kayanmu organic ne bana bleaching ba suna tsagwaran gyaranjiki ne fiye da tunaninku kuyi kokari kushigo Kuma adama daku Wanda bayada halin siyan set toh sabulun mg's kadai kukarike kankat ne insha Allah
Set dinmu yakunshi
Soap,body cream,face cream,body nd face scrub, cleanser,
Price:13k
Kaman ynd nafadi Wanda bazasu iyasiya set ba sabulun kadai zaibaku mamaki shikadai kukayi anfanidashi zaigoge duk wn prblm na skin living the skin fresh,smooth nd make the skin to glow set din kawai zaikara murje fatane buh ko soap mutum yake anfani dashi ba'a magana
Soap price:3k
Mai bukatan Kaya should chat:08062991549
Call:08064532391
To plc ur order
Munada komai available now so hurry nd grb urs before you hear sold out
Karkubari abarku abaya ko abaku lbr domin kynm yanagyara ko fatan d Mai yabata komutum bashida komai zai iya using kayan zaisa jikin k yafidda wn kyau medaukan hnkl duk inda kikayi se ankalla,show ur skin some luv domin mata da gyara akasanmujust gv it a try nd ur skin will definitely/forever thank you❤️
Mn Kaya kowani gari buh delivery is not free
Team glow♀️
Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
*DR. SAIF*
Writer: Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
Wannan page d'in kyautane ga y'an group dina wato OUM HANAN CONVERSATION, Ina matuk'ar jin dad'in comments d'inku sosai fa idan kunayi sai inga abin kamar gaske a cigaba da comments thanks so much ALLAH yabar k'auna ILYSM❣️❣️❣️.
No. 39.
Da Asubah.
A hankali ya bud'e idanunshi ya zubesu kan Ayshaa datake barci saidai dagani bawai cikin jin dad'i take barcin ba duba da yadda fuskar tata take a k'wabe kamar wadda zata saki kuka saman idanunta duk sun kumbura tausayinta ne kamashi yasan tasha bak'ar wuya jiya a hannunsa mara misali shima kuma bawai dason ranshi yayi mata wannan zuwan ba. Peck ya bata a goshinta ya zareta daga jikinshi a hankali ya k'ara rufa mata bargo ya nufi bathroom, wanka yayi ya taarkake jikinshi ya d'aura alwalah ya fito baisamu zuwa masjeed bama dan yana fitowa yaji har an idar da sallah hakan yasa ya gabatar da tashi a gida ya dad'e zaune bisa darduma yana addu'o'e kafin ya tashi ya koma bed d'in, hannu yasa ya yaye blanket d'in ya tsurawa fuskarta Ido son samune yabarta ta huce barcin gajiya amma kuma dole zatayi sallah ai dan haka ya kai bakinshi cikin kunnenta yana kiran sunanta a hankali.
A hankali ta bud'e idanunta da sukayi mata matuk'ar nauyi ta zubasu kanshi anan ta shiga tariyo abinda ya faru jiya tasaki kuka kuwa harda shasshek'a saboda azabar zafin dataji daga k'asanta duk saiya rud'e cikin rawar jiki ya kamota jikinshi ta zame ta k'ara kwanciya tana cigaba da kukanta.
"I'm so sorry A'eesh, my queen my everything my angel my babynah, uhm muje kiyi wanka kinga time d'in sallah yanata wucewa please". Ya k'arasa maganar yana lashe hawayen dake zubowa.
Banza tayi masa kamar bata jinshi a ranta take fad'in
'Kagama cin zalin nawa zakazo kana wani lak'aba min sunaye'.
"Kinji A'eesh". Ya fad'a cikin muryar rok'o.
Cikin dasasshiyar murya tace
"Nika k'yaleni dama ai nasan ba sona kakeba ka kaini gurin Mamie kawai".
"Wayace miki bana sonki I swear I love you very very much kece komai nawa, uhm muje in gyara miki jikinki kiyi sallah".
Bata kulashi ba ta cigaba da kukanta, duk wani kalar rarrashi Saif ya gwada yinshi amma a banza dama kuma da k'yar yake had'a rarrashin tunda ba sabawa yayiba.
K'aramin tsaki yaja ya sauka daga kan gadon yaga alamun yarinyar nan taurin kan tsiya gareta maybe saiya fito mata a true color d'inshi tunda ita ba'a fad'a mata magana taji, saidai kuma bazai iya hakanba a yanzu dan tana b'ukatar a lallab'ata.
Bathroom ya wuce ya tara ruwa mai d'umi ya dawo inda take har lokacin kuka take blanket d'in ya yaye gaba d'aya tana ganin haka ta k'arawa kukanta volume tana k'ank'ame jikinta. Ganin yana shirin d'aukarta yasa ta dinga fad'in ita bataso ya k'yaleta baibi ta kantaba ya tarairayota jikinshi ya d'agata cak ya nufi bathroom da ita, sam bata da k'arfin da zata yimasa jayayya hakan yasa tayi lak'was a jikinshi tana sauke ajiyar zuciya.
Yana shiga ya sanyata cikin ruwan daya tara, wata k'ara tasaki tareda fashewa da wani kukan cikin kukan take fad'in
"Dan girman ALLAH kayi hak'uri Yah Saifu ka cireni wllhy inajin zafi please dan ALLAH".
Ido ya lumshe cikin jin tausayinta saiyake jin tamkar shima yayi kukan, a hankali cikeda rarrashi yace
"I'm sorry My Easha kiyi hak'uri ki zauna zakiji dad'in hakan kinji". Ya k'arasa yana shafa gashin kanta daya barbaje saboda wuyar dayaji.
Duk yadda yaso ta zauna sosai cikin ruwan tak'i sai uban kuka take tana zuba masa raki dolenshi ya cireta yayi mata wanka tayi alwalah ya nad'ota cikin towel. Kan bed ya kwantar da ita ya fita zuwa bedroom d'inta, doguwar riga ya d'auko mara nauyi ya dawo yasa mata yasamata hijabinta wanda yayi fatali dashi jiya kan dardumar dayayi sallah ya tsaidata yace tayi sallahr ya zauna yana kallonta, da k'yar tayi sallahr tana hawaye saboda zafi musamman idan tazo yin sujjadah tana idarwa kuwa ta zube bisa dardumar ta k'udundune cikin hijab d'inta.
Numfashi ya sauke tareda fesar da iskar bakinshi ya lumshe idanunshi yana murza goshinshi ya rasa ta inda zai b'ullowa lamarin, tashi yayi ya isa inda take ya d'auketa cak ya maidata kan gadon gabanshi ya fad'i lokacin dayaji hucin zafi wanda ya kasa b'oyuwa ya fito ta cikin hijabin.
"My Goodness". Ya furta hakan yana d'an runtse Ido gamida dukan goshinshi, zazzab'i ne kenan ya rufeta Yaa ALLAH.
