Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

MATAN ASOKORO COMPLETE HAUSA NOVEL

_MATAN ASOKORO_   ✍M SHAKUR DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JINKAI. _NOTE: WANAN LABARIN KAGAGGEN LABARINE, BAN KWAFI RAYUWAN WATA KOWANI BA._ _RANAKUN POSTING NEW EPISODE ARE *SUNDAYS*, *TUESDAYS* AND *FRIDAYS*_   _Duk wata diya mace inhar tawuce 18 needs to read this book, yan mata, iyaye, zaurawa, single moms, everyone, I mean it RECOMMEND THIS BOOK MA DUK WATA MACEN DAKIKAGA SHE NEEDS IT, now let's go to the story, kubiyoni Fanmily as am about to carry you into another world CHAT ME M SHAKUR DIRECTLY BY CLICKING ON THIS LINK BELOW https://wa.me/+2347012181461   THE ONLY FREE PAGE EPISODE 1️⃣ Dakine mai bala'in kyau, kana ganin dakin kaga office sabida office settings ne dakin, ga dogon couch mai shegen laushi da yaran kujera(throw pillows) saikuma chan gayar desk dake dauke da desktop keyboard da sauran su, gakuma book shelve dake dauke da litattafai daban daban daya karamai kyau, dakin cool sanyi ketashi ciki na AC. Wata mata da akalla zatai 35 ko 36yrs ne ke zaune kan couch din office din, tai shiga ta alafarma tai crossing legs dinta tanadan karkadawa, kafar yaji jan lalle tana sanye dawani takalmin hermes simple mara kwalliya orange color sai jakarta itama product din Hermes shima orange color, tana sanye dawani doguwan riga na atampa mai tsadan gaske da akamai stone work baja baja ga babban mayafinta dakana gani kasan naira tai kuka awajen nan, hannunta kuma rikeda IPhone 12 Pro Max tana daddannawa fuskanta dauke dadan murmushi daya kara bayyana kyawunta da yanda chocolate fatarta ke kyalli, kyallin hutuda jin dadi, jin karan anbude kofa yasa tadago kanta takalli kofar, wata chocolate skin likita ce dan tana sanye da farin labcoat, kana ganinta kaga baturiya amman all this black Americans tana sanye da half gown mai kyan gaske da wani red hill tadaura lab coat kan gown din, hannunta kuma rikeda wani pad mai kyau dake attach to wani kalan pen da kana gani kasan narubutu kan iPad dinne, murmushi tayi tamaida kofan tarufe sanan ta shigo ciki saida takarasa daidai kan desk dinta sanan tadau farin glasses tasaka a idanunta kafin tazauna kan kujera ta danna pad dinta sanan tadago ta kalli matar cikeda fara'a dakuma murmushi tace "Hello, Mrs Bakori right"? gyadamata kai matar tayi tace "yes" dauko pad din tayi sanan taja kujeran baya tafito tazagayo tagaban table din ta zauna kan one seater couch dake facing na matar sanan tai crossing leg itama ta kwantar da pad din ajikinta tace "this is your first time in our facility right"? Gyadamata kai matan tayi tace "right" gyadakai tayi cikeda gamsuwa tace "my name is Dr Elizabeth Matthew Browns, I am the Psychotherapist of this facility, before we start i want to assure you anything we will be discussing here is strictly confidential, all ur information and ur identity are very safe with us here, so fill free to talk to us, talk to me your Dr, I am a counselor, a Consultant, a therapist and so much more, so Mrs Bakori....." tai maganan tana daukan pad dinta tarike da pen din a hannunta da kyau sanan tadago kanta ta kalli matar tace "I want to know u better tell me who you are" gyara zama tayi saikuma tai danjim kaman mai tunanin wani abu saikuma tace "My name is Hassana Lawal Bakori, we are twins, i have Hussaina but bata Nigeria ita, tana Dubai, am 35yrs old, am married to Alhaji Alhassan Bakori" tai shiru, iPad din Dr ta kalla sanan tace "what about kids, your record here says kinada yara, is that right"? Gyadamata kai tayi tace "oh yes, I have two children, Boys, Khalid and Khalil, twins nesu suna boarding school, they're 14yrs old, suna SS2 dukansu" anatse Dr tace "which means sau daya kawai kika haihu? How long have u been married"? Anatse tace "15yrs" ahankali Dr tace "why? Maisa kika tsayarda haihuwa? Health complications ne yasa baki kara haihuwa ba, kokuma kece bakiso"? Dan murmushi tayi tace "my husband doesn't want plenty children saisa bankara haihuwa ba" murmushi Dr tayi tace "so Mrs Bakori why are you here? What do you want to discuss with me, how can I be of help to you"? Tai maganan anatse ta yanda patient dinta zata kara natsuwa dakuma aminta da ita, ahankali ta gyarazama sanan ta ijiye wayanta dake hannunta gefenta sanan ta rungune hannayenta biyu akirji tareda fuzarda iska tace "is about my husband" gyadamatakai Dr tayi alamun okay tana jinta tacigaba, sake dan shiru tayi Dr ta tsaya bataredatai pressuring nataba, saikuma ahankali tadago kanta ta kalli matar tace "I don't have feelings for my husband! kwata kwata banjin sonshi araina daidai da digo daya! baya burgeni! I don't find him attractive! I don't find him sexy! Bana sha'awan shi! Banmason yaneman! Bawai banajin sha'awa bane, a'a inaji amman idan yazo nemana sai inji raina na baci, kwata kwata banmason yatabani ballema wani abu ya shiga tsakaninmu, I don't know why am like that, I need help, serious help" duk maganan datayi Dr kallonta take, saida tagama tsaf sanan tadanyi yan rubuce rubuce akan pad din sanan tadago ta kalleta, ahankali tace "you want some coffee, tea or water"? Dan facility haka sukeyi duk wanda yazo ana kawomishi any of the 3 yasha, girgizamata kai tayi tace "no am good, thank u" gyadamata kai Dr tayi itama, sanan tace "akwai wani mugun hali da mijinki yakeda shine, kokuma yana cutardake? Koyana miki wani abu dabakiso ne"? Girgizamai matakai tayi ahankali saikuma tace "not really, kawaidai mijina yana yawan gwasaleni, ya gwaleni idan inamai magana kokuma ina magana a inda yake koda badashi nakeba" "hakan nabaki haushi"? Dr tajefo mata tambayan, dan shiru tayi ta kalli Dr saikuma ahankali tace "eh, hakan nabani haushi, yana bakantamin rai" "do you think abinda yasa bakijin sonshi aranki kenan sabida yana gwasaleki"? Dr tasake mata wanan tambayan, shiru tayi takasa magana takai kusan 3min, Dr na kallonta kyar, dan ajiyan zuciya tasauke sanan tace "nasan na tsani idan mijina ya gwaleni, agaban yan aikina, yarana saikiga ya gwaleni, idan nace kaza saiyace ai kazane ban saniba koban iyaba this this this, i know is very annoying but I don't think shine abinda yasa naji bana sonshi, No! I don't think so" takarashe maganan ahankali, zama Dr tagayara tace "and what do you think made u not to have feelings for ur husband anymore Mrs Bakori"? Shiru tadanyi saikuma ta numfasa tace "I.....I.....I....." muryanta yasoma breaking sosai, hakan yasa Dr tace "take a deep breath Mrs Bakori" kaman jira take ahankali tai taking deep breath sanan tafuzar, Dr tace "are you ready? Mucigaba"? Gyadamata kai tayi ahankali tace "yes Dr i am ready" gyadakai Dr tayi tace "good, I asked u a question, me kike tunanin yasa bakijin kinason mijinki yanzu? What do you think made u not to have feelings for your husband again"? Ahankali tace "because I feel he don't love me too, shima bayasona" dan shiru Dr din tayi tana kallonta yanda taga idanunta sun kada sunyi ja, tace "auren soyayya kukayi ko auren hadi"? Ahankali tace "auren soyayya" "to mesa kike ganin bayasonki yanzu"? Shiru tayi tace "Dr my husband baisan menene lallashin mace ba, and he don't know how to say sorry, idan zan fadi agabanshi faduwa sosai mutumin nan bazaima tashi daga inda yakeba balle yataso yazo yadagani yacemin sannu ba, saidai ya kalleni yadaukekai yace banda natsuwa saina kashe kaina hankalina zai kwanta, idan na yanke bazai cemin sannu ba, idan kaina naciwo bazai cemin sannu ba, munada family Dr kome ke damunka kana kiranshi zaizo yabamu magani, amman bazai taba tambayana konasha magani ko banshaba koyajiki ba, ko naci abinci ko banci ba, anything nida rayuwata mutumin nan babu ruwanshi, inason mijina saisa na aure shi but wanan halin dayakemin na rashin kula, na rashin damuwa dani, ko uhum ko ajikinshi yasa naji zuciyata batajin sonshi to akanme zanzo wanda bai damu da lafiya ta ba, akwai lokacin danai zazzabi sosai saida Dr yasamin ruwa barin dakin yayi wai bazai iya kwana daniba ina warin allurai da magunguna, wani zubin haka zai tafi aiki ko lekoni baiyiba, Dr kinsan mene" tai maganan tana goge wani hot hawaye daya zubomata da sauri saikuma tai murmushi tace "don't tell me I am crying" "oh yes u are" Dr tafadi haka ahankali tareda juyawa tadauko tissue dake kwali tajuyo tabata, karba tayi ahankali sanan tadaura akan fuskanta tana goge hawayen suna zubowa tana kuma murmushi at the same time, tace "Dr i am a very very strong woman, dawuya kiga kukana, koshi banjin natabamai kuka kan abubuwan dayakemin ba, nafi karfin namai kuka, but bansan mesa yanzu nake kuka ba, eh? Why am I crying? Look what Baban Khalid is doing to my confidence and self esteem" tai maganan tana share hawayen tana murmushi duk Dr na kallonta taking note of everything, kana ganinta kasan she's deeply hurt, babu abinda yacika zuciyanta sai lot of sorrows da damuwa but she's wearing that strong woman face, MATA! we are going through a lot!! Dr tafadi aranta, yanda taga hawayen sun kasa dena zuba saikuma murmushi take trying to stop them takasa yasa ahankali dawani irin heart soothing voice tace "Mrs Bakori" ahankali tadago fuskanta ta kalli Dr hawaye nazubowa har lokacin tace "na'am" ahankali Dr tace "let them out, cry to me, cry for me, cry all your problems out, is part of the psychotherapy, cry, yi kuka" cikeda gardama dakuma kunanrai tace "no Dr akanme zanyi kuka kan Baban Khalid, akanme zandinga kuka kan namijin dabai damudani ba, bai damuda damuwataba, akanmene, wlh yayi kada........" saikuma gakukan yazo bashiri, sauran maganan ma makalewa yayi awuya takasa yi, sake juyawa Dr tayi kawai tadauko kwalin tissue gabaki daya tamika mata karba tayi tazaro tana goge fuskanta, cikin kuka take magana. "Idan yara suka dawo hutu har tsoron magana nake dasu kokuma wata hira tashiga tsakanina dasu idan babbansu na nan saikiji ya gwasaleni, kinsan yara maza basuda hankali da wayau ba kaman mata bane, idan mahaifinsu ya gwasaleni dariya suke sosai fa, but bantaba nunamai yamin ciwoba saidai inyi murmushi inbarmusu wajen shikuma ya kwashesu yafita, ni kadaice baida wata matar balle nace sabida ita yakemin wulakanci kuma baya neman mata, shifa baida lokacin mata ma wani irin likimon mutumne kawai neman kudi yasani arayuwanshi, neman kudi kawai da tara kudi, weekend kawai yake zama agida shima ba kowanne ba, weekdays sai dare zai dawo, bannemi komi narasa ba, sai kulawanshi da nuna yadamu dani, this are what my heart wants, but bana samu daga wajen mijina me akayi kenan, saisa bana sonshi banajin sha'awan ba, banmaso yanemeni".   Saida tagama kukan tsaf which was taci kusan 6min sanan, tashare fuskanta tsaf takalli Dr tasake murmushi tace "don't mind me Dr, I am not the crying type so banmasan mesa nake kukaba, so yanzu dai kinji this is my issue, banson mijina kuma sabida shima bayasona, a online naga advert na facility naku, ku baturai ne kuma psychotherapy shine specialty naku, idan mutum yanada matsala yazo yagaya muku zaku taimakamai da matsalanshi, after paying those huge money for consultation I hope zan sami maganin matsalata, kisa naso mijina back" dan murmushi Dr tayi jin maganganunta tace "I will help you Mrs Bakori, but u have to be willing to help yourself" gyadamatakai tayi, Dr tace "first of all I want to ask you one question dazai taimakamin wajen samo miki solution, was ur husband like this dakika aureshi? Haka halinshi yake lokacin dakuke dating"? Da sauri tagirgizakai tace "no bahaka yakeba, lokacin damuke soyayya wlh ko zazzabi nake zakiga shima yafara zazzabi duk yabi yadamu sosai fa bana wasaba, everything yafarane danazo na haifamai yan biyu lokacin yafara wani mahaukacin kudi, kinsan engineer ne yana harkan construction, building, titi, yanzu haka yanada kampanoni sunfi goma, manya manyan, government contracts yake samu nayin titina da wasu irin crazy building, a Nigeria kap babu kampanin daya buge nashi indai harkan kera gini ne da titina, su kansu gwamnatin Nigeria naji dashi sabida iya aikinshi da talent dinshi, to dayazo yay wanan bastard kudin shine yazo tashi daya ya chanzamin sabida yaga yadawo hot cake nima zai maidamin da kanshi hot cake, baibi takaina kawai amman ban rasa komiba, duk month inajin alert na monthly allowance dina huge sum of money, ga kayan abinci na komi da komi dakika sani inadasu adakina, kumani nafi karfi nazauna namai kuka kowani abu wlh ai yasanni, kafin yasan kudi dudda kudinshi yanzu zai iyafin na mahaifina nima nasani, Babana shine ambassador Nigeria na Thailand, kuma babana yana daya daga cikin mutanen dasuka samai hannu yazama abinda yazama yau dinan harya bunkasa, tomezai gayamin"? Shiru Dr tayi tana kallonta one thing dazata iya fadi kan this her new patient is tanada girman kai dajida kanta itama, and in this her case da mijinta dolefa daya yasauko daya ya takashine sanan zata iya samin abinda takeso wato care and his affection, wow asibiti kullum kake ganin patient daban daban, numfasawa tayi tace "Mrs Bakori, I think the first thing danaga aurenki da Mr Bakori ke lacking is communication, and that's the first thing we are going to work on, now zanbaki one week, ur next appointment will be rana itiyau zaki dawo, but this 7days dana baki I want you to use them in trying to establish communication tsakaninki da mijinki, idan yadawo daga aiki kina zama kitayashi hira koki tayashi wanka" girgiza kai tayi, tace "ina tattara abincinshi nake kaimai dakinshi asama dan baya iya sakkowa yaci a dinning, ina ijiyewa zanfito kafin yafara kyarata, idan andan jima zan koma naje na kwaso nafito dannikadai ke shiga dakinshi sanan inwuce dakina na kwanta da safema haka, bana shiga harkanshi shima baya shiga tawa kowa yakama kanshi" shiru kawai Dr tayi tana kallonta, ahankali tace "okay, from today go u will have to change that, idan kika kaimai abinci ki zauna dashi kimai hira mai dadi" "hira!" Tafadi dadan daga murya sanan tace "dazaran nafara bashi labarin abufa zaicemin ai bahaka bane, wlh Dr bakisan mutumin nan bane, he's so impossible, nikuma bazan bashi kaina yaraina ba chan tamatsemai a matsematsi" girgizamata kai Dr tayi, tace "Mrs Bakori, the way kike rayuuwa with ur husband is not even marriage, and u are so damn hurt pretending to be happy, if u want and respect ur happiness u need to drop this ur mentality and work things up between you two, babu laifi dan mijinki yaga weak side of u, there's nothing wrong dan mijinki yaga kukanki, ko yaga damuwanki, inma yamiki dariya kanshi yamawa dan the two of you are one, there's nothing wrong dankin nunama mijinki u are not as strong and harsh as yanda ake tunani, deep down u are so weak like a little baby who needed some love and support to light up her day, lemme tell u this, for u to bring yourself to this facility is because ke kanki kinsan burden din dakika daurama kanki yasoma miki yawa saura kadan ya kayar dake and u needed help, so I want you to drop all this act and listen to me and do as I say I am ur Dr" Dr tai maganan bawasa dayasa taga matar ta natsu, sanan tace "abinda nakeso dake is daga yau no more ki kaimai abinci kifito, ki kaimai sit there, help him shower ya shirya yazo yaci, if possible feed him, start conversation, a respectful conversation, idan ya gwaleki karki karaya continue batare danuna fushi or anything ba, zaigaji yadena and listen to you, idan ya gwaleki yau, gobe, jibi, gata bazai yiba, do this of this week, next week kika dawo u will tell me how it goes and we go into the next step, understood"? Ahankali ta gyadamata kai, murmushi Dr tamata tace "if that's the case munxo karshen our session, saikuma next week right" murmushi tayi ahankali ta tashi tsaye tana gyara mayafinta, Dr tabita da kallo, matar badai kyauba, ga curve, tanada ass, ga manyan nono, tanada kiba kosasshiyar mace ce ba ramamma ba, ga fatarta baka mai kyalli, taji Jan lalle a hannu da kafa kana ganinta kaga irin matan nan masu gyara bana wasaba, matan Alhazawa but mentality ta yasa she's not enjoying life yanda yakamata tayi. Jakanta tadauka da wayanta sanan tajuyo ta kalli Dr tace "thanks" sanan tawuce tasakai tafice tana tafiya daidai cikeda isa, kana ganinta kaga Hajiya, like real Hajiya kudi sun zauna. Premises din facility tayi takarasa gaban wani mota wata black SUV da batada banbanci da sabuwa karasawa gaban car din tayi saikuma ta tsaya chak ranta amugun bace takine fuska kaman ba itane tasha kuka ba, tajuyo ta kalli wajen asibitin da idanunta dasu chanza launi har yanzu suna nuna alamun sunyi kuka, wani dogon saurayine dake sanye da riga har zuwa guiwa ash color na shadda dakuma wani bakin wando shima har kasa, yana sanye da silifas din roba, yanada tsawo dakuma dan jiki kadan, fuskarshi nada haske, sai gashin kanshi so curly and a bit blonde dan ba bakin gashi bane dababu gyara kana ganinshi kaga bafulatani gakuma dan gemu shima blonde dabasuda yawa, yana gaban wani mai baron rake hannunshi rikeda rake yana balla yanasha yana hirada mai rake dake feremai wasu da wuka yana yanyankawa yana sawa aleda, dukaduka yaron bazai wuce 25-26yrs ba..... wani irin mugun tsaki taja kaman tahadiye zuciya tamutu, wanan dan kauyen direban da Baban Khalid yakawo mata shine d worst direba daya taba kawomata in her life, gashi kazami gashi dan kauye, tarasa why on earth is Baban Khalid treating her that way shiya hanata driving sanan yakawo mata wani dan kauye that can not even read anything, ita batamasan daga ina yasamo yaronba just 1month ago yakawo matashi sabida direban ta nada yakoma garinsu kulada mahaifiyarshi da aka cemai batada lpy, shi professional direba yakeda shi kullum direbanshi cikin suit yake da agogo shikuma wanan local dan kauyen yakawo mata that cannot even read ABCD to Z, koyanaso tai bala'i dashine dan tasan dagangan yamata haka ohonmai. Jin ranta na tafarfasa yasa tajawo wayanta daga cikin jaka taciro tashiga dial calls dinta saiko ga number Martala Driver tai dailing number shi, yana tsaye bakin titi suna hirada mai rake dake yanka rake saiga wayanshi tashiga ringing dasauri yatura hannunshi cikin wandon yaciro wayan techno yar rakani toilet, musamman yasa akamai Saving number Hajiya da S shikuma Alhaji da A dan yagane idan takira yana ganin kiranta yadaura hannunshi aka amugun rude cikin hausanshi nayan kauye yace "na shiga uku na lalace, Hajiya" dawani irin gudu yajuya ya kalli asibitin hangota tsaye yasa damugun sauri yajuya yasake tura hannu cikin aljihu yaciro wata 500 yamikama mai raken yace "kai bani Hajiya ta tafito, yau nidai nasan na shiga uku" baima jira cewanshi ba ya fizge ledan yawuce, Mai rake yace "ga chanjin ka kabari" titi yashiga da gudunshi yace "nabaka" da gudu ya tsallaka titin ya shiga asibitin duk tana binshida mugun kallo, yana karasowa gabanta ko wata wata baiyiba yawani irin zubewa agabanta yace "Hajiya dan Allah kiyakuri, wlh nasan kinsha gayamin muka fita na tabbatar ina cikin mota idan kinfito, tuba nake Hajiya, Allah yahuci zuciyanki, Allah ya sanyaya kafadunki, tubanake Hajiya" ayanda takejin haushi zata iya shureshi da kafafunta tadai daure cikin fushi tace "my friend will u stand up and open car for me" dasauri yace "eh Hajiya mekikace"? Wani irin runtse ido tayi cikeda takaici tuna bamaya gane turenci, dan dagokai yayi ya kalleta ganin yanda tayi yasa yace "dan girman Allah kiyakuri Hajiya wlh daman rake nasayo miki wlh" yamikamata raken dake leda, bude idanunta tayi tadakamai tsawa. "Murtala katashi kabudemin mota nabar wajen nan!" Abirkice dukya rude yatashi garin hakama yasaki ledan raken suka watse awajen tabishi da mugun kallo dayasa yatashi da sauri yatura hannu a aljihu yaciro hadadden car key sanan yadanna lock tabudu, kafin yabude kofar owner sit yasaukarda kanshi kasa yace "Allah yahuci zuciyan Hajiya, tuba nake matan ranka shi dade, takawanki lpy uwargijiyata, shiga muje" mtswww taja wani wahalallen tsaki tajuya tashiga cikin motar ahankali kanta na mugun sarawa yamaida kofan yarufe, raken daya watse awajen ya kalla har ranshi soyake yatsugunna ya kwashe kayanshi amman tsoron masifan hajiya yake, bude gaban motan yayi ya shiga ya rufe yaja sit belt yasaka saikuma ahankali yaleko bayan sit din ya kalleta kanta na kasa tana kallon wayanta datake latsawa kaman mara gaskiya ahankali yace "Allah huci zuciyan Hajiya" dagokanta tayi tazubamai red eyes dinta dahar lokacin suke nuna alamun kuka, hakuri zai batafa amman ganin yanayin idanunta yasa dasauri yace "Hajiya kuka kikayi? Innalillahi maiya sameki anmiki wani abu a asibitin nanne? Waya batamiki rai eh inje inkoyamai hankali wlh saina barar da mutum na shemar dashi, waye ne Hajiya"? Yanda taga yadamu sosai danya nuna afuskanshi yasa har ranta saitaji dadi, dan yatsine fuska tayi cikedason yamata shiru dakuma tarin gajiya tace "nagaji ne kaini gida kawai nahuta Murtala" da sauri yajuya yatada motar yajada sauri yace "Hajiya sannu, kinga baki saba wanan aiki hakaba, keda kikeda likita dayake zuwa har gida yadubaki maisa kikazo asibiti nan kikabi layi saisa kanki keciwo, sannu Hajiya, Allah huci zuciyanki, yanda kikagajin nan bazanbi hanyar zuwa ASOKORO ba dan akwai go slow, akwai wata short cut hanya dazanbi yanzun nan zakiga munkai ranki shi dade".   Chat me up directly by clicking on this link https://wa.me/+2347012181461   _This is the only free page of this book, like I said, wanan novel din bakaman normal novel dina bane, I interviewed so many couples, I want to show the world inda akafi samun matsaloli arayuwan auren mu tayau and how to go about it. I trust my fans, u all knows yanayin rubuta, ku gyara zama, wanan littafi shine ga darasi gakuma dadi, lemme say it again please , anybody less than 18 shouldn't read this book, thank you._ Chat me up directly by clicking on this link https://wa.me/+2347012181461 _This book is 2k, idan kinaso pay into 3107021073 aisha Muhammad first bank and send evidence of payment to my watsapp number 07012181461 sainai adding naki a group din danake posting_ _MATAN ASOKORO_ _MATAN ASOKORO_   ✍M SHAKUR _RANAKUN POSTING *SUNDAYS*, *TUESDAYS,* *FRIDAYS*_ _DAN GIRMAN ALLAH KARKI KARANTA THIS BOOK IN BAKI BIYABA, KUJI TSORON ALLAH_   EPISODE 2️⃣ Ko alamun taji magananshima batayiba saima cigaba da danne dannenta datayi awaya tana chatting a group dinsu na ASOKORO WIVES, gajiya tayi saikawai ta ijiye wayan sabida yanda kanta kewani irin sarawa datarasa maisa, sanan gently ta jinginar da kanta jikin kujera ta lumshe ido. "Hajiya wai lapiyanki kalau"? Bude idanunta tayida sauri jin Murtala yasake mata tambaya ta madubin mota suka hada ido dan gajeren wahalallen tsaki taja tamaida idanunta ta lumshe su ahankali back, maida hankalinshi yayi kan tukin harsu ka shigo ASOKORO District, Usman katsina street suka shiga yay horn agaban wani makeken mansion da tsayawa bayaninshi aikine ganin ba'a bude gate dinba yasa yace "auuuu kullum saina manta abin nan" yay maganan yanadan juyowa ya saci kallon Hajiya yaga tana kaman bacci danhar lokacin idanunta a lumshe yasan inda idanunta biyu datamai bala'i kan kullum saiya mantada remote din da ake bude gate dinsu dashi, remote din dake motar yadauka ya danna gate din yabude sanan yasa kan motan suka shiga cikin gidan gate din yarufe kanshi, kafin ahankali yabude kofa yafito sanan yazagayo ta bangarenta yabude kofa tareda bending kanshi cikeda respect yakira sunanta ahankali danya tadata daga bacci. "Hajiya, Hajiya" dan bude idanunta tayi ahankali tazubasu akanshi awulakance, baidamuba yace "mun iso gida ne daman saisa natadake" yunkurowa tayi tanajin kaman kanta zai fice amman saita daure tafito hakan yasa shima ya matsa yakoma baya, fitowa tayi daga motar ta tsaya da kyau da sauri tasake kulle idanunta jin wani irin jiri take gani hakanan all of a sudden, hakan yasa Murtala daya koma baya yace "Hajiya karkice nacika tambaya amman kaman bakida lpy wlh, duk jikinki ya nuna hakan" bude idanunta tayi tazubamai wani matsiyacin kallo dayasa yaji cikinshi ya murda ahankali yamaida kanshi kasa, daukekai tayi tace "kwasomin jakata da wayata" tai maganan sanan tajuya tafara tafiya gashi daganan parking space zuwa flat dinta dadan tafiya, amman hakan take tafiya ahankali dai dai gudun kartaje tazube dan bamatasan meke damuntaba jitake kaman sauran kiris jikinta yakasa daukanta, akwai staircase haka dazai sadata da kofan shiga flat dinta ahankali take hawa staircase din cikeda karfin hali irin nata da kyar ta iya daga kafanta tahau na karshe batasan meya faruba tadaijita akasa sharaf, sanan kuma taji ihun Murtala sama sama, kara lumshe ido tayi tabude sanan taga Murtalan agabanta ya tsugunna ya haukace yakasa tabata sama sama takeji yana Hajiya, Hajiya, sake lumshe tayi tabude batasan meke going on ba tadaiga waya akan kunnenshi saikuma kawai taji yadauketa, kadan kadan take bude idanunta she could feel and see yanda heart dinshi ke beating, ke racing sosai na fargaban kar wani abu yasameta saikuma dip ta dauke wuta. Kwantarda ita yayi akan katafaren doguwan kujeran dake falon cikin jerin hadaddun kujerun dake wajen, sanan yatashi da sauri hannunshi har rawa yake ya shiga dailing number Alhaji for the second time yamugun damu dudda yasan Hajiya was never nice to him but still baisan wani abu yasameta.......   Wajen 30 big men ne zaune awani babban conference room, sunci uban suit, wani hadadden magidanci mutum dake zaune kan kujeran CEO ne ke magana yana bayani da turenci, ringing dawayanshi yasakeyi for the forth time yasa yakalli wayan, daukan wayan yayi a hannu yatashi tareda fadin "excuse me" sanan yafita daga conference hall din yakara wayan akunnenshi, kafinma Murtala yay magana yashiga balbaleshi da masifa. "Ka kirani kace tasuma nace ka dauketa ka shiga da ita ciki zan kira Dr, basaika jiraba, saidamuna kake da kira kasan wani irin meeting nakeyi ne? Kaiwani irin wawan bakauyen yarone wai? In nagama I will call d Dr yazo yadubata, kawai yanzu ka tsaya tareda ita, karka barta ita kadai, babu abinda zai sameta ai Hassana is a strong woman she will be fine" ya katse wayan zai maida a aljihu saikuma yaciro yama kashe wayan gabaki daya dan yasan Murtala baida hankali he will keep calling him this meeting is very important anjima idan suka gama zai kira Dr su yasa yaje yadubata, da sauri yawuce yakoma ciki wearing a smile akan face nashi yace "sorry gentlemen let's continue"......   