Tashi yayi ya shiga zagaye a d'akin gashi bashida injection bare yayi mata ya tabbatar Mamie tana da ita amma aida kunya ya tunkareta da wannan maganar jin ta cigaba da kukan yasa ya tashi ya nemi pain reliever ya zubo ruwa a cup ya kawo mata saida yayi mata jan ido sannan tasha ta koma ta kwanta ta d'ora daga inda ta tsaya. Shidai baisan me kuma zaiyiwa yarinyar nan ba tayi shiru yaga alamun rarrashin nashi ma tamkar k'ara zugata yake ga jikin nata dayake k'ara zafi. Kusa da ita ya kwanta ya rungumeta sosai duk yadda ta dinga zamewa hakan baisa ya saketa ba dolenta ta hak'ura tayi shiru tana kukan a hankali kafin daga bisani barci ya k'ara surarta shima barcin dabai shirya masa bane yayi awon gaba dashi.
***
Mamie da duk hankalinta ya fara tashi jin shiru ba alamun motsinsu, saita dinga tsoron kar dai ciwon nashine yadawo tayi sauran kauda tunanin a ranta, amma dai zuwa yanzu ai yaci ace sun tashi musamman Ayshaa data saba shiga da wuri itadai duk hankalinta bai kwanta ba hakan yasa ta tura Imaan tace taje tagani ko lafiya?, Saboda duk ta kikkira wayoyinsu is switched off.
Knocking Imaan ta dingayi amma ba'azo an bud'e ba tadawo ta fad'awa Mamie, nan tai hankalinta ya k'ara tashi dan haka ta nufi side d'in da kanta.
Kamar daga sama yaji knocking d'in cikin nutsuwa da dabara yafara k'ok'arin rabata da jikinshi dan karta tashi ta k'ara rud'ashi ALLAH ya taimakeshi tayi barci, aikuwa yana motsata ta tashi ta fara kuka.
"OH My God! Yace cikin runtse Ido da dafe goshinshi yaso ya rarrasheta saidai kuma knocking d'in da aketa k'ara yi yasa ya sauko daga gadon yasa jallabiyyah ya zura slipper ya fita dan ganin waye.
Yana bud'e k'ofar parlor'n yaci karo da Mamie, gabanshi ya fad'i dan sam hasashen shi bai kawo masa Mamie ce ke knocking d'inba duk saiya diririce ya rissina yana gaisheta.
Ajiyar zuciya Mamie ta saki saboda ganinshi datayi lapia lau ta amsa gaisuwar ta d'ora da tambayarshi Ayshaa.
Kanshi ya shiga shafawa batarda yayi magana ba sai data k'ara tambayarshi sannan yace batada lafiya.
A rud'e Mamie ke tambayar abinda ya sameta, baiyi magana ba sai sosa k'eya dayake, tsaki Mamie taja ta wuceshi tana fad'in
"Kuma shine dan shashanci zaka zauna da ita haka saboda wautar d'an fari na d'awainiya dakai". (Kai Mamie bai dad'e da tashi bafa).
Baice dai uffan ba yabi bayanta cikin fad'uwar gaba jiyake tamkar yace mata tadawo basai ta shigaba, jin sautin kukan Ayshaa daga bedroom d'in Saif yasa Mamie ta nufi can da sauri dan da alamu abin babbane tunda kaji tana kuka (shagwab'a ce kawai Mamie da hegen rakin tsiya, team Ayshaa kar a cinyeni d'anya).
A k'udundune ta sameta tana faman kuka, gefen gadon ta zauna tana fad'in
"Subhanallahi mamana meke damunki haka yace min bakida lafiya".
Jin Mamie yasa ta k'ara b'arkewa da wani kukan sai Mamie ta k'ara rud'ewa kuwa tasa hannu zata janyota jikinta, ba shiri ta fasa k'ara saboda azabar zafin daya ratsa k'asanta ta langab'e jikin Mamie tana kuka.
"Ya salaam! Babana wai meyake damunta haka?". Ta fad'a tana kallon Saif dayake jingine jikin bango ya rungume hannayenshi a k'irjinshi, duk yabi ya muzanta saboda kunya yasan dai Mamie ta riga tasan komai tunda tazo yarinyar nan tayi mugun gamawa dashi wllhy sunyi abinsu a sirri tazo ta tona gani yake ma harda shagwab'a da rakinta.(Kunji fa reader's ).
"Wai badakai nakeba zakamin irin halin naka daka saba". Mamie tace a fusace tana kallonshi.
Duk yadda yaso yayi magana kasawa yayi to koya bud'e baki baisan me zaiceba, cemata zaiyi ya kwanta da itane ko kuwa?.
"ALLAH ya shiryaka". Mamie tace tana sakin k'wafa, tana k'ara motsa Ayshaan ta k'ara sakin k'ara. Zuwa yanzu dai Mamie ta fara d'aukar haske kan abinda ya wakana duk saitaji tausayin yarinyar ya shigeta.
Kai ta d'ago ta kalli Saif daya kasa ko motsin kirki saboda azabar kunya, jiyake tamkar k'asa ta tsage ya shige ciki ta ko Ina kunya ke dukanshi.
"A matsayinka na likita wane taimakon ka bata?". Ya tsinkayi muryar Mamie.
"Tasha pain reliever Mamie". Yayi maganar a rarrabe yana shafa sumar kanshi.
"Gidanku da pain reliever d'in, tace tana jefa masa dak'uwa sai yai k'asa da kanshi yana d'an tura baki, fisabilillahi tana irin wannan yanayin shine zaka barta haka a matsayinka na doctor kaji jikinta kuwa yadda ya d'auki zafin zazzab'i danme bazaka yimin waya ba inzo inyi mata allura kokuma kai kaje ka karb'a kayi mata idan ma bakada itane saikuma dan sakarci kabarta haka...... Ayshaa jin an balbale Saif da fad'a yasa ta k'ara langab'ewa jikin Mamie aikuwa Mamie ta k'ara tunzura cikin fad'a tace
"Ka sata cikin ruwan d'umi ko".
Saif dayake jin tamkar ya tsala ihu saboda tsabar kunya ya girgiza mata kai alamun A'ah. Ganin yadda Mamie ta tsura masa Ido yasa yace
"K'in zama tayi Mamie dana sata".
Tsaki Mamie taja tace
"Oyaa daure ki mik'e mamana muje, ba abinda babana ya iya sai sakarci". Ta k'arasa maganar tana taimakawa Ayshaan ta sauko da ita daga kan gadon sai cije baki take tana k'wallah. Rik'eta tayi suka fita daga bedroom d'in suka barshi nan tsaye.
'Gaskiya yarinyar nan ko? Humm zasu had'u ne next.
Bedsheet d'in ya d'auke ya shimfid'a wani shikanshi yanajin jikinshi ba dad'i dama kuma yasan da wuya duk ranar daya tara da mace ba'a samu wannan matsalar ba, wani zazzab'i ne mai zafi yakeson kamashi.
Kai tsaye bedroom d'in Mamie suka wuce da k'yar Ayshaa ke takawa, ita Mamie ma tsoronta d'aya kar ace yajiwa y'ar mutane rauni dan haka dole saita dubata, yaran zamani wato daga tashinshi jiyan nan shine har yayi wannan aika aikan.
Gefen gado ta zaunar da ita ta shiga bathroom ba'a jimaba ta fito ta kama Ayshaan suka shiga ciki tace ta shiga cikin ruwan data tara mata, duk sai a lokacin kuma taji kunya ta kamata tafara nuk'u nuk'u, itadai Mamie bata kulata ba. Da rarrashi da dabara Mamie ta samu ta shiga cikin ruwan aikuwa tasha kuka saboda zafi itadai Mamie sai aikin rarrashi take (Babanki ya b'aro miki aiki). Ruwa biyu tayi mata kuma duk kukan datake baisa Mamie ta rabuda itaba saidata tabbatar ta gasu sosai ta kamota suka fito Ayshaa sai kunya take ji Mamie dai batasan ma tanayi ba dan ita a ranta duk abinda take mataba bawai a matsayin suruka ta d'auketa ba A'ah kallon d'iyarta ta cikinta take mata yadda Amminta zata tsaya ta kula da ita haka itama zatayi.
Tana zaunar da ita kan gadon ta b'ingire ta kwanta, fita Mamie tayi bata wani dad'e ba tadawo hannunta d'auke da mug had'add'en tea ne a ciki mai kauri ta bata tasha ta koma ta kwanta dan bata iya zaman sosai. Wata drawer Mamie ta janyo daga k'asan wardrobe ta ciro hand glove ta saka tadawo tace ta gyara zata dubata kar aje koda ciwo ayita zama kuma a haka, da k'yar Ayshaa ta yadda Mamie ta dubata, Dole yarinya tai kuka Mamie ta raya cikin ranta ganin yadda gaban Ayshaan ya koma bata k'aru ba dai amma kowaye yagani yasan taji jiki ba kad'an ba dagani zuwan dayayi mata bana hankali bane, duk tausayinta ya k'ara kamata. Allura ta had'a ta zazzab'i nan ma da k'yar ta yadda akayi mata tanata kuka.
"Haba mamana kukan ya isa haka mana uhm, kiyi hak'uri duk wata mace da kika gani saida ta taka wannan mataki kizama jaruma mana masu sunanki da jarumta aka sansu shikuma ki k'yaleni dashi zamu gauraya nida shi I'm sorry kinji Momynah". Kai ta d'aga mata tana share hawaye kwantar da ita tayi ta lullub'a mata k'aton bargo tace tayi barci sannan tabar d'akin.
)(((()))))(
Saif dayaji abin na k'ara gaba duk yadda yaso ya daure ya kasa dole saiyaga Dr Sooraj yana faran akwai irin allurar dayake b'ukata.
Wanka yayi ya shirya cikin bak'in wando da farar riga da akayiwa ado da bak'in fenti a gaban rigar rolex watch ya d'aura mai bak'ar fata ya d'ora P. Cap bak'a mai adon fari a gaban hular yayi matuk'ar yin kyau ya fesa turaruka ya d'auki wayarshi da key d'in motarshi ya fito bayan ya rufo part d'in.
Yana k'ok'arin bud'e mota yaji anyi horn maigadi ya bud'e saiga Mukhtar ya shigo a motarshi, tsaye yayi yana kallonshi yana tunanin ubanda yazoyi kuma. Parking Mukhtar yayi ya fito sai a lokacin ma ya kula da Saif motar ya kulle ya nufo Saif d'in yana murmushi yana k'arasawa ya bashi hannu sukayi musabiha.
"Yaaa Ina zuwa ne?". Mukhtar yayi tambayar.
Saif dabaiso ya gane halin dayake ciki yace
"Me kazo yine wai Mukhtar".
"Ina ruwanka, Hajiyata ce ta aikoni wajen Mamie, amma yana ganka kamar ba lafiya ba?".
Ido ya runtse saboda yadda yaji jikinshi ya d'auka cikin k'ashinsa sai wani irin zuuu yake masa, driving d'inma ba lallai ya iyaba dan haka ya kalli Mukhtar yace
"Muje please ka kaini hospital banida lafiya".
Ido Mukhtar ya d'an zaro yana fad'in
"Meya sameka haka?".
Cikin fad'a yace
"Dallah malam muje banson d'an banzan surutu". Gaba Mukhtar yayi yana fad'in
"Aifa ka tashi masifaffe".
Tunda suka tafi Saif baiyi magana ba duk kuwa da uban surutun da Mukhtar ke zuba masa baisa ya kulashi ba shi kad'ai yasan meyake ji, relaxing yayi kan seat d'in ya rufe idonshi da P.Cap d'in idanunshi a rufe moment d'in daya shiga jiya yake tunawa hak'ik'a Ayshaa ta kaishi wata duniya ta daban mai dad'in gaske wadda zai ajiyeta cikin kundin tarihin rayuwarsa ta cikin P.cap d'in ya saki wani murmushin gefen baki saboda tuna irin action d'in daya dinga yi jiya lokacin dayake tare da ita duk da bawai yana cikin hankalinshi bane amma yana tuna wasu maganganun dayayi na sambatu.
Har suka isa hospital d'in bai bud'e fuskarshi ba, bayan sunyi parking Mukhtar ya sauka shima ya fito yana gyara P.cap d'in kanshi aikuwa yana fitowa akayo kanshi ma'aikatan asibitin leburori da masu kula da masu jinya kowa yana tayashi murnar tashi da yayi dole ya d'an saki fuskar ya shiga gaggaisawa da mutane tuni aka bud'e masa office d'inshi dayake a gyare tsaf kamar lokacin dayake nan da alamu kullum sai an gyarashi, saidaya shiga office d'in sannan suka barshi, suna shiga ya nemi guri ya kwanta kan doguwar kujera dake cikin office d'in saboda jirin dayake d'ibanshi, hannun kujerar da Saif ya kwanta Mukhtar ya zauna yana shirin yin magana Dr Sooraj ya shigo.
"Ur highly welcome back DR SAIFULLAH". Dr Sooraj ya fad'a yana mik'a masa hannu sukayi musabiha sannan ya mik'awa Mukhtar shima sukayi yana k'ara taya Saif murna.
Da turanci Saif yake tambayar Dr Sooraj allurar dayake so ayi masa.
Murmushin shak'iyanci Dr Sooraj yayi yace
"Akwai ta big doctor ALLAH yayi kenan an amayar dashi". Harara Saif ya maka masa batare dayayi magana ba dai, Mukhtar kam dayake hankalinshi nakan waya suna chatting da Imaan hakan yasa bai kulada abinda suke fad'a ba.
Fita Dr Sooraj yayi bai jimaba ya dawo hannunshi d'auke da drip dawasu allurai ya fara had'awa sai lokacin Mukhtar ya tambayi Dr Sooraj allurar meye wannan?.
Dayake kanshi na k'asa yasa baiga irin kallon da Saif yake masaba alamun karya fad'a masa Dr Sooraj ya shiga yiwa Mukhtar bayani a tak'aice. "Yesssooo". Mukhtar ya fad'a yana dunk'ule hannayenshi tareda sakin wani d'an k'aramin ihu, shegen gora yaushe hakan ta faru?". Banza Saif yayi masa ya tashi zaune yana nad'e hannun rigarshi inda za'ayi masa allurar.
Aifa Mukhtar ya samu abinyi nan ya tasashi gaba da shegantaka iri iri shidai bai kulashi ba ya koma ya kwanta akasa masa drip d'in Dr Sooraj ma saidaya d'an tab'a tashi tsokanar sannan ya fita yana yiwa Mukhtar dariya jin irin maganganun dayake b'arowa ba abinda yasha masa kai.
"D'an iska wato kaida jin dad'i shine zaka bar mana Mamien mu da jinya ko?".
A fusace Saif ya d'age P.cap d'in daya rufe idanunshi yace
"Na rantse Mukhtar zanci ubanka waikai d'an iskan inane". Ya k'arasa maganar yana sakin k'wafa tareda maida hular ya k'ara rufe idanunshi.
"Ka dallah kauce, munafuki nan ka gama cika mana baki kai yarinyar nan ba abinda zatayi maka kaza kaza finally dai k'aramar yarinyar dai ka saukewa jarabar taka girman dai da ba'a so ya fad'i ya riga ya fad'i". Ya k'arasa maganar yana sakin dariya.
K'ala Saif baice masa ba dan iskancin Mukhtar yafi k'arfinshi.
"Wai dan ALLAH da zaka fara mekace mata?". Ya tsinkayi muryar Mukhtar na fad'a.
"Ubanka nace mata". Saif yace kai tsaye batareda ya bud'e idonshi ba.
Dariya Mukhtar ya shek'e da ita yana mik'ewa tsaye da fad'in
"Masha ALLAH yaro ya girma, bari mutum shima dai yazo yayi auren nan muji abinda masu shi sukeji". Bai saurari Saif ba ya fice daga office d'in.
Tsaki Saif yayi a fili yace
"Shege uban y'an surutu mutum saikace aku.
*** *** ***
Ayshaa barcinta tasha sosai sai Azhar sannan Mamie ta tasheta lokacin zazzab'in ya sauka ta k'ara had'a mata wani ruwan d'umin ta shiga tayi wanka tayi sallah ta kawo mata abinci, da k'yar ta samu taci kad'an saboda yadda bakinta ke mata d'aci ta k'ara komawa ta kwanta.
Koda Imaan taga Ayshaa a d'akin Mamie a kwance take tambayar Mamien saitace mata batada lafiya ne zazzab'i take. Imaan dai tasan a zahiri ba abinda aka fad'a mata bane yayanta ne yayi aiki duk sai tausayin Ayshaan ya kamata ashe da aiki a gabanta yadda Yah Mukhtar yake da shegen rawar kan nan aita kad'e koda yake ace irinsu Yah Saifu masu simi simi d'in nan da rashin magana sunfi sanin takan tsiyar.
Barci ne mai nauyi ya d'auki Saif, sai Azhar ya tashi yayi sallah ga cikinshi dake neman agaji yunwa yakeji matuk'a, ALLAH ya taimakeshi Dr Sooraj ya shigo ya bashi wata leda da take away yace Mukhtar ne yakawo masa. Bayan yagama ci yayi brush ya k'ara kwanciya dan kamar allurar tanasa barcine. Amma sosai yaji dad'in jikinshi garau yake jinshi.
Lokacin daya farka ma la'asar ta d'an wuce, yayi alwalah ya gabatar da farali daga nan ya kira Mukhtar yace yazo ya d'aukeshi.
Tunda suka tafi hanya Mukhtar yake tatawa Saif iya shege, bai tanka masaba dan baisan me zaice d'in ba seat d'in ya kwantar ma ya shiga latse latsenshi a waya batare dayabi takan Mukhtar ba.
Mukhtar yaso shiga yaba Mamie sak'on da hajiyan shi tabashi saikuma Babanshi yayi masa waya yana nemanshi da gaggawa hakan yasa ya juya batare daya shiga ba yace dai zai dawo da dare idan kuma baisamu dawowar ba sai zuwa gobe in ALLAH ya kaimu.
Bai samu kowa a parlor'n ba, yaso ya wuce side d'insu saidai kuma zuciyarshi daketa ingizashi yaje yaga halin da babynshi ke ciki hakan yasa ya wuce bedroom d'in Mamie yana addu'ar ALLAH yasa Mamie bata ciki.
Addu'ar shi kuwa ta karb'u dan baisamu Mamien a cikiba, ya hango Ayshaa a kwance daga gefen gadon tana barci a lullub'e da blanket duka jikinta sai iya kanta dake bud'e. Ajiyar zuciya yasaki yana d'an lumshe ido a hankali ya shiga takawa inda take, tsaye yayi a bakin gadon yana k'are mata kallo yadda fuskarta tayi wani fayau hancinta ya k'ara fitowa ta tsuke bakinta mai kama da gidan tsutsa saboda k'ank'anta.
"Sleep beautiful, wato a barcin ma rashin kunya takeyi". Yace k'asa k'asa yana tsugunawa gaban gadon inda take kwance, cikin nutsuwa yakai bakinshi kan goshinta ya sumbata tareda kai hannu kanta da hular ta zame fiyeda rabi yafara shafa gashin kanta.
Kamar a mafarki taji kamar ana tab'a ta, a hankali ta fara bud'e idon harta bud'esu gaba d'aya ganin wanda ke gabanta yasa tayi saurin zabura saikuma tasaki k'ara tana komawa ta kwanta tana cije baki.
"Oh I'm sorry baby ya jikin naki?".
Kai tsaye tace
"Ba sauk'i". Yayin da k'wallah tafara cika idonta, ita wllhy tsoronshi ma takeji
"Oh my God, A'eesh ba sauk'i fa kikace?".
"Eh, kuma ka fita wllhy ko in kira maka Mamie".
"Really?". Yace yana wani waro idanu, ganin kamar rainin wayo ne abin nashi yasa ta bud'e baki da niyyar kiran Mamie da hanzari yasa hannunshi kan bakin nata shiru tayi tana kallonshi shima kallon nata yake fuskarshi d'auke da wani tattausan murmushi, hannun nashi ya cire ya tsurawa bakinta Ido kafin ya fara kusanto da fuskarshi zuwa tata, Ido waje take kallonshi a tsorace ganin abinda yake shirin yi, cikin rawar murya da son yin kuka tace
"Please Yah Saifu kabari dan ALLAH ka fita kar Mamie ta shigo ta ganka".
"Kiss kawai zanyi bawani abu ba A'eesh".
Kai ta shiga girgizawa kamar zatayi kuka tana fad'in
"Na rok'eka Yah Saif dan ALLAH bedroom d'in Mamie nefa".
"Malama sai nayi kiss d'in nan fa". Bai bata damar magana ba ya shigar da bakinshi cikin nata idanunshi a rufe rabin jikinshi duk yana kanta.
((Saif dama haka kake macijin sari ka nok'e)).
Mrs Salees Mu'az ❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu
(Ummee).
Haske writer's association
(Home of expert & perfect writer's).
*DR. SAIF*
Writer: Oum Hanan.
Bismillahir Rahmanir Raheem.
No. 40.
Cikin nutsuwa yake kissing d'inta, Ayshaa k'wallah kawai take a ranta tana raya cewa 'Mutum mara kunya dai baiyiba wllhy dan ALLAH dubi abinda yake mata a d'akin Mamie akan gadonta wllhy mutumin nan wanda baisan shiba bazai tab'a kawowa haka yakeba ita kad'ai zata d'orar da hakan yanzu, batada k'arfin da zata iya k'watar kantaba to koma tanada k'arfin Ina zata iya da wannan k'akk'arfan?.
Saif kam tuni ya fara manta a inda yake har hannayenshi sun fara yawo a sassan jikinta hakan ya k'ara tada hankalin Ayshaa ta shiga tunanin yanzu idan Mamie ta shigo ta gansu a haka fa saboda ALLAH wani irin kallo zatayi mata. Jin kamar tafiya yasa Ayshaa k'ara rud'ewa ta shiga kici kicin k'wacewa, shima d'in daya fara barin jihar dayake ALLAH ya taimakeshi yaji hakan yasa yayi saurin tashi yana sauke numfashi a jajjere tareda gyara hularshi data kusa fad'uwa. Mamie ce ta bud'e k'ofar ta shigo hannunta d'auke da k'aramin cup mai murfi, turus tayi tana kallon Saif dayayi wuri wuri da ido alamun mara gaskiya, tun daga bakin k'ofar Mamie ke dank'ara masa harara harta isa inda yake tsaye. kallon tuhuma tabishi dashi cikin had'e fuska tace
"Me kazo yi nan?". Bai amsaba sai k'eya dayake ta faman sosawa yana idonshi a k'asa.
"Bakaji abinda nace ba?". Mamie ta k'ara fad'a a hasale tana kallonshi.
"Nazo duba jikinta ne Mamie". Ya fad'a cikin in Ina da rarraba maganar yana shafa gefen wuyanshi.
Hanyar fita ta nuna masa da hannunta tace
"Toh zoka wuce, idan kasake na k'ara ganin k'afarka a d'akin nan ALLAH saina b'ata maka rai, kabar yarinya ta huta kaji na fad'a maka".
Wucewar yayi yana satar kallon Ayshaa da tun shigowar Mamie ta rufe kanta da blanket tayi shiru kamar mai barci.
"Fitsararre". Mamie tace tana binshi da kallo lokacin dayake ficewa daga d'akin, batasan yaushe babanta yazama mara ta Ido hakaba.
"Mamana tashi ga kunun gyad'a na damo miki maybe idan kikasha kiji dad'in bakin naki". Mamie tayi maganar tana ajiye cup d'in bisa side drawer.
Shiru Ayshaa tayi tamkar irin mai barcin nan, itakam kunyar had'a Ido take da Mamie wllhy shiyasa tayi shirun nan. Murmushi Mamie tayi dan tasan tana jinta ta juya ta fita tana fad'in idan ta tashi tasha.
Da dare.
Har dare Ayshaa tana d'akin Mamie ko parlor bata fitoba, Saif ya kafa ya tsare a cikin parlor'n sai raba idanuwa yake yana hangen ta inda zata b'ullo saidai ba ita ba labarinta gashi yanajin kunyar tambayar Mamie.
Mamie tana kula dashi ta nuna kamar ma batasan yanayi ba dan tayi alk'awarin ko zata koma sai gobe ta d'an warware kar yaje ya k'ara b'aro wani aikin kuma na daban.
Ganin bawani labari yasa ya tashi yayiwa Mamie sallama ya shige side d'insu.
Ayshaa kam dad'i taji sosai dataji Mamie tace tayi kwanciyarta a nan dan dama harga ALLAH zullumin had'uwarsu da Yah Saifu take dan gamonta dashi bataji da dad'i ba.
Wanka yayi ya shirya cikin kayan barci ruwan madara, ya fito zuwa kitchen ya had'a coffee ya koma bedroom yasha ya kwanta, da k'yar bacci ya d'auke shi saboda kewar Ayshaansa jiyake inama tana tare dashi a yanzun.
Ayshaa dai sai washegari da yamma Mamie tace ta koma part d'insu ta warware itadai bataso hakaba dan ba yadda zatayine kawai, da Imaan sukaje ta tayata gyaran part d'in tare sukayi girki ma tayi wanka ta shirya cikin doguwar riga ta wani plain yadi orange color sai k'amshi take bulbulawa. Sai bayan sallahr magreebah Imaan tabar side d'in.
Shikam saida akayi sallahr Esha ma ya shigo gidan, bayan yaje ya gaida Mamie ya wuce part d'insu.
Tunda ya shiga yake manne da Ayshaa ba damar ta d'ara nan da can itadai dayake a tsorace take yasa bata wani saki jikinta ba.
Lokacin da sukazo kwanciya kuwa tun kafin ya fara komai tafara kuka tana bashi hak'uri a yadda yake jinshi kam bazai iya d'aga mata k'afa ba hakan yasa cikin rarrashi da dabara da dad'ad'an kalamai yasamu ta yarda dashi amma duk da haka a tsorace take, A hankali yabi da ita cikin nutsuwa bataji zafiba kamar na farko amma duk da haka saidata cikashi da rakinta shikuma ya lalace nan wajen rarrashi.
Cikin lokacin nan suke dagargazar amarcinsu, wata muguwar shak'uwa da soyayya data ninka tada ta k'ara shiga tsakaninsu zamansu gwanin sha'awa,Mamie tana matuk'ar jin dad'in hakan kullum cikin binsu da addu'a take. Saif dai ya fitsare dan baya shakkar nuna mata soyayya ko a gaban waye ba ruwanshi inka ganshi bazakace zai aikata ba shiyasa Ayshaa batason suna shiga wajen Mamie tare dan ya dinga bata kunya kenan, Mamie kam saidai tace ALLAH ya shiryashi dan mace ta canzashi kuma bawai ya daina miskilancin nashi gaba d'aya bane dan ita kanta Ayshaan wani lokacin idan suka motsa saita kasa gane kanshi. Ya cigaba da gininshi dan angama komai ma saidai y'an sauran gyare gyaren daba za'a rasaba, ginine irin na zamani bawani irin k'aton gida bane saidai an narka masa dukiya an kuma tsarashi irin tsarin gidajen turawa.
Mukhtar ma ansa rana da Imaan duka 3mnt akasa inda bayan auren zata cigaba da karatunta zokuga rawar k'afa wajen Mukhtar aikuwa yasha zagi wajen Saif harda cemasa k'aton banza sai rawar k'afa yake akan k'aramar yarinya Mukhtar yace tsakaninsu dai za'a ga k'aton banzan tunda dai duk yaran ne saiya rasa amsar mayarwa Mukhtar yaita masa dariya.
★★★ ★★★ ★★★
Mansurah.
Gaba d'aya ta gama fita hayyacinta kullum cikin surutai take marasa tushe saita fara magana kamar mai lafiya saikuma ta baud'e ta koma na marasa hankali ga makanta har yanzu bata gani abin yana matuk'ar damun Madeenah yau dai ta d'auki aniyar zataje ta rok'i Safnah ta rakasu wajen Saif ta nemi yafiyarshi, farko Safnah cewa tayi ba inda zata kuka Madeenah tasa ta shiga rok'onta Hajia Binta dai tausayin Madeenah yasa tacewa Safnah ta rakasu d'in. Safnah yanzu ta cire Saif a ranta gaba d'aya tunda abin nan yafaru ta k'ara sallamawa lamarin
ubangiji tayi ala wadai da halinta na baya ta kasa gano cewar dama can ALLAH bai tsara Saif mijinta bane dama kuma fad'ar ubangiji cikin Alqur'ani mai girma dayake cewa.
Sau dayawa zakaso abu dakake tunanin alkhairi ne saiya zamar maka sharri, wanda kake tunanin sharrine saiya zamar maka alkhairi to k'ila Saif d'in ba alkhairi bane a gareta tayi matuk'ar murna dataji Saif ya warke kuma tasan addu'ar da aketayi ce tayi tasiri har akayi sanadin da asirin ya karye ta hanyar Madeenah. Zuwa yanzu ta rik'e Naseer da hannu bibbiyu tana fatan yazame mata alkhairi a rayuwarta har ansa rana ma sai jiran lokaci idan ALLAH yakai rai.
Washegari Safnah ta jagoranci Madeenah da Mansurah zuwa gidansu Saif, sai shirme Mansurah ke zuba musu a mota, ita Safnah ma tsoronta take ji duk da bata komai.
Su Mamie sunyi mamakin ganin Safnah dasu Madeenah sukaita mamakin abinda ya had'ata da mai tab'in hankali, Safnah ce tayiwa Mamie bayani kan cewar Saif sukeson gani zasu rok'i afuwarshi nan Mamie ta shiga tunanin meye kuma ya had'a yaronta da wad'annan mutanen musamman dataji Safnah tace wai tsakanin Saif ne da mara hankalin. Bata dai tambayi ba'asin abinda ya had'asu ba koma meye zasuji idan Saif d'in yazo dan haka tayi kiran wayarshi tace suzo shida Ayshaa tana nemansu dayake weekend ne yana gida lokacin yana nane da Ayshaa sunata shan love d'insu
Hijabi har k'asa Ayshaa ta d'ora kan matsattsun riga da wandon dake jikinta, shikuma yasa wandon shaddar daya cire ya d'ora jallabiyyah akai suka fita.
Tunda suka shigo ya d'ora idonshi kan Mansurah gabanshi yayi mugun fad'uwa da tunanin abinda ya kawota gidan nan, zama sukayi yana k'ara kallon Mansurah daketa zuba shirme.
"Mamie meya kawo wad'annan gidan nan".
Saif ya tambaya yana nuna su Mansurah da hannunshi.
"Toh gasu nan dai Safnah ta kawosu wai zasuyi magana dakai ka sansu ne?". Mamie ta amsa masa.
Ido ya d'an runtse tareda sauke numfashi kamar bazaiyi magana ba saikuma yace
"Na santa Mamie bazan tab'a mantawa da fuskarta ba". Da mamaki Mamie da Ayshaa harda Imaan suka kalleshi sai Daddy daya shigo parlor'n yanzu.
"Meya had'aka da ita har k'anwarta take fad'in sunzo neman yafiyarka me kuma tayi maka har take neman afuwarka". Daddy ne yayi maganar yana kallon Saif.
Numfashi Saif ya sauke kafin a hankali ya shiga basu labarin had'uwarshi da Mansurah.
Flashback.
Saif bai dad'e da dawowa daga karatu ba Daddy ya tab'a aikenshi da sak'o wajen Hajia Binta wato maman Safnah a kaduna.
Bai tafi da wuriba dama dan haka sai yammaci lik'is sannan ya isa, bayan sun gaisa ya bata sak'on bai wani zauna sosai ba yayi haramar tafiya kasancewar lokacin damuna ne hadari ya had'o sosai lokacin ga magreebah tayi hakan yasa Hajia Binta ta nemi daya kwana sai washegari ya wuce shikuma yace A'ah tafiya zaiyi, sanin taurin kan Saif yasa Hajia Binta bata matsa masaba tabishi da addu'ar sauka lafiya ya tafi.
Yana shiga motarshi kuwa iska ta taso mak k'arfi kafin ruwa ya biyo bayanta hakan baisa Saif ya komaba haka ya fita daga layin ya d'auki hanya.
Lokacin daya hau babban titi yafara tafiya kenan d'an nesa dashi ya hango wata mata sanye da hijab tana tsaida shi, koda yazo inda take bai tsayaba yayi gaba abinshi ba kuma yak'i tsayawa bane dan tsoro saidai dan yadda duniyar nan tamu ta lalace wani zaka ganshi yana b'ukatar taimako amma mugune kuma taimakon dazakayi masa bashi zaisa ya k'yaleka ba shiyasa mutane dayawa sukejin tsoron taimakawa mabuk'ata da basu saniba a wannan zamanin namu mai cikeda abubuwan ban tsoro da al'ajabi.ALLAH yasa mu dace .
Har yayi gaba dai kuma wata zuciyar ta dinga umartarshi daya dawo ya taimaka mata shima baisan ta inda ALLAH zai taimakeshi ba hakan yasa yayi ribas ya dawo inda take tsaye yayi parking tareda bud'e mata front seat alamun ta shiga, aikuwa cikeda jin dad'i ta bud'e ta shiga ruwa duk ya jik'ata.
"Nagode fa". Matar ta fad'a lokacin datake k'ara daidaita zamanta akan kujerar.
Lokacin yana ganiyar y'an miskilancin hakan yasa ko kallonta baiyiba ya cigaba da driving d'inshi kamar ma ba magana tayiba, saitaji gayen yayi matuk'ar burgeta take shayd'an yafara raya mata wasu mugayen nufi a kanshi, kamar ance ya waigo kawai idanunshi suka sauka kan matar nan ta cire hijab daga ita sai bra and pant sai wani shafa k'irjinta take tana lumshe ido, wani mugun fad'uwa gabanshi yayi ya zaro ido gamida saurin kauda kai yana ta'awizi cikin ranshi da k'arfi yace
"Ke meye haka dama y'ar iska ce ke?".