Jikin Murtala har bari yake gabaki daya yama rasa maizaiyi gashi babu kowa gidan, dan ka'idan su shine ma'aikatansu basu kwana, da maid, gardener da sauransu duk dasafe suke zuwa suyi aiki sutafi, koma sunanan shibaisan mezaimataba, yana tsaye kanta chan yaga tai wani irin nishi ta bankare ta tashi, saikuma tafara Jan numfashi kaman numfashinta naso yadauke tana kakkama wuyanta, tsugunnawa yayi gaban kujeran cikeda damuwa yana tura hannunshi a aljihu yana ciro wayanshi zai sake dailing number Alhaji yace "Hajiya meke damunki na shiga uku, Hajiya badai mutuwa zakiyiba" ina Hajiya bamatasan wayeke akanta ba, yay dailing number kashe, sau uku yana kira wai akashe daidai lokacin tafado dagakan kujera tana nishin idanunta na kakkapewa shibaimasan meyakeba kawaidai yaganshi ya dauketa ko nauyinta bayaji yafita da ita daga dakin yawuce yabude mota yasata yagyaramata kafafuwa yarufe sanan yashiga gaba danna remote yayi gate yabude yasakai yafice aguje yana tuki yana juyowa yana kallonta yanda yaga tana battling da numfashi yasa kawai yasaki kuka. "Hajiya kiwa Allah karki mutu, kar yan biyu sudawo Marayu wayyo Allahna" kawai shima yahau kuka kaman yaro, wani babban government asibiti dakenan a ASOKORO yakaita yay parking yana kuka sosai yay cikin asibitin yana ganin wani Dr yafito shida nurse kawai fizgo hannun Dr yayi yana kuka sosai, Dr ma tsorata yayi dan yadauka mahaukaci ne yace "Malam lafiya"? Cikin kuka Murtala yace "Hajiyata batada lpy likita zoka taimaka mata dan Allah bata iya numfashi" jin maganan dayayi yasa Dr yabishi Nurse din dasuke tarena binsu har motansu yakaishi yabude Dr naganin yanda takeyi yama nurse alamu data kawo gado dasauri nurse tajuya shikuma Dr yashiga motan trying to help her yabude mata baki yana tambayan Murtala dake kuka har lokacin yace "meya sameta"? Cikin kuka sosai yace "kaman kanta keciwo saita sume saikuma tafara nishi haka" daidai ankawo gadon da za'a daurata, kallon gadon yayi ya kalli yanda Dr da Nurse ke kokarin cirota su sakata agado yace "ina zaku kaita"? Dr da hankalinshi baya kanshi yace "ward mu mata treatment" dasauri yace "likita karufamin asiri kabata magani anan cikin mota kokamata allura kawai mutafi yan gidansu basa kwanciyan asibiti sunada likitansu na gida, yanzu ma babu kowa agidan ne" likitan baimabi takanshi ba dan daga gani kasan illiterate ne, idan yabar matarnan within good 10min heart dinta zai daina aiki tamutu dan as it is ma yanzu heart dinta is very weak, ciki sukaida ita Murtala nabinsu abaya yana gayamusu zasu sashi a matsala, suna shigarda ita emergency room suka rufo kofa hakan yahanashi shiga, zama yayi akasan wajen yana share hawaye na tausayi dakuma fargaban irin fadan dazaisha awajen Hajiya da Alhaji yau yamusu asalin karambani wlh.   Yana zaune wajen wata nurse tabude kofa tafito yana ganinta yatashi da sauri yace "Ya jikin Hajiya"? "Da sauki, yanzu munsamata oxygen and per hour is 15k, yanzu anaso kai deposit din naira dubu hamsin" da sauri ya kalleta yace "eh dubu hamsin" gyadamai kai tayi tace "yes inba hakaba bazamu cigaba da treatment dinta ba, yanzu dai ansamu munyi stabilizing situation din idan kabiya kudine zamu cigaba" shiru yayi kaman wawa saikuma yace "kucigaba to bari naje nadauko kudin agida" Nurse din tace "you have an hour daga yanzu zuwa Magrib" juyawa yayida sauri yafita yaciro wayanshi yana dailing number Alhaji amman har lokacin akashe, rasa yanda zaiyi yayi yawuce yakoma mota yaja motar yakoma chan gidan, bangarensu boysqutars dakinsu yawuce direct, wata katuwar ganamasgo yayi yabude sanan ya shiga cirowa yana ijiyewa kan katifa sanan yaciro watayar leda baka yakoma gefe ya zauna yabude ledan albashinshine dayake cirewa yayi saving duka duka 80k ne yamaida ledan ya kulle sanan yatashi yafito daga dakin dasauri lokacin ana shirin kiran salla komawa asibitin yayi yabiya kudin komi yarike sauran 30 a aljihu sanan yatafi masallaci kafin yadawo yasake samun wuri gaban dakin ya zauna yasake ciro wayanshi yay dailing har lokacin wayanshi akashe abin yabatamai rai amman kuma meruwanshi shidan aikine tashi yayi yawuce masallaci jin ana kiran isha'i yayi yafita waje yaje yasha shayi da indomie sanan yadawo yasake zama awajen shiru babu wanda ya cemai wani abu har bacci yasake kwasheshi yay kwanciyanshi kan yar kujeran yana sharara baccin shi gwanin ban tausayi kana ganinshi kasan yagaji.....     Kaman an tsikareta tabude idanunta ahankali tanabin inda takeda kallo tabbas tasan nanba gidanta bane, ahankali tajuyarda kanta karin ruwa datagani dakuma oxygen da akai hanging datagani yasa ta lumshe ido dan tagane she's sick but inane nan? Yunkurawa tayida kyar ta tashi tazauna tanadanjin jiri kadan, sanan ta kakkalli gefenta but babu jakanta babu wayanta balle takira wani, sakebin dakin asibitin tayida kallo taga emergency room ita kadaine aciki nothing to talk about wanan wani irin local daki takene, jitayi warin asibiti da dakin keyi na irritating nata yasa cikeda karfin hali irin nata ta yunkura tasauka daga kan gado tana zura takalminta takama karfen da ruwan kejiki dasauri ta lunshe ido, ahankali taja tasaka hannu tabude kofan tafita tana tafiya kaman zata fadi, tabi wajen dakallo babu kowa a wajen kaman ance ta kalli side dinta Murtala tagani ya kudundune jikinshi kan kujeran wajen yana bacci yana sosa hannu daga gani kasan sauro ke cizonshi, tsareshi tayida idanu ranta nabaci mesa zaikawota irin wanan asibitin, wani irin sarawa kanta yayi sabida bacin ran dataji saikuma wani irin mahaukacin jiri yazomata tai baya zata fadi tana kokarin rike karfwn da ruwanta ke sagale shikuma yabugi bango yay lara hakan yasa firgigit Murtala yafarka tareda dagokanshi ganin Hajiya idanunta na juyawa tana kokarin faduwa but tana kokarin hana kanta yasa yawaniyi tsalle yace "Hajiya" tareda tarota tafada kan kirjinshi, ko kawo wani abu baiyiba kawai yadauketa chak dukya rude sanan yaja karfen ruwan yabude dakin yace "mesa kika fito Hajiya aidakin kirani" ahankali tabude idanunta tana kallon fuskanshi yanda damuwa yanuna ko'ina akan fuskan, kirjinshi nabugawa fat fat fat tsoron karta fadi dayaji yasa taji something that is very very strange azuciyanta, she just wish and wish inama Baban Khalid ne haka looking so worried and so concern about her datafi kowace murna aduniyan nan. "Hajiya!" Firgigit tafarka daga tunanin dataje ashema harya zaunar da ita kan gado, cikeda damuwa yace "menene kikeso maiyasa kika fito tsakar daren nan? Jirifa ke mugun damunki? Meke miki ciwo yanzu? Nakira Dr"? Tunda yakemata tambayoyin take kallonshi saida yagama sanan tahade rai tace "ubanme nakeyi awanan kazamin asibitin? Wayakawoni nan?" Shiru yayi yasaukarda kanshi kasa shidaman yasan yayi laifi. "Ina maka magana kamin shiru Murtala!" Tadakamai tsawa dayasa tasake kama kanta dasauri jin kaman zaifita tace "wa....." ganin yadago kanshi ya kalleta yasa tahadiye sauran wash din tai maza ta cire hannun tasake daure fuska zatai magana yace "Hajiya dan Allah kiyihakuri kinji, bakida lafiya baki bukatan hayaniya da fada ko fushi, kinajin sauki zan gayamiki komi kinji Hajiya" ahankali tajinginar da bayanta da bango tanadan yatsine fuska tace "ka kira Alhaji? Meyasameni, mesa kakawoni nan"? Yanda tamai maganan babu wasa yasa yace "kina sauka akan mota kika fita kin fara hawa stairs kawai naganki akasa kina wani irin nishi........." nan yagayamata komi har zuwa yanzu, dan murmushi tayi tace "ayya meeting din must be very serious, jeka kiramin Dr" tai maganan kaman bakomi da sauri yafita daga dakin, daidainan hawayen data rikesu tunda yafara gayamata abinda yafaru yazubo mata sharrrr yanzu inda ace Murtala bai kawota wanan kazamin asibitin ba dahaka zata mutu abanza, Baban Khalid bai kira Dr ba saima kashe wayanshi dayayi irin ko ajikinshi dinan, baimaso adameshi da batun rashin lafiyanta yana aikin office, Baban Khalid Mijine wai ko Makiyi? Ta tambayi kanta! Jin alamun tafiya yasa da sauri ta share hawayenta tass, daidai anbude kofa Dr yashigo Murtala biyedashi yana kallonta yace "Hajiya kuka kikayi"? Wani irin mugun kallo tamai tace "fita daga dakin nan zanga Dr" babu gardama yajuya yafita yarufomusu kofa, Dr yay murmushi yace "why are u treating someone that saved your life today like this"? Murmushi yayi yakaraso gabanta yana gyara karin ruwan yace "I understand he's your driver, but koma a direban ne i must applaud his effort, I am telling u dabadan guy dinan ba we would've lost you by now, at the time daya shigo dake this hospital inda ace kin kara just 5min without seeing a Dr da heart dinki yadaina aiki, haka yashigo dake he was crying sosai" dasauri ta kalli Dr tace "crying"? Murmushi Dr yayi yace "abin yabaki mamaki ko kema, aiko kuka sosai kaman yaro wai dan Allah mutaimaki Hajiyan shi, ya tsareni wai a mota zan miki treatment baki zuwa asibiti da kyar fa yabari muka shigodake that zakiyi fada" for the first time tadansaki murmushi iya lebe, saikuma ta kalli Dr tace "what is wrong with me Dr, maisa nai passout like that"? Kujera Dr yaja yazauna sanan yace "kinada wata damuwa ne, is there anything wrong with you or bothering u"? Wani kallo tamai saikuma ta tabe baki tace "ni babu abinda kedamuna, namaka kala damai damuwa ne kakemin wanan tambayan" shiru Dr yayi yana kallonta, daga this magana datayi yagane yes tanada damuwan but she's the hard and strong type no need to even pressure her bazata fadimai ba hakan yasa yace "some of your results are out, some kuma sai gobe dasafe, kinada hypertension, and heart dinki at this junction is very very weak, bawai kinada ciwon zuciya or anything bane no! Just that heart dinki is weak, dole ki kulada kanki tsantsa dam at any point u can just collapse kimutu, dole kicire ma kanki damuwa, you should put yourself first before anything and anyone, kome kikasani dat will make u happy just be doing it, duk wani abu dake baki damuwa da matsala avoid it, I am sorry idan maganan nan yazo miki like this, I see u are strong u can handle it, and I also believe now that I tell u you will do all u can to keep yourself happy and healthy, so just do that" tunda yafara maganan tai shiru tana sauraronshi harya gama, sanan ya kalleta yace "any question" murmushi tayi kaman ba ita yabama wanan hard details din on her health ba, tace "i want to leave dazaran gari yawaye how much is my bill zan muku transfer" da sauri Dr yace "is not advisable for you to leave kibari mugama miki treatment, and issue of bill kuma your driver yayi taking care of that" da sauri ta kallai saikuma tasauke kanta ta kwanta akan gado tace "once it's morning am leaving, I have my Dr he will take it from here" yanda take maganan zaka gane bawai permission take magana ba, murmushi Dr yayi yasakai yafice yasaba da irin matan nan masuji dakansu ga shegen girman kai da fadin rai shidai Murtala na zaune bakin kofa yaga Dr yafito yawuce hakan yasa yatashi ahankali yabude kofan kaman matsoraci yaleka hada ido sukayi da Hajiya yanda tabishida kallo ba kyaftawa yasa yasauke idanunshi kasa yace "Hajiya dama na leko nagaya miki ina nan bakin kofa idan kina bukatan wani abu kawai kidan bubbuga wanchan drawer inajin karan zan shigo kinji" yanda ta tsareshi da idanu batare datace wani abuba yasa ahankali yajuya yamaida matada kofa yarufe ahankali tasauke ijiyan zuciya itama tarufe idanunta.   Hakanan tasami kantada mikarda hannunta zuwa kan drawer kaman mai tsoron drawer tadan buga kadan kafin tagama janye hannuwanta tadawo dashi jikinta taji anbude kofa da sauri karasowa gabanta yayi yadukar dakanshi kasa cikeda girmamawa yace "Hajiya gani, me kikeso? Nakiramiki likita ne"? Samin kanta tayida bude idanuwanta kadan ta kallai saikuma ta dauke kanta ta kwanta akan gadon taredajan bargo ta juyamai baya sanan ahankali murta chan kasa tace "ga kujera kazauna anan, waje akwai sauro gari na wayewa zamu tafi" "angama Hajiya yanda kikeso haka za'ayi ranki shi dade, Allah karamiki lafiya Hajiya" yay maganan yana daukan kujeran ya matsarda ita baya zuwa chan jikin bango sanan ya zauna, yaso zamanshi awaje atleast yadan mike hakarkari akan kujeran amman wanan dole sai zama yatsine fuska yayi yana gyara zama ya jinginar da kanshi ga bango sanan ahankali ya lumshe ido yana sauke ijiyan zuciya, ko 2min ba'a yiba bacci yay awon gabadashi sai minshari waaaauuuuuu! Juyowa tayida sauri ta kallai jin yanda yake munshari kaman rago, ahankali ta gyara kwanciyanta tana binshi da kallo tundaga kan kafarshi dake cikin silisaf din gida, yanada babban kafa dan diddigenshi ma awaje yake silifas din yamai kadan ga kafarshi fara itama, sai bakin wandon jikinshi na jeans dayay datti sosai, yatsine fuska tayi tabi rigan da kallo itama tai datti gashi kirjinshi very huge ga fadi gakuma cika kaman yana daga karfe, ahankali tasauke idanunta kan wuyanshi fatarshi suli suli gadan gemunshi dabaida wani yawa, saikuma tasauke idanunta akan fuskarshi ahankali tafadi azuciyanta Murtala fa mugun kyakkyawane, kauyanci darashin son gyarane yasa yake hakafa, and he is so innocent, despite the fact bata sakinmai fuska, batamai murmushi kullum cikin fada takemai dudda mugun tsoronta dayakeyi dan yana mugun jin tsoronta samada Alhaji ma dan yana hira da Alhaji sosai, itako bayayi da ita, but despite all of this he saved her life, yamata abinda ko mijinta baitaba mataba, she's so grateful to him dudda bata nunamai ba but har kasan zuciyanta taji dadin abinda yamata and for the first time duk tsanan nan datamai na dan kauye ne bai iya karatu ba duksai taji yakau. Kiran salla dataji anyi yasa tadan gyara kwanciya tace bari atada sallan asuba saita tadashi sutafi gida she needs a very clean and hot shower, lumshe idanunta tayi ahankali tana sauke ijiyan zuciya komida Dr yafadi mata suna kara mata yawo akanta, how will she stay happy now, kodai ta tattara taje gidansu tazauna cikin family tane koda na one month ne, but tana zuwa za'ai sensing something is wrong and Baban Khalid ma zai yardane yabarta taje gida tai one month, sarawa da kanta yayi yasa tahakura da tunanin tasake juyowa tazuba idanunta kan Murtala lokacin ana shirin tada sallan asuba. "Murtala" takirashi ahankali, firgigit yabude idanunshi dake cikeda bacci ya kalleta hada ido sukayi da sauri yatashi tsaye yana sosa kanshi yace "Hajiya gani, akira likita ne? Mekike bukata"? Girgizamai kai tayi softly tace "tafi masallaci kai salla kana dawowa saimu tafi" gyadamata kai yayi yajuya yana tafiya ahankali yafita tabishi da kallo ita karan kanta tasan yagaji.   _Hi Ladies let's deliberate small on this issue. Yanzu if Hajiya start developing something ma Murtala will you all blame her or blame mijinta?_ _zuciya batada kashi, kuma zuciya aba ce da bata tambayan permission dinka kafin taso abu, idan tarasa abu anan dazaran tasami abun awani wuri saita fara son abun, hakane ko bahaka bane ladies?_ _Alhaji Alhassan Bakori ya kyauta abinda yayi???_ _mezakuce game da Murtala our 26yrs old driver that is simply doing his work? Mekuke ganin nan gaba zai faru tsakanin shi da Hajiya?_ _so far what have you learnt in this page??_ 07012181461 chat me up a watsapp this is my number. ✍M SHAKUR EPISODE 3️⃣ 6 nasafe dot yashigo tareda Dr, duk zaune suka sameta abakin gado, Murtala dake gefen Dr ya rusuna yace "ina kwana Hajiya" ko kallon Murtalan batayiba ta kalli Dr yace "i told you am leaving" dan murmushi Dr yayi yakaraso inda take rikeda da wata yar paper da pen yace "I just need you to sign this then u can go" karban takardan tayi tana karanta content din yace "is DAMA form, discharge against medical advice" signing tayi tabashi sanan tasauka daga gado ahankali harda dan gudu Murtala yakaraso gabanta yace "Hajiya zaki iya tafiya kona daukeki kokuma na dauko miki kujeran guragu"? Yanda yayi maganan saida yasa murmushi yadan subuce mata daga baki kawai tawuce tai gaba tabishi yabita abaya harzuwa motansu, baya yabude mata tashiga ahankali tazauna yarufomata kofan sanan yakoma gaba ya shiga yaja motar, itakuma tadauki jakanta dake kasan motan tabude taciro wayanta dake ciki hakanan tasami kanta dacire lock din wayan ganin babu miss call kodaya na Alhaji yasa ta maida wayan ta ijiye ta kauda tunaninshi aranta, har gida suka karaso ya danna remote gate yabudu ga mamakinta saitaga motan Baban Khalid direbanshi na wanke motan, tunkafin ta sauko direban ke gaidata, fitowa tayi ahankali rikeda jakanta Murtala yafito yashiga gabanta yamika mata hannu yace "kawo jakan narike" girgizamai kai tayi tace "jeka huta kayi kokari" sanan tawuce shi, juyawa yayi ya kalleta sanan yace "Hajiya zaki iya wuce benen"? Chak ta tsaya jin tambayanshi har ranta taji diran maganan kaman zata juyota kallai saikuma ta daure bata amsashi ba tashiga hawa benen dazai sadata da kofar shiga falon ta, tanajin muryan Murtala yana Alhamdulillah Hajiya tawuce batare data sake sumewa ba, Emus sannu da aiki, shikuma Emus yana sai yanzu kaganni, bude kofa tayi ahankali tashiga falonta.   Zaune Alhaji yake kan dogon kujera dagashi sai wata white jallabiya hannunshi rikeda remote yana kallon tashar CNN dayan hannunshi kuma rikeda mug na lipton yana, jin anbude kofa yasa yadago kanshi ya kalleta hada ido sukayi yace "Hassana ina kika kwana"? Kaman bazata kulashiba tajuya tamaida kofan tarufe sanan tajuyo ta kalleshi ahankali tace "asibiti" da sauri yadaura hannunshi asaman goshinshi yace "laaaa kinganni fa ba shaf na manta wanchan direban yaron naki yakirani ba nacemai bari nagama meeting zan kira Dr yazo, kwata kwata bamu gama meeting dawuri ba, I came back very late dakina nawuce na kwanta sai this morning ma naga bakinan ashe" jitayi wani abu ya tsayamata awuya saikuma ta daure takakalomai murmushi batare datace komiba tashigo zatai stairs yace "ina magana kuma zaki wuce" juyowa tayi ta kalleshi tace "kace mene"? Wani kallan kallo yamata yace "fushi kikeyine I told u meeting nake saisa ban kira Dr ba na manta, but bagashinan u are fine ba, ainasan ki u are a very strong woman" ahankali tace "Allah ko, tom godiya nake" tana maganan tajuya da sauri tai sama gudun kar hawayen dake gabda zubomata yazubo yagansu kofar dakinta tabude tashiga ta maida dasauri tarufe saikukan yazo sosai tacigaba da dannewa tasaki jakanta awajen tabude bathroom dinta da sauri tabude tap tafashe da kuka sosai jikinta har wani bari yake, what is this life? Is her husband husband ko enemy? This is the second time take tambayan kanta, tayaya za'ace mutumin da aka dauramusu auren, akace cinta shanta, suturanta, lafiyanta komi nata yatashi dagakan iyayenta yakoma kanshi yadawo mata haka, ankira bawan Allahan nan ancemai tasume she's unconscious, yama kashe wayanshi batare dayakira Dr ba, yadawo baima dubata adaki ko lafiyanta lauba, sanan yaganta yanzu koyace mata yajiki, so yanzu idanda tamutu baidama hassara saidai yaranta suyi kuka ko, she's not his business, baima sonta dan saikanason wani zaka damudashi, jin kanta yafara sarawa yasa dole ta tsayarda kukan tawanke fuskanta tareda kashe tap din tacire riga tai wanka da ruwan zafi sosai tadauro towel tafito daga bayin, gaban mirror ta tsaya idanunta sunyija tana goge jikinta da karamin towel, ahankali ta ijiye towel din kan chair bayan tagama tsanewa sanan tamika hannu zata dauki cream kenan taji anbudemata kofa hakan yasa tadaga kanta, Alhaji ne yashigo daure da towel a waist washemata baki yayi yamaida kofan yarufe itakuma tacire idanunta daga kanshi shigowa dakin yayi yazota bayanta ya tsaya yakai hannunshi kan kafadunta yakama yana kallon fuskanta tamudi yace "harkinyi wanka Hassana"? Bataredata kalleshi ba ta tsiyaya mai a hannu tace "uhm nayi wanka" murmushi yasakeyi yasaukar da kanshi yana kallon very big ass dinta yakai hannunshi yadaura akai yace "how far? Come please let's do it sharp sharp danna fita I have a meeting by 9" batare data kalleshiba still tana shafamai a hannunta tace "not today please, cus am not in the mood" daure fuska yayi yadago kanshi ya kalleta tamadubi ganin mai abinta take shafawa yasa yakai hannunshi kafadanta yawani irin juyoda ita da karfi ranshi abace yace "what do you mean by u are not in the mood? Look how erect I am" yanuna dick dinshi dayamike ta towel yace "is this how u want me to go to the office, waike wace irin mace ce"? Yay maganan da fushi daidai lokacin tadago idanunta dasukai ja sosai takallai tace "kaima wani irin mijine Alhassan? I was so sick kakasa kiramin Dr, nadawo you couldn't ask me yajiki or me akace yana damunki, meyasa kika suma, all you want is sex and sort out your desire ta jikin your sick wife? What kind of husband are you Baban Khalid? Mtswww u piss me off i swear" tafadi tanaji kaman ta watsamai mari, cikeda zuciya yace "nikikama tsaki"? Wani kallon raini tamai tace "I hope u know u deserve much more than that, I would've done more kawai darajan su Khalid kaci, and get out of my room please bazan iya hayaniya dakaiba I need absolute rest" tana maganan ta tashi daga gabanshi tawuce gaban wardrobe tabude tana kokarin nemo kayan dazata saka, shikuka yabita da kallo, strictly yace "as your dutiful husband Hassana, I command you to come here kibani hakkina" ko kallonshi batayibama tacigaba da neman kayan dazata saka kaman batajima meyaceba, takowa yayi yazo gabanta cikin fushi yace "waini kika komarda mahaukaci badake nake magana ba? Nace kizo kibani hakkina"? Juyowa tayi kaman yanda yake mata ihu tamai itama tace "tell me which of my hakki kaima kake saukewa? Nai rashin lafiya ko ajikinka inda namutu mai zaka gayama yaranmu eh? Kadamu dani ne ko kadamu da lafiyata wanne daga ciki? Kamin yajiki ko sannu dajiki? And kanada audacity kawani zo kanacemin nabaka hakkinka" cikin fushi yace "ke yarinya ce dazan tsaya ina tambayanki yajiki? Are u not old enough to take care of yourself? Yara ake tambaya yajiki not a 36yrs old woman maman 14yrs old children, see banda time dinki, jikinki nedai ko kici kanki, tafiyan ma danace nafasayi zan tafi, am going to China zanje nasayo some machines na construction, bansan randa zan dawoba, it might take a month or 2, bye woman" yawuce fuuuu yafita daga dakin, hawaye taji zasu zubomata tadaure tahana kanta tadau wata simple gown na cotton tasaka tahau gado taja bargo tarufa tana kokarin sa kanta bacci, tana kwance awajen taji fitowanshi yanajawo suit case ko lekowa baiyiba balle yamata sallama yawuce yatafi abinshi._DUK WACCE TAKARANTA THIS BOOK BATARE DAYA BIYABA ITADA ALLAH._ Tun tana tunane tunane sama sama har bacci yay nasaran awon gaba da ita, batawani jimaba ta tashi sake sako wani wankan tayi sanan tai salla ta tashi ta shirya cikin wata gangariyan shadda orange sanan tasauko kasa rikeda wayanta, dinning takaraso tana bude hadaddun kulan dake wajen taga maid tai lafiyayyen girki kala kala, masa tadeba da miya sanan tazuba ruwan lipton a cup tazauna tanafaraci ahankali tana tunanin kota kira Dr ne kokuma karta kira yazo yadubata, yatsine fuska tayi tace "anjima zata kirashi" saida taci tai nak sanan ta tashi ahankali tafito falo tazauna tareda daukan remote zata saka wani abuta kalla, zee world tasa sanan tamikarda kafafuwanta kan table din din tsakiyan falon tafara kallo.   Sosai tai nisa a kallon taji anyi knocking kofa, ahankali tajuyoda fuskarta ta kalli kofan, wani bakauyene still knock doors bayan akwai door bell. "Hajiya nine Murtala direba ne" yafadi da karfi dayasama tabude idanu kadan wondering saikace yashiga zuciyanta yaji metacene, dan daga murya kadan tayi sabida yajita tace "shigo" bude kofan yayi ahankali kaman matsoraci sanan yadago kanshi ya kallo cikin falon hada ido yayida Hajiya dake zaune kan kujera itama tajuyo tana kallonshi lumshe ido tayi kadan saikuma tadauke kanta tamaida kan TV ganin Murtalane wanan karan yayi wanka yasaka wasu riga da jean wankakku dayamai kyau dan rigan jane, ganin yanda tadauke kai yasa yashigo dakin da sauri gudun karya batamata lokaci yarufo kofan sanan yakaraso har tsakiyan falon ahankali ya zube akan center carpet din yana facing nata, kanshi akasa yace "dama nazo naduba kine Hajiya, ya karfin jiki"? Kaman bazata kulashi ba amman har ranta taji kalman yazo yadubatane, ahankali tajuyo tazuba idanunta akanshi, cikin soft voice tace "naji sauki Murtala" dasauri yadago kanshi yakalleta kaman yanda take kallonshi yawani sakin mata one cute smile dayasa tadauke kanta da sauri jin gabanta yafadi cikeda murna sosai yace "Hajiya naji mugun dadi kince kinji sauki, wayyo Allah na wlh dadi nakeji" shifa harga Allah yake magana yanda yakeji kuma haka yake fadi, batare data kalleshi cikeda isan nan daji dakai irin nata tace "maisa kaji dadi dannace naji sauki" ko kadan baikawo komi aranshi with a very free mind and innocent heart yace "sabida ina sonki Hajiya!" Dasauri tajuyo ta kalleshi sabida yanda maganan ta dira aranshi, baidena murmushin dake karamai kyauba yana kallonta yace "wlh Hajiya bakiga yanda nadamu ba dabaki da lpy ba, inason uwardakina banson naji komi yasameta" ganin yanda tafarsara maganan daban abinda shi yake nufi daban from the look in his face yasa tasake daukekai but she could feel the sound na dariyanshi and his excitement. "Hajiya kina bukatan wani abune naje nasayo miki" kin kallonshi tayi ta girgizamai kai, hakan yasa ahankali yatashi yana murmushi yace "bari natafi, babu kowa agidan idan kina bukatan wani abu ki kirani awaya Hajiya, Allah karamiki lpy, Allah yaja kwana Maman Yan biyu" yafadi tareda juyawa yay hanyar kofa, harya daura hannunshi kan kofa ahankali yaji tace "Murtala" dasauri yajuyo yace "na'am" saikuma yadawo harda dan gudunshi yazo gabanta yazube yace "gani Allah yataimaki ran Hajiya" batare data kalleshiba har lokacin tv take kallo tace "shekaranka nawa" da sauri yace "ashirin da shidda Hajiyar Allah" gyadamai kai tayi still bata kallaiba saidai shi dake kallonta kaman yasami TV, ahankali tace "a ina Alhaji yasamoka? Bani labari" washe baki yayi ya gyara zama da kyau yace "a kauyenmu yanada gona, munamai aiki, duk cikin masumai aiki nafisu kwazo sabida inaso nai aiki sosai dan afi biyana natara kudi sosai" juyowa tayi ta kalleshi tace "mezakayi da kudi haka"? Murmushi yamata sosai saikuma ya lankwaya kai yace "Umma na zan kaimawa" "Maman ka"? Gyadamata kai yayi, dasauri tace "ina jinka, bani labarin Mamanka maisa kake aiki sosai sabida ita" murmushi yadanyi yace "tanada ciwon daji, amman yanzu ma taji sauki sosai, kingako Hajiya ni kadai Umma ta haifa, nida nataso bansan Babana ba tace yarasu, itama Umma ta tsufa sosai, tanada gona itake daukana muje gona harna iya noma, muna noman albasa, ridi, masara da sauransu shimuke saidawa musami kudi, to data fara ciwone ina fitowa daga kauye na kaita asibiti shine harna saida gonanmu mukai magani dashi amman bata warkeba muka dawo, shine makotanmu mutumin yadauki Umma kaman mamanshi dagashi har matarshi yace mukowa na hausa muna kaita wani kauye kusada namu karban magani kuma saishi yay aiki, nikuma ya nemamin aikin gonan Alhaji nafara, har ranan da Alhaji yazo yaganni yace namai wai inada gwazo ga iya aiki zai kaini binni yasani makarantan koyan mota, koda nafadawa Umma ya yarda duk sukace naje ni namijine dole nafita na nema, Alhaji yasa aka kawoni_DUK WACCE TAKARANTA BATA BIYABA BAN YAFEBA_ aka kaini koyan mota ko sati biyu banyiba na iya shikenan bayan kusan wata biyu naga yakawomin wanan katin nan yauwa license na tuki yakawo ni gidan nan yace zan dinga tukaki shikenan" yakarake maganan yana murmushi sosai take kallonshi zucuyarta na ayyana mata abubuwa kala kala, murya chan kasa tace "kadade rabonka da ganin Umma" gyadamata kai yayi ahankali, murya chan kasa tace "baka kewanta"? Dan murmushi yayi yace "inayi....." saikuma yaydan shiru ya saukarda kanshi kasa kafin ahankali yace "inayi sosai" yanda taga yasaukarda kanshi kasa yasa takirashi gently. "Murtala" dagokanshi yayi yace "na'am Hajiya" gani tayi idanunshi sun cikada hawaye sosai dasauri tadauke kai jin heart dinta na beating sosai tama kasa magana, ahankali taji yanajan majina dadan shesheka, kasa daurewa tayi tajuyo ta kalleshi taga kuka yake awurin, dan murmushi tayi tace "inane kauyenku"? Bayan hannunshi yakai yana share fuskanshi sanan yace "chan wani kauyene hanyan Kano" murmushi tasakeyi tace "tomka shirya gobe zakaje kagano Umma jibi saika dawo ko" tai maganan ahankali da murya kaman tana lallashinshi, dago rinannun idanunshi yayi yakalleta sanan ahankali yace "dagaske Hajiya" gyadamaikai tayi batare datai magana ba hakan yasa yafashe da murna dakuka duka biyun yanajin wani irin farin ciki da kaunar Hajiya dabaitaba jiba yace "Hajiya nagode, nagode" saikuma yatashi yana share fuskanshi yace "nagode Hajiya, Allah yamiki albarka" saikuma yajuya yace "bari naje Hajiya, wayyo yau ina cikin farin ciki sosai Hajiya nagode" yay maganan tareda bude kofa yafice duk tana kallonshi she don't know why kodan yakulada ita ne but she finds him so attractive and adorable gashi dan kauye dashi so innocent, kwanciya tayi akan dogon kujeran haka tana kallo buni buni yana fadomata arai har tahau bacci. _DUK WACCE TAKARANTA BATA BIYABA BAN YAFEBA__DUK WACCE TAKARANTA THIS BOOK BATARE DAYA BIYABA ITADA ALLAH._ Tun tana tunane tunane sama sama har bacci yay nasaran awon gaba da ita, batawani jimaba ta tashi sake sako wani wankan tayi sanan tai salla ta tashi ta shirya cikin wata gangariyan shadda orange sanan tasauko kasa rikeda wayanta, dinning takaraso tana bude hadaddun kulan dake wajen taga maid tai lafiyayyen girki kala kala, masa tadeba da miya sanan tazuba ruwan lipton a cup tazauna tanafaraci ahankali tana tunanin kota kira Dr ne kokuma karta kira yazo yadubata, yatsine fuska tayi tace "anjima zata kirashi" saida taci tai nak sanan ta tashi ahankali tafito falo tazauna tareda daukan remote zata saka wani abuta kalla, zee world tasa sanan tamikarda kafafuwanta kan table din din tsakiyan falon tafara kallo.   