"Bawani iskanci kawai kayi parking mu biyawa juna b'ukata ko a cikin mota ne dama wajen wani Alaji zanje tunda gaka shikenan". Wani mugun birki ya taka ji kake k'uuuu ya juyo da nufin ya koreta daga motar tayi hanzarin shak'a masa wani abu a handkerchief tun daga lokacin bai k'ara sanin inda kanshi yakeba.
Daf dazata cimma burinta a kanshi cikin k'udura da hikmar ubangiji Saif ya farka, dishi dishi ya fara gani kafin ya fara gani sosai ceiling d'in d'akin ya shiga bida kallo yanason ya tuna a inda yake da kuma abinda ya kawoshi, take k'wak'walwarshi tafara tariyo masa abinda ya faru. abinda yagani ne da wanda yaji yayi mugun girgizashi tareda muguwar fad'uwar gaba da suka sameshi lokaci d'aya na farko dai jikinshi ba kaya saikuma mace daya gani a kanshi tanata sha'aninta ita kad'ai dan batasan ya bud'e Ido bama saboda yadda tayi nisa cikin abinda take. Wani irin k'arfine yazo masa ya hankad'ata da k'arfi saigata a k'asa kanta ya bugi wani k'aramin tebur, a hanzarce da wani irin mugun sauri ya tashi ya fara neman abinda zai suturta jikinshi nan k'asa ya hango kayanshi a yashe yayi saurin d'aukar jeans d'inshi ya saka baiko saurari saka rigaba ya zare belt d'in jikin jeans d'in ya nufeta lokacin da take shirin tashi tana dafe da goshinta ya shiga lafta mata belt d'in gaba d'aya idanunshi sun rufe dukanta kawai yake tako ina tana ihu da bashi hak'uri amma Ina Saif bayajin abinda ma take fad'a lafta mata kawai yake gashi dama ba kaya a jikinta saida yayi mata duka na fitar hankali sannan ya maida belt d'in yasa rigarshi ya d'auki key d'in motarshi da wayarshi har zai fita ya juya ya kalleta tana takure ko motsi batayi hannunta yaja k'iiii ya fita da ita ya yasar da ita a waje inda ake tsaka da makad'a ruwan sama daga nan ya fice daga gidan yana jin wani irin takaici da tsanar wannan matar da bai santaba harkar taimako ta had'asu.
Yana tafe a mota yana istighfar har k'wallah na tarar masa cikin idanunshi wannan wace irin masifa da bala'i ne ace wai y'a mace ita zata yiwa namiji fyad'e? Me duniya tazama ne yanzu, a fusace yake sarrafa kan motar ba k'aramin b'ata masa rai abinnan yayiba wani irin tuk'uk'i da zafi zuciyarshi keyi mashi uban gudu yake shararawa bisa titin batare daya damuba.
Lokacin daya isa gida 11:pm ta gota, su Mamie da duk zatonsu can zai kwana saboda ruwa da kuma dare dayayi sun kikkira wayarshi kuma tak'i shiga haka wayar Hajia Bintan saboda ruwan da ake yasa ko sun kira tayi picking ba'a jin abinda take fad'a, sunyi mamaki da suka ganshi duk a hargitse suka tambayeshi abinda ke faruwa yace ba komi. Ranar baiyi barcin kirki ba daya farka kuma sai abun ya fad'o masa cikin ranshi yana k'ara tirr da halayyar yarinyar.
Mansurah kam wannan dukan dayayi mata sai data kwanta gadon asibiti tayi jiyya ga ruwan daya daketa hakan ya haddasa mata kamuwa da Pneumonia, tun daga lokacin ta d'auki alk'awarin saita d'auki fansar abinda mutumin nan yayi mata indai ALLAH ya k'ara had'asu, bata tab'a sanin d'an uwan su Safnah bane kuma shine mutumin da Safnahr ta mato masa sai a lokacin bikin da sukaje ranar dinner kamar tasani ta halarci bikin ta matsawa kuma Safnah suje wajen dinner dan da farko Safnah cewa tayi bazata jeba tun daga nan ta shiga k'ulle k'ullen yadda zata nakasta rayuwar Saif saikuma taci sa'a Safnah takawo mata kukanta dan haka tayi amfani da wannan damar da sukaje a matsayin za'a yiwa Ayshaa data koma saita juya abin ya koma kan Saif aka bata wata k'aramar tukunyar k'asa akace duk ranar data fashe to asirin zai karye kuma zata makance, dayake idanunta sun rufe a lokacin yasa batayi la'akari da cewar duk daren dad'ewa zata iya fashewa ba kawai ta amsa tana ganin bazatayi saken da har zata fasheba sai gashi kuma tsananin addu'a da akai tayi da saukar Alqur'ani mai girma ALLAH yakai Madeenah wajen tayi sanadin fad'owar tukunyar yau gashi abinda ta shuka take girba son zuciya ya kaita ya barota akan abinda koma meye it's tafara jan duk abinda yayi mata gashi nan shiya samu lafiya itakuma tanata fama da matsala, ALLAH ya datar damu .
Shiru parlor'n ya d'auka bayan Saif ya gama bada labarin abinda ya had'asu da Mansurah, daga nan kuma Safnah ta d'ora da nata labarin cikin kuka ta sanar dasu duk abinda ya faru tun zuwansu wajen boka, abin yayi matuk'ar girgizasu suka cika da mamakin wai Safnah ceta ta aikata wannan abin wato badan Mansurah taje ta juya aikin ba da Ayshaa ce zata koma haka kenan, Saif tashi yayi, yayi kan Safnah a fusace saida Daddy ya rik'oshi ya shiga kwantar masa da hankali yana nuna masa shi d'inma da aka yiwa yanzu bagashi itace ta kwana a cikiba. Ayshaa kam al'ajabi ya hanata ko motsi kai rayuwar nan ALLAH ya kyauta dai ita tana nan batasan dasuba sukuma suna can suna k'ulla mugun nufi akan akansu da mijinta ita wllhy batasan Safnah bama gaba d'aya tanajin sunanta dai a bakin Imaan amma bata tab'a ganinta ba. Safnah tana kuka take rok'onsu yayin da itama Mansurah ke kukan tana nemarwa y'ar uwarta yafiya ko zata samu sauk'in wani abun, da kam Saif k'in kulasu yayi ya tashi ma zai shige part d'insu Ayshaa tayi saurin tarar gabanshi ta shiga rok'onshi da nuna masa muhimmancin yafiya da hak'uri a wajen musulmi ita ta saukar dashi harya furta ya yafe musu sannan ya shige ciki yana maijin bak'in cikin kasancewar Safnah a matsayin y'ar uwarshi da yadda taso saka iyalinshi cikin matsala.
A gurguje.
Saif ya kammala gininshi harma sun tare an k'ayata ko Ina da ababen more rayuwa, rayuwar su suke cikeda jin dad'i da walwala zamane suka had'u suka ginashi ingantacce da soyayya mai tsayawa a rai, kwanaki ya ware na musamman sukayi ziyara shida Ayshaa sunje gidansu saikuma dangin Mamie dana Daddy sun yayyawata sosai. Suna dawowa kuma Ayshaa ta fara rashin lafiya yauda lafiya gobe babu, gwajin farko dayayi mata yagano ciki, yayi matuk'ar yin farin ciki ya shiga godewa ALLAH su Mamie ma da sukaji sunyi murna k'warai da fatan sauka lafiya.
Rayuwar ta cigaba da gangarawa wataran farin ciki wataran kuma akasin haka dama duk mai rai cikin hakan yake rayuwa.
Ansha shagalin bikin Mukhtar da Imaan, ba nisa tsakaninsu dasu Saif. washegarin da aka kaita tun sassafe saiga kiran Mukhtar ya shigo wayar Saif lokacin Ayshaa tana jikinshi tana faman zuba masa shagwab'a da rigimar data saba dan wannan cikin abinda ya sata kenan.
Picking yayi ya kara a kunne yayi sallama tareda fad'in
"Kana angoncin ma bazaka barni in hutaba Mukhtar?".
"Nidai taimako nake nema please". Mukhtar ya fad'a yana wani k'asa da murya.
"Ina jinka". Saif yace yana shafa gashin Ayshaa datake kwance a k'irjinshi.
"Dan ALLAH ka kawomin Madam d'inka ta taimakawa baby wlhy tak'i yarda in taimaketa ko d'akin na shiga saita fara kuka".
"Uban me kayi mata Mukhtar?". Saif ya fad'a bawai dan bai gane abinda yake nufiba.
"A'ah ban gane menayi mataba, mutum akawo masa mata kace menayi mata saboda kai d'an iska ne".
"To zakaci ubanka kuwa ba inda matata zatazo aiba y'ar aikinku bace". Ya fad'a yana shirin kashe wayar Mukhtar yayi saurin tsaidashi yana bashi hak'uri harda cewa ya tuba.
K'wafa yayi yace
"Basan halinka ba wllhy". Yayi hang up d'in wayar.
Ayshaa ya fad'awa yadda sukayi da Mukhtar yace ta tashi ta shirya suje, dama a shirye take dan haka mayafi kawai ta d'auka suka fita.
Ba kowa a parlor'n lokacin da suka shiga, sai bayan sun shigane Mukhtar ya fito daga kitchen yana sanye da jallabiyyah suka gaisa da Ayshaa ta nufi bedroom d'in daya nuna mata yace Imaan d'in tana ciki.
"Waifa indomie nake dafawa duk ta kwab'e wllhy bansan ma ya zanyi da itaba". Mukhtar ne yayi maganar yana zama kusada Saif.
"Dama ka iya wani abun arzik'i ne kai idan ba iskanci ba". Saif ya bashi amsa yana harararshi.
"Ai kai ka iya". Shima ya amsa masa yana jefa masa hararar.
"Idan ban d'auki matata munbar gidan nan ba kace........dan ALLAH kayi hak'uri Yah Saifu, Mukhtar ya katseshi.
"Amma fa k'anwar nan taka tayi wllhy ba k'arya so sweet".
"Naga ranar da zaka daina shashanci banza". Dariya Mukhtar kawai yayi to kunsan dai irin dramar da ake tsakanin Saif da Mukhtar idan aka had'u .
A k'udundune Ayshaa ta samu Imaan tanata kuka nan ta shiga rarrashinta cikin kukan take fad'in
"Wllhy Aunt Ayshaa Yah Mukhtar mugune duk hak'urin dana dinga bashi baijiba sai ALLAH ya sakamin wllhy". Itadai Ayshaa rarrashi ne nata dan ba k'arya dagani Imaan taji jiki gashin kanta daya sha gyara duk ya mimmik'e abun gwanin ban tausayi da dariya. Duk irin taimakon da Mamie ta bata lokacin da Saif ya jik'a mata nata aikin shita bawa Imaan ta gyara ko Ina tayi musu girki sannan sukabar gidan.
★★★★★★
Tunda cikin Ayshaa ya shiga watan haihuwa Mamie ta d'auketa daga gidan, duk da dai ba haka Saif yasoba saidai ba yadda zaiyi kullum yana gidan nane da Ayshaa ko kunya bayaji daga k'arshe ma gidan ya dawo ya tare.
Kwananta takwas da komawa ta haihu, ta haifi k'aton d'anta mai kama da babanshi sak tamkar yayi kaki ya tofar, dayake haihuwar dare ce baisan ma ta haihu ba sai washegari da safe dayazo dubasu ya sameta da d'anta,zokuga murna wajen Saif bakinshi ya kasa rufuwa murnarshi ta kasa b'oyuwa ya rungume yaron yanajin wata k'aunarshi ta musamman tana ratsashi irin son da ALLAH yake kimsawa tsakanin iyaye da y'ay'ansu soyayya ce zalla mara had'i da algus, ALLAH yaji k'an iyayemu badan sun mutuba ya saka musu da mafificin alkhairi na d'awainiyar da sukayi damu Aamin .
Ansha shagalin suna sosai, yaro yaci sunan Daddy wato Abubakar Sadeeq inda suke masa alkunya da Aareef wasu kam little daddy suke cemasa. Ayshaa tayi b'ulb'ul da ita jegon ya amsheta sosai. A kullum cikin godewa ALLAH take da irin ni'imar da ALLAH yayi mata na samun suruka mai k'aunarta da gwarzon mijinta dayake nuna mata soyayya, ta fannin cigaba ma Alhamdulillah kullum ana samunshi ya gina wani hospital d'inma daya zuba kud'ad'e masu yawa kuma duk abinda za'a yiwa mutum kyauta ne bako biyar d'inshi shiyasa kullum cikin shan addu'o'e yake daga bakunan mutane da dama rayuwar tayi dad'i sosai saidai d'an abinda ba'a rasaba tunda dama bazai yiwu ace d'an Adam yana rayuwar jin dad'i koda yaushe ba dole sai ansamu tawaya ta wani b'angaren fatanmu dai ubangiji ALLAH yasa mu dace dan arzik'in ANNABI.
Wannan shi ake kira a dunk'ule dama yawan book bashi bane sak'on dake ciki shine abin dubawar.
Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah
Fatana ALLAH yasa sak'on ya isa inda ake b'ukata Ina muku fatan alkhairi, nagode sosai da irin kulawar da kuka bawa book din nan daga lokacin dana fara zuwa yanzu dana kare shi Allah ya sakada alkhairi yabar zumunchi nagode kwarai masoya.
Ina mik'a d'inbin godiyata ga kungiyata ta HASKE WRITER'S ASSOCIATION, hazikan marubuta kuma fasihai a cigaba da haskakawa ❣️❤️
Sai group dina na OUM HANAN CONVERSATION kuma ga taku jinjinar ta musamman thanks so much ILYSM ❣️❤️❤️
Mrs Salees Mu'az ❤️
Maryam Ibraheem Aleeyu
(Ummee).
Post a Comment for "DR. SAIF RETURN Complete Hausa Novel"