Sosai tai nisa a kallon taji anyi knocking kofa, ahankali tajuyoda fuskarta ta kalli kofan, wani bakauyene still knock doors bayan akwai door bell. "Hajiya nine Murtala direba ne" yafadi da karfi dayasama tabude idanu kadan wondering saikace yashiga zuciyanta yaji metacene, dan daga murya kadan tayi sabida yajita tace "shigo" bude kofan yayi ahankali kaman matsoraci sanan yadago kanshi ya kallo cikin falon hada ido yayida Hajiya dake zaune kan kujera itama tajuyo tana kallonshi lumshe ido tayi kadan saikuma tadauke kanta tamaida kan TV ganin Murtalane wanan karan yayi wanka yasaka wasu riga da jean wankakku dayamai kyau dan rigan jane, ganin yanda tadauke kai yasa yashigo dakin da sauri gudun karya batamata lokaci yarufo kofan sanan yakaraso har tsakiyan falon ahankali ya zube akan center carpet din yana facing nata, kanshi akasa yace "dama nazo naduba kine Hajiya, ya karfin jiki"? Kaman bazata kulashi ba amman har ranta taji kalman yazo yadubatane, ahankali tajuyo tazuba idanunta akanshi, cikin soft voice tace "naji sauki Murtala" dasauri yadago kanshi yakalleta kaman yanda take kallonshi yawani sakin mata one cute smile dayasa tadauke kanta da sauri jin gabanta yafadi cikeda murna sosai yace "Hajiya naji mugun dadi kince kinji sauki, wayyo Allah na wlh dadi nakeji" shifa harga Allah yake magana yanda yakeji kuma haka yake fadi, batare data kalleshi cikeda isan nan daji dakai irin nata tace "maisa kaji dadi dannace naji sauki" ko kadan baikawo komi aranshi with a very free mind and innocent heart yace "sabida ina sonki Hajiya!" Dasauri tajuyo ta kalleshi sabida yanda maganan ta dira aranshi, baidena murmushin dake karamai kyauba yana kallonta yace "wlh Hajiya bakiga yanda nadamu ba dabaki da lpy ba, inason uwardakina banson naji komi yasameta" ganin yanda tafarsara maganan daban abinda shi yake nufi daban from the look in his face yasa tasake daukekai but she could feel the sound na dariyanshi and his excitement. "Hajiya kina bukatan wani abune naje nasayo miki" kin kallonshi tayi ta girgizamai kai, hakan yasa ahankali yatashi yana murmushi yace "bari natafi, babu kowa agidan idan kina bukatan wani abu ki kirani awaya Hajiya, Allah karamiki lpy, Allah yaja kwana Maman Yan biyu" yafadi tareda juyawa yay hanyar kofa, harya daura hannunshi kan kofa ahankali yaji tace "Murtala" dasauri yajuyo yace "na'am" saikuma yadawo harda dan gudunshi yazo gabanta yazube yace "gani Allah yataimaki ran Hajiya" batare data kalleshiba har lokacin tv take kallo tace "shekaranka nawa" da sauri yace "ashirin da shidda Hajiyar Allah" gyadamai kai tayi still bata kallaiba saidai shi dake kallonta kaman yasami TV, ahankali tace "a ina Alhaji yasamoka? Bani labari" washe baki yayi ya gyara zama da kyau yace "a kauyenmu yanada gona, munamai aiki, duk cikin masumai aiki nafisu kwazo sabida inaso nai aiki sosai dan afi biyana natara kudi sosai" juyowa tayi ta kalleshi tace "mezakayi da kudi haka"? Murmushi yamata sosai saikuma ya lankwaya kai yace "Umma na zan kaimawa" "Maman ka"? Gyadamata kai yayi, dasauri tace "ina jinka, bani labarin Mamanka maisa kake aiki sosai sabida ita" murmushi yadanyi yace "tanada ciwon daji, amman yanzu ma taji sauki sosai, kingako Hajiya ni kadai Umma ta haifa, nida nataso bansan Babana ba tace yarasu, itama Umma ta tsufa sosai, tanada gona itake daukana muje gona harna iya noma, muna noman albasa, ridi, masara da sauransu shimuke saidawa musami kudi, to data fara ciwone ina fitowa daga kauye na kaita asibiti shine harna saida gonanmu mukai magani dashi amman bata warkeba muka dawo, shine makotanmu mutumin yadauki Umma kaman mamanshi dagashi har matarshi yace mukowa na hausa muna kaita wani kauye kusada namu karban magani kuma saishi yay aiki, nikuma ya nemamin aikin gonan Alhaji nafara, har ranan da Alhaji yazo yaganni yace namai wai inada gwazo ga iya aiki zai kaini binni yasani makarantan koyan mota, koda nafadawa Umma ya yarda duk sukace naje ni namijine dole nafita na nema, Alhaji yasa aka kawoni aka kaini koyan mota ko sati biyu banyiba na iya shikenan bayan kusan wata biyu naga yakawomin wanan katin nan yauwa license na tuki yakawo ni gidan nan yace zan dinga tukaki shikenan" yakarake maganan yana murmushi sosai take kallonshi zucuyarta na ayyana mata abubuwa kala kala, murya chan kasa tace "kadade rabonka da ganin Umma" gyadamata kai yayi ahankali, murya chan kasa tace "baka kewanta"? Dan murmushi yayi yace "inayi....." saikuma yaydan shiru ya saukarda kanshi kasa kafin ahankali yace "inayi sosai" yanda taga yasaukarda kanshi kasa yasa takirashi gently. "Murtala" dagokanshi yayi yace "na'am Hajiya" gani tayi idanunshi sun cikada hawaye sosai dasauri tadauke kai jin heart dinta na beating sosai tama kasa magana, ahankali taji yanajan majina dadan shesheka, kasa daurewa tayi tajuyo ta kalleshi taga kuka yake awurin, dan murmushi tayi tace "inane kauyenku"? Bayan hannunshi yakai yana share fuskanshi sanan yace "chan wani kauyene hanyan Kano" murmushi tasakeyi tace "tomka shirya gobe zakaje kagano Umma jibi saika dawo ko" tai maganan ahankali da murya kaman tana lallashinshi, dago rinannun idanunshi yayi yakalleta sanan ahankali yace "dagaske Hajiya" gyadamaikai tayi batare datai magana ba hakan yasa yafashe da murna dakuka duka biyun yanajin wani irin farin ciki da kaunar Hajiya dabaitaba jiba yace "Hajiya nagode, nagode" saikuma yatashi yana share fuskanshi yace "nagode Hajiya, Allah yamiki albarka" saikuma yajuya yace "bari naje Hajiya, wayyo yau ina cikin farin ciki sosai Hajiya nagode" yay maganan tareda bude kofa yafice duk tana kallonshi she don't know why kodan yakulada ita ne but she finds him so attractive and adorable gashi dan kauye dashi so innocent, kwanciya tayi akan dogon kujeran haka tana kallo buni buni yana fadomata arai har tahau bacci._RANAKUN POSTING ARE SUNDAYS, TUESDAYS, FRIDAYS_ Wuraren 6 family Dr su yashigo gidan, Murtala ya shigodashi har falo sanan yafita bayan Hajiya tasauko kasa cikin shiga ta alfarma. Boysqutars dinsu yawuce yashiga yana hada kayanshi bini bini Hajiya nafadomai arai saiyay murya ahaka har aka kira magrib yawuce yatafi masallaci saida akai isha'i sanan yafito yadawo gidan yana tafiya ahankali, wayanshine tadau ringing ciro wayan yayi ganin Hajiyane yasa yakai wayan kunne dagudu yace "Allah ya taimaki Hajiya" "ina jiranka afalo" tafada ba wasa atattare da ita, da sauri ya katse wayan yay hanya flat dinta bude kofa yayi ahankali yashiga bakinshi dauke da sallama zaune yaganta kan kujera tana sanyeda wani simple gown na cotton dayakaimata har kasa irin na baccin nan pink color, kanta sanye da pink turban mai kyau idanunta sanyeda white glasses tadaura pillow kan laps dinta dai Mac book kan pillow tana aiki a system kafafuwanta sanye da indoors shoes pink masu shegen kyau kaganta she looks so adorable bazata taba yarda ta haifi 13yrs old children ba, kasama gaisheta yayi saiwani irin kallonta dayahauyi gabaki daya tatafi da imaninshi, jin shiru not the usual Murtala mai zuba yasa tajanye idanunta dagakan laptop din tadago kanta ta kalleshi hada ido sukayi dan kamashi tayi yana kallonta wani irin kunyane yakamashi saiyadan juyarda kanshi ahankali cikeda kunya kaman ta tuhumeshi yace "Hajiya wlh wlh kinyi kyau, gelashin nan yamiki kyau" yakarashe maganan yana juyarda kanshi gabaki daya, har kasan ranta taji dadin maganan shi this is abunda Baban Khalid bai taba nunamata ba, duk kyan dazatayi aduniyan nan ko kalloma bata isheshi ba, daurewa tayj bata nunamai ba saitadau wani rapa data ijiye agefen ta nayan 500 sababbi gal tajuyo tace "gashi" juyowa yayi ahankali yasake kallonta hada ido sukayi gabanshi nafaduwa sosai sake ganinta dayayi, babu gardama yakaraso yasaka hannunshi yakarbi kudin cikin muryanta dake nuna tsantsan natsuwa dakuma isa ga dadi tace "kudinka daka kashe a asibiti ne wanan" murmushi yamata sosai still yana kallonta yakasa magana, sake daukan another rapa nayan 500 tayi tamikamai kai hannu yayi zai karba yana kallon fuskanta still kaman yanda take kallonshi, mistakenly hannunshi yataba fatar nata wani irin shock sukaji dukansu atare da sauri ta sakinmai kudin ya karba sanan yadan koma baya jikinshi narawa ahankali batare data kalleshi ba tace "kai using wanan kasaima Umman ka abu" zubewa yayi awajen yace "Allah ya ampana, Allah yabiya bukatu Hajiya, Allah kuma yataimaka" "zaka iya tafiya" kaman jira yake yajuya da sauri yafice daga falon, yasauka yadauki hanyan side dinsu yana mamakin what is wrong with him idan yana tareda Hajiya. _DUK WACCE TAKARANTA BATA BIYABA BAN YAFEBA_ aka kaini koyan mota ko sati biyu banyiba na iya shikenan bayan kusan wata biyu naga yakawomin wanan katin nan yauwa license na tuki yakawo ni gidan nan yace zan dinga tukaki shikenan" yakarake maganan yana murmushi sosai take kallonshi zucuyarta na ayyana mata abubuwa kala kala, murya chan kasa tace "kadade rabonka da ganin Umma" gyadamata kai yayi ahankali, murya chan kasa tace "baka kewanta"? Dan murmushi yayi yace "inayi....." saikuma yaydan shiru ya saukarda kanshi kasa kafin ahankali yace "inayi sosai" yanda taga yasaukarda kanshi kasa yasa takirashi gently. "Murtala" dagokanshi yayi yace "na'am Hajiya" gani tayi idanunshi sun cikada hawaye sosai dasauri tadauke kai jin heart dinta na beating sosai tama kasa magana, ahankali taji yanajan majina dadan shesheka, kasa daurewa tayi tajuyo ta kalleshi taga kuka yake awurin, dan murmushi tayi tace "inane kauyenku"? Bayan hannunshi yakai yana share fuskanshi sanan yace "chan wani kauyene hanyan Kano" murmushi tasakeyi tace "tomka shirya gobe zakaje kagano Umma jibi saika dawo ko" tai maganan ahankali da murya kaman tana lallashinshi, dago rinannun idanunshi yayi yakalleta sanan ahankali yace "dagaske Hajiya" gyadamaikai tayi batare datai magana ba hakan yasa yafashe da murna dakuka duka biyun yanajin wani irin farin ciki da kaunar Hajiya dabaitaba jiba yace "Hajiya nagode, nagode" saikuma yatashi yana share fuskanshi yace "nagode Hajiya, Allah yamiki albarka" saikuma yajuya yace "bari naje Hajiya, wayyo yau ina cikin farin ciki sosai Hajiya nagode" yay maganan tareda bude kofa yafice duk tana kallonshi she don't know why kodan yakulada ita ne but she finds him so attractive and adorable gashi dan kauye dashi so innocent, kwanciya tayi akan dogon kujeran haka tana kallo buni buni yana fadomata arai har tahau bacci. _DUK WACCE TAKARANTA THIS BOOK BATARE DAYA BIYABA ITADA ALLAH._ Tun tana tunane tunane sama sama har bacci yay nasaran awon gaba da ita, batawani jimaba ta tashi sake sako wani wankan tayi sanan tai salla ta tashi ta shirya cikin wata gangariyan shadda orange sanan tasauko kasa rikeda wayanta, dinning takaraso tana bude hadaddun kulan dake wajen taga maid tai lafiyayyen girki kala kala, masa tadeba da miya sanan tazuba ruwan lipton a cup tazauna tanafaraci ahankali tana tunanin kota kira Dr ne kokuma karta kira yazo yadubata, yatsine fuska tayi tace "anjima zata kirashi" saida taci tai nak sanan ta tashi ahankali tafito falo tazauna tareda daukan remote zata saka wani abuta kalla, zee world tasa sanan tamikarda kafafuwanta kan table din din tsakiyan falon tafara kallo.   Sosai tai nisa a kallon taji anyi knocking kofa, ahankali tajuyoda fuskarta ta kalli kofan, wani bakauyene still knock doors bayan akwai door bell. "Hajiya nine Murtala direba ne" yafadi da karfi dayasama tabude idanu kadan wondering saikace yashiga zuciyanta yaji metacene, dan daga murya kadan tayi sabida yajita tace "shigo" bude kofan yayi ahankali kaman matsoraci sanan yadago kanshi ya kallo cikin falon hada ido yayida Hajiya dake zaune kan kujera itama tajuyo tana kallonshi lumshe ido tayi kadan saikuma tadauke kanta tamaida kan TV ganin Murtalane wanan karan yayi wanka yasaka wasu riga da jean wankakku dayamai kyau dan rigan jane, ganin yanda tadauke kai yasa yashigo dakin da sauri gudun karya batamata lokaci yarufo kofan sanan yakaraso har tsakiyan falon ahankali ya zube akan center carpet din yana facing nata, kanshi akasa yace "dama nazo naduba kine Hajiya, ya karfin jiki"? Kaman bazata kulashi ba amman har ranta taji kalman yazo yadubatane, ahankali tajuyo tazuba idanunta akanshi, cikin soft voice tace "naji sauki Murtala" dasauri yadago kanshi yakalleta kaman yanda take kallonshi yawani sakin mata one cute smile dayasa tadauke kanta da sauri jin gabanta yafadi cikeda murna sosai yace "Hajiya naji mugun dadi kince kinji sauki, wayyo Allah na wlh dadi nakeji" shifa harga Allah yake magana yanda yakeji kuma haka yake fadi, batare data kalleshi cikeda isan nan daji dakai irin nata tace "maisa kaji dadi dannace naji sauki" ko kadan baikawo komi aranshi with a very free mind and innocent heart yace "sabida ina sonki Hajiya!" Dasauri tajuyo ta kalleshi sabida yanda maganan ta dira aranshi, baidena murmushin dake karamai kyauba yana kallonta yace "wlh Hajiya bakiga yanda nadamu ba dabaki da lpy ba, inason uwardakina banson naji komi yasameta" ganin yanda tafarsara maganan daban abinda shi yake nufi daban from the look in his face yasa tasake daukekai but she could feel the sound na dariyanshi and his excitement. "Hajiya kina bukatan wani abune naje nasayo miki" kin kallonshi tayi ta girgizamai kai, hakan yasa ahankali yatashi yana murmushi yace "bari natafi, babu kowa agidan idan kina bukatan wani abu ki kirani awaya Hajiya, Allah karamiki lpy, Allah yaja kwana Maman Yan biyu" yafadi tareda juyawa yay hanyar kofa, harya daura hannunshi kan kofa ahankali yaji tace "Murtala" dasauri yajuyo yace "na'am" saikuma yadawo harda dan gudunshi yazo gabanta yazube yace "gani Allah yataimaki ran Hajiya" batare data kalleshiba har lokacin tv take kallo tace "shekaranka nawa" da sauri yace "ashirin da shidda Hajiyar Allah" gyadamai kai tayi still bata kallaiba saidai shi dake kallonta kaman yasami TV, ahankali tace "a ina Alhaji yasamoka? Bani labari" washe baki yayi ya gyara zama da kyau yace "a kauyenmu yanada gona, munamai aiki, duk cikin masumai aiki nafisu kwazo sabida inaso nai aiki sosai dan afi biyana natara kudi sosai" juyowa tayi ta kalleshi tace "mezakayi da kudi haka"? Murmushi yamata sosai saikuma ya lankwaya kai yace "Umma na zan kaimawa" "Maman ka"? Gyadamata kai yayi, dasauri tace "ina jinka, bani labarin Mamanka maisa kake aiki sosai sabida ita" murmushi yadanyi yace "tanada ciwon daji, amman yanzu ma taji sauki sosai, kingako Hajiya ni kadai Umma ta haifa, nida nataso bansan Babana ba tace yarasu, itama Umma ta tsufa sosai, tanada gona itake daukana muje gona harna iya noma, muna noman albasa, ridi, masara da sauransu shimuke saidawa musami kudi, to data fara ciwone ina fitowa daga kauye na kaita asibiti shine harna saida gonanmu mukai magani dashi amman bata warkeba muka dawo, shine makotanmu mutumin yadauki Umma kaman mamanshi dagashi har matarshi yace mukowa na hausa muna kaita wani kauye kusada namu karban magani kuma saishi yay aiki, nikuma ya nemamin aikin gonan Alhaji nafara, har ranan da Alhaji yazo yaganni yace namai wai inada gwazo ga iya aiki zai kaini binni yasani makarantan koyan mota, koda nafadawa Umma ya yarda duk sukace naje ni namijine dole nafita na nema, Alhaji yasa aka kawoni_RANAKUN POSTING ARE SUNDAYS, TUESDAYS, FRIDAYS_ Wuraren 6 family Dr su yashigo gidan, Murtala ya shigodashi har falo sanan yafita bayan Hajiya tasauko kasa cikin shiga ta alfarma. Boysqutars dinsu yawuce yashiga yana hada kayanshi bini bini Hajiya nafadomai arai saiyay murya ahaka har aka kira magrib yawuce yatafi masallaci saida akai isha'i sanan yafito yadawo gidan yana tafiya ahankali, wayanshine tadau ringing ciro wayan yayi ganin Hajiyane yasa yakai wayan kunne dagudu yace "Allah ya taimaki Hajiya" "ina jiranka afalo" tafada ba wasa atattare da ita, da sauri ya katse wayan yay hanya flat dinta bude kofa yayi ahankali yashiga bakinshi dauke da sallama zaune yaganta kan kujera tana sanyeda wani simple gown na cotton dayakaimata har kasa irin na baccin nan pink color, kanta sanye da pink turban mai kyau idanunta sanyeda white glasses tadaura pillow kan laps dinta dai Mac book kan pillow tana aiki a system kafafuwanta sanye da indoors shoes pink masu shegen kyau kaganta she looks so adorable bazata taba yarda ta haifi 13yrs old children ba, kasama gaisheta yayi saiwani irin kallonta dayahauyi gabaki daya tatafi da imaninshi, jin shiru not the usual Murtala mai zuba yasa tajanye idanunta dagakan laptop din tadago kanta ta kalleshi hada ido sukayi dan kamashi tayi yana kallonta wani irin kunyane yakamashi saiyadan juyarda kanshi ahankali cikeda kunya kaman ta tuhumeshi yace "Hajiya wlh wlh kinyi kyau, gelashin nan yamiki kyau" yakarashe maganan yana juyarda kanshi gabaki daya, har kasan ranta taji dadin maganan shi this is abunda Baban Khalid bai taba nunamata ba, duk kyan dazatayi aduniyan nan ko kalloma bata isheshi ba, daurewa tayj bata nunamai ba saitadau wani rapa data ijiye agefen ta nayan 500 sababbi gal tajuyo tace "gashi" juyowa yayi ahankali yasake kallonta hada ido sukayi gabanshi nafaduwa sosai sake ganinta dayayi, babu gardama yakaraso yasaka hannunshi yakarbi kudin cikin muryanta dake nuna tsantsan natsuwa dakuma isa ga dadi tace "kudinka daka kashe a asibiti ne wanan" murmushi yamata sosai still yana kallonta yakasa magana, sake daukan another rapa nayan 500 tayi tamikamai kai hannu yayi zai karba yana kallon fuskanta still kaman yanda take kallonshi, mistakenly hannunshi yataba fatar nata wani irin shock sukaji dukansu atare da sauri ta sakinmai kudin ya karba sanan yadan koma baya jikinshi narawa ahankali batare data kalleshi ba tace "kai using wanan kasaima Umman ka abu" zubewa yayi awajen yace "Allah ya ampana, Allah yabiya bukatu Hajiya, Allah kuma yataimaka" "zaka iya tafiya" kaman jira yake yajuya da sauri yafice daga falon, yasauka yadauki hanyan side dinsu yana mamakin what is wrong with him idan yana tareda Hajiya.This book nakudine idan kinaso chat me up directly by clicking on this link https://wa.me/+2347012181461   Harya bude kofa yafita bin bayanshi tayida kallon sha'awa, kawai pride ne da wlh she can ask this boy nawa yakeso tabiyashi just to fuck her, yaron is super caring, and he appreciate her, yanzu dudda ta girmeshi sosai tana 36 yana 26 but still yana ganin kyanta a idanunshi kyanda haryama tafida Imaninshi, she is tired gosh! Tagaji da everything and anything, but taje therapy Dr Elizabeth tace "she should try and make things work between ita da shi, dudda tasan dazu dinan ya mugun bata haushi ne tadawo daga asibiti baima cemata sannu ba yazo waikuma yana bukatan sex, now see rashin shi, rashin kulawan shi, tsananshi datakeji yasa she's seeing the bright side of this illiterate direba, ahankali tasaukar da system dinta ta ijiye a gefenta kan kujeran, sanan tamika hannu tadauki wayarta taciro number shi datai saving da Husband tana kallo, jitake kaman inta kirashi ajinta dakomi nata yazube, daurewa tayi da kyar tai dialing number shi, kaman bazai daukaba wayan na gabda tsinkewa yadauka, akufule kaman inda yanada iko zai iya dukanta ta wayan yace "why are you calling me woman"? Arayuwanta abu nafarko data tsana shine miji yawani dinga kiran matanshi da woman, she find the word way too insultive, daurewa tayi tahadiye komi tace "I call to check up on you ne, naga 10 yayi baka dawo...b......" "akan ubanme zan dawo eh Hassana" yamata uban ihu dayasa ta matsar dawayan daga kunneta dan kaman zai ciremata dodon kunne, cikeda fushi yacigaba yace "Hassana nifa, me Alhassan Bakori ina nemanki, kibani hakkina but u were telling me all sort of nonsense you this wawiya woman, kinsan waye ni? How dare u turn me down like this eh"? Yasake dakamata tsawa kaman wata yarshi dayasa ta lumshe ido tana nishi sama sama, anya kuwa, can she do this, Dr I don't think this man can change, sake daurewa tayi tasauko da pride dinta to the lowest, ahankali tace "kayakuri! Nasan baka tafi China ba tunda nakiraka naji wayanka yashiga, kamanta dakomi just come back home let's talk properly" "you must be very very stupid Hassana!" Yazuba mata zagi da turenci dayasa tawani ware ido irin ni mutumib nan ke zaga haka, cikeda fada yace "kindauka ni Khalid ne dazakiyi manipulating like that after everything you've done to me, wlh bazan dawo gidan nanba nai yaji, harsai kin kira all your family members you told them what you've done to me, sanan su kira secretary dina suyi booking appointment na ganina sanan suzo subani hakuro suyi biko inba hakaba wlh bazan dawo gidan nanba anan hotel dinan zancigaba da, what you did was so unforgiving, ni ni Hassana, ni mijinki nine zakiyi turning down, kiki barina nasami natsuwa when u know moretban anyone u are all I have as a wife, ki aiko ayi bikona if u are really sorry" at this junction ma dariya yabata irin dariyan takaicin nan, dan murmusawa tayi kadan cikeda muryan rainin wayo dan dama ta iya muryan tace "ashe zaka shekara kasha zamanka ko ajikina" subhanallah jiyayi kaman tazubamai barkono ajiki ihu yayi yace "nikike gayawa haka"? _RANAKUN POSTING ARE SUNDAYS, TUESDAYS, FRIDAYS_ Wuraren 6 family Dr su yashigo gidan, Murtala ya shigodashi har falo sanan yafita bayan Hajiya tasauko kasa cikin shiga ta alfarma. Boysqutars dinsu yawuce yashiga yana hada kayanshi bini bini Hajiya nafadomai arai saiyay murya ahaka har aka kira magrib yawuce yatafi masallaci saida akai isha'i sanan yafito yadawo gidan yana tafiya ahankali, wayanshine tadau ringing ciro wayan yayi ganin Hajiyane yasa yakai wayan kunne dagudu yace "Allah ya taimaki Hajiya" "ina jiranka afalo" tafada ba wasa atattare da ita, da sauri ya katse wayan yay hanya flat dinta bude kofa yayi ahankali yashiga bakinshi dauke da sallama zaune yaganta kan kujera tana sanyeda wani simple gown na cotton dayakaimata har kasa irin na baccin nan pink color, kanta sanye da pink turban mai kyau idanunta sanyeda white glasses tadaura pillow kan laps dinta dai Mac book kan pillow tana aiki a system kafafuwanta sanye da indoors shoes pink masu shegen kyau kaganta she looks so adorable bazata taba yarda ta haifi 13yrs old children ba, kasama gaisheta yayi saiwani irin kallonta dayahauyi gabaki daya tatafi da imaninshi, jin shiru not the usual Murtala mai zuba yasa tajanye idanunta dagakan laptop din tadago kanta ta kalleshi hada ido sukayi dan kamashi tayi yana kallonta wani irin kunyane yakamashi saiyadan juyarda kanshi ahankali cikeda kunya kaman ta tuhumeshi yace "Hajiya wlh wlh kinyi kyau, gelashin nan yamiki kyau" yakarashe maganan yana juyarda kanshi gabaki daya, har kasan ranta taji dadin maganan shi this is abunda Baban Khalid bai taba nunamata ba, duk kyan dazatayi aduniyan nan ko kalloma bata isheshi ba, daurewa tayj bata nunamai ba saitadau wani rapa data ijiye agefen ta nayan 500 sababbi gal tajuyo tace "gashi" juyowa yayi ahankali yasake kallonta hada ido sukayi gabanshi nafaduwa sosai sake ganinta dayayi, babu gardama yakaraso yasaka hannunshi yakarbi kudin cikin muryanta dake nuna tsantsan natsuwa dakuma isa ga dadi tace "kudinka daka kashe a asibiti ne wanan" murmushi yamata sosai still yana kallonta yakasa magana, sake daukan another rapa nayan 500 tayi tamikamai kai hannu yayi zai karba yana kallon fuskanta still kaman yanda take kallonshi, mistakenly hannunshi yataba fatar nata wani irin shock sukaji dukansu atare da sauri ta sakinmai kudin ya karba sanan yadan koma baya jikinshi narawa ahankali batare data kalleshi ba tace "kai using wanan kasaima Umman ka abu" zubewa yayi awajen yace "Allah ya ampana, Allah yabiya bukatu Hajiya, Allah kuma yataimaka" "zaka iya tafiya" kaman jira yake yajuya da sauri yafice daga falon, yasauka yadauki hanyan side dinsu yana mamakin what is wrong with him idan yana tareda Hajiya.WANT BUSINESS ADVERT OR PROMOTION AWANAN NOVEL DIN CHAT ME UP DIRECTLY BY CLICKING ON THIS LINK https://wa.me/+2347012181461 Cikin fushi tace "akwai wani a inda kakene banda kai"? Cikeda fushi yace "are you talking to me Hassana, me me your husband dani kike"? Cikeda takaicinshi tace "please i want to sleep if you don't mind zan katse wayan" "you dare not cut that call Hassana!" Yafadi sounding so serious and so pissed off hakan yasa bata katse wayanba ta tsaya, cikeda zuciya yace "ni kikema rashin kunya, talking to me kaman am your mate, Hassana ni kika raina, wlh to bari kiji saina kara aure" "is that all you got?" Ta tambayay tace "bismillah ai kanada gidaje dayawa ka auro dubu ma inkaka dama, indai wanan bakin halin nakane daka koyo to wlh babu macen dazata iya zama dakai, baka damu dakowaba sai kanka selfish man" kaman zai fasa wayan tsabagen ihu yace "I will deal with you wlh, mad woman kawai, nabarmiki gidan, kuma I will tell all your friends na Matan ASOKORO nan how stupid and disrespectful u are towards me your husband, I will tell them namiki yaji sai kinyo bikona, I will shame u in this world, daikin kasa fita waje, zakiga abinda zan miki, that girman kai da pride din dakikeji I will so shatter it en, dani kike I will break your ego u will see" yana fadin haka ya katse wayan yarda wayan itama tayi ta jinginar da kanta jikin kujera tareda lumshe ido, it seems kaman mijinta shine her biggest enemy in this world, wai what is missing in aurenta ne? She is doing her best, Baban Khalid yasha mata abubuwa tana dannewa bata nunamai, just today data hanashi kanta shine zai yadata sabida yasan abinda tafi tsana kenan, what is all this Ya Ilahi, she hates this man and yanzu ma he's making her to hate him more, all this therapy data fara sabida shi is all bull shit._RANAKUN POSTING ARE SUNDAYS, TUESDAYS, FRIDAYS_ Wuraren 6 family Dr su yashigo gidan, Murtala ya shigodashi har falo sanan yafita bayan Hajiya tasauko kasa cikin shiga ta alfarma. Boysqutars dinsu yawuce yashiga yana hada kayanshi bini bini Hajiya nafadomai arai saiyay murya ahaka har aka kira magrib yawuce yatafi masallaci saida akai isha'i sanan yafito yadawo gidan yana tafiya ahankali, wayanshine tadau ringing ciro wayan yayi ganin Hajiyane yasa yakai wayan kunne dagudu yace "Allah ya taimaki Hajiya" "ina jiranka afalo" tafada ba wasa atattare da ita, da sauri ya katse wayan yay hanya flat dinta bude kofa yayi ahankali yashiga bakinshi dauke da sallama zaune yaganta kan kujera tana sanyeda wani simple gown na cotton dayakaimata har kasa irin na baccin nan pink color, kanta sanye da pink turban mai kyau idanunta sanyeda white glasses tadaura pillow kan laps dinta dai Mac book kan pillow tana aiki a system kafafuwanta sanye da indoors shoes pink masu shegen kyau kaganta she looks so adorable bazata taba yarda ta haifi 13yrs old children ba, kasama gaisheta yayi saiwani irin kallonta dayahauyi gabaki daya tatafi da imaninshi, jin shiru not the usual Murtala mai zuba yasa tajanye idanunta dagakan laptop din tadago kanta ta kalleshi hada ido sukayi dan kamashi tayi yana kallonta wani irin kunyane yakamashi saiyadan juyarda kanshi ahankali cikeda kunya kaman ta tuhumeshi yace "Hajiya wlh wlh kinyi kyau, gelashin nan yamiki kyau" yakarashe maganan yana juyarda kanshi gabaki daya, har kasan ranta taji dadin maganan shi this is abunda Baban Khalid bai taba nunamata ba, duk kyan dazatayi aduniyan nan ko kalloma bata isheshi ba, daurewa tayj bata nunamai ba saitadau wani rapa data ijiye agefen ta nayan 500 sababbi gal tajuyo tace "gashi" juyowa yayi ahankali yasake kallonta hada ido sukayi gabanshi nafaduwa sosai sake ganinta dayayi, babu gardama yakaraso yasaka hannunshi yakarbi kudin cikin muryanta dake nuna tsantsan natsuwa dakuma isa ga dadi tace "kudinka daka kashe a asibiti ne wanan" murmushi yamata sosai still yana kallonta yakasa magana, sake daukan another rapa nayan 500 tayi tamikamai kai hannu yayi zai karba yana kallon fuskanta still kaman yanda take kallonshi, mistakenly hannunshi yataba fatar nata wani irin shock sukaji dukansu atare da sauri ta sakinmai kudin ya karba sanan yadan koma baya jikinshi narawa ahankali batare data kalleshi ba tace "kai using wanan kasaima Umman ka abu" zubewa yayi awajen yace "Allah ya ampana, Allah yabiya bukatu Hajiya, Allah kuma yataimaka" "zaka iya tafiya" kaman jira yake yajuya da sauri yafice daga falon, yasauka yadauki hanyan side dinsu yana mamakin what is wrong with him idan yana tareda Hajiya.This book nakudine idan kinaso chat me up directly by clicking on this link https://wa.me/+2347012181461   Harya bude kofa yafita bin bayanshi tayida kallon sha'awa, kawai pride ne da wlh she can ask this boy nawa yakeso tabiyashi just to fuck her, yaron is super caring, and he appreciate her, yanzu dudda ta girmeshi sosai tana 36 yana 26 but still yana ganin kyanta a idanunshi kyanda haryama tafida Imaninshi, she is tired gosh! Tagaji da everything and anything, but taje therapy Dr Elizabeth tace "she should try and make things work between ita da shi, dudda tasan dazu dinan ya mugun bata haushi ne tadawo daga asibiti baima cemata sannu ba yazo waikuma yana bukatan sex, now see rashin shi, rashin kulawan shi, tsananshi datakeji yasa she's seeing the bright side of this illiterate direba, ahankali tasaukar da system dinta ta ijiye a gefenta kan kujeran, sanan tamika hannu tadauki wayarta taciro number shi datai saving da Husband tana kallo, jitake kaman inta kirashi ajinta dakomi nata yazube, daurewa tayi da kyar tai dialing number shi, kaman bazai daukaba wayan na gabda tsinkewa yadauka, akufule kaman inda yanada iko zai iya dukanta ta wayan yace "why are you calling me woman"? Arayuwanta abu nafarko data tsana shine miji yawani dinga kiran matanshi da woman, she find the word way too insultive, daurewa tayi tahadiye komi tace "I call to check up on you ne, naga 10 yayi baka dawo...b......" "akan ubanme zan dawo eh Hassana" yamata uban ihu dayasa ta matsar dawayan daga kunneta dan kaman zai ciremata dodon kunne, cikeda fushi yacigaba yace "Hassana nifa, me Alhassan Bakori ina nemanki, kibani hakkina but u were telling me all sort of nonsense you this wawiya woman, kinsan waye ni? How dare u turn me down like this eh"? Yasake dakamata tsawa kaman wata yarshi dayasa ta lumshe ido tana nishi sama sama, anya kuwa, can she do this, Dr I don't think this man can change, sake daurewa tayi tasauko da pride dinta to the lowest, ahankali tace "kayakuri! Nasan baka tafi China ba tunda nakiraka naji wayanka yashiga, kamanta dakomi just come back home let's talk properly" "you must be very very stupid Hassana!" Yazuba mata zagi da turenci dayasa tawani ware ido irin ni mutumib nan ke zaga haka, cikeda fada yace "kindauka ni Khalid ne dazakiyi manipulating like that after everything you've done to me, wlh bazan dawo gidan nanba nai yaji, harsai kin kira all your family members you told them what you've done to me, sanan su kira secretary dina suyi booking appointment na ganina sanan suzo subani hakuro suyi biko inba hakaba wlh bazan dawo gidan nanba anan hotel dinan zancigaba da, what you did was so unforgiving, ni ni Hassana, ni mijinki nine zakiyi turning down, kiki barina nasami natsuwa when u know moretban anyone u are all I have as a wife, ki aiko ayi bikona if u are really sorry" at this junction ma dariya yabata irin dariyan takaicin nan, dan murmusawa tayi kadan cikeda muryan rainin wayo dan dama ta iya muryan tace "ashe zaka shekara kasha zamanka ko ajikina" subhanallah jiyayi kaman tazubamai barkono ajiki ihu yayi yace "nikike gayawa haka"?WANT BUSINESS ADVERT OR PROMOTION AWANAN NOVEL DIN CHAT ME UP DIRECTLY BY CLICKING ON THIS LINK https://wa.me/+2347012181461 Cikin fushi tace "akwai wani a inda kakene banda kai"? Cikeda fushi yace "are you talking to me Hassana, me me your husband dani kike"? Cikeda takaicinshi tace "please i want to sleep if you don't mind zan katse wayan" "you dare not cut that call Hassana!" Yafadi sounding so serious and so pissed off hakan yasa bata katse wayanba ta tsaya, cikeda zuciya yace "ni kikema rashin kunya, talking to me kaman am your mate, Hassana ni kika raina, wlh to bari kiji saina kara aure" "is that all you got?" Ta tambayay tace "bismillah ai kanada gidaje dayawa ka auro dubu ma inkaka dama, indai wanan bakin halin nakane daka koyo to wlh babu macen dazata iya zama dakai, baka damu dakowaba sai kanka selfish man" kaman zai fasa wayan tsabagen ihu yace "I will deal with you wlh, mad woman kawai, nabarmiki gidan, kuma I will tell all your friends na Matan ASOKORO nan how stupid and disrespectful u are towards me your husband, I will tell them namiki yaji sai kinyo bikona, I will shame u in this world, daikin kasa fita waje, zakiga abinda zan miki, that girman kai da pride din dakikeji I will so shatter it en, dani kike I will break your ego u will see" yana fadin haka ya katse wayan yarda wayan itama tayi ta jinginar da kanta jikin kujera tareda lumshe ido, it seems kaman mijinta shine her biggest enemy in this world, wai what is missing in aurenta ne? She is doing her best, Baban Khalid yasha mata abubuwa tana dannewa bata nunamai, just today data hanashi kanta shine zai yadata sabida yasan abinda tafi tsana kenan, what is all this Ya Ilahi, she hates this man and yanzu ma he's making her to hate him more, all this therapy data fara sabida shi is all bull shit. _MATAN ASOKORO_ WANT BUSINESS ADVERT OR PROMOTION AWANAN NOVEL DIN CHAT ME UP DIRECTLY BY CLICKING ON THIS LINK https://wa.me/+2347012181461 Cikin fushi tace "akwai wani a inda kakene banda kai"? Cikeda fushi yace "are you talking to me Hassana, me me your husband dani kike"? Cikeda takaicinshi tace "please i want to sleep if you don't mind zan katse wayan" "you dare not cut that call Hassana!" Yafadi sounding so serious and so pissed off hakan yasa bata katse wayanba ta tsaya, cikeda zuciya yace "ni kikema rashin kunya, talking to me kaman am your mate, Hassana ni kika raina, wlh to bari kiji saina kara aure" "is that all you got?" Ta tambayay tace "bismillah ai kanada gidaje dayawa ka auro dubu ma inkaka dama, indai wanan bakin halin nakane daka koyo to wlh babu macen dazata iya zama dakai, baka damu dakowaba sai kanka selfish man" kaman zai fasa wayan tsabagen ihu yace "I will deal with you wlh, mad woman kawai, nabarmiki gidan, kuma I will tell all your friends na Matan ASOKORO nan how stupid and disrespectful u are towards me your husband, I will tell them namiki yaji sai kinyo bikona, I will shame u in this world, daikin kasa fita waje, zakiga abinda zan miki, that girman kai da pride din dakikeji I will so shatter it en, dani kike I will break your ego u will see" yana fadin haka ya katse wayan yarda wayan itama tayi ta jinginar da kanta jikin kujera tareda lumshe ido, it seems kaman mijinta shine her biggest enemy in this world, wai what is missing in aurenta ne? She is doing her best, Baban Khalid yasha mata abubuwa tana dannewa bata nunamai, just today data hanashi kanta shine zai yadata sabida yasan abinda tafi tsana kenan, what is all this Ya Ilahi, she hates this man and yanzu ma he's making her to hate him more, all this therapy data fara sabida shi is all bull shit. ✍M SHAKUR EPISODE 5️⃣     some bandir na yan dubu dubu tell her u don't like seeing her like this gawanan taje tabata kanta dasu kai bari kaji har kukan dadi saitamaka poor thing" wani irin kashewa sukayi suna dariya kaman mahaukata, da kyar suka tsagaita dariyan Attajiri tace "itakuma danyar kabar komi a hannuna, akwai wasu yan shuwa dana sani talakawan bala'i suna saida zuma abakin titi da yar da kanwar kamar mamansu ce ba lafiya, to da kanwar zakai wuf" suka sake kashewa suna dariya, yace "meanwhile kacigaba da zama anan wanan karka koma but ka aikama da Hassana sako, anan 7 nema ko 8bedroom flat mansion dinan datake ciki data cika ko'ina dakaya tom ta tattare, bedrooms bedrooms dinan nasama guda 5, damakai daya nakane aciki ko" dasauri ya gyadamai kai yace "tom daya zai zama nata wanda take ciki, daya kuma na amarya, daya na bazawara, idan yaso insu Khalid suka dawo su koma dakunan kasa, wanan fa dukdan ka gumamata ne takoka, falon kasa kuma yadawo falon kowa, kitchen ma nakowa idanun Hassana will read koda batadamu da aurendaka karaba, but sharing wanan palace dinan da mata ba dayaba har uku will leave her shattered" sake kwashewa da dariya sukayi Baban Khalid harda faduwa akasa yace "Hassana zakisan kinyi kuskure wlh akaina" dasauri Attajiri yace "barta batasan ba'a mana hakaba" Baban Khalid yace "kuma bawai narasa wajen sasu bane ko mata goma zan aura inada separate big big house dazan sakasu wlh" dasauri Attajiri yace "nida nasan komi, ko agidan nan naka ga flats nan barkatai u can put them, yanzu dai zaka kira kasake all the furnitures na gidan na falo dana sama wanan dakunan dazaka sakasu acire komi azuba sababbin kaya babu abinda yarage saicin mata kana zuba ihu kana kuntata mata" wani mugun dariyan da Baban Khalid yakeyi zaka dauka yazare ne nanko duk hango kalan tsiyan dazaiyi yakeyi, tashi yayi yace "kaga tashi katafi kaje gidansu shuwan, nikuma bari nawuce office danna hadu da Mrs Saudat kafin tagama gyare gyaren office tatafi, kokuma ma bari nakira secretary dina nacemai ta tsaya tajirani nazo office inada magana da ita" "hakanma yayi nibari nawuce to" Attajiri yafadi yana tashi dagakan kujeran yana ggyara riga, sanan sukai sallama yawuce yatafi.Bude kofan falo tayi around 1 na daren nan tafara tafiya babu takalmi tai hanyar boysqutars, tana zuwa ahankali tabude kofa, bama ta ganin komi afalon kawai tai bedroom dinsu dakin warin maza, hannu tasa takunna wutar dakin, kwance taganshi kan katifa yana sharara bacci harda minshari dagashi sai gajeren wando irin na yan kwallo dinan, bin gajeren wandon tayi idanunta suka sauka akan kan dick dinshi baki kirin daya leko ta kafan boxer din wajen cinyanshi, hannunta takai tashare idanunta tass ganin what dan kauyen Murtalan nan has, tagadai yes ba mafarkine ba kan dick take hangowa haka hakan yasa tasake fita daga hayyacinta, hannu tamika takashe wutan dakin, sanan tacire doguwan rigan baccin dake jikinta da pant tayar awajen kafin dasauri tahaukan gadon kwanciya tayi tashige jikinshi dataji yay dumi takai hannunta saman wandonshi babu wani tsoro tasaka hannunta taciro dick din duka tarike gam sanan tashiga murzawa da sauri da sauri tana nishi tanakai boobs dinta daya bakinshi, kaman amafarki yaji ana tabashi dayakejin mugun dadin hakan danhar gabanshi yasoma mikewa saikuma ahankali yabude idanunshi tass, ganin mace kuma mutum kusadashi tana shafamai dick ga nono kan bakinshi yasa yawanija baya yace "auzubillahi, ture akamin ne" cikin wani irin murya tabishi saikawai tahau kan jikinshi ta kwanta cikin muryanta dabaya fita sosai tace "Hajiyanka ce Murtala, sonake kabiyamin bukata, inaso kacini cimai kyau zan biyaka gobe dasafe" bakinshi har rawa yake yace "Ha......Haj...." bata bari yakarasa magana ba tachakpe bakinshi tashiga kissing nashi tana murza dick dinshi da hannu dayan hannunta kuma nakan nipple dinshi nanda nan yaji yana neman zaucewa shiko mace ba baijin yataba rikewaba bandadai ranan daya rike Hajiya gabaki daya wani irin tashi gabanshi yayi yamike kyam kuma sambal a hannunta, sakin nipple dinshi tayi takama hannunshi takai kan manyan boobs dinta tace "matsemin su Murtala da kyau......."SHAKUR EPISODE 6️⃣   "Hajiya!" Taji muryan Murtala ya rangadamata kira, wlh har ranta taji dadin hakan dabama tasan lokacin data lumshe idoba sanan tasake budewa jin yamata kira nabiyu. "Hajiya nadawo" batasan meya shigetaba samin kanta tayi datashi dagakan dadduma da saurinta bamata tsaya saka takalmi ba tabude kofanta tafito sanan tasauko kasa ahankali atsakiyan falon taganshi yana rikeda jakanshi yanamata wanan cute smile din nashi dayasaba yace "wlh Hajiya nayi kewanki sosai, mota yalalace ahanya saisa nadade da tuntuni nadawo, Hajiya inasonki sosai wlh" yasake fadi ranshi daya yana murmushi sosai kaman wamda yay shekara baigantaba, kasa hadiye murmushinta tayi tace "sannu da zuwa Murtala, yakabaro su Umma" dasauri yace "Umma tace nagaisheki sosai, tamabani sako nakawo miki bari na shigodashi" yana maganan yasaki jakanshi yajuyada sauri yafita wata katuwar buhune da goruba, aduwa, magarya dawace tsiyace aciki dayasa tai murmushi ganin ya ijiye tace "dukni kadai" yanda tayi yasa yasakeyin murmushi yace "eh ke kadai Hajiya tace navamawa" "to Allah amfana nagode" dakin yabida kallo yace "gyara akeyi" gyadamai kai tayi tace "eh" kallonta yayi yace "intafi dakina"? Yanda yay maganan yana kallonta yasa tama kasa bashi amsa tai kuri tana kallonshi kaman mai kallon wani abu, yanda take kallonshi haka shima ya tsaya kallonta yana ganin wani kyau datake dashi, shi kibanta kara burgeshi yake. Kallonshi take babu tunanin dabaya mata yawo aranta yanzu wanan dan yaron inda ace zata iya tuni zatai amfani dashi kuma zai mata yanda takeso sabida yanda yake sonta dinan, saikuma kawai yaga tajuya da sauri tai sama, harya bude baki zai kirata saikuma yay shiru yadan dade tsaye awajen saiya juya yafice yatafi side dinshi. _MATAN ASOKORO_   ✍M Jakanshi ya ijiye sanan yacire kayan jikinshi, dudda yanda baiwaniso yay wanka amman sabida yanda jikinshi ke danko yasa yashga dan bayinsu na boys quaters din yayo wanka da ruwan sanyi sanan yafito, yar fale falen katifansu guda biyu nashi da direban Alhaji ya kakkabe sanan yahadesu ya shimfida yar zanin gadonsu sanan yajuya yakashe wuta, kafin yazo ya kwanta ahankali yana tunane tunane wanda duka na Hajiya ne, tun ranan da aka kawoshi gidan nan Alhaji yakaishi falo wurin Hajiya cewa shine direban ta shi hakanan kawai matar tamai, fadanta, masifan ta, jan ajinta oho shidai ko ubanme zatayi ko zatamai burgeshi take, baisan ko sabida baitaba ganin Babban mace yar gayu irinta bane, baisani ba Amman Hajiya na burgeshi saisa koda yaushe cikin kallonta yake, shi kadai yadinga tunane tunane har bacci yay awon gabadashi awurin.   Har karfe shabiyu zaune take adakinta tai shiru babu komi nadubiyan nan dake mata dadi. Kasa daurewa tayi tajuya takalli wayarta dake kan gadon kaman batason dauka saita mika hannunta tadauka ahankali tabude taciro number Baban Khalid kaman bazatai wani abuba saikuma kawai takira, wayan na gabda tsinkewa yadauka yace "lafiya"? Ahankali tace "Baban Khalid wai dagaske kake bazaka dawo gidaba kan garin nan yau rana na uku kenan bansaka a idoba" cikeda gadara da isa yace "to sai akai yaya? Idan kinason dawowata kihada team din dazasuzo bikona" shiru tayi abu natasomata awuya, amman saita daure zubarda duk wani girmankai tayi ta daure iya daurewa tace "koma menamaka kayakuri kadawo gida, nagaji da zaman gidan nan nikadai kaman mayya, kayakuri kaji" wani fashewa da dariya yayi yace "wanan hakuri ne? Yarinya baki tubaba, Like I said idan kinshirya kituro team biko kibiyosu sanan u come and kneeldown and then beg me nayakuri nayafemiki wata kila na sauko nahakura inba hakaba wlh kidinga zama ke kadai kenan kuma nemanki bazan sakeyiba harsai kin durkusa kin roki gafaran wulakanci dacin mutuncin dakikamin, inba hakaba ai kemadai mutumce kinada jini ajiki sanan dole kiji sha'awa to wlh ban baki burata bazan kara saduwa dakeba saikin durkusa kin nemeni gafara inba hakaba kisan yanda zakiyi da kanki, saida safe dama kwanciya zanyi kika kirani nagama zoom meeting na masumin supplying kaya daga Vietnam" katse wayanshi yayi tareda nata tsaki, ahankali hawaye yasake zubomata ta sharesu da sauri sanan tafada gado takife kanta, saikuma ahankali tadauki pilow ta tura akasanta kotadanji sanyi sanyin yanda takejin kanta, amman ina! Yanzu mezatama kanta, tashi tayi tashiga bayi tayo tsarki da ruwan zafi amman kaman karama kanta tayi sha'awan sanan tafito tama kwanta akasa wanan karan tana lumshe ido kawai hoton Murtala yafado mata, tota kirashi ne? Wayarta tamika hannu tadauka zata kirashi saikuma takasa ta ijiye bazata iyaba, saikuma chan kaman an dagata ta tashi ko dankwali bata sakaba idanunta sun kankance sosai tafito bamata tsaya saka takalmi ba kaman wacce bata hayyacinta.Tana zaune a falo itada yar aikinta dake matsa mata kafa akai sallama yar aikin ta tura ta amsa saigata tashigo tace "wai Alhaji yaturosu" shigodasu tasa akayi, gaidata sukayi cikeda respect sanan sukace "Hajiya Alhaji ya aikomu, yace mu kwashe duka kayan falon nan, da kayan kitchen dakuma kayan dakunan sama banda naki mukai chan store, wai za'a zuba komi sababbi ne" shiru tayi kaman mai tunani saikuma tace "okay" tashi tayi takalli yar aikinta tace "zaki iya wucewa gida yanzu Bibalo tunda kinga aiki za'a min" "tom Hajiya" tai maganan tanayin hanyan waje itakuma tawuce sama tashige dakinta tareda maida kofa tarufe, daman dakunan saman bawani kayan kirki bane aciki dudda kowanne da hadaddun gado aciki ga dakunan fadi da girma sosai, tanaji anata kwashe kwashe ana fitarda kaya hakanan taji tana kewan Murtala dayananan dayanzu tasa yafita da ita dan kara ya isheta, haka sukai aikin nan har yamma basu gamaba saidai suka hakura gobe zasu dawo sukarasa, koda ta sauko kasa saitaga gidan kaman banata ba, komawa kawai tayi sama abinta.   Washegari ne suka karasa fitarda komi sanan aka fara wani irin mahaukacin Fendi, ko'ina na gidan harda kitchen din, dansai fentin yabushe tass sanan za'a shigoda sababbin kaya, kawai she's feeling way to lonely inama ace ranan visiting yaranta ne yau dataje school dinsu wlh kota gansu taji dadi, tama rasakan gane gyaran me Baban Khalid yakeyi duddda tasan yanada yawan gyara gida, but tasan at this point dasukai fada bazai gyara gidaba to kodai that's his own way of saying sorry ne, kwanciya tayi kan gado sanan takalli agogo taga 6 but haryanzu Murtala bai dawoba kodai bazai dawo yaubane amman kuma baya ketare dokanta, gashi har masu aiki sun gama sun bude kofofi da windunan falo sun tafi sabida fentin yasha iska, tashi tayi tawuce bayi tadauro alwala tazo tai salla tazauna tana lazimi tai kewan gidansu tanaso taje gidansu taga Babanta, kuka takeji amman tahana kanta tadaure kawai tazauna tai shiru tana wajen aka kira isha'i ta tashi tayi tai shafa'i da wuturi sanan tasake zama tai shiru gabaki daya ranta bayamata dadi.Wuraren 12 yakai office direbanshi yafito yabudemai baya yafito yana sanye cikin suit yayi kyau, security guard nahangoshi yabudemai kofa ya shiga, anan reception yaga wata mata zaune da Hijabinta ash color ajikinta dayadan kunne takusada gefen wuya, black beauty ce itama kyakkyawa abinta kana ganinta kasan ba yarinya bace zata iyayin 39 kokuma 40yrs haka, saidai batada jiki kaman Hassana, ita siririya ce, tana ganinshi harwani ijiyan zuciya tasauke tana addu'a Allah yasa ba laifi tayiba wanan da sakatare yace "Oga yakira yace tajirashi karta tafi, batare daya kalleta ba ko amsa gaisuwansu yawuce sama sanan yabude katafaren office dinshi dayake a gyare yashiga tareda zama a chair, saida yabata kusan 15min dudda babu abinda yake sanan yadauki wayar office yakira sakatare yace "aturomai ita" ijiye wayan sakatare yayi ya kalleta yace "Sir is ready to see you now" gyadamaikai tayi ahankali sanan ta tashi itama tai sama saida tai knocking kofar aka bata izinin shigowa sanan ta shiga ahankali tareda kofa yana zaune yakafeta da idanu, sanan yanuna mata daya daga cikin kujerun dake gaban desk dinshi yace "sit" karasowa tayi tazauna gabanta nafaduwa tama kasa magana batasan anything dazaisa tarasa this her work dan ana biyanta da kyau dashi take saima yaranta da mahaifiyarta yan abubuwan daba'a rasaba, anatse cikeda tsoro tace "yallabai gani nan Allah dai yasa bawani laifin nayiba, ance kana nemana duk tsoro yakamani" murmushi yasakin mata ahankali saikuma yagyara zama yadaura hannunshi kan table yace "niba yaro bane, sanan kema ba yarinya bace, so I would like to skip all the talk and cut to the chase" dasauri ta gyadamaikai har lokacin gabanta nafaduwa, sanan anatse yace "aurenki nakeso nayi Saudat, ni bana harkan yara ko harkan iskanci, kinmin inaso na aureki na killaceki agidana a inuwata, all abinda kawai nake bukata itace yardanki da amincewanki, banson kiyi tunanin kaza kaza kaza ko abubuwan dazaki kawo gidana kokuma wani abu, nariga nasan kewacece, nasan karfinki saisa zandaukemiki duk wani nauyin kayan daki dawace tsiyace ke kawai kadai zaki shigo gidana, sanan bansan wanan hayaniyan bikin da sauransu niba yaro bane, sonake dazaran kin yarda kawai a daura aure dayar walima nazo nadaukeki nakaiki dakinki" yanakaiwa nan yay shiru yana kallonta kaman yanda take kallonshi in a total shock, saikuma tadaura hannunta akan kirji tace "Yallabai ni? Kodai mistake kayi? Ninefa Mrs Saudat mai shara da wanke bayi da mopping a kampaninka" gyadamata kai yayi yace "kwarai kuwa nasan kece, kuma kedin yanzu nake kokarin namaidake matar mai kampanin gabaki daya" yay maganan yana kallonta yana murmushi yace "by the way bazan takuraki ba, zan baki dagayau zuwa gobe dan banison bata lokaci kiyi tunani, idan kin yarda ayi, gobe war haka ina jiran amsa" gyadamai kai tayi tama kasa magana still, saikuma ahankali tatashi zata juya yace "tsaya" juyowa tayi takalleshi wasu code ya danna a drawer table dinshi sanan yajawo table din kudine burjik aciki, rappa na dubu dubu yadauko guda uku that's 300k yamika mata yace "take this, use it ki bata kanki dashi, ina jiranki gobe" kallon kudin tayi tana zaro ido daikuma ta kalleshi, babu wasa yace "karba mana Saudat nakine" mika hannu tayi ta karba zata zube tamai godiya yace "banson godiya wuce kitafi" wucewa tayi tafita daga office din rikeda kudi, tana fita ta tsaya taciro handbag dinta tazuba kudin aciki sanan tasauka kasa tafita tana wani irin farinciki wayyo dadi. Tana fita yakira number Attajiri yace "nayi yanda muka tsara" kwashwwa da dariya Attajiri yayi yace "she is coming back with a yes na me tell u kawai kaman kayi aure kagama, ga wanan gidan, uwarsu da su kansu yaran sun rude, Maman harda kukan murna, nace musu gobe zamuzo tare, sati biyu mukeso asa sunce sun yarda, yanzu kira masu furnitures azuba kaya afalo, kasake komi sabo sabida kar hassana tabaka problem kayan falon dana kitchen duk akai store kazuba sabo komi yazama mallakinka kayanta atattare matasu a store" cikeda farinciki yace "angama abokina" . *************[9/5, 10:14 PM] +234 703 974 7464: _MATAN ASOKORO_   ✍M Jakanshi ya ijiye sanan yacire kayan jikinshi, dudda yanda baiwaniso yay wanka amman sabida yanda jikinshi ke danko yasa yashga dan bayinsu na boys quaters din yayo wanka da ruwan sanyi sanan yafito, yar fale falen katifansu guda biyu nashi da direban Alhaji ya kakkabe sanan yahadesu ya shimfida yar zanin gadonsu sanan yajuya yakashe wuta, kafin yazo ya kwanta ahankali yana tunane tunane wanda duka na Hajiya ne, tun ranan da aka kawoshi gidan nan Alhaji yakaishi falo wurin Hajiya cewa shine direban ta shi hakanan kawai matar tamai, fadanta, masifan ta, jan ajinta oho shidai ko ubanme zatayi ko zatamai burgeshi take, baisan ko sabida baitaba ganin Babban mace yar gayu irinta bane, baisani ba Amman Hajiya na burgeshi saisa koda yaushe cikin kallonta yake, shi kadai yadinga tunane tunane har bacci yay awon gabadashi awurin.   Har karfe shabiyu zaune take adakinta tai shiru babu komi nadubiyan nan dake mata dadi. Kasa daurewa tayi tajuya takalli wayarta dake kan gadon kaman batason dauka saita mika hannunta tadauka ahankali tabude taciro number Baban Khalid kaman bazatai wani abuba saikuma kawai takira, wayan na gabda tsinkewa yadauka yace "lafiya"? Ahankali tace "Baban Khalid wai dagaske kake bazaka dawo gidaba kan garin nan yau rana na uku kenan bansaka a idoba" cikeda gadara da isa yace "to sai akai yaya? Idan kinason dawowata kihada team din dazasuzo bikona" shiru tayi abu natasomata awuya, amman saita daure zubarda duk wani girmankai tayi ta daure iya daurewa tace "koma menamaka kayakuri kadawo gida, nagaji da zaman gidan nan nikadai kaman mayya, kayakuri kaji" wani fashewa da dariya yayi yace "wanan hakuri ne? Yarinya baki tubaba, Like I said idan kinshirya kituro team biko kibiyosu sanan u come and kneeldown and then beg me nayakuri nayafemiki wata kila na sauko nahakura inba hakaba wlh kidinga zama ke kadai kenan kuma nemanki bazan sakeyiba harsai kin durkusa kin roki gafaran wulakanci dacin mutuncin dakikamin, inba hakaba ai kemadai mutumce kinada jini ajiki sanan dole kiji sha'awa to wlh ban baki burata bazan kara saduwa dakeba saikin durkusa kin nemeni gafara inba hakaba kisan yanda zakiyi da kanki, saida safe dama kwanciya zanyi kika kirani nagama zoom meeting na masumin supplying kaya daga Vietnam" katse wayanshi yayi tareda nata tsaki, ahankali hawaye yasake zubomata ta sharesu da sauri sanan tafada gado takife kanta, saikuma ahankali tadauki pilow ta tura akasanta kotadanji sanyi sanyin yanda takejin kanta, amman ina! Yanzu mezatama kanta, tashi tayi tashiga bayi tayo tsarki da ruwan zafi amman kaman karama kanta tayi sha'awan sanan tafito tama kwanta akasa wanan karan tana lumshe ido kawai hoton Murtala yafado mata, tota kirashi ne? Wayarta tamika hannu tadauka zata kirashi saikuma takasa ta ijiye bazata iyaba, saikuma chan kaman an dagata ta tashi ko dankwali bata sakaba idanunta sun kankance sosai tafito bamata tsaya saka takalmi ba kaman wacce bata hayyacinta. [9/5, 10:14 PM] +234 703 974 7464: _DUK WACCE TAKARANTA THIS BOOK BATARE DATA BIYABA BAN YAFEBA_ 07012181461 IS MY NUMBER CHAT ME UP DIRECTLY. ✍M SHAKUR Yautunsafe ya shiryo kayanshi tsaf yafito yayi wanka yasa wata shadda blue datamai kyau sai kallon flat din Hajiya yake yasan idan yakirata yanzu bata tashiba baikuma son yatadata hakanan yabude kofa rikeda kayanshi yawuce yatafi saikuma yanaji kaman karya tafi yabar Hajiya ita kadai agidan dudda yasan yanzu dagari yawayen nan nan badajimawaba yan aiki zasu cika gidan da kyar ya lallashi kanshi yawuce yatafi.       Zaune yake a hotel din wuraren 10 na safe yana sanye da bathrobe yadauki system yana aiki as usual kana ganin dakin hotel din kasan bakaramin daki bane dan baida banbanci dagida har cikin yanada shi dan presidential suit yakarba, knocking dayaji anyi yamasan waye dansunyi magana yace "common in Attajiri" tunawa yayi kofan bazai budeba yasa ya ijiye system din yatashi yay kofan yabude wani budewa wani babban mutum ne dazasuyi mate saidai shi yafishi kiba gakuma katon pot belly, yana sanye dawata mahaukaciyar shadda yaci babban riga, hannunshi kulle da Rolex gakuma takalmin kafanshi na Luciano, shaking hannu sukayi Baban Khalid yace "kai namijin duniya, kai namijin duniya, Attajiri ko Attarudu" wani irin dariyan manya mutumin yayi kikikiki yace "kowanne daga cikinsu is fine, muje daga ciki kagani Gwamnati" shiga sukayi dakin Baban Khalid nagaba Attajiri nabinshi abaya yana binshi da kallo harya zauna saikuma shi ya tsaya yace "yanaganka awani bubbushe ne iyye? Jibi fatarka bata kyalli bata mai mai saikace talaka, kai meke damunka hakane? Masu kudi irinka idan kaga fatarsu zaka dauka madara ce tsabagen kyau daban sha'awa" tabe baki Baban Khalid yayi yace "uhmm, kadai kawai zauna" couch din dake facing gadon yazauna yana facing nashi cikeda rashin jin dadi yace "ince badai Hassana bane"? [9/5, 10:14 PM] +234 703 974 7464: Cikeda takaici yace "towayene ma inba itaba Attajiri" cikeda masifa Attajiri yace "bakaine ka tsaya kaman wani baho ba duk lokacin da matanka taga dama tai fitsari acikin ka sanan kazubar, kanada irin wanan kudin kana sauraron iskancin mace, tuni zan karo mata uku duka alokaci dayama idan tana bala'inta ni inachan ina morewa" cikeda takaici yace "Attajiri kaima kasan bana sha'awan mata biyu tun muna yara kasan wanan bangaren nawa, kai kafi kowa sanin wahalan danasha a hannun kishiyan Mamata, I can't imagine any woman on this planet ta wulakanta min yarana yan biyu na koma tamusu ihu" dasauri Attajiri yace "tokai gwamnati banda abunka wace mace ta isa tamaka haka, ai duk shegiyar daka cire daga kangin wahalan gidan ubanta ka kawota gidanka ta tabamaka yara danna mata saki zakayi washe gari kaje ka auro wata, ga matanan kaman leda duk ina ka danna kafa zaka gansu pacha pacha, indai da kudinka babu macen data isa ko kallon banza tama yaranka dane ake wanan wlh Gwamnati, kai banda abinka dama ina zamanka da Hassana zaiyi dadi? Kanada kudi ubantama nada kudi, ai yanda kakeji da kanka haka itama takeji da kanta, katashi aure yar gidan talaka sharaf zaka auro kuma yarinya yar shila, saidai matsalan yayan talakawa basu iya samun wuriba, hahahhahha"   yadan kwashe da dariyanshi irin na boss sanan yace "yar talaka zaka auro wacce zaka batada kudi tadinga binka irin matan nan da idan kayi fushi har kuka zasu dinga maka suna rokonka karufa musu asiri, ance kudi baya sayan komi billahillazi abokina karyane, kudi nasiyan komi na duniyan nan saidai in mutum baisan ta yanda ake siyaba" suka kwasheda dariyan iskanci, cikeda takaici Baba Khalid yace "can you believe it Attajiri waini zanjema yarinyar nan tacemin ita bazata bayarba sabida tai rashin lafiya bance mata yajiki ba, ni namayi yaji bazan komaba" dasauri Attajiri yace "ohoho, banda abunta irinmu bamu tambayan mata komi yooo ita tama isa ai saidai suyi rashin lafiyan sanan suzo sucemana sunji sauki Baby nagode da kuladani, kuma bazaka komaba katashi komawa gidan nan saidai ka koma da amarya, inda ninekai mata biyu zan kara alokaci daya, daya bazawara wacce mijinta ya danna mata saki, tayanda tana auranka zata darajaka tasan aurenta nada auren wahala tayi sanan tabiyu kuma ka auro yarinya danya sharaf, kabula abunka kaci ana maka godiya iyaye na zuwa maula, kuma kanuna musu duk wacce tamaka hauka danna mata saki zakayi ka koreta daga gidan nan fess zakaga ana kappa kappa dakai, sanan dukansu agidan nan zaka zubasu wlh kanayi kana gumama Hassana tasan cewa kaiba nawasa baneba" wani irin kwashewa sukayi da dariya bana wasaba, da kyar suka tsayarda dariyan Baban Khalid yace "to yanzu yaya za'ayi zanyi managing mata guda biyu a lokaci daya kuwa? Sanan gakuma Hassana su uku kenan" "kai waketa wani maganing kai manager ne? Suyi managing kansu dai kai kazuba musu kudi kayi gaba abunka" dasauri yace "itakuma Hassana nasan yanda zanyida ita wlh zata ganewa hayazaki saitasan tayi kuskure abinda tamin" "correct yanzu kai magana Gwamnati amman da ka tsaya kana wani magana kaman wani wawa" murmushi yayi sosai yace "to yanzu dai yaya zamuyi banda wacce nakeso" dasauri yace "kai! Wake maganan wani wacce akeso anan wurin? Yanzu dai akwai wata mata danagani a office dinka, mai zuwa muku shara da mopping" dasauri yace "Mrs Saudatu" dasauri yace "yes ita kaga matarnan akwai kayan harka ajikinta kuma bakacemin mijinta yamutu ba?" Dasauri yace "yes mijinta yamutu, tanada yara uku though wai basa tareda ita suna family mijin ni tausayi ma tabani nabata aikin sabida yaran" dasauri yace "to itace bazawaran dazaka aura, worker dinka ce dagudu zata yarda and kabata kudi dajin dadi she go craze follow u, banda haka kanuna mata bakasan auren yadauki lokaci zaka mata komi na kayan daki, kawai tafadama nawa takeso sadaki azo adaura aure bakason bata lokaci period zakaga jikinta yafara rawa, kafin auren ma kana kiranta office fara da bata... Inkika karanta batare dakin biyaba zaki biyani ranan dabaki dashi, this book is not a free book, pls support me.Matsa boobs din yayi dasauri hannunshi nawani irin rawa, tunda yake jikinshi baitabayin rawa irin wanda yakeyi yauba, unexpectedly kawai yaji bakin Hajiya akan bananar shi wani irin ihu yayi kaman wanda aka yanka tsabagen dadin dayaji kaman zai fasamai kwanya. "Wayyooo Allah burata, Hajiya yasin zan sume miki da dadi, nashiga uku na lalace, Hajiya kibari waiiiiiii yoooo, Hajiya dadi, wayyo kaciyata, Hajiya zan mutum miki faaaa ahhhhh" yay maganan yana zare hannayenshi daga boobs dinta yana bankaremata yakai hannun arude kanta yawani danna kanta kan buran yana bankaremata yana nishi kaman yana nakuda yana sakin all pre-cum dinshi abakinta tana hadiyewa tana tsuke mouth dinta duka a bananar dayakesa yanaji kaman zaibar duniya tsabagen dadi, chan kuma tafara sha dawani irin sauri sauri tana nishi tadaga hannunta takai sama ta ture hannunshi daga kanta taciro kanta tareda kwanciya gefenshi tana kama buran dakarfi daduk yajike da yawunta dakuma pre-cum dinshi, cikin muryanta da baya fitada kyau tace "zokacini kai amfani dani yanda kakeso, Murtala kafin Baban Khalid komi wlh, gakada strong erection,Ajiyan zuciya yasauke kafin yatattaro duka karfinshi da jarumtarshi ahankali yace "Hajiya ranan wanka ba'a boye cibiya, yau ranace da nasan wanan ce dama ta karshe dazan samu infadi miki raina, Hajiya niba sha'awanki nakeba ni sonki nake!!!!" Yay dan shiru sanan yace "yanda kikemin kallon wawa wawa, banza banza duk bahaka nakeba dudda inada shekara ashirin da shidda aduniya anamin kallon yaro inada mugun hankali, da wayau dakuma sanin yakamata" yadanyi shiru, saikuma ahankali yacigaba. "Nasan banyi karatun nasara ba amman nai karatu islamiya, nayi makarantan allo kaman bagobe, nasan abinda nakeyi, inada ilimi inada kuma Qur'ani akaina" yasakeyi shiru, saikuma chan yanisa yakasa magana, Ahankali ta tashi ta zauna saikuma ta matso ta inda yake tadaura fuskanta akan kirjinshi ta kankameshi, murya chan kasa dake rawa sosai tace "please, kasadu dani Murtala" runtse ido yayi cikeda damuwa, ahankali takifa kanta akan kirjin nashi tanajin yanda heart dinshi ke bugawa bim bim bim tama kasa magana saikawai numfarfarshi take saukewa gwanin ban tausayi. Nisawa yayi sanan gently yace "kiyakuri, nafi kowa kwadayin naga abu yashiga tsakanina dake" yasakeyin shiru sanan yace "Hajiya ranan dana fara dora idanuna akanki ranan nafara sonki! So....Sai....." muryanshi yashiga rawa hakan yasa yadakatar damaganan, ahankali yace "nasan ke matan aure ce, kinada yara, sanan kin girmamin, ke bama macen dazata taba kallon mutum ko sha'awan irina bane, but wayeni dazan gayama kaina da zuciyata abinda zataso da abinda bazata soba, wlh da Alhaji yashigodani falo nunamin ke dazandingawa aiki kika dago kikamin wanan kallon wulakanci kawai naji Allah ya jarabceni dasonki, nasan kinada aure hakan yasa nadinga fada da zuciyata, ina hantaranta kan ba abu mai kyau take neman daura nida ke akaiba, hakan yasa nakara zamarda kaina kaskantacce na karshe awajen ki sabida kicigaba da wulakantani kinamin fada koyasa nadena sonki in tsaneki amman ina ko kadan nakasa, idan kina farinciki ina kallonki zan gane, idan kina bakin ciki kallo daya zan miki nagane, idan kinci abinci zan gane, idan kinyi kuka zan gane, nasan me kikafiso, nasan me kikafi ki, nasan meyafi baki haushi, Hajiya duk wani abu daranki keso nasanshi sabida yanda nake lurada komi naki, duk bandauka wani son kirki nake miki ba saida kikai ciwon nan" yay shiru sanan yacigaba yace "danaje gida wanan yar tafiyan danayi nazaunar da mahaifiyata namata bayanin komi, nafadi mata kaddaran dana fadaciki gameda yanda nakeji akanki sabida abin yasomamin yawa, tabani shawara nasaki aikin nan shine abu mafi a'ala agareni, dan muddin ina ganinki son matan aure zaita cigaba da ginuwan mini araine, nadawo kaiwa gida nacigaba da aikin gonana, nakumayi na'am da maganan ta, Alhaji kawai nakejira yadawo nagayamai na tattara natafi" saikuma6 yasakeyin shiru jin saukar hawayenta akan kirjinshi dawani hucin zafi dake fitowa daga hancinta da bakinta, wlh kaman yamata kuka yakeji, kafin ahankali cikin murya mai rauni sosai yace "Hajiya nasan halin dakike ciki, nasan komi da Alhaji yake miki kawai dai banso daidai dasau daya na nunamiki na gane wani abu gameda rayuwanku ne, gwara kucigaba da daukana wawa mara wayau dan kauye, yafimini Alkhairi" yay dan shiru, ahankali yace "soyayyar danake miki na tsakani ga Allah ne kadai yasa nahanaki aikataAjiyan zuciya yasauke kafin yatattaro duka karfinshi da jarumtarshi ahankali yace "Hajiya ranan wanka ba'a boye cibiya, yau ranace da nasan wanan ce dama ta karshe dazan samu infadi miki raina, Hajiya niba sha'awanki nakeba ni sonki nake!!!!" Yay dan shiru sanan yace "yanda kikemin kallon wawa wawa, banza banza duk bahaka nakeba dudda inada shekara ashirin da shidda aduniya anamin kallon yaro inada mugun hankali, da wayau dakuma sanin yakamata" yadanyi shiru, saikuma ahankali yacigaba. "Nasan banyi karatun nasara ba amman nai karatu islamiya, nayi makarantan allo kaman bagobe, nasan abinda nakeyi, inada ilimi inada kuma Qur'ani akaina" yasakeyi shiru, saikuma chan yanisa yakasa magana, Ahankali ta tashi ta zauna saikuma ta matso ta inda yake tadaura fuskanta akan kirjinshi ta kankameshi, murya chan kasa dake rawa sosai tace "please, kasadu dani Murtala" runtse ido yayi cikeda damuwa, ahankali takifa kanta akan kirjin nashi tanajin yanda heart dinshi ke bugawa bim bim bim tama kasa magana saikawai numfarfarshi take saukewa gwanin ban tausayi. Nisawa yayi sanan gently yace "kiyakuri, nafi kowa kwadayin naga abu yashiga tsakanina dake" yasakeyin shiru sanan yace "Hajiya ranan dana fara dora idanuna akanki ranan nafara sonki! So....Sai....." muryanshi yashiga rawa hakan yasa yadakatar damaganan, ahankali yace "nasan ke matan aure ce, kinada yara, sanan kin girmamin, ke bama macen dazata taba kallon mutum ko sha'awan irina bane, but wayeni dazan gayama kaina da zuciyata abinda zataso da abinda bazata soba, wlh da Alhaji yashigodani falo nunamin ke dazandingawa aiki kika dago kikamin wanan kallon wulakanci kawai naji Allah ya jarabceni dasonki, nasan kinada aure hakan yasa nadinga fada da zuciyata, ina hantaranta kan ba abu mai kyau take neman daura nida ke akaiba, hakan yasa nakara zamarda kaina kaskantacce na karshe awajen ki sabida kicigaba da wulakantani kinamin fada koyasa nadena sonki in tsaneki amman ina ko kadan nakasa, idan kina farinciki ina kallonki zan gane, idan kina bakin ciki kallo daya zan miki nagane, idan kinci abinci zan gane, idan kinyi kuka zan gane, nasan me kikafiso, nasan me kikafi ki, nasan meyafi baki haushi, Hajiya duk wani abu daranki keso nasanshi sabida yanda nake lurada komi naki, duk bandauka wani son kirki nake miki ba saida kikai ciwon nan" yay shiru sanan yacigaba yace "danaje gida wanan yar tafiyan danayi nazaunar da mahaifiyata namata bayanin komi, nafadi mata kaddaran dana fadaciki gameda yanda nakeji akanki sabida abin yasomamin yawa, tabani shawara nasaki aikin nan shine abu mafi a'ala agareni, dan muddin ina ganinki son matan aure zaita cigaba da ginuwan mini araine, nadawo kaiwa gida nacigaba da aikin gonana, nakumayi na'am da maganan ta, Alhaji kawai nakejira yadawo nagayamai na tattara natafi" saikuma6 yasakeyin shiru jin saukar hawayenta akan kirjinshi dawani hucin zafi dake fitowa daga hancinta da bakinta, wlh kaman yamata kuka yakeji, kafin ahankali cikin murya mai rauni sosai yace "Hajiya nasan halin dakike ciki, nasan komi da Alhaji yake miki kawai dai banso daidai dasau daya na nunamiki na gane wani abu gameda rayuwanku ne, gwara kucigaba da daukana wawa mara wayau dan kauye, yafimini Alkhairi" yay dan shiru, ahankali yace "soyayyar danake miki na tsakani ga Allah ne kadai yasa nahanaki aikata[9/9, 6:38 AM] Maman Nasreen: .....Afirgice nuratu tayi saurin bud'e k'ofar sbd gudun karyayiwa net d'in illah"kinganta can mommy"cewar Nisaibah tana nuna nuratu da yatsa.bayin Allah suwaye kune?"baffa ado yafad'a Yana kallon su"wani banzan kallo na raini da wulak'anci mommy tamishi tana yatsina.kafin ta had'e fuska tace".nice mahaifiyar faruq malaminsu wannan kazamar y'ar taka...wani mugun fad'uwa gaban nuratu yyi"cikin tashin hankali tayi baya ta koma d'akin"Nisaibah taja tsaki had'e da cewa munafuka aida kinfito manah.bewar Allah inason jin dalilinku nazuwa gidana"baffa ado yafad'a cikin mamakin nusaibah nazagin nuratu datayi...wanikallon rainin wayo mommy tayiwa gidan.kafin tace"wannan kangon shine gida?to bara nafad'a maka da babbar Murya"ruwa basa'an kwando bane"Kuma wutsiyar rak'umi tayi nesa da k'asa wlh"munfi k'arfin had'a zuri'a da irinku matsiyata"kajawa y'ar ka kunne"tarabu da d'ana bbushi bbu itah har abada... wannan wane irin rainin hankali da wulak'anci ne?ku dabbobin inane dazaku shigo gidan mutane Kuna wannan burgar?"cewar goggo kande amatsife tana fitowa dg cikin d'akin ta.baffa ado yaji dad'in abinda tace sbd shi yakasa cewa komai.sai kallonsu kawai yakeyi.idan kin Isa dashi d'an naki shiya kamata kijawa kunne bamuba ko?tsaki mommy taja had'e da cewa kekuma asuwa?Kuna fama da bak'in talauci d'aya muku Kant....matsowa kusada ita goggo kande tayi tana cewa"kinci kanbura ubaki"idan banmiki shegen dukaba"kice Nina y'a bace.nadakeki nadaki banza sbd gidana kikazo.kufice. Kubawa mutane wuri"Allah yarabamu da irin arzik'inku naciwa mutane zarafi.k'ilama inza'a bibbiya kud'in naku Bata hanyar halak kuka samesuba" Gaba d'aya mommy shiru kawai tayi, sbd batayi zaton za'a musu hakanba.nur dake d'aki tana sauraron komai sai kuka takeyi"yyinda baffa ado yamaidasu kamar TV" saida yaga goggo kande ta Kai aya alafazinta tukum yace"kufita kubawa mutane guri.tsaki Nisaibah taja had'e da cewa mommy muje zasu gane kuransu wlh.kudai gane kuranku y'an wahala"cewar goggo kande tanajan tsaki,yyinda mommy taja kwafa had'e da cewa kundaiji abinda nafad'a muku?muddin bata rabu dashiba"tokuyi kuka da abinda zai biyo baya..tana fad'in hakan suka fice dg gidan... Alhassan kuwa har yanzun Yana nan zaune kan dakali"suna fitowa sir faruq nakawowa ...wani mummunan fad'uwa gaban sa yayi"arikice yanufesu Yana cewa mommy mekukaje yi gidansu nurr?"tsaki taja had'e da cewa bbukai bbu talaka har abada"wuce muje banyarda kasake zuwa gidan nanba ko zuwa gunta.idan hakan yafaru banyafe makaba.... innalillahi wa inna ilaihir raju'un"ya fad'a arud'e Yana runtse ido.mommy kinsan mekike fad'a kuwa?bansaniba "zaka wuce muje ko kuwa? alhassan dake zaune Yana sauraren komai yakece da dariyar mugunta Yana tab'e baki.wata iriyar zuciya tazowa sir faruq iya wuya.k'ok'arin nufar alhassan yakeyi.. mommy ta ruk'osa da sauri"tana cewa bakaji mena fad'a maka bane?"adedenan Kuma baffa ado yafito dg soron gidan Yana rik'e da hannun nurr daketa kuka shab'e shab'e da hawaye.gabanta yakoma fad'uwa sbd ganin sir faruq"yakafeta da ido babu ko kiftawa. Jitake abun kamar amafarki ne ba gaskeba... b'ata tab'a zaton haka iyayensa sukeba"azatonta suma masu kirkine irinsa"zaka wuce muje ka tsaya kana kallonta.kasani bazan canzaba"muddin kazo inda take kokulata banyafe makaba...zaro ido nurr tayi cikin tashin hankali tana k'ok'arin barin wurin"baffa ado yace"gidan uwarwa zakije? alhassan yayi saurin cewa"ah ah baba barta ta tafi ko ranta yadena k'unci"zuwa dare insha Allah zandawo gunta fira...sakar Mata hannu baffa ado yyi"da gudu nurr Takoma cikin gida tana kuka..sir faruq kuwa jiyakeyi tamkar alhassan yawatsa mishi wuta akan kalamansa ga nurr"zare hannunsa da mommy tarik'e yyi yabar gun da k'yar. zuciyar sa na wani irin k'una"ya wuce inda yayi parking motarsa" Suma su Mommy gun tasu motar suka wuce"yyinda baffa ado yatsaya suna mgn da alhassan... Nuratu kuwa d'akinta tashige tafad'a kan katifarta tasaki kuka mecin rai"meyasa sadaukinah kashigo rayuwata?bacin kasan mahaifiyarka bata k'warai bace"bazan iya jure rashinkaba sadaukinah! Allah yasa mafarki nakeyi bagaske bane...duk tafad'a afili tana kuka.baffa ado yashigo gidan Yana k'wala Mata kira"banza tamishi tana cigaba da kukanta"yyinda goggo kande ta fito"tana kallonsa tace"nagaji da mugun halinka wlh"asanadin k'wadayinku kaida y'ar ka kunjawo anzo har gida za'a cimana mutunci ko?"Allah yawadaran kwad'ayi wlh...tana fad'in hakan ta wuce d'akin ta.baffa ado yaja kwafa had'e da cewa zanyi maganinki kema... d'akin nurr yanufa yasameta tana kuka"Dan uwarki akansa kike kuka sbd bakida zuciya ko?banza tamishi"to Bari kiji ko kukan jini zakiyi bbuke bbushi"sannan aurenki da alhassan Dole ne.sbd haka kishirya da dare zaizo tad'i agunki"Yana fad'in hakan yajuya ya fice.jitakeyi kawai gara ta mutu kota huta da wannan masifar datake ciki" *hasbinallahu wani imal wakeel* Taketa ambata aranta"tana sakin ajiyar zuciya"Kiran Sallar la'asar yasakata tashi tafito ta wanke fuskarta tayi alwallah.. Sir faruq !inbacin tsaron ubangiji dayyi accident"gaba d'aya tamkar bashiba haka yakejin kansa.ga wani abu daya tsaya mishi azuciya daya tuna Wai alhassan zai dawo anjima gun nurr"ga zafin mommy zata mishi baki"wani tsanar Nisaibah yaji da mugun k'inta.sbd yatabbatar da cewa itace ta sanar da mommy komai akan nurr"saidai yyi mamakin ta Yaya suka gano gidansu nurr d'in?tausayinta yaji sbd yatabbatar bak'aken maganganu tafad'a musu"tunda yaga nurr d'in nakuka sosai"gabansa yaji yafad'i"daya tuna tace bbushi bbu talaka"afili yace"kotana nufin son nurr nakeyine?yatambayi kansa yanajin fad'uwar gaba.ga wani gudu dayakeyi asaman titi..gaba d'aya tunanin sa yararraba"hakan yasa direct yacanza akalar motar "zuwa gidansu mubarak sbd yasamu mafita"tunda bashida wani amini ko abokin daya wucesa.. Mubarak na zaune a haraban gidan su"kan resting chair"yaji ana wani mugun horn"kallon get d'in yyi lokacin dame gadi ke bud'ewa sbd yaga wace mota zata shigo....mamaki sosai yyi sbd ganin motar sir faruq ta shigo da wani irin mahaukacin gudu...da ido yabishi sbd ganin yafito dg motar ko rufewa beyiba"kallon d'aya yamishi yagano Yana cikin damuwa da tashin hankali...tashi tsaye yyi yanufesa.yana cewa abokina lfy daiko?"girgiza mishi kansa yyi had'e da cewa muje d'akinka.bbu musu suka wuce d'akin Mubarak d'in. bayan sun zauna, Mubarak yadubesa yace"abokina lfy?kamun bayani Dan Allah naga alamar damuwa aranka...cikin wani yanayi sir faruq yace"tayaya ake gane SO?sosai abin yayiwa mubarak dad'i"dama wannan ranar yake jira.amma bara yagaya Masa"yaji damuwarsa ,tukum sai yamishi shegantaka.abokina manyan alamomi na SO asanina 3 ne.amma sunada yawa sosai da sosai.na farko *kishi* Kaji kana jin haushin ganin wacce kakeso da wani ko Kuma ,taji haushin ganinka da wata idan yariya kesonka.. Na biyu *fad'uwar gaba* Idan kaganta /kota ganka zataji fad'uwar gaba sosai.sai na 3" *gudun b'acin ranta /ko gudun b'acin ransa dason kyautatawa Wanda kakeson sbd kagansa cikin farin ciki.kuma kak'i me munana Masa.* Iya sanina wad'an nan sune manyan alamomi na mutum yakamu da SO! wata iriyar ajiyar zuciya sir faruq yasaki"aransa Yana cewa wato yanzun shi son nurr yakeyi kenan?sbd abinda mubarak yalissafo mishi.dukansu yanaji game da ita.harda masu abubuwan"to ita nurr d'in tanasonshi ko kuwa?"yatambayi kansa...waimeke damunkane? Mubarak!Ina cikin matsala da damuwa.intak'aita maka zance"mommy tamun baki akan nasake zuwa gun nurr"bata yafemunba! yafad'a Yana runtse ido.innalillahi wa inna ilaihir raju'un! Mubarak yafad'a arud'e"kallon sir faruq yyi yace"tayaya kabari Mommy tasan Kuna tare da ita? wannan y'ar iskar yarinyar Nisaibah Mana"itace tasanar Mata sbd d'azun da safe taje skul d'in.tasamemu Muna tare da nurr.gsky bata kyautaba"gashi na lura yanzun kundena fad'a da nur d'in ko? Hmmm!abokina menene mafita yanzun?bansan Ina zansaka rainaba"idan nakwana banga my nurr ba"kobanji muryartaba nikawai nasan yanakeji.yafada Yana dafe kansa"Mubarak yace".ni aganina kayiwa mahaifiyarka biyayya hakan kawai zafe...cikin wani yanayi yafara bashi labarin rayuwar nurr"dason abin duniya irin na marik'inta baffa ado"dakuma alhassan ayanzun dayadawo Yana son ya aureta.bacin abaya yayi k'ok'arin b'ata Mata rayuwa Allah be bashi nassaraba...sir faruq yak'are zancen da cewa"damuwata shine takasance tare da d'an iskan yaron nan (alhassan) sannan bbu wani namijin da ya Isa *ya auri nurrinah sai ni sadaukinta* Sosai mubarak yagimtse dariyarsa"bansan inayiwa yarinyar nan mahaukacin soba sai yanzun daka sanarmu taya ake ganewa"meye mafita pls?"ajiyar zuciya mubarak yasaki"kafin yace"ni aganina barin gidan k'anin mahaifinta shine mafita babba"sbd kaga zata gujewa auren abokin takarar ka(alhassan) sannan tunda basonshi takeyiba zata zama acikin damuwa 2"anrabata dakai,an aura Mata Wanda bataso.gashi Kuma mommy tace karta koma ganinka da ita.dasai kayi wani abu akai.ajiyar zuciya sir faruq yasaki Yana tunanin Anya zai iya furtawa nurr kalmar yanasonta?tana amatsayin d'alibarsa..kayi shiru bakace komaiba!cewar mubarak cike da tausayawa abokin nashi"ajiyar zuciya yasaki kafin yace".inaso yanzun ka kira nurr kace Mata nace ta had'a kayanta duka ta tafi gidan kakarta. zan turaka kayi komai bbu abinda zai faru.bazata auri alhassan ba..Mubarak yace".okay bani number d'in ta.. Bayan yasakamishi number ta"nurr na zaune tayi tagumi"taji wayarta na ringing"da sauri ta duba sbd azatonta ko sadaukinta ne.saitaga bak'uwar number"kamar kada ta d'aga tadai daure ta d'auka tana sallama"muryar sir Mubarak taji.hakan yasa ta nutsu yamata bayanin komai"ta amsa cike da gamsuwa da bayaninsa.hawayenta ta share"tanajin zafin baffa ado dashine sanadin komai.tashi tayi ta had'a duka kayanta a cikin Ghana"tad'auki duka takalminta da hand bag nata guda 2 da sir faruq yasiya Mata tasaka awata leda VIVA"katifarta kawai ta bari da tabarma"hijab tasaka ta fito tsakar gidan taji k'arar ruwa abayi"da alama goggo kande wanka takeyi"yyinda d'akin baffa ado arufe"da sauri tasaka kwad'o ta rufe k'ofar net d'in bayan ta fito da kayanta duka atsakar gidan.asoro ta had'u da wani almajiri"tabashi ghanar yad'aukar mata"ita Kuma ta d'auki leda viva suka nufi bakin titi.cikin sa'a tasami nafef"50 nera tabawa almajirin bayan tashiga nafef din.suka wuce anguwar kawo... Sir faruq kuwa Yana ganin mubarak yakashe wayar yace"tashi muje muyi sallar la'asar muwuce police station.zaro ido Mubarak yyi had'e da cewa bangane muje police station ba?kaidai kazo muje plaine zamu had'a da inspector Salim"yabika kuje gun baffanta. atsoratar dashi akan za'a rufesa koyabarta tazauna agidan kakarta" ta zab'i Wanda takeso ta kawoshi ya aura Mata..akan hujjar beciyar da ita kotufatarwa ko nema Mata ilimi"akan me zai Mata auren Dole?wannan hujjace Mai k'arfi.kuma ma Wanda yakeso ta aura ba mutum ne na gariba. Mubarak yace"gsky wannan itace kawai mafita abokina.fatana Allah yasa ita nurrin taka tana sonka....Kuma Allah yasa mommy ta janye bakin data maka saikaje kusasanta kanku.wani banzan kallo sir faruq yamishi Yana cewa d'an iska kawai.dukda suna cikin yanayi narashin jin dad'i saida Mubarak ya murmusa... Bayan sun gama sallar la'asar suka wuce police station d'in...sosai suka tsarawa inspector salim yadda komai zai kasance"kafin su tafo gidan baffa ado su hud'u"inspector salim,Mubarak da wasu y'an sanda 2.yyinda sir faruq ya wuce gida da nufin duk yadda akayi to Mubarak yakirashi yasanar mishi... goggo kande data fito dg wanka taga d'akin nurr arufe"saitayi zaton islamiyya ta tafi"har 6 ta wuce bata dawoba"hakan Kuma bedami goggo kande ba,tanata hidimarta" Tamkar anjohosa haka yashigo gidan yanata tsami da k'arin rana"kallo d'aya goggo kande ta mishi ta d'auke kanta"Wai yarinyar nan batadawo dg islamiyyar bane?banza goggo kande ta mishi..Yana k'ok'arin mgn yaro yyi sallama yace".Wai ance ana sallama damai gidan..suwaye ne?"cewar baffa ado azatonsa k'ila ma alhassan ne.wasu y'an sandane!me? yafad'a Yana zaro ido"goggo kande tace"kwad'ayi mabud'in wahala"Kai yaro jekace baninan..Kai kace musu Yana nan"cewar goggo kande.yaron kuwa yafice"baffa ado da gudu ya wuce bayi sbd cikinsa yajuya...Yana fitowa yasami yaron yadawo"Kai wai ubanme sukace ne?sunce inhar ka wuce minti2 baka fitoba zasu shigo sutafi dakai..wani mugun tsoro da fad'uwar gaba baffa ado yaji"jikinsa na kirma yafice Yana zare ido. Lokacin da Mubarak yahangoshi sai yasake tamke fuska sosai...bayin Allah Lfy kuke nemanka?"cewar baffa ado Yana tsaye bakin k'ofar shiga gidan" Mubarak yadubesa yace"sunana Mubarak!ni malamin su nurr ne a islamiyya.(yyi k'arya) Muna lura da ita tana cikin damuwa da rashin walwala"ayau mukaga abun yafi na kullum.shine muka tursasata tasanar Mana"shine bayan tasanar Mana" mukazo anan anguwar muka bincika domin gano gaskiyar abinda kake aikatama marainiyar Allah.kuma duk mak'otanku sun bada shaida...inkana yiwa Allah kayi hakuri! natuba nabi Allah..yafad'a sbd yasan yyi duk jama'ar anguwar sun san Yana zalintarta.yimana shiru!cewar inspector salim"tafiya zamuyi dakai"abima yarinya hakk'in ta"kanaso kamaida ita karuwa sbd takamaka kud'i ko?sbd kana tsohon banza"ga yaro ba mutimin kirkiba kanaso ka aura matashi sbd kaga kud'i ko?wlh bahaka bane"Ina ita nuratun take Dan Allah Zan gyara mugun halina karku kulleni a ofishinku Dan Allah..yaduk'ana Yana basu hakuri... Mubarak kuwa tamkar yyi dariya. yanata yiwa abokinsa recoding d'in duk maganar dasukayi da baffa ado...yyinda su salis me tireda shida abokansa suketa kwasar dariya dg nesa.wasu Kuma sunyi tsaye suna kallon me akeyi...Mubarak ne yace"ya Isa katashi muyi mgn"jikinsa na kirma yatashi Yana cewa to inajinka wlh.zamu k'yaleka!Amma da sharad'i"jiki na kirma baffa ado yace"nayarda dakoma wane sharad'ine"yafad'a cikin tsoro sbd be manta sadda sir faruq yasaka aka Kama alh tukur ba.kuma yanada kud'i,to balle shi talaka"k'ilama sudake sa acan station d'in... Mubarak yace"nabawa nuratu umarnin data koma gidan kakarta dazama tabar hannunka"sbd bincike yanuna ko iyalanka baka d'aukar nauyinsu ,balle ita"Abu nakarshe bbu maganar katakura akan Mata auren dole. Kabari tazab'i Wanda takeso takamaka ka aura Mata shi....wlh tallahi na amince zanbi umarninku y'allabai"tab'e baki sir Mubarak yyi kafin yace"dg k'arshe Dole kasanar wa alhassan yanemi wata sbd batasonsa.... inspector salim ya karb'e zancen da cewa idan bahaka ba kuwa hmmm!Yana fad'in hakan suka wuce batare da sun sake bi takansaba..ajiyar zuciya baffa ado yasaki Yana hararan wasu yara dake tsaye suna kallonsa.gida yakoma Yana tsinewa nuratu aransa"goggo kande daketa kaida kawowarta bema isheta kalloba... suna isowa police station d'in suka sami sir faruq acan "sbd Mubarak yakirashi yace su had'e acan....lokacin dayagama sauraron recording d'in"yasaki ajiyar zuciya cike da tausayin nurinsa"yanaji Anya gobe zaije skul nasu kuwa"sbd bazai iya ganinta yak'i kulata ba"dukda bama a aiki exems sukeyi.mubarak yadafa kafad'ar sa"yace bara idan naje anguwar kawon nakira ta ta Mun kwatancen gidan. [9/9, 6:38 AM] Maman Nasreen: .....Wani irin mugun fad'uwa gaban ta yayi"atake ta had'e ranta tana jifansa da wani irin kallo....shikuwa murmushi yyi Yana Zama kan dankalin k'ofar gidan"miye yakawoka k'ofar gidanmu?abinda nuratu ta fad'a kenan tana janye idanunta dg barin kallonsa.fatanta yayi gaggawar barin wurin kafin sadaukinta yazo yanzun yasameshi."talura yayi mugun canjawa"hutu had'e da wayewa sun zauna ajikinsa...bak'onka annabinka nuratu!banyi zaton har yanzun kina akan bakanki natsanata ba"Amma wlh kina araina har gobe inasonki"SO bana wasaba"SO na aure nake Miki nuratu.nayi nadamar abinda na aikata agareki kiyi hakuri pls&pls!!kaga kadena maido mun abinda yarigada ya wuce Allah yashiryamu gaba d'aya"zaka iya tafiya nizan shiga cikin gida.maganar SO atsakanin mu bbushi har abada"bazan iya auren wanda yayi k'ok'arin cimun zarafi ba...pls nuratu jiyafa nadawo Amma wlh naji bazan iya jure rashinkiba.sainazo naganki zansami sukuni araina....d'ago kanta tayi da nufin ta mishi mgn suka had'a ido da sadaukinta dake binsu dawani irin kallo...Yana nufosu..wani mugun bugawa k'irjin ta yyi"da sauri ta nufesa kafin yak'araso gurin... alhassan kuwa kallonta yyi yaga tana k'ok'arin zuwa gurin sadauki"da kallo d'aya yamasa yasan akwai inda yasanshi.da ido kawai yake binsu , still Yana zaune kan dankalin. sadaukinah!banason ji komai"waye shi zakifad'an kawai?"labarin nada tsayi dan Allah karki fushi kaji sadaukinah?takarashe maganar tana langab'e kanta"my Nurr kinsan bazan iya juran fushi dakeba ko?maimakon Kuma kidinga kiyaye b'acin raina"wlh bansan shibane yazo fa"azatona kaine!sbd bayan mungama waya ya Aiko kirana.yanzun ma nafad'a mishi yayi tafiyarsa ne... menene tsakanin ku? *sona yakeyi* wani zafi sosai yaji kalmar ta mashi"besan lokacin dayaja tsaki ba. yawuce ta, yanufi gurin dakalin inda alhasan ke zaune Yana latsaya waya"dukda abad'ini hankalinsa na gunsu"ransa yabashi tabbas wancan saurayin nuratune...sadauki karka kulashi pls! tafad'a ahankali tana biyosa abaya...yyinda salis me tireda da wani abokinsa suna zaune suna lura dasu dukda basujin mesuke cewa ba. Hii!cewar sir faruq fuska bbu annuri"banza alhassan yamasa , yad'ago kansa Yana kallon nuratu dake nufosu.my sweet heart yakamata ki sallamesa kizo mu Ida maganar mu... alhassan yafad'a Yana wani hura hanci had'e da basarwa" what's?sir faruq yafad'a da k'arfi Yana zaro ido"nibbu wata magana dazamuyi dakai"kab'ace Mana dg nan.kuma karka koma kirana da sweet heart d'inka.cewar nurr tana hararar sa"tashi tsaye yyi Yana kallon sir faruq ido cikin ido yace"mlm Ina ruwanka danine?nuratu tawace nikad'ai !bbu Wanda ya Isa yarabani da ita"Koda ita dakant....wata wawar shakuma sir faruq yamasa da hannu guda Yana huci"Murya akausashe yace"maimaita mun abinda kace...sadauki sakesa pls"kaga da jama'a masu saka idanuwa dan ALLAH.nuratu ta fad'a tana tsaye abayansa..banza yamata saima sake shak'ar wuyan alhassan yyi"alhassan kuwa tari yafarayi"yyinda idanuwan sir faruq sunji jajir sbd b'acin rai da zuciyar data taso mishi iya wuya...nashiga ukku sadauki kasakesa pls.tafad'a da k'arfi.kallonsu salis tayi da sauri ta matsa tana k'ok'arin musu mgn.suka taso da sauri"dan Allah kurabasu salis.. tafad'a tana fashewa da kuka.sbd ganin kusan mutum 5 suna kallonsu.. k'ok'arin rabasu akeyi amma yak'i sakinsa.yanata faman maimaita kalmar zaka koma zuwa gunta?"wai hayaniyar menake jine haka ne "ana k'ok'arin Kiran magrib?cewar baffa ado daya fito dg soron gidansa yalek'o waje.innalillahi wa inna ilaihir raju'un!kaikuwa meyayi zafi?kisan Kai zakayi Mana kome? "nuratu na kuka tafara k'ok'arin matsawa dab da sir faruq har jikinsu nagugan juna tace"tunda bazaka sake shiba kayi yadda kakeso.tana fad'in hakan ta juya da nufin ta tafi gida"dukda kawai tafad'a ne bazata iya tafiyaba"sakinsa yyi yahankad'asa.su salis suka rik'e alhassan sbd ganin zai Fadi k'asa.baffa ado kuwa yagane alhassan.sannan wani mugun tsoron sir faruq yakamashi..nurr karki tafi zokiji!tana share hawayenta ta tsaya cak abakin k'ofar.baffa ado dake binsu da kallo ya wuce cikin gida da nufin idan tashigo yatambayeta wanda kesonta yaturo. tunda yalura sunada kud'i.shi indai za'a bashi kud'i bbu abinda yadamesa... Alhassan kuwa janye jikinsa yyi dg gurinsu salis"sukuma suka koma inda suke zaune. yanajan tsaki"yamaida kallonsa ga sir faruq dake k'ok'arin tsayawa kusada nur"hmmm idan da zaka burgeni shine kayi abu 2"sannan insan ka Isa namiji"na farko shine daka kasheni baka barni da rainaba.na 2 shine acikin satin nan ka aureta.inkayi hakan sannan zansan Kai namijin duniyane.nuratu kuwa baka isa karabani da itaba wlh"ko ita kanta da iyayenta basu isa sura bani da itaba.balle Kai! wani murmushin takaici sir faruq yyi"kafin yace"nafi k'arfin yin jayayya dakai"domin inkaga antsaya ana jayayya to k'arfi yazo d'aya kenan.magana guda my Nurr tamaka nisa...and last kabar gun nan tun kana iya mgn cikin jin dad'i.kisa dakake mgn"ban iyashiba bazan Kuma Fara akankaba.tarbiyyar dabakada ita ! ita ta furta mgn itace nakoyar dakai"Yana fad'in hakan yadubi nurr daketa kallonsa yace"shiga ciki zanje nayo sallah"shagwabe fuska tayi had'e da cewa "amma zaka dawo ko?tsaki alhassan yaja yabar gurin, da k'udurin gobe zaidawo yasakarwa baffa ado kud'i.hakan kawaine mafita"aganinsa fa amma... zandawo Mana my nurr"gsky banji dad'in abinda kayiba sadaukinah"wai sai yaushe zaka Dena wannan halin naka ne dan Allah? zandena my Nurr"Koda yaushe haka kake cewafa"bazan komaba kinji?Amma banji dad'i ba"dakika tsaya dashi"to Wai wama kikayiwa wannan kwalliyar ne?sadaukinah kaimana"bakace nadinga shafa lipstick ba?shine nashafa makako?kin kyauta Kuma kinfi kyau sosai akan inbakiyi make up.kidingayi pls!amma nikawai zaki dinga mawa.to shikenan sadaukinah"my nurr wannan shine yaron dakika tab'a aiki agidansu last 3yrs?cikin zaro ido da mamakin ta Yaya yasani tace"eh shine !kwafa yaja Yana cewa jekiyi sallah! saina dawo..bejira cewartaba yawuce"ajiyar zuciya tasaki tashige cikin gidan..baffa ado dake tsaye Yana jiran shigowarta yace"ke acikinsu wake sonki da aure? gabanta na fad'uwa tace".bbu kowa"k'arya kike munafuka!duk Wanda yariga daya turo magabatansa shine zaki aura bbu ruwana dasai kingama karatu...kaji kunya wlh!sbd wannan zak'ewar dakakeyi badan Allah bane. sbd kasami kud'i ko?"cewar goggo kande data fito dg bayi zatayi alwallah.eh sbd kud'in Ina ruwankine?wlh zansakeki inkikayi wasa"bud'a goggo kande tayi"had'e da cewa"dakuwa nazuba ruwa k'asa nasha sbd murnan narabu da zalamamme me matacciyar zuciya irinka.ko yanzun sbd yarana 2 nake zaune dakai"Amma bacin wannan gidan damuke zaune cikinsa.bbu hanyar danake k'aruwa dakai...sai indare yyi kad'ebo k'azamin jikinka kanamun y'ar muryar nabaka kaina kayi....da sauri nurr tabar gurin ta nufi d'akin ta.tana musu addu'ar shiriya.sbd jin goggo kande naneman b'aro mgn babba.ruwa tazuba abuta ta cire kayanta tasaka wata doguwar riga ta atamfa roba .lokacin data fito bbu kowa tsakar gidan da alama sun gama fad'an su yafice dg gidan... Alwallah tayi Takoma d'akinta ta kabbara sallah"tana nan azaune aka Kira isha'i"baya tagama ta canza kayanta"wani gefen zuciyarta tana tuna maganganun alhassan *idan zaka burgeni ka aureta acikin satin nan* .....wayarta tayi ringing"taduba taga sadaukinah!sunan datayi seving number d'insa dashi kenan. ahankali ta d'aga tana mishi sallama"okay fafad'a tana kashewayar.tajawo net d'in k'ofar ta fice dg gidan... Yana tsaye bakin k'ofar shiga cikin gidan"yakunna fitilar wayarsa"Yana sanye da yadi ash colour na riga da wando.riga iya gwiwa"Masha Allah tafad'a aranta" sbd d'azun ma hankalinta ba ajikinta yakeba batama luraba da kayan jikinsa ba. Assalamu alaikum!wa'alaikissalam ya amsa Yana haskota"hannuwanta tasaka tana rufe fuskarta had'e da turo baki"sosai yaji ta birgesa"my nurr malamin naki kike turowa baki?to bakaine kajaba!danayi me?daka haskani mana"hmmm kin iya shagwaba wai?na iya Mana"to meyasa ni ba'amun? zandinga maka to"da gske ?eh"to shikenan gashi kije gida"inkingama abinda kikeyi kimun flashing saimuyi firan ko?"yafad'a Yana mik'o Mata wata leda"eh insha Allah"sadaukinah meye aciki?nidai banason Kanata wannan faman kashe kashen kud'in. Wanda kayi abaya ya Isa wlh"nide be isheniba my nur!ki karb'a inkuma kinfison b'atan rai shikenan"batace komai ba ta amsa badan tasoba.domin yanzun d'awainiyyar dayake Mata tafara bata tsoro.my nurr!yakira sunanta"menene?muryarta asanyaye tace"bbu komai"my Nurr nifa banida wani mummunan abu akanki sai alkhairi.banaso zuciyar ki ta sak'a Miki wani Abu daban"ahankali tace"na aminta dakai sadaukinah 100%...nima haka my Nurr"Amma zakimun shagwab'ar Taki naji" idan nakiraki anjiman?" Tana murmushi tace"eh manah"yauwa tawan , yanzun kishiga ciki saimunyi waya.godiya ta mishi ta shige cikin gidan" ruwa ta watsa tayi shafa'i da wuturi"tazauna dg ita sai vest da zani.kafin tajawo ledar ta bud'a"kazace gasassa da ice cream....kat ta zauna tayiwa cikinta.kafin taje tayi brush tadawo d'akinta.zama tayi zata mishi flashing suit d'in sa dake hannunta kusan 3 weeks tafad'o Mata arai.wayarce datayi ringing tadawo da ita dg duniyar tunanin datakeyi...tana murmushi ta d'aga sbd ganin sadaukinah akan wayar"ahankali tace"dafa yanzun zanmaka flashing d'in"my Nurr nima nagaji da jiran kiyo flashing d'in.nace gara dai nakiraki"hakane sadaukinah"Amma Dan Allah Yaya akayi kasan nayi aiki agidansu alhassan?hmmm!abin sirrine bazan fad'aba...niiiiidai Allah saika fad'a mun ko mu b'ata dakai"tafad'a cikin shagwab'a"lumshe idanunsa yyi"cikin wata iriyar murya yace"ai bazamu iya fushi da junanmuba my nurr"toba saina Fara yi dg yanzuba.nifa saika fad'amun tam"duk tana mgn ne cikin shagwab'a.ahankali yace". dama haka kika iya shagwab'a?Kuma Saida na rok'a za'a mun ma ko?"turo baki tayi had'e da cewa tonasan kobasonta ne?inaso my Nurr"yanzun idan muka had'u a skul gobe zakimun?"um um nidai inajin kunya wlh"hmmm! sadaukin naki kike jiwa kunya my Nurr?"eh mana"to yanzun nidai bazan b'oyemiki ba"nabinciko tarihirin rayuwarkine sbd banajin dad'i akan zaman dakikeyi gun baffanki Yana cutar dake.yanzun idan Babu damuwa zansan yadda nayi kikoma gun kakarki da zama.kinason haka?cikin farin ciki tace".eh wlh sadaukinah nagode sosai.yana murmushi yace"karki damu"yanzun bara nabarki ki kwanta Kar kiyi latti gobe idan Allah yakaimu.nifa bangaji da mgn dakaiba.saidai indai Kaine ka gaji d mgn dani.bana fatan hakan my Nurr"Yaya !Yaya !!cewar nusaiba tana shigowa parlourn"gaban nur yafad'i,batasan lokacin da tace"wacece sadaukinah kodai kanada matane??"sorry my Nurr zankiraki back!Yana fad'in hakan yakashe wayar yana hararan Nisaibah dake binsa da kallon sha'awa. tana hangosu amatsayin ma'aurata... ke!lfy zakizo yanzun har 10 ta kusa?daddy ne yace"nazo nasanar maka gobe kaciro Masa kud'i 200k ta bank" kafin katafi gurin aiki. Okay Zaki iya tafiya"batace komai ba tafice"saidai ranta yagama yadda nurr d'in nan budurwarce"da ita yakeyin waya"Dole tasanar wa mommy sbd tayi wani abu akai.gaba d'aya hangosa take kwance kan 3seeter Yana waya dg shi sai vest d boxer..ta lumshe ido tana ayyana yadda zataji dad'i idan ta auresa. Nurr kuwa zafi taji aranta sosai"dama yanada Mata betab'a sanar Mata ba"wata zuciyar tace"to ke Ina ruwanki da matarsane?meye naki najin zafin.... ringing d'in wayar yakatse mata tunaninta.kamar kada yad'aga tadai daure ta d'auka. My nurr kina jina?" "Uhumm! kina tambayar inada Mata ko? Da sauri tace".eh" Yana murmushi yace".ah ah nibbu wata macen Dana tab'aji ta burgeni saike kawai"yarinyar nan dakikaji ta kirani da Yaya"kanwata ce uwa d'aya uba d'aya.ajiyar zuciya tasaki ab'oye"kafin tace".hmmm!nikawai ma ke burgeka to meyasa? nima bazan iya ganewa ba my nurr!Wai sadaukinah kana nufin bakada budurwa? tafad'a tana dariya k'asa k'asa.hmmm Allah yakyauta mun yin wata budurwa.wannan sai Mubarak(sir Mubarak) to meyasa sadaukinah?bbu komai my Nurr"kokinaso nayi budurwar?hmmm kabari sai lokacin dakamun aure saikayi taka budurwar...gabansa yaji yafad'i sosai ,ga haushi yaji na maganarta.wanda yarasa dalilin jin hakan.sadaukinah !uhumm inajinki my Nurr"aure kikesone?lahh nifa wasa nakeyi bayanzunba.ah ah inkinaso fad'amun naji waye saurayin naki ko?"yafad'a Yana jin fad'uwar gaba.fatansa tace". bbu saurayin datake dashi.cikin turo baki tace".nima kamar yadda bakada budurwa to nima Banda saurayi..to shikenan hakan yafimana ko my Nurr? eh Mana"yanzun Kinga 10 ta wuce da asuba zankiraki kitashi sallah.to sadaukinah nagode.karki damu kikularmun da kanki"insha Allah"tafad'a tana kashe wayar. Ajiyar zuciya yasaki"Yana tunanin abubuwa masu yawa dayakeji ko yake tsintar kansa dashi akan nurr"Amma zai yiwa Mubarak wasu tambayoyi akan abubuwan dayakeji game da itah... Nisaibah kuwa"tana zuwa tasanarwa da daddy amsar sir faruq ta wuce bed room d'in mommy. Harma tafara bacci "Amma Saida Nisaibah ta tayar da ita... cikin damuwa tace"wlh mommy Yaya soyayya yakeyi da wata yarinya NURR! Toke tayaya kikasan hakan?"yanzun daddy ya aikeni gunsa ,shine nasamu suna waya da ita wlh.mommy tace"karki damu kibarni dashi"mommy abin nan fa abin dubawa ne"Ina zaton kamar fa yarinyar d'alibarsace"sbd naji Yana cewa gobe taje skul da wuri kartayi latti...to indai hakane Dole gobe kije skul d'in kibinciko Mana ita ko y'ar gidan uban wacece ita.dole tarabu dashi wlh"zankuma mishi barazanar Zan tsine mishi albarka koyarabu da ita.to mommy kinsan tsinuwarki bazata iya binsaba tunda bakece kika haifesaba. Eh Mana"sbd natsoratar dashine Mana"to Kuma in dg baya kuka bijiro Masa da maganar aurena"bazai Miki kallon Maison kantaba....hakane Kuma kinyi gsky"yanzun kibincika yarinyar"inhar Yar gidan matsiyata ce.to Kinga saina fake da hakan nace yarabu da ita.kuma Mije gidansu muyi Mata barazana itada iyayenta. dole tarabu dashi"abinda yasa yanzun bazamu yarda muce ya aurekiba.sai kingama matsewa sosai sbd zubar miki cikin da akayi.inkuma kinje kinsake bawa wani kanki ke kika sani"munaso nan da wata 5 haka.lokacin zakiyi service naki sai asaka ranar aurenku ko?"eh wlh mommy hakan yyi.kwanciyarta mommy tayi ,itakuma ta wuce nata d'akin da d'okin safiya tayi take skul d'in su nurr... Washe gari....✍️[9/9, 2:08 PM] Maman Nasreen: *washe gari* cike da d'oki nurr ta shirya.tanata zuba k'amshi yanzun har wata y'ar kiba tayi sbd kulawar data ke samu agun sadaukinta.tasaka suit nashi awata leda"ta fito dg gidan.nafef ta hau sbd tayi saurin zuwa tunma 7."tana isowa office nashi ta hango abud'e"skul bag nata takai class ta ajiye. kafin ta fito ta nufi office nashi....sir faruq kuwa har mafarkin nurr yyi jiya"da wuri yashigo skul d'in sbd kawai yaganta.amma dayaga alamar batazo ba"ya wuce office nashi yad'auki wayarsa yafara k'ok'arin kiranta..saidai yaji wayar akashe"my Nurr kodai kintaho ne?naso ace abud'e wayar take dasai naje nad'akkoki kawai.yafada afili shi d'aya"Yana tsaye gaban table nasa"gefen window yakoma Yana k'ok'arin bud'e window d'in yaji siririyar muryarta tayi sallama"juyowa yyi suka had'a ido"atare suka sakarwa juna murmushi...tana k'arasowa ciki tace". sadaukinah Ina kwana?"lfy qlau my Nurr"yanzun nakiraki naji wayar akashe"eh nabarta agida ne shiyasa.okay kizauna mana Aida sauran kusan 35 minit akoma class tunda ba'a assembly.zama tayi kan kujerar kusada table d'in"ahankali tace".kaima sadaukinah kazauna Mana"zama yyi Yana murmushi yace".my Nurr inafatan kinyi karatu sosai?sbd Kinga nine foamaster naku"Kuma nizanyi invigelating naku"nasani Mana sadaukinah.nayi karatu sosai insha Allah bbu damuwa"paper d'in ka za'a yi after break ko? eh itace"Kuma zanyi Kuma kamun masu satar amsa.to nidai bazance komaiba"gashi kayan aro"tafad'a tana ajiye mishi ledar da suit nashi ke ciki ta bud'a"murmushi yyi yace"ni wlh nama manta da ita my Nurr"kokinaso nabakine?um um wlh taya zansaka wannan? tamun yawafa"tafad'a cikin shagwab'a.inyeee!nurrin sadaukinta"shagwab'ar tamiki kyaufa.rufe idanunta tayi tana murmushi"nifa gsky banason wannan kunyar taki gsky"to ai kunya adoce ga mace sadaukinah"hakane my nurr!wai yaushe zamuje agyara Miki gashin ki?"sai mungama exams"ok to shikenan"meyasa bakyayin lalle?banaso ne(ta b'oye Masa ne..qda tanama ta abinda zata sawa cikinta ta Ina zata sami damar yin wani lalle) to nikuma inaso naganshi ahannunki da k'afafunki"shikenan insha Allah zanyi maka idan angama paper.... k'ok'arin mgn yakeyi Nisaibah ta shigo cikin office d'in bbu ko sallama...da ido ta tsare nurr tana kallo tamkar me nazartar wani abu"K!lfy zaki shigo bbu ko sallama?wani abu yafarune agidan??"duk sir faruq ya tambayeta fuskarsa agimtse.yyinda itama nur ta kalleta sau d'aya taji gabanta yafad'i.nisaibah kuwa gabanta yafad'i sbd ta tsorata da kyawun yarinyar...kayi hakuri Yaya dama mommy tace"nazo na karb'i key d'in motarka zata aikeni.. tafad'a tana k'ok'arin had'a ido da nur"ita kuwa nur d'auke kanta tayi batasake kallon nusaibah ba...Kinga motata b bata sa'anki bace"kije gun driver yakaiki ko ina kike so Mana... shikenan Yaya na wuce"bece komaiba"juyowa tayi had'e da cewa nurr!da sauri nurr tad'ago kanta suka had'a ido.adedenan akayi ringing d'in tafiya class"Nisaibah batace komai ba" ta juya tafita sbd tagane wannan itace nurr d'in dayakeso"sir faruq kuwa yasha alwashin zata gane kuranta namishi shishshigi"sbd yagano tsabar jin gulma yasakata Kiran sunan nur"sbd tagane idan itace nurr..kallon nuratu yyi wacce keta mamakin wannan budurwa data fita..my Nurr kitafi class ganinan zuwa zanje na amso Question paper naku.dato ta amsa tana tashi ta fice dg office d'in. Nisaibah kuwa bata tafiba ashe"saima wata SS 2"ta tsayar tana tambayarta tasan wata nurr?"tace ah ah"kafin nisaibah tace wani abu nurr nafitowa dg office d'in"ta nunawa wadda suke tare itah"tace"kinsan waccan yarinyar?lubna tace"eh mate d'in muce sunanta nuratu ai...yauwa ga wannan amma fad'amun sunan anguwarsu.nisaibah tafad'a tana mik'a Mata dubu 1"da sauri ta karb'a tana jin dad'i"kafin ta sanar mata, da Mata kwatance. sbd anguwarsu guda da nuratun..da sauri Nisaibah ta wuce sbd hango sir faruq yafito Yana rufe k'ofar office nashi... Masha Allah paper tayi sauk'i alhmdllh"Kuma yamusu tsanani Gurin invigelating d'in" Koda aka fito break k'in fitowa nurr tayi sbd bataso yace tazo suje skul shop yasiya Mata wani abun. Lokacin da aka koma break kuwa"sir faruq harda dorina yashigo ajin "bbu mutunci ,fuskarsa agimtse ya shigo yabawa nurr Questions papers d'in ta raba"sannan akayi tsit kowa yaduk'ufa rubuta abinda yasani"yyinda barira gabanta keta fad'uwa sbd ba duka ta iya amsoshinba"nurr na lura da ita saida tagama tukun"taciri gefen Question paper d'in ta rubuta Mata kamar haka *ki kwafi inda baki ganeba"amma kibi asannu sbd sir* Tana rubutawa ta faki idonsa ta ajiye kan cinyar barira.ajiyar zuciya barira ta saki tana k'ok'arin d'an kwafan abinda zata iya sbd tana tsoron Kar sir faruq yaganta... ************** Alhassan kuwa yakasa samun nutsuwa akan soyayyar nurr .balle yanzun yadda yaga kyanta ya bayyana.tazama cikakkiyar budurwa.gefe guda Kuma har yanzun Yana barikinsa"sbd yanada yawan buk'atar mace.amma iyayensa sunk'i mishi aure sbd sunfiso yagama karatunsa.duk abinda sir faruq yamasa bawai mantawa yyiba"yabarshine saiya mallaki nurr sannan yamaida mishi da murtani.sbd Saida yyi bincike yagano ashema yasan sir faruq d'in. Da wuri yashirya ya nufi anguwarsu su nurr"aka kuwayi sa'a baffa ado na nan lokacin daya aika amishi sallama dashi.. Baffa ado cike zumud'i yafito k'ofar gidan"alhassan yarusuna Yana gaidashi"baki washe yace"ah ah tashi tashi"dama Kaine ke tafe?ai nuratun ma tatafi wannan k'addarar rar makarantar ta boko.alhassan yace"bbu komai baba ga wannan ayi cefane....zaro ido baffa ado yyi sbd uban damin kud'in da alhassan yamik'o mishi"hannuwansa na kirma ya amsa Yana cewa ayi haka kaikuwa?bbu komai baba indai zaka bani dama na auri nurr" ashirye nake danamaka abinda yafi wannan ma.bakada matsala yaro nabaka nuratu har abada katuro magabatanka"nagode baba "Amma inaso kayiwa wannan saurayin nata mgn yadena zuwa gunta...yo ai bana zaton sonta yakeyi ai malamin sune aboko...d'an Jim alhassan yyi Yana tunani"saikuma yace"amm baba yanzun inaso mudaidaita kanmu nida ita tukum saina turo magabata na.baffa ado yace"hakan yyi kyau"yanzun anjima saika dawo tad'i ko? alhassan na murmushi yace" to baba nagode.sallama sukayi ya wuce da nufin yadawo anjiman...baffa ado yashige gida cike da farinciki"Amma har ransa yanajin shakkar sir faruq, musammun akan abinda yayiwa alh tukur"hakan yasa shi jin tsoro ,yanzun ko dukan nur yadena.yanajin bazai iya yiwa sir faruq mgn ba wai yadena zuwa gun nurr... Su nurr kuwa itace tafara submitten"sir faruq yasakata ta k'arb'i nakowa"shikuma Yana zaune yanamata kallon k'asan ido"komai nata burgesa yakeyi"atsarinsa bayason farar mace irinsa"gashi ita black beauty ce"yalura nurr Bata cika yadda suna had'a ido dashiba"koma sun had'an zatayi saurin d'auke kanta"Yana lura da ita sai idan Yana latsa waya ko Yana note jikin Allo take kallonsa.kunyarta da kawaicinta had'e da batada son abin duniya"sunfi komai burgesa sosai ahalayenta"ayanzun haka soyake da anyi hutu suka dawo last term sukayi exams d'in shiga SS 3 zai maida ita private skul ta Ida SSCE d'inta acan...kallonta yyi lokacin dayaga saura mutum 1 zata bada paperta duk sauran members d'in class sunyi submitten sun fita.satar kallonsa tayi..caraf suka had'a ido"murmushi suka sakarwa junansu atare.bayan ta gama karb'a tace"sadaukinah gashi !konakaimaka office?saina wuce gida..um um tare zamuje namaidake da kaina...turo baki tayi cike da shagwaba tana nok'e kafad'ar ta tace".wlh anfara samana ido dg y'an anguwarmu har y'an skul d'in nan...tab'e baki yyi had'e da cewa susuka sani"bana tsoro ko shakkar kowa idan natashiyin abu.duk Wanda yafassaramu da wani abu"damuwarsace"hakane sadaukinah Amma pls kabarshi nahau adaidaita Mana"nagama mgn my Nurr nizankaiki gida na ajiyeki titin farko kafin ashoga layinku"is okay?to sadaukinah nibazan yi musu dakaibah"yauwa my nurrinah!Amma meyasa yau bakice nayi kyauba?"yafad'a fuska bbu walwala.kallonsa tayi"dariya ta tuntsure da ita" har fararen hak'oranta suka bayyana.yana kafeta da ido Yana kallo"cike da burgewa"hmmm! sadaukinah banace kafi kyau da manyan kayaba?shine yau kasaka k'ananun Kaya ko?"my Nurr nafasa sakasu sosai awannan satin"gara nad'an sabinta ko kuwa?hakane Kuma"suma ai sunamaka kyau k'ananun Kayan"kinsan wani abu?batare data kallesa ba tace".ah ah"nabada Mana d'inki nidake na shadda" sadaukinah baka gajiya da kashe kud'i wlh"indai akankine Zan iya kashe konawane.murmushi kawai tayi"sbd ita azatonta bawai iri d'aya yabada ba ad'inka.shikuwa iri d'aya yabada ,ita doguwar riga.. Fitowa sukayi dg class d'in"duk skul d'in anwatse kowa yatafi gida"sai jefi jefin mutane kawai.. office nashi suka wuce ta rakashi ya ajiye papers d'in"kafin suwuce bakin get suka shige motarsa...saida suka hau kan titi yace"my Nurr dame dame kikeda buk'ata ne? girgiza Kai tayi had'e da cewa bana buk'atar komai wlh.sadaukina bansan dame zan sakamaka ba?" akan d'awainiyya da kulawa da kakeyi dani..karki damu my Nurr kinji"yau zakije islamiyya ne?eh zanje insha Allah"okay"idan wannan yaron yazo gunki bance kifitaba"to insha ALLAH namaka alk'awari.. gsky week end zanzo nakaiki wani shago amiki lalle"inaso naganshi ahannunki"kinji?to za'amun tunda kanaso"tafad'a tana murmushi"parking yyi agefen titi"ta fito Yana cewa ki kunna wayar my Nurr kinji?jinake kamar karki tafi..nima haka sadaukinah"kibari Zan kamiki babbar waya mudinga video call"kamar tayimishi gaddama"saita tuna ai bayaso.hakan yasa tayi shiru kawai"kikulamun da kanki my nurr"to sadaukinah Allah yatsare hanya.ya amsa da ameen Yana kallonta"harta b'acewa ganinsa.. Koda ta Isa gida"bacci ta kwanta sbd lokacin 12 tunda exams akeyi da wuri aketashi skul..sai 1:30 tafarka"wanka tayi da sallah.kafin ta share d'akinta"taci bread da kifin gwangwani ta kora da fanta"duk acikin kayan da sadaukinta ke siyamata..doguwar riga tasaka ta feshe jikinta da turaruka"ta zauna tana karatun exams...baffa ado yashigo d'akin Yana cewa ke maza tashi kije ga alhassan can"yazo kugaisa dashi,shine nazab'a miki amatsayin mijin aurenki"d'ago kanta tayi ta kallesa"tanajin Bata tab'a jin tsanarsa ba irin yau"gsky baffa saidai kayi hakuri Amma bazan fitaba.tunda banasonshi to akanme Zan b'ata mishi lokaci? kutumar ubancan!ke kin Isa nace Abu kimusamun ko?to dan ubanki Baki isaba wlh"Dole kije ko kinaso ko baki so"Yana fad'in hakan yafice dg d'akin Yana cewa bara nadawo nasameki ad'akin nan...tana ganin yafice tasakawa k'ofar net d'in sakata.tayi zamanta" Baffa ado kuwa fita yyi waje yasami alhassan dayazo tun d'azun.yace mishi gatanan zuwa" Saidai lokacin da yaga bbu ita bbu alamar fitowarta yasakashi fitowa Afusace yanufi"k'ofar d'akin"saidai yajita arufe"cikin b'acin rai yace"ke y'ar iska wuyanki yyi k'wari ya Isa yanka ko?shine kikeyin musu Dani"wlh koki bud'e k'ofar d'akin nan kokuwa ninasan mezan miki..kaga shegiyar yarinya,shi waccan baturen dakika k'wallafa ranki akanshi inda gaske yakeyi yafito yafad'a Mana..uffan nurr batace ba"ak'ule baffa ado yace"bara naje nadawo yanzun"nazo na balle k'ofar naga ta k'aryar iskanci.yana fad'in hakan yajuya ya bar gidan.awaje yabawa alhassan hakuri akan yak'ara jira.alhassan kuwa duk yak'agu yaganta.yace"to shikenan Yana jira"saima gyara zamansa yyi akan dankalin k'ofar gidan. Nurr kuwa kuka tafashe dashi"tarasa meyasa baffa ado kemata haka?gashi har 3 tayi sotake 4 ta wuce islamiyya"yanzun idan ya b'alle Mata d'an net d'in dashine rufin asirin d'akin tayi Yaya?wayarta dake ringing ta katse mata tunanin ta.. *sadaukinah* d'agawa tayi tana sakarmishi kuka...my Nurr lfy kisanarmun meke damun ki??yanzun nan naji gabana yafad'i Dana tunaki ,shine nace bara nakira"agajerance tasanar mishi alhassan yazo Yana waje"Kuma baffa ado yanzun zaizo ya b'alle k'ofar d'akin" yadaketa sbd tak'i zuwa gun alhassan..kinutsu my nurrinah bbu abinda zaimiki ganinan zuwa yanzun gidan naku..share hawayenta tayi had'e da cewa to shikenan.amma sadaukinah karkayi fad'a da alhassan ko baffana"kaji Dan ALLAH?"karki damu my Nurr"Yana fad'in hakan yakashe wayar.... k'ok'arin ajiye wayar takeyi taji sallamar wasu mata"nacewa Wai bbu kowa agidan anata sallamane?"mik'ewa tsaye tayi sbd hango Nisaibah datayi itada wata matsa suna jifar tsakar gidan da kallon wulak'anci"hakan Kuma yayi daidai da shigowar baffa ado.wanda da zarto ahannunsa sbd yab'alle k'ofar...✍️ [9/9, 2:08 PM] Maman Nasreen: .....Afirgice nuratu tayi saurin bud'e k'ofar sbd gudun karyayiwa net d'in illah"kinganta can mommy"cewar Nisaibah tana nuna nuratu da yatsa.bayin Allah suwaye kune?"baffa ado yafad'a Yana kallon su"wani banzan kallo na raini da wulak'anci mommy tamishi tana yatsina.kafin ta had'e fuska tace".nice mahaifiyar faruq malaminsu wannan kazamar y'ar taka...wani mugun fad'uwa gaban nuratu yyi"cikin tashin hankali tayi baya ta koma d'akin"Nisaibah taja tsaki had'e da cewa munafuka aida kinfito manah.bewar Allah inason jin dalilinku nazuwa gidana"baffa ado yafad'a cikin mamakin nusaibah nazagin nuratu datayi...wanikallon rainin wayo mommy tayiwa gidan.kafin tace"wannan kangon shine gida?to bara nafad'a maka da babbar Murya"ruwa basa'an kwando bane"Kuma wutsiyar rak'umi tayi nesa da k'asa wlh"munfi k'arfin had'a zuri'a da irinku matsiyata"kajawa y'ar ka kunne"tarabu da d'ana bbushi bbu itah har abada... wannan wane irin rainin hankali da wulak'anci ne?ku dabbobin inane dazaku shigo gidan mutane Kuna wannan burgar?"cewar goggo kande amatsife tana fitowa dg cikin d'akin ta.baffa ado yaji dad'in abinda tace sbd shi yakasa cewa komai.sai kallonsu kawai yakeyi.idan kin Isa dashi d'an naki shiya kamata kijawa kunne bamuba ko?tsaki mommy taja had'e da cewa kekuma asuwa?Kuna fama da bak'in talauci d'aya muku Kant....matsowa kusada ita goggo kande tayi tana cewa"kinci kanbura ubaki"idan banmiki shegen dukaba"kice Nina y'a bace.nadakeki nadaki banza sbd gidana kikazo.kufice. Kubawa mutane wuri"Allah yarabamu da irin arzik'inku naciwa mutane zarafi.k'ilama inza'a bibbiya kud'in naku Bata hanyar halak kuka samesuba" Gaba d'aya mommy shiru kawai tayi, sbd batayi zaton za'a musu hakanba.nur dake d'aki tana sauraron komai sai kuka takeyi"yyinda baffa ado yamaidasu kamar TV" saida yaga goggo kande ta Kai aya alafazinta tukum yace"kufita kubawa mutane guri.tsaki Nisaibah taja had'e da cewa mommy muje zasu gane kuransu wlh.kudai gane kuranku y'an wahala"cewar goggo kande tanajan tsaki,yyinda mommy taja kwafa had'e da cewa kundaiji abinda nafad'a muku?muddin bata rabu dashiba"tokuyi kuka da abinda zai biyo baya..tana fad'in hakan suka fice dg gidan... Alhassan kuwa har yanzun Yana nan zaune kan dakali"suna fitowa sir faruq nakawowa ...wani mummunan fad'uwa gaban sa yayi"arikice yanufesu Yana cewa mommy mekukaje yi gidansu nurr?"tsaki taja had'e da cewa bbukai bbu talaka har abada"wuce muje banyarda kasake zuwa gidan nanba ko zuwa gunta.idan hakan yafaru banyafe makaba.... innalillahi wa inna ilaihir raju'un"ya fad'a arud'e Yana runtse ido.mommy kinsan mekike fad'a kuwa?bansaniba "zaka wuce muje ko kuwa? alhassan dake zaune Yana sauraren komai yakece da dariyar mugunta Yana tab'e baki.wata iriyar zuciya tazowa sir faruq iya wuya.k'ok'arin nufar alhassan yakeyi.. mommy ta ruk'osa da sauri"tana cewa bakaji mena fad'a maka bane?"adedenan Kuma baffa ado yafito dg soron gidan Yana rik'e da hannun nurr daketa kuka shab'e shab'e da hawaye.gabanta yakoma fad'uwa sbd ganin sir faruq"yakafeta da ido babu ko kiftawa. Jitake abun kamar amafarki ne ba gaskeba... b'ata tab'a zaton haka iyayensa sukeba"azatonta suma masu kirkine irinsa"zaka wuce muje ka tsaya kana kallonta.kasani bazan canzaba"muddin kazo inda take kokulata banyafe makaba...zaro ido nurr tayi cikin tashin hankali tana k'ok'arin barin wurin"baffa ado yace"gidan uwarwa zakije? alhassan yayi saurin cewa"ah ah baba barta ta tafi ko ranta yadena k'unci"zuwa dare insha Allah zandawo gunta fira...sakar Mata hannu baffa ado yyi"da gudu nurr Takoma cikin gida tana kuka..sir faruq kuwa jiyakeyi tamkar alhassan yawatsa mishi wuta akan kalamansa ga nurr"zare hannunsa da mommy tarik'e yyi yabar gun da k'yar. zuciyar sa na wani irin k'una"ya wuce inda yayi parking motarsa" Suma su Mommy gun tasu motar suka wuce"yyinda baffa ado yatsaya suna mgn da alhassan... Nuratu kuwa d'akinta tashige tafad'a kan katifarta tasaki kuka mecin rai"meyasa sadaukinah kashigo rayuwata?bacin kasan mahaifiyarka bata k'warai bace"bazan iya jure rashinkaba sadaukinah! Allah yasa mafarki nakeyi bagaske bane...duk tafad'a afili tana kuka.baffa ado yashigo gidan Yana k'wala Mata kira"banza tamishi tana cigaba da kukanta"yyinda goggo kande ta fito"tana kallonsa tace"nagaji da mugun halinka wlh"asanadin k'wadayinku kaida y'ar ka kunjawo anzo har gida za'a cimana mutunci ko?"Allah yawadaran kwad'ayi wlh...tana fad'in hakan ta wuce d'akin ta.baffa ado yaja kwafa had'e da cewa zanyi maganinki kema... d'akin nurr yanufa yasameta tana kuka"Dan uwarki akansa kike kuka sbd bakida zuciya ko?banza tamishi"to Bari kiji ko kukan jini zakiyi bbuke bbushi"sannan aurenki da alhassan Dole ne.sbd haka kishirya da dare zaizo tad'i agunki"Yana fad'in hakan yajuya ya fice.jitakeyi kawai gara ta mutu kota huta da wannan masifar datake ciki" *hasbinallahu wani imal wakeel* Taketa ambata aranta"tana sakin ajiyar zuciya"Kiran Sallar la'asar yasakata tashi tafito ta wanke fuskarta tayi alwallah.. Sir faruq !inbacin tsaron ubangiji dayyi accident"gaba d'aya tamkar bashiba haka yakejin kansa.ga wani abu daya tsaya mishi azuciya daya tuna Wai alhassan zai dawo anjima gun nurr"ga zafin mommy zata mishi baki"wani tsanar Nisaibah yaji da mugun k'inta.sbd yatabbatar da cewa itace ta sanar da mommy komai akan nurr"saidai yyi mamakin ta Yaya suka gano gidansu nurr d'in?tausayinta yaji sbd yatabbatar bak'aken maganganu tafad'a musu"tunda yaga nurr d'in nakuka sosai"gabansa yaji yafad'i"daya tuna tace bbushi bbu talaka"afili yace"kotana nufin son nurr nakeyine?yatambayi kansa yanajin fad'uwar gaba.ga wani gudu dayakeyi asaman titi..gaba d'aya tunanin sa yararraba"hakan yasa direct yacanza akalar motar "zuwa gidansu mubarak sbd yasamu mafita"tunda bashida wani amini ko abokin daya wucesa.. Mubarak na zaune a haraban gidan su"kan resting chair"yaji ana wani mugun horn"kallon get d'in yyi lokacin dame gadi ke bud'ewa sbd yaga wace mota zata shigo....mamaki sosai yyi sbd ganin motar sir faruq ta shigo da wani irin mahaukacin gudu...da ido yabishi sbd ganin yafito dg motar ko rufewa beyiba"kallon d'aya yamishi yagano Yana cikin damuwa da tashin hankali...tashi tsaye yyi yanufesa.yana cewa abokina lfy daiko?"girgiza mishi kansa yyi had'e da cewa muje d'akinka.bbu musu suka wuce d'akin Mubarak d'in. bayan sun zauna, Mubarak yadubesa yace"abokina lfy?kamun bayani Dan Allah naga alamar damuwa aranka...cikin wani yanayi sir faruq yace"tayaya ake gane SO?sosai abin yayiwa mubarak dad'i"dama wannan ranar yake jira.amma bara yagaya Masa"yaji damuwarsa ,tukum sai yamishi shegantaka.abokina manyan alamomi na SO asanina 3 ne.amma sunada yawa sosai da sosai.na farko *kishi* Kaji kana jin haushin ganin wacce kakeso da wani ko Kuma ,taji haushin ganinka da wata idan yariya kesonka.. Na biyu *fad'uwar gaba* Idan kaganta /kota ganka zataji fad'uwar gaba sosai.sai na 3" *gudun b'acin ranta /ko gudun b'acin ransa dason kyautatawa Wanda kakeson sbd kagansa cikin farin ciki.kuma kak'i me munana Masa.* Iya sanina wad'an nan sune manyan alamomi na mutum yakamu da SO! wata iriyar ajiyar zuciya sir faruq yasaki"aransa Yana cewa wato yanzun shi son nurr yakeyi kenan?sbd abinda mubarak yalissafo mishi.dukansu yanaji game da ita.harda masu abubuwan"to ita nurr d'in tanasonshi ko kuwa?"yatambayi kansa...waimeke damunkane? Mubarak!Ina cikin matsala da damuwa.intak'aita maka zance"mommy tamun baki akan nasake zuwa gun nurr"bata yafemunba! yafad'a Yana runtse ido.innalillahi wa inna ilaihir raju'un! Mubarak yafad'a arud'e"kallon sir faruq yyi yace"tayaya kabari Mommy tasan Kuna tare da ita? wannan y'ar iskar yarinyar Nisaibah Mana"itace tasanar Mata sbd d'azun da safe taje skul d'in.tasamemu Muna tare da nurr.gsky bata kyautaba"gashi na lura yanzun kundena fad'a da nur d'in ko? Hmmm!abokina menene mafita yanzun?bansan Ina zansaka rainaba"idan nakwana banga my nurr ba"kobanji muryartaba nikawai nasan yanakeji.yafada Yana dafe kansa"Mubarak yace".ni aganina kayiwa mahaifiyarka biyayya hakan kawai zafe...cikin wani yanayi yafara bashi labarin rayuwar nurr"dason abin duniya irin na marik'inta baffa ado"dakuma alhassan ayanzun dayadawo Yana son ya aureta.bacin abaya yayi k'ok'arin b'ata Mata rayuwa Allah be bashi nassaraba...sir faruq yak'are zancen da cewa"damuwata shine takasance tare da d'an iskan yaron nan (alhassan) sannan bbu wani namijin da ya Isa *ya auri nurrinah sai ni sadaukinta* Sosai mubarak yagimtse dariyarsa"bansan inayiwa yarinyar nan mahaukacin soba sai yanzun daka sanarmu taya ake ganewa"meye mafita pls?"ajiyar zuciya mubarak yasaki"kafin yace"ni aganina barin gidan k'anin mahaifinta shine mafita babba"sbd kaga zata gujewa auren abokin takarar ka(alhassan) sannan tunda basonshi takeyiba zata zama acikin damuwa 2"anrabata dakai,an aura Mata Wanda bataso.gashi Kuma mommy tace karta koma ganinka da ita.dasai kayi wani abu akai.ajiyar zuciya sir faruq yasaki Yana tunanin Anya zai iya furtawa nurr kalmar yanasonta?tana amatsayin d'alibarsa..kayi shiru bakace komaiba!cewar mubarak cike da tausayawa abokin nashi"ajiyar zuciya yasaki kafin yace".inaso yanzun ka kira nurr kace Mata nace ta had'a kayanta duka ta tafi gidan kakarta. zan turaka kayi komai bbu abinda zai faru.bazata auri alhassan ba..Mubarak yace".okay bani number d'in ta.. Bayan yasakamishi number ta"nurr na zaune tayi tagumi"taji wayarta na ringing"da sauri ta duba sbd azatonta ko sadaukinta ne.saitaga bak'uwar number"kamar kada ta d'aga tadai daure ta d'auka tana sallama"muryar sir Mubarak taji.hakan yasa ta nutsu yamata bayanin komai"ta amsa cike da gamsuwa da bayaninsa.hawayenta ta share"tanajin zafin baffa ado dashine sanadin komai.tashi tayi ta had'a duka kayanta a cikin Ghana"tad'auki duka takalminta da hand bag nata guda 2 da sir faruq yasiya Mata tasaka awata leda VIVA"katifarta kawai ta bari da tabarma"hijab tasaka ta fito tsakar gidan taji k'arar ruwa abayi"da alama goggo kande wanka takeyi"yyinda d'akin baffa ado arufe"da sauri tasaka kwad'o ta rufe k'ofar net d'in bayan ta fito da kayanta duka atsakar gidan.asoro ta had'u da wani almajiri"tabashi ghanar yad'aukar mata"ita Kuma ta d'auki leda viva suka nufi bakin titi.cikin sa'a tasami nafef"50 nera tabawa almajirin bayan tashiga nafef din.suka wuce anguwar kawo... Sir faruq kuwa Yana ganin mubarak yakashe wayar yace"tashi muje muyi sallar la'asar muwuce police station.zaro ido Mubarak yyi had'e da cewa bangane muje police station ba?kaidai kazo muje plaine zamu had'a da inspector Salim"yabika kuje gun baffanta. atsoratar dashi akan za'a rufesa koyabarta tazauna agidan kakarta" ta zab'i Wanda takeso ta kawoshi ya aura Mata..akan hujjar beciyar da ita kotufatarwa ko nema Mata ilimi"akan me zai Mata auren Dole?wannan hujjace Mai k'arfi.kuma ma Wanda yakeso ta aura ba mutum ne na gariba. Mubarak yace"gsky wannan itace kawai mafita abokina.fatana Allah yasa ita nurrin taka tana sonka....Kuma Allah yasa mommy ta janye bakin data maka saikaje kusasanta kanku.wani banzan kallo sir faruq yamishi Yana cewa d'an iska kawai.dukda suna cikin yanayi narashin jin dad'i saida Mubarak ya murmusa... Bayan sun gama sallar la'asar suka wuce police station d'in...sosai suka tsarawa inspector salim yadda komai zai kasance"kafin su tafo gidan baffa ado su hud'u"inspector salim,Mubarak da wasu y'an sanda 2.yyinda sir faruq ya wuce gida da nufin duk yadda akayi to Mubarak yakirashi yasanar mishi... goggo kande data fito dg wanka taga d'akin nurr arufe"saitayi zaton islamiyya ta tafi"har 6 ta wuce bata dawoba"hakan Kuma bedami goggo kande ba,tanata hidimarta" Tamkar anjohosa haka yashigo gidan yanata tsami da k'arin rana"kallo d'aya goggo kande ta mishi ta d'auke kanta"Wai yarinyar nan batadawo dg islamiyyar bane?banza goggo kande ta mishi..Yana k'ok'arin mgn yaro yyi sallama yace".Wai ance ana sallama damai gidan..suwaye ne?"cewar baffa ado azatonsa k'ila ma alhassan ne.wasu y'an sandane!me? yafad'a Yana zaro ido"goggo kande tace"kwad'ayi mabud'in wahala"Kai yaro jekace baninan..Kai kace musu Yana nan"cewar goggo kande.yaron kuwa yafice"baffa ado da gudu ya wuce bayi sbd cikinsa yajuya...Yana fitowa yasami yaron yadawo"Kai wai ubanme sukace ne?sunce inhar ka wuce minti2 baka fitoba zasu shigo sutafi dakai..wani mugun tsoro da fad'uwar gaba baffa ado yaji"jikinsa na kirma yafice Yana zare ido. Lokacin da Mubarak yahangoshi sai yasake tamke fuska sosai...bayin Allah Lfy kuke nemanka?"cewar baffa ado Yana tsaye bakin k'ofar shiga gidan" Mubarak yadubesa yace"sunana Mubarak!ni malamin su nurr ne a islamiyya.(yyi k'arya) Muna lura da ita tana cikin damuwa da rashin walwala"ayau mukaga abun yafi na kullum.shine muka tursasata tasanar Mana"shine bayan tasanar Mana" mukazo anan anguwar muka bincika domin gano gaskiyar abinda kake aikatama marainiyar Allah.kuma duk mak'otanku sun bada shaida...inkana yiwa Allah kayi hakuri! natuba nabi Allah..yafad'a sbd yasan yyi duk jama'ar anguwar sun san Yana zalintarta.yimana shiru!cewar inspector salim"tafiya zamuyi dakai"abima yarinya hakk'in ta"kanaso kamaida ita karuwa sbd takamaka kud'i ko?sbd kana tsohon banza"ga yaro ba mutimin kirkiba kanaso ka aura matashi sbd kaga kud'i ko?wlh bahaka bane"Ina ita nuratun take Dan Allah Zan gyara mugun halina karku kulleni a ofishinku Dan Allah..yaduk'ana Yana basu hakuri... Mubarak kuwa tamkar yyi dariya. yanata yiwa abokinsa recoding d'in duk maganar dasukayi da baffa ado...yyinda su salis me tireda shida abokansa suketa kwasar dariya dg nesa.wasu Kuma sunyi tsaye suna kallon me akeyi...Mubarak ne yace"ya Isa katashi muyi mgn"jikinsa na kirma yatashi Yana cewa to inajinka wlh.zamu k'yaleka!Amma da sharad'i"jiki na kirma baffa ado yace"nayarda dakoma wane sharad'ine"yafad'a cikin tsoro sbd be manta sadda sir faruq yasaka aka Kama alh tukur ba.kuma yanada kud'i,to balle shi talaka"k'ilama sudake sa acan station d'in... Mubarak yace"nabawa nuratu umarnin data koma gidan kakarta dazama tabar hannunka"sbd bincike yanuna ko iyalanka baka d'aukar nauyinsu ,balle ita"Abu nakarshe bbu maganar katakura akan Mata auren dole. Kabari tazab'i Wanda takeso takamaka ka aura Mata shi....wlh tallahi na amince zanbi umarninku y'allabai"tab'e baki sir Mubarak yyi kafin yace"dg k'arshe Dole kasanar wa alhassan yanemi wata sbd batasonsa.... inspector salim ya karb'e zancen da cewa idan bahaka ba kuwa hmmm!Yana fad'in hakan suka wuce batare da sun sake bi takansaba..ajiyar zuciya baffa ado yasaki Yana hararan wasu yara dake tsaye suna kallonsa.gida yakoma Yana tsinewa nuratu aransa"goggo kande daketa kaida kawowarta bema isheta kalloba... suna isowa police station d'in suka sami sir faruq acan "sbd Mubarak yakirashi yace su had'e acan....lokacin dayagama sauraron recording d'in"yasaki ajiyar zuciya cike da tausayin nurinsa"yanaji Anya gobe zaije skul nasu kuwa"sbd bazai iya ganinta yak'i kulata ba"dukda bama a aiki exems sukeyi.mubarak yadafa kafad'ar sa"yace bara idan naje anguwar kawon nakira ta ta Mun kwatancen gidan. [9/9, 2:08 PM] Maman Nasreen: .....Wani irin mugun fad'uwa gaban ta yayi"atake ta had'e ranta tana jifansa da wani irin kallo....shikuwa murmushi yyi Yana Zama kan dankalin k'ofar gidan"miye yakawoka k'ofar gidanmu?abinda nuratu ta fad'a kenan tana janye idanunta dg barin kallonsa.fatanta yayi gaggawar barin wurin kafin sadaukinta yazo yanzun yasameshi."talura yayi mugun canjawa"hutu had'e da wayewa sun zauna ajikinsa...bak'onka annabinka nuratu!banyi zaton har yanzun kina akan bakanki natsanata ba"Amma wlh kina araina har gobe inasonki"SO bana wasaba"SO na aure nake Miki nuratu.nayi nadamar abinda na aikata agareki kiyi hakuri pls&pls!!kaga kadena maido mun abinda yarigada ya wuce Allah yashiryamu gaba d'aya"zaka iya tafiya nizan shiga cikin gida.maganar SO atsakanin mu bbushi har abada"bazan iya auren wanda yayi k'ok'arin cimun zarafi ba...pls nuratu jiyafa nadawo Amma wlh naji bazan iya jure rashinkiba.sainazo naganki zansami sukuni araina....d'ago kanta tayi da nufin ta mishi mgn suka had'a ido da sadaukinta dake binsu dawani irin kallo...Yana nufosu..wani mugun bugawa k'irjin ta yyi"da sauri ta nufesa kafin yak'araso gurin... alhassan kuwa kallonta yyi yaga tana k'ok'arin zuwa gurin sadauki"da kallo d'aya yamasa yasan akwai inda yasanshi.da ido kawai yake binsu , still Yana zaune kan dankalin. sadaukinah!banason ji komai"waye shi zakifad'an kawai?"labarin nada tsayi dan Allah karki fushi kaji sadaukinah?takarashe maganar tana langab'e kanta"my Nurr kinsan bazan iya juran fushi dakeba ko?maimakon Kuma kidinga kiyaye b'acin raina"wlh bansan shibane yazo fa"azatona kaine!sbd bayan mungama waya ya Aiko kirana.yanzun ma nafad'a mishi yayi tafiyarsa ne... menene tsakanin ku? *sona yakeyi* wani zafi sosai yaji kalmar ta mashi"besan lokacin dayaja tsaki ba. yawuce ta, yanufi gurin dakalin inda alhasan ke zaune Yana latsaya waya"dukda abad'ini hankalinsa na gunsu"ransa yabashi tabbas wancan saurayin nuratune...sadauki karka kulashi pls! tafad'a ahankali tana biyosa abaya...yyinda salis me tireda da wani abokinsa suna zaune suna lura dasu dukda basujin mesuke cewa ba. Hii!cewar sir faruq fuska bbu annuri"banza alhassan yamasa , yad'ago kansa Yana kallon nuratu dake nufosu.my sweet heart yakamata ki sallamesa kizo mu Ida maganar mu... alhassan yafad'a Yana wani hura hanci had'e da basarwa" what's?sir faruq yafad'a da k'arfi Yana zaro ido"nibbu wata magana dazamuyi dakai"kab'ace Mana dg nan.kuma karka koma kirana da sweet heart d'inka.cewar nurr tana hararar sa"tashi tsaye yyi Yana kallon sir faruq ido cikin ido yace"mlm Ina ruwanka danine?nuratu tawace nikad'ai !bbu Wanda ya Isa yarabani da ita"Koda ita dakant....wata wawar shakuma sir faruq yamasa da hannu guda Yana huci"Murya akausashe yace"maimaita mun abinda kace...sadauki sakesa pls"kaga da jama'a masu saka idanuwa dan ALLAH.nuratu ta fad'a tana tsaye abayansa..banza yamata saima sake shak'ar wuyan alhassan yyi"alhassan kuwa tari yafarayi"yyinda idanuwan sir faruq sunji jajir sbd b'acin rai da zuciyar data taso mishi iya wuya...nashiga ukku sadauki kasakesa pls.tafad'a da k'arfi.kallonsu salis tayi da sauri ta matsa tana k'ok'arin musu mgn.suka taso da sauri"dan Allah kurabasu salis.. tafad'a tana fashewa da kuka.sbd ganin kusan mutum 5 suna kallonsu.. k'ok'arin rabasu akeyi amma yak'i sakinsa.yanata faman maimaita kalmar zaka koma zuwa gunta?"wai hayaniyar menake jine haka ne "ana k'ok'arin Kiran magrib?cewar baffa ado daya fito dg soron gidansa yalek'o waje.innalillahi wa inna ilaihir raju'un!kaikuwa meyayi zafi?kisan Kai zakayi Mana kome? "nuratu na kuka tafara k'ok'arin matsawa dab da sir faruq har jikinsu nagugan juna tace"tunda bazaka sake shiba kayi yadda kakeso.tana fad'in hakan ta juya da nufin ta tafi gida"dukda kawai tafad'a ne bazata iya tafiyaba"sakinsa yyi yahankad'asa.su salis suka rik'e alhassan sbd ganin zai Fadi k'asa.baffa ado kuwa yagane alhassan.sannan wani mugun tsoron sir faruq yakamashi..nurr karki tafi zokiji!tana share hawayenta ta tsaya cak abakin k'ofar.baffa ado dake binsu da kallo ya wuce cikin gida da nufin idan tashigo yatambayeta wanda kesonta yaturo. tunda yalura sunada kud'i.shi indai za'a bashi kud'i bbu abinda yadamesa... Alhassan kuwa janye jikinsa yyi dg gurinsu salis"sukuma suka koma inda suke zaune. yanajan tsaki"yamaida kallonsa ga sir faruq dake k'ok'arin tsayawa kusada nur"hmmm idan da zaka burgeni shine kayi abu 2"sannan insan ka Isa namiji"na farko shine daka kasheni baka barni da rainaba.na 2 shine acikin satin nan ka aureta.inkayi hakan sannan zansan Kai namijin duniyane.nuratu kuwa baka isa karabani da itaba wlh"ko ita kanta da iyayenta basu isa sura bani da itaba.balle Kai! wani murmushin takaici sir faruq yyi"kafin yace"nafi k'arfin yin jayayya dakai"domin inkaga antsaya ana jayayya to k'arfi yazo d'aya kenan.magana guda my Nurr tamaka nisa...and last kabar gun nan tun kana iya mgn cikin jin dad'i.kisa dakake mgn"ban iyashiba bazan Kuma Fara akankaba.tarbiyyar dabakada ita ! ita ta furta mgn itace nakoyar dakai"Yana fad'in hakan yadubi nurr daketa kallonsa yace"shiga ciki zanje nayo sallah"shagwabe fuska tayi had'e da cewa "amma zaka dawo ko?tsaki alhassan yaja yabar gurin, da k'udurin gobe zaidawo yasakarwa baffa ado kud'i.hakan kawaine mafita"aganinsa fa amma... zandawo Mana my nurr"gsky banji dad'in abinda kayiba sadaukinah"wai sai yaushe zaka Dena wannan halin naka ne dan Allah? zandena my Nurr"Koda yaushe haka kake cewafa"bazan komaba kinji?Amma banji dad'i ba"dakika tsaya dashi"to Wai wama kikayiwa wannan kwalliyar ne?sadaukinah kaimana"bakace nadinga shafa lipstick ba?shine nashafa makako?kin kyauta Kuma kinfi kyau sosai akan inbakiyi make up.kidingayi pls!amma nikawai zaki dinga mawa.to shikenan sadaukinah"my nurr wannan shine yaron dakika tab'a aiki agidansu last 3yrs?cikin zaro ido da mamakin ta Yaya yasani tace"eh shine !kwafa yaja Yana cewa jekiyi sallah! saina dawo..bejira cewartaba yawuce"ajiyar zuciya tasaki tashige cikin gidan..baffa ado dake tsaye Yana jiran shigowarta yace"ke acikinsu wake sonki da aure? gabanta na fad'uwa tace".bbu kowa"k'arya kike munafuka!duk Wanda yariga daya turo magabatansa shine zaki aura bbu ruwana dasai kingama karatu...kaji kunya wlh!sbd wannan zak'ewar dakakeyi badan Allah bane. sbd kasami kud'i ko?"cewar goggo kande data fito dg bayi zatayi alwallah.eh sbd kud'in Ina ruwankine?wlh zansakeki inkikayi wasa"bud'a goggo kande tayi"had'e da cewa"dakuwa nazuba ruwa k'asa nasha sbd murnan narabu da zalamamme me matacciyar zuciya irinka.ko yanzun sbd yarana 2 nake zaune dakai"Amma bacin wannan gidan damuke zaune cikinsa.bbu hanyar danake k'aruwa dakai...sai indare yyi kad'ebo k'azamin jikinka kanamun y'ar muryar nabaka kaina kayi....da sauri nurr tabar gurin ta nufi d'akin ta.tana musu addu'ar shiriya.sbd jin goggo kande naneman b'aro mgn babba.ruwa tazuba abuta ta cire kayanta tasaka wata doguwar riga ta atamfa roba .lokacin data fito bbu kowa tsakar gidan da alama sun gama fad'an su yafice dg gidan... Alwallah tayi Takoma d'akinta ta kabbara sallah"tana nan azaune aka Kira isha'i"baya tagama ta canza kayanta"wani gefen zuciyarta tana tuna maganganun alhassan *idan zaka burgeni ka aureta acikin satin nan* .....wayarta tayi ringing"taduba taga sadaukinah!sunan datayi seving number d'insa dashi kenan. ahankali ta d'aga tana mishi sallama"okay fafad'a tana kashewayar.tajawo net d'in k'ofar ta fice dg gidan... Yana tsaye bakin k'ofar shiga cikin gidan"yakunna fitilar wayarsa"Yana sanye da yadi ash colour na riga da wando.riga iya gwiwa"Masha Allah tafad'a aranta" sbd d'azun ma hankalinta ba ajikinta yakeba batama luraba da kayan jikinsa ba. Assalamu alaikum!wa'alaikissalam ya amsa Yana haskota"hannuwanta tasaka tana rufe fuskarta had'e da turo baki"sosai yaji ta birgesa"my nurr malamin naki kike turowa baki?to bakaine kajaba!danayi me?daka haskani mana"hmmm kin iya shagwaba wai?na iya Mana"to meyasa ni ba'amun? zandinga maka to"da gske ?eh"to shikenan gashi kije gida"inkingama abinda kikeyi kimun flashing saimuyi firan ko?"yafad'a Yana mik'o Mata wata leda"eh insha Allah"sadaukinah meye aciki?nidai banason Kanata wannan faman kashe kashen kud'in. Wanda kayi abaya ya Isa wlh"nide be isheniba my nur!ki karb'a inkuma kinfison b'atan rai shikenan"batace komai ba ta amsa badan tasoba.domin yanzun d'awainiyyar dayake Mata tafara bata tsoro.my nurr!yakira sunanta"menene?muryarta asanyaye tace"bbu komai"my Nurr nifa banida wani mummunan abu akanki sai alkhairi.banaso zuciyar ki ta sak'a Miki wani Abu daban"ahankali tace"na aminta dakai sadaukinah 100%...nima haka my Nurr"Amma zakimun shagwab'ar Taki naji" idan nakiraki anjiman?" Tana murmushi tace"eh manah"yauwa tawan , yanzun kishiga ciki saimunyi waya.godiya ta mishi ta shige cikin gidan" ruwa ta watsa tayi shafa'i da wuturi"tazauna dg ita sai vest da zani.kafin tajawo ledar ta bud'a"kazace gasassa da ice cream....kat ta zauna tayiwa cikinta.kafin taje tayi brush tadawo d'akinta.zama tayi zata mishi flashing suit d'in sa dake hannunta kusan 3 weeks tafad'o Mata arai.wayarce datayi ringing tadawo da ita dg duniyar tunanin datakeyi...tana murmushi ta d'aga sbd ganin sadaukinah akan wayar"ahankali tace"dafa yanzun zanmaka flashing d'in"my Nurr nima nagaji da jiran kiyo flashing d'in.nace gara dai nakiraki"hakane sadaukinah"Amma Dan Allah Yaya akayi kasan nayi aiki agidansu alhassan?hmmm!abin sirrine bazan fad'aba...niiiiidai Allah saika fad'a mun ko mu b'ata dakai"tafad'a cikin shagwab'a"lumshe idanunsa yyi"cikin wata iriyar murya yace"ai bazamu iya fushi da junanmuba my nurr"toba saina Fara yi dg yanzuba.nifa saika fad'amun tam"duk tana mgn ne cikin shagwab'a.ahankali yace". dama haka kika iya shagwab'a?Kuma Saida na rok'a za'a mun ma ko?"turo baki tayi had'e da cewa tonasan kobasonta ne?inaso my Nurr"yanzun idan muka had'u a skul gobe zakimun?"um um nidai inajin kunya wlh"hmmm! sadaukin naki kike jiwa kunya my Nurr?"eh mana"to yanzun nidai bazan b'oyemiki ba"nabinciko tarihirin rayuwarkine sbd banajin dad'i akan zaman dakikeyi gun baffanki Yana cutar dake.yanzun idan Babu damuwa zansan yadda nayi kikoma gun kakarki da zama.kinason haka?cikin farin ciki tace".eh wlh sadaukinah nagode sosai.yana murmushi yace"karki damu"yanzun bara nabarki ki kwanta Kar kiyi latti gobe idan Allah yakaimu.nifa bangaji da mgn dakaiba.saidai indai Kaine ka gaji d mgn dani.bana fatan hakan my Nurr"Yaya !Yaya !!cewar nusaiba tana shigowa parlourn"gaban nur yafad'i,batasan lokacin da tace"wacece sadaukinah kodai kanada matane??"sorry my Nurr zankiraki back!Yana fad'in hakan yakashe wayar yana hararan Nisaibah dake binsa da kallon sha'awa. tana hangosu amatsayin ma'aurata... ke!lfy zakizo yanzun har 10 ta kusa?daddy ne yace"nazo nasanar maka gobe kaciro Masa kud'i 200k ta bank" kafin katafi gurin aiki. Okay Zaki iya tafiya"batace komai ba tafice"saidai ranta yagama yadda nurr d'in nan budurwarce"da ita yakeyin waya"Dole tasanar wa mommy sbd tayi wani abu akai.gaba d'aya hangosa take kwance kan 3seeter Yana waya dg shi sai vest d boxer..ta lumshe ido tana ayyana yadda zataji dad'i idan ta auresa. Nurr kuwa zafi taji aranta sosai"dama yanada Mata betab'a sanar Mata ba"wata zuciyar tace"to ke Ina ruwanki da matarsane?meye naki najin zafin.... ringing d'in wayar yakatse mata tunaninta.kamar kada yad'aga tadai daure ta d'auka. My nurr kina jina?" "Uhumm! kina tambayar inada Mata ko? Da sauri tace".eh" Yana murmushi yace".ah ah nibbu wata macen Dana tab'aji ta burgeni saike kawai"yarinyar nan dakikaji ta kirani da Yaya"kanwata ce uwa d'aya uba d'aya.ajiyar zuciya tasaki ab'oye"kafin tace".hmmm!nikawai ma ke burgeka to meyasa? nima bazan iya ganewa ba my nurr!Wai sadaukinah kana nufin bakada budurwa? tafad'a tana dariya k'asa k'asa.hmmm Allah yakyauta mun yin wata budurwa.wannan sai Mubarak(sir Mubarak) to meyasa sadaukinah?bbu komai my Nurr"kokinaso nayi budurwar?hmmm kabari sai lokacin dakamun aure saikayi taka budurwar...gabansa yaji yafad'i sosai ,ga haushi yaji na maganarta.wanda yarasa dalilin jin hakan.sadaukinah !uhumm inajinki my Nurr"aure kikesone?lahh nifa wasa nakeyi bayanzunba.ah ah inkinaso fad'amun naji waye saurayin naki ko?"yafad'a Yana jin fad'uwar gaba.fatansa tace". bbu saurayin datake dashi.cikin turo baki tace".nima kamar yadda bakada budurwa to nima Banda saurayi..to shikenan hakan yafimana ko my Nurr? eh Mana"yanzun Kinga 10 ta wuce da asuba zankiraki kitashi sallah.to sadaukinah nagode.karki damu kikularmun da kanki"insha Allah"tafad'a tana kashe wayar. Ajiyar zuciya yasaki"Yana tunanin abubuwa masu yawa dayakeji ko yake tsintar kansa dashi akan nurr"Amma zai yiwa Mubarak wasu tambayoyi akan abubuwan dayakeji game da itah... Nisaibah kuwa"tana zuwa tasanarwa da daddy amsar sir faruq ta wuce bed room d'in mommy. Harma tafara bacci "Amma Saida Nisaibah ta tayar da ita... cikin damuwa tace"wlh mommy Yaya soyayya yakeyi da wata yarinya NURR! Toke tayaya kikasan hakan?"yanzun daddy ya aikeni gunsa ,shine nasamu suna waya da ita wlh.mommy tace"karki damu kibarni dashi"mommy abin nan fa abin dubawa ne"Ina zaton kamar fa yarinyar d'alibarsace"sbd naji Yana cewa gobe taje skul da wuri kartayi latti...to indai hakane Dole gobe kije skul d'in kibinciko Mana ita ko y'ar gidan uban wacece ita.dole tarabu dashi wlh"zankuma mishi barazanar Zan tsine mishi albarka koyarabu da ita.to mommy kinsan tsinuwarki bazata iya binsaba tunda bakece kika haifesaba. Eh Mana"sbd natsoratar dashine Mana"to Kuma in dg baya kuka bijiro Masa da maganar aurena"bazai Miki kallon Maison kantaba....hakane Kuma kinyi gsky"yanzun kibincika yarinyar"inhar Yar gidan matsiyata ce.to Kinga saina fake da hakan nace yarabu da ita.kuma Mije gidansu muyi Mata barazana itada iyayenta. dole tarabu dashi"abinda yasa yanzun bazamu yarda muce ya aurekiba.sai kingama matsewa sosai sbd zubar miki cikin da akayi.inkuma kinje kinsake bawa wani kanki ke kika sani"munaso nan da wata 5 haka.lokacin zakiyi service naki sai asaka ranar aurenku ko?"eh wlh mommy hakan yyi.kwanciyarta mommy tayi ,itakuma ta wuce nata d'akin da d'okin safiya tayi take skul d'in su nurr... Washe gari....✍️[9/14, 9:34 PM] +234 813 854 4097: _kina neman Hijabai na zamani, masu kyau, na gayu, ga rahusa gakuma sauki? Koko kina neman hadaddun dogayen riguna masu fitinannen kyau na dinki different styles, different prints dakuma designs?? A'a tokodai su iloka, tuwon madara, kwakumeti, hanjin ligidi, charbin malam, topi dakuma tsami gaye, coconut cincin kike nema?_ _basaikin wahala ba yau nakawo muku ita har gida, S-square fashion, treat and more got you covered, suna saida all abubuwan nan dakukaji na lissafa, zaki iya tuntubar su ta wanan number 07030037697, sanan zaki iya following nasu a Instagram @ssquarefashion and more_ Don tuntubansu direct a watsapp just click on this link https://wa.me/+2347030037697   Koda tashiga dakinta kashe komi tayi sanan tahau gado ta kwanta tanajan bargo ta lullube tana tunani. "She really wanted this marriage to work, tai trying all that she could, is not like tamai wani laifi hasalima all this while shine ke mata laifi yana neman kasheta da depression, bai damuda itaba bai damu da lafiyanta ba bai damu dakomi nataba, she tried so hard to make things work cikinsu harda zuwama counseling but it seems like Baban Khalid that can't work for him, tai rashin lafiya yaki kulata hakan yasa tai rejecting nashi that's the only datamai shine yake mata wanan punishment din, cikin harda karo mata biyu duka cikin just 2 weeks, sanan yadage dudda tabashi hakuri yace saita kira yan uwanta suzo bikonta, is this really fair? Why are men like that? Not just this, at this point before Murtala and anything ma wlh batajin son Baban Khalid aranta ko daya sai haushi da tsanan shi dajin haushin shi, she's only trying to make things work tsakanin su suyi zaman lafiya sabida yaransu ne but at this junction she needs to look after herself first, she wants to live long ma yaranta and zama da Baban Khalid kullum kara matsar da ita kusada kabari yakeyi, yanzu mezatayi? Yaya zatay........" yankewa maganan zucin datakeyi yayi sabida ihun Baban Khalid dataji.   _kina neman Hijabai na zamani, masu kyau, na gayu, ga rahusa gakuma sauki? Koko kina neman hadaddun dogayen riguna masu fitinannen kyau na dinki different styles, different prints dakuma designs?? A'a tokodai su iloka, tuwon madara, kwakumeti, hanjin ligidi, charbin malam, topi dakuma tsami gaye, coconut cincin kike nema?_ _basaikin wahala ba yau nakawo muku ita har gida, S-square fashion, treat and more got you covered, suna saida all abubuwan nan dakukaji na lissafa, zaki iya tuntubar su ta wanan number 07030037697, sanan zaki iya following nasu a Instagram @ssquarefashion and more_ Don tuntubansu direct a watsapp just click on this link https://wa.me/+2347030037697   "Wayyo Saudatu, ke nabaki komi nawa, wlh sai yanzu nasan nayi aure, wlh kinfi Hassana dadi" dasauri ta tashi zaune daga kan gadon ganin kaman kunnenta ne yaji mata magana haka badagaske bane, amman gamamakinta saitaji yay wani irin ihu da kara dayafi nadazu kosoyake tajishi oho dan dakin Saudat din na facing natane yace "wlh kinfi Hassana dadi da zaki da tsukewa, sai yanzu naji zaki amman da kaman dusa nakeji, Saudat kika rabudani saina mutu, wayyo babanmu, wayyo dadi, kinfimin wancan sau dub......" dasauri taja pillow tarufe kunnenta don bazata oya jure maganganun nan ba dudda haka bai hanata jin maganganun da Alhaji yakeyi gareta ba na batanci da wulakanci dayasa tai kuka sosai, duksun tai bacci datakeso tayi kasawa tayi saida suka gama sanan bacci ya kwasheta na wahala.   Wuraren 10 nasafe tatashi dawani irin mahaukacin ciwon kai shima tasanadin bugamata kofa dataji anayi kaman za'acire, da kyar takarasa bude idon sanan tadafe kan tana yatsine fuska tadagakai tareda kallon kofan dan sanin wanda ke knocking. "Bake nake kiraba Hassana kikai banza dani" jin muryan Baban Khalid har faduwa saida gabanta yayi dasauri ta tashi tasauko dagakan gadon tai wajen kofa, ahankali tabude kofan hada ido sukayi dashi yaci wata mahaukaciyar gizna mai shegen kyau fara fat tana kyalli, wani irin mugun kallo yabita dashi yace "ba'a koyamiki gaisuwa agidanku bane" saukarda kanta kasa tayi kafin ahankali tace "ina kwana Baban Khalid" juyawa yayi yace "biyoni dakina" dagakai tayi ta kalleshi taidan jim saikuma takoma tadauki hijabinta dake kan gadon tadaura kan kayan baccin dake jikinta tai dakin, kasancewan tasan yanzu va ita kadaice matarshi ba yasa tai knocking kofar, saida tabata kusan 2min tsaye awajen sanan agadarance taji yace "shigo" bude kofan tayi ta shiga daidai lokacin Saudat nafitowa daga wanka tana murmushi daga ita saidan towel fari data daura akirji kanta na jijjiga da ruwa, yana ganinta duddan yabata haushi yay wajenta da sauri yay wani cupping fuskarta yace "hope ban gajiyar dake sosai ba Saudat dina" murmushi tayi tace "ai ba'a gajiya da dadinka Alaji" sata yayi a side dinshi sanan yajuyo yakalli Hassana dake tsaye wajen kofa, cikeda wulakanci yace "baki iya gaisuwaba Saudat tafito daga wanka bazaki gaidataba" kafin tamayi magana dan mamaki maganan shi yabata Saudat tace "ahhh Alhaji bakomi wlh, yarinta ne ai nizan gaish......" dasauri yace "nace ki gaidata" yasake kallonta yamata maganan ranshi abace, sosai take kallonshi, but at the same time tanaso takara gasgatama zuciyanta ita Baban Khalid ke treating haka, dan murmushi tayi takalli Saudat tace "barka da safiya" duk iskancin Saudat kasa amsawa tayi sabida tamugun cikamata ido, wani irin murmushin keta Baban Khalid yayi feeling so accomplish sanan yasake daure fuska yanuna mata kan gadonshi dasuka gama iskanci akai, gadon da bargon yayi kaman anyi dambe akai sanan ga kayansu dasuka cire dagashi har ita sun jejjefar akasa harda bra da pant da boxer sanan Baban Khalid yace "inaso ki gyara dakin nan da gadon nan, Saudat tagaji zan kaita dakinta naje namata tausa, so please clean the room, and ki washing bedspread dinan dan munbatashi, anyway just clean the room perfectly sabida anjima we will use it" yakalli Saudat yace "muje babyna" yaja hannunta suka wuce duk tana wani irin kallonshi. IN KECE ZAKIYI? [9/15, 11:43 AM] +234 803 205 4850: _kina neman Hijabai na zamani, masu kyau, na gayu, ga rahusa gakuma sauki? Koko kina neman hadaddun dogayen riguna masu fitinannen kyau na dinki different styles, different prints dakuma designs?? A'a tokodai su iloka, tuwon madara, kwakumeti, hanjin ligidi, charbin malam, topi dakuma tsami gaye, coconut cincin kike nema?_ _basaikin wahala ba yau nakawo muku ita har gida, S-square fashion, treat and more got you covered, suna saida all abubuwan nan dakukaji na lissafa, zaki iya tuntubar su ta wanan number 07030037697, sanan zaki iya following nasu a Instagram @ssquarefashion and more_ Don tuntubansu direct a watsapp just click on this link https://wa.me/+2347030037697   Koda tashiga dakinta kashe komi tayi sanan tahau gado ta kwanta tanajan bargo ta lullube tana tunani. "She really wanted this marriage to work, tai trying all that she could, is not like tamai wani laifi hasalima all this while shine ke mata laifi yana neman kasheta da depression, bai damuda itaba bai damu da lafiyanta ba bai damu dakomi nataba, she tried so hard to make things work cikinsu harda zuwama counseling but it seems like Baban Khalid that can't work for him, tai rashin lafiya yaki kulata hakan yasa tai rejecting nashi that's the only datamai shine yake mata wanan punishment din, cikin harda karo mata biyu duka cikin just 2 weeks, sanan yadage dudda tabashi hakuri yace saita kira yan uwanta suzo bikonta, is this really fair? Why are men like that? Not just this, at this point before Murtala and anything ma wlh batajin son Baban Khalid aranta ko daya sai haushi da tsanan shi dajin haushin shi, she's only trying to make things work tsakanin su suyi zaman lafiya sabida yaransu ne but at this junction she needs to look after herself first, she wants to live long ma yaranta and zama da Baban Khalid kullum kara matsar da ita kusada kabari yakeyi, yanzu mezatayi? Yaya zatay........" yankewa maganan zucin datakeyi yayi sabida ihun Baban Khalid dataji.   _kina neman Hijabai na zamani, masu kyau, na gayu, ga rahusa gakuma sauki? Koko kina neman hadaddun dogayen riguna masu fitinannen kyau na dinki different styles, different prints dakuma designs?? A'a tokodai su iloka, tuwon madara, kwakumeti, hanjin ligidi, charbin malam, topi dakuma tsami gaye, coconut cincin kike nema?_ _basaikin wahala ba yau nakawo muku ita har gida, S-square fashion, treat and more got you covered, suna saida all abubuwan nan dakukaji na lissafa, zaki iya tuntubar su ta wanan number 07030037697, sanan zaki iya following nasu a Instagram @ssquarefashion and more_ Don tuntubansu direct a watsapp just click on this link https://wa.me/+2347030037697   "Wayyo Saudatu, ke nabaki komi nawa, wlh sai yanzu nasan nayi aure, wlh kinfi Hassana dadi" dasauri ta tashi zaune daga kan gadon ganin kaman kunnenta ne yaji mata magana haka badagaske bane, amman gamamakinta saitaji yay wani irin ihu da kara dayafi nadazu kosoyake tajishi oho dan dakin Saudat din na facing natane yace "wlh kinfi Hassana dadi da zaki da tsukewa, sai yanzu naji zaki amman da kaman dusa nakeji, Saudat kika rabudani saina mutu, wayyo babanmu, wayyo dadi, kinfimin wancan sau dub......" dasauri taja pillow tarufe kunnenta don bazata oya jure maganganun nan ba dudda haka bai hanata jin maganganun da Alhaji yakeyi gareta ba na batanci da wulakanci dayasa tai kuka sosai, duksun tai bacci datakeso tayi kasawa tayi saida suka gama sanan bacci ya kwasheta na wahala.   Wuraren 10 nasafe tatashi dawani irin mahaukacin ciwon kai shima tasanadin bugamata kofa dataji anayi kaman za'acire, da kyar takarasa bude idon sanan tadafe kan tana yatsine fuska tadagakai tareda kallon kofan dan sanin wanda ke knocking. "Bake nake kiraba Hassana kikai banza dani" jin muryan Baban Khalid har faduwa saida gabanta yayi dasauri ta tashi tasauko dagakan gadon tai wajen kofa, ahankali tabude kofan hada ido sukayi dashi yaci wata mahaukaciyar gizna mai shegen kyau fara fat tana kyalli, wani irin mugun kallo yabita dashi yace "ba'a koyamiki gaisuwa agidanku bane" saukarda kanta kasa tayi kafin ahankali tace "ina kwana Baban Khalid" juyawa yayi yace "biyoni dakina" dagakai tayi ta kalleshi taidan jim saikuma takoma tadauki hijabinta dake kan gadon tadaura kan kayan baccin dake jikinta tai dakin, kasancewan tasan yanzu va ita kadaice matarshi ba yasa tai knocking kofar, saida tabata kusan 2min tsaye awajen sanan agadarance taji yace "shigo" bude kofan tayi ta shiga daidai lokacin Saudat nafitowa daga wanka tana murmushi daga ita saidan towel fari data daura akirji kanta na jijjiga da ruwa, yana ganinta duddan yabata haushi yay wajenta da sauri yay wani cupping fuskarta yace "hope ban gajiyar dake sosai ba Saudat dina" murmushi tayi tace "ai ba'a gajiya da dadinka Alaji" sata yayi a side dinshi sanan yajuyo yakalli Hassana dake tsaye wajen kofa, cikeda wulakanci yace "baki iya gaisuwaba Saudat tafito daga wanka bazaki gaidataba" kafin tamayi magana dan mamaki maganan shi yabata Saudat tace "ahhh Alhaji bakomi wlh, yarinta ne ai nizan gaish......" dasauri yace "nace ki gaidata" yasake kallonta yamata maganan ranshi abace, sosai take kallonshi, but at the same time tanaso takara gasgatama zuciyanta ita Baban Khalid ke treating haka, dan murmushi tayi takalli Saudat tace "barka da safiya" duk iskancin Saudat kasa amsawa tayi sabida tamugun cikamata ido, wani irin murmushin keta Baban Khalid yayi feeling so accomplish sanan yasake daure fuska yanuna mata kan gadonshi dasuka gama iskanci akai, gadon da bargon yayi kaman anyi dambe akai sanan ga kayansu dasuka cire dagashi har ita sun jejjefar akasa harda bra da pant da boxer sanan Baban Khalid yace "inaso ki gyara dakin nan da gadon nan, Saudat tagaji zan kaita dakinta naje namata tausa, so please clean the room, and ki washing bedspread dinan dan munbatashi, anyway just clean the room perfectly sabida anjima we will use it" yakalli Saudat yace "muje babyna" yaja hannunta suka wuce duk tana wani irin kallonshi. IN KECE ZAKIYI?[9/18, 6:28 AM] +234 806 509 9503: _kina neman Hijabai na zamani, masu kyau, na gayu, ga rahusa gakuma sauki? Koko kina neman hadaddun dogayen riguna masu fitinannen kyau na dinki different styles, different prints dakuma designs?? A'a tokodai su iloka, tuwon madara, kwakumeti, hanjin ligidi, charbin malam, topi dakuma tsami gaye, coconut cincin kike nema?_ _basaikin wahala ba yau nakawo muku ita har gida, S-square fashion, treat and more got you covered, suna saida all abubuwan nan dakukaji na lissafa, zaki iya tuntubar su ta wanan number 07030037697, sanan zaki iya following nasu a Instagram @ssquarefashion and more_ Don tuntubansu direct a watsapp just click on this link https://wa.me/+2347030037697   Koda tashiga dakinta kashe komi tayi sanan tahau gado ta kwanta tanajan bargo ta lullube tana tunani. "She really wanted this marriage to work, tai trying all that she could, is not like tamai wani laifi hasalima all this while shine ke mata laifi yana neman kasheta da depression, bai damuda itaba bai damu da lafiyanta ba bai damu dakomi nataba, she tried so hard to make things work cikinsu harda zuwama counseling but it seems like Baban Khalid that can't work for him, tai rashin lafiya yaki kulata hakan yasa tai rejecting nashi that's the only datamai shine yake mata wanan punishment din, cikin harda karo mata biyu duka cikin just 2 weeks, sanan yadage dudda tabashi hakuri yace saita kira yan uwanta suzo bikonta, is this really fair? Why are men like that? Not just this, at this point before Murtala and anything ma wlh batajin son Baban Khalid aranta ko daya sai haushi da tsanan shi dajin haushin shi, she's only trying to make things work tsakanin su suyi zaman lafiya sabida yaransu ne but at this junction she needs to look after herself first, she wants to live long ma yaranta and zama da Baban Khalid kullum kara matsar da ita kusada kabari yakeyi, yanzu mezatayi? Yaya zatay........" yankewa maganan zucin datakeyi yayi sabida ihun Baban Khalid dataji.   _kina neman Hijabai na zamani, masu kyau, na gayu, ga rahusa gakuma sauki? Koko kina neman hadaddun dogayen riguna masu fitinannen kyau na dinki different styles, different prints dakuma designs?? A'a tokodai su iloka, tuwon madara, kwakumeti, hanjin ligidi, charbin malam, topi dakuma tsami gaye, coconut cincin kike nema?_ _basaikin wahala ba yau nakawo muku ita har gida, S-square fashion, treat and more got you covered, suna saida all abubuwan nan dakukaji na lissafa, zaki iya tuntubar su ta wanan number 07030037697, sanan zaki iya following nasu a Instagram @ssquarefashion and more_ Don tuntubansu direct a watsapp just click on this link https://wa.me/+2347030037697   "Wayyo Saudatu, ke nabaki komi nawa, wlh sai yanzu nasan nayi aure, wlh kinfi Hassana dadi" dasauri ta tashi zaune daga kan gadon ganin kaman kunnenta ne yaji mata magana haka badagaske bane, amman gamamakinta saitaji yay wani irin ihu da kara dayafi nadazu kosoyake tajishi oho dan dakin Saudat din na facing natane yace "wlh kinfi Hassana dadi da zaki da tsukewa, sai yanzu naji zaki amman da kaman dusa nakeji, Saudat kika rabudani saina mutu, wayyo babanmu, wayyo dadi, kinfimin wancan sau dub......" dasauri taja pillow tarufe kunnenta don bazata oya jure maganganun nan ba dudda haka bai hanata jin maganganun da Alhaji yakeyi gareta ba na batanci da wulakanci dayasa tai kuka sosai, duksun tai bacci datakeso tayi kasawa tayi saida suka gama sanan bacci ya kwasheta na wahala.   Wuraren 10 nasafe tatashi dawani irin mahaukacin ciwon kai shima tasanadin bugamata kofa dataji anayi kaman za'acire, da kyar takarasa bude idon sanan tadafe kan tana yatsine fuska tadagakai tareda kallon kofan dan sanin wanda ke knocking. "Bake nake kiraba Hassana kikai banza dani" jin muryan Baban Khalid har faduwa saida gabanta yayi dasauri ta tashi tasauko dagakan gadon tai wajen kofa, ahankali tabude kofan hada ido sukayi dashi yaci wata mahaukaciyar gizna mai shegen kyau fara fat tana kyalli, wani irin mugun kallo yabita dashi yace "ba'a koyamiki gaisuwa agidanku bane" saukarda kanta kasa tayi kafin ahankali tace "ina kwana Baban Khalid" juyawa yayi yace "biyoni dakina" dagakai tayi ta kalleshi taidan jim saikuma takoma tadauki hijabinta dake kan gadon tadaura kan kayan baccin dake jikinta tai dakin, kasancewan tasan yanzu va ita kadaice matarshi ba yasa tai knocking kofar, saida tabata kusan 2min tsaye awajen sanan agadarance taji yace "shigo" bude kofan tayi ta shiga daidai lokacin Saudat nafitowa daga wanka tana murmushi daga ita saidan towel fari data daura akirji kanta na jijjiga da ruwa, yana ganinta duddan yabata haushi yay wajenta da sauri yay wani cupping fuskarta yace "hope ban gajiyar dake sosai ba Saudat dina" murmushi tayi tace "ai ba'a gajiya da dadinka Alaji" sata yayi a side dinshi sanan yajuyo yakalli Hassana dake tsaye wajen kofa, cikeda wulakanci yace "baki iya gaisuwaba Saudat tafito daga wanka bazaki gaidataba" kafin tamayi magana dan mamaki maganan shi yabata Saudat tace "ahhh Alhaji bakomi wlh, yarinta ne ai nizan gaish......" dasauri yace "nace ki gaidata" yasake kallonta yamata maganan ranshi abace, sosai take kallonshi, but at the same time tanaso takara gasgatama zuciyanta ita Baban Khalid ke treating haka, dan murmushi tayi takalli Saudat tace "barka da safiya" duk iskancin Saudat kasa amsawa tayi sabida tamugun cikamata ido, wani irin murmushin keta Baban Khalid yayi feeling so accomplish sanan yasake daure fuska yanuna mata kan gadonshi dasuka gama iskanci akai, gadon da bargon yayi kaman anyi dambe akai sanan ga kayansu dasuka cire dagashi har ita sun jejjefar akasa harda bra da pant da boxer sanan Baban Khalid yace "inaso ki gyara dakin nan da gadon nan, Saudat tagaji zan kaita dakinta naje namata tausa, so please clean the room, and ki washing bedspread dinan dan munbatashi, anyway just clean the room perfectly sabida anjima we will use it" yakalli Saudat yace "muje babyna" yaja hannunta suka wuce duk tana wani irin kallonshi. IN KECE ZAKIYI? [9/18, 6:28 AM] +234 806 509 9503: Saida yazo daidai ta gefenta sanan tawani irin kallai eye to eye sanan tace "Baban Khalid wai mekamayar danine"? Kaman abinda yake jira kenan yasaki Saudat yace "wuce dakinki" sanan yajuyo ya kalleta kaman irin daman an shiryen nan yake yace "mekike tunani nake nufi? Cewa nayi clean this room ga kayan munan ko'ina harda breziya da pant din Saudat, sanan kicire zanin gadon damuka bata ki wanke ki shimfida sabo" yanda idanunta sukai ja saida yaji kaman yahadiya ruwan sanyi at that moment tsabagen dadi, shan gabanshi tayi tace "Baban Khalid wlh wlh kokai wayene baka isaba kasani na gyara dakin dakai da Matan ka kuka kwana ba, kayi kadan ne!" Tafadi cikeda zuciya dan tasoma kaiwa wuya, tace "mena maka dakake min all this humiliation? What have I done to you? Nabaka hakuri harna gaji kaki sauka akan bakanka aisai kacigaba, and barina kafa maka warning" tai maganan tana zaro idanu tace "koda wasa I mean it koda wasa karka sake sakani a harkanka da matanka inba hakaba komenai maka kaik......." bata karasa maganan ba taji saukan mari akan kuncin ta pau!!!! Da sauri tadafe kuncin ta ta kalli fuskan Baban Khalid daya batarai sosai sanan yanunata yace "wacece ke dahar kike ganin zaki iya koramin warning? Ubanwaye ke? Mena gayamiki? Banace miki I will shatter ur ego ba? Saina kaskantar dake nai breaking girman kan nan dakike ji kike takama dashi? Wlh saina wulakantaki Hassana, saina wulakantar dake, jaka kawai" yaja tsaki tareda daukan key mota yabita gefenta yawuce fuuuuu.   Baima jira Direbanshi yadaukeshi ba yaja motan yafice fuuu bai tsaya ko inaba sai office din Attajiri, baima tsaya knocking ba shiga kawai yayi kai tsaye, Attajiri na ganinshi yace "Kai Ango, kafadomin office haka kaman ana yaki meyafaru ne"? Wani dogon tsaki yaja saikuma yashiga zagaye a office din yana sakin tsaki akai akai, hakan yasa Attajiri yatashi da sauri yazagayo yazauna kan table yace "talk to me now nace meyafaru?" Cikin wani irin masifa da kunan rai yace "mema bai faruba" dasauri Attajiri yace "kaida waye"? "Hassana mana" yay dan shiru saikuma yacigaba da masifa, yace "I thought by now yanda nai auren nan kullum zanganta tana kuka ta rame, tana ciwo, tai sanyi sosai tana rokona nayafemata nayakuri da sauransu, but I was strong, shegiyar halitta ce Hassana, ga bakin rai, ga taurin kai da bakin zuciya, yau wai har nine take koroma warning........" nan yashiga bama Attajiri labarin abinda yafaru, saida yagama tsaf Attajiri yace "karka karaya, koma wani kalan wulakanci ne kai doubling dinshi kana mata, sannu sannu zata fara kuka tana rokonka yafiya, yanzu dai mubar zancen Hassana, Yaya Saudat kaji dadinta kuwa" dan shiru yayi saikuma ya yatsine fuska yace "ba laifi amman ba kaman Hassana ba, Hassana daban ce wlh, ni inda zata kwantar dakanta tazo tana kuka tana rokona da wlh na sadu da ita, nai kewan kasanta sosai, wajen dabanne kawai bazaka gane abinda nake fadiba" dariya duk sukayi, Attajiri yace "bari kaji xancen Hassana yadena damunka, mata fa biyu gareka yanzu kana gamawa da Saudat zakaje dakin budurwa dazaka bare dakanka daga leda kaci kai nak, koda ta tafi gidansu karka kuskura kabita zata dawo da kanta kaman yanda tadawo dafarko, sanan kama manta da ita, duk randa kasami chance kana gasamata wulakanci dazaisa tadinga hawaye zata baka hakuri, ai wlh kayafemata ahaka batare daka ciremata wanan girman kanba kaci baya nagayamaka, kaci baya" nan yacigaba da bashi shawarwari na banza.......   Da kyar ta lallaba takoma dakinta tai salla sanan ta tashi taja key motarta da wayanta, ko kadan bamata gani da kyau kanta wani irin bugawa yake kaman mutuwa ma zatayi, lallabawa tayi tana dafa bango tafito tasauko kasa sanan tafito compound, direban Alhaji kadai tagani a compound yana wanke sauran motocin Alhaji, yanayin yanda yaganta yasa dasauri yazo wajenta yace "Hajiya bakida lafiya ne"? Kasamagana tayi tabashi key dinta kawai tace "gidan.....mu" dasauri yakarbi key yana kallonta saikuma yadan kama gefen hannunta yace "sannu muje ki shiga mota" har mota yakaita yasata sanan yashiga gaba yaja, yasan gidansu hakan yasa yadauki hanya yakaita harchan gidansu.   Horn yayi agaban gidansu saida gateman yafito yaduba sanan yakoma da sauri yabude musu gate din, suka shiga ciki yay parking sanan yace "Hajiya mun iso" shirun dayaji yasa da sauri yawaiga baya, kaman ma sandarewa tayi tana zaune inda take a sume bata numfashi wani irin bude kofa yayi yafito saikuma yay ihu sosai yace "help, Hajiya ba lafiya" dasauri mai gadin yazo wajen dayaga yanda Hajiya take saiyawani irin famfala damugun gudu yay flat dinsu, ko one minute ba'a yiba saiga Mahaifinta wani black beauty magidanci kakkyawa yana sanye da suit kaman yashirya zai fita aiki ne, gefenshi kuma mazane manya guda biyu saiga Maman su (step Mum) tafito dasauri itama, suna zuwa wajen motan babanta yafara kai hannu yatabata saikuma yajuyo yakalli yaron dake bayanshi direct yace "Mustapha zoka dubata" matsama yaron yayi yazo yadubata, sanan yakalli dan uwanshi Hydar yace "mukaita ciki" daukanta sukayi Mama tafara salati tace "maiya sami Hassana, kai direba maiya sameta? Nan yafada musu yanda yaganta daharma yadauko ta. Afalon Mama yakaita suka kwantar da ita tareda ciremata hijab, dukansu sai kallon yanda tarame suke sanan yayan nata yafita da sauri yadauko medical kit dinshi yazo bp ta yafara dubawa kawai saiya saki salati, Baba da Mama dake kanshi sukace "meya faru Mustapha"? Baice musu komiba yashiga hada wata allura sanan yakama hannunta yamata a vein saikuma yamata daya a bumbum sanan yasauke ijiyan zuciya yakalli Baba yace "Baba kaga yanda jininta yahau kuwa wlh tana gab da samin paralyze, meke damunta hakane?" Fashewa da kuka Mama tayi tace "tunda naga yarnan kwanakin baya nasan bata hayyacinta, Hassana menene meke damunki? Har Hussaina nakira nacemata takirata taji ko kalau take" duk tsayawa sukai akanta suna kallo sai gashi chan tadanyi motsi dasauri Baba yazauna agefenta dan yanason yaranshi ba kadanba, kanta yashafa yace "Yan Biyu" dan haka yake kiransu tun suna yara, bude idanunta tayi ahankali ta kalleshi saikuma tafashe musu dakuka sosai dayasa jikin kowa yay sanyi. "Kinci abinci"? Baba yatambayeta ahankali, girgizamai kai tayi hakan yasa ya kalli Hydar yace "kawomata shayi da chips" dasauri yafice baiwani jimaba yadawo da shayi mai kauri da chips da egg, Da Mama da Baba ne suka dagota atare sanan yadauki tea yabata takarba kai tea bakinta tayi takurbi kadan saikuma tasake fashewa da kuka ahankali tace "Baba kaima kasan tun ina yarinya am a strong girl, Baba alot are happening agidana, I thought I can handle it alone, maybe matsalan daga nine, nafara zuwa ganin therapist, I did everything cus I want the marriage to work sabida su Khalil da Khalid, but I've heard enough........." tana kuka tasanar dasu daga farko har karshen abinda yake faruwa batare data musu karya ko dayaba, nan fa Baba yafara, Baba wani irin mutum ne dako kadan baiso yaji wani d'a namiji ya wulakantamai yarshi, shifa kafin ma yabaka auren yarshi zai gayamaka idan kagaji da y'ata kadawomin da abata gida batare daka cutarmin da itaba yarana sune rayuwana sune komi nawa, dakaci zalunsu gwara kaci nawa. Shi Baba yamafi iyaye mata supporting yaranshi, cikin fushi sosai yafara masifa yana kallon su Mustapha yace "angaya mishi banson y'ata ne dazai wulakantamin ita haka harda maran min ya? Koyazaci nagaji da itane eh Mustapha? Shi waye waye ubanshi waye kuma yadaure mishi gindi anan Nigeria dazai daga hannunshi yabugi y'ata" yanda Baba yahau zazzaga bala'i bil hakki yasa sai suka shiga bashi hakuri da kyar yay shiru sanan yajuyo ya kalli Hassana dake kuka sosai, yace "stop crying, karki kara kuka sabida shi" share hawayenta tayi tass tana haki, sanan yatashi yace "nabaki 24hrs ki yanke decision din dakikeso kinason cigaba da zamadashi ko bakiso" sanan yajuya yakalli Mustapha yace "zaka tafi da ita asibiti ne ko zaka mata treatment anan"? Ahankali yace "zanje nasayo magunguna anan zan mata" gyadakai Baba yayi yace "tom" saikuma yacigaba da masifa yace "koku su Mustapha ban yarda ku wulakanta matan kuba, ba'a rayuwa haka, yaza ayai ku dauko yara daga gatan iyayensu ku auro saiku kawosu kuna wulakanta su kun zaci iyayensu basa sonsu ne eh? Koko basuda gatane? Idan kaji bakason mace ta gundureka ka tsaneta karabu da ita baka wulakantata kana azabtar da ita ba, inna dinna yusrun, shi addininmu fa mai sauki ne, wlh bazan lamunta ba, zaisan yatabamin y'a" yasakai yafice daga dakin fuuuu yaran suka bishi.   _Bari nai amfani da wanan daman namuku tallan clases din danakeyi na matan aure kadai mai suna EROTIC IDEAS, na wanan October._   _Erotic Ideas group na matan aure zalla ne, group ne damuke program guda HUDU aduk sati, ranakun sune ALHAMIS, JUMMA'A ASABAR da LAHADI._ _Duk ranan Alhamis munayin program mai suna MARRIAGE LIFESTYLE, wato ZAMANTAKEWAN AURE, inda nakema mata lectures kan yanda ake zama da miji dakuma dabarun zama da miji, ranan jumma'a kuma muna program din damuke kirada TALK & HEAL wato yi magana ka warke, inda matan aure zasu gayamana matsalolin dasuke fuskanta agidajen mazajen su, zasu iya turamin ta pc idan basuson asansu nisainai forwarding group mu taimaka musu da shawarwari dakuma dabarun dazasubi su magance wanan matsalolin, sai ranan asabar shine ranan LECTURES, inda zan dauki darasi dake dauke da dombin ilimi abu wanda ya dace mata su iya dangane da aurensu, mu koya musu ayi magana akai sosai, sai ranan Lahadi zamuyi lectures akan ilimin daya danganci yanda zaki gamsar da mijinki sanan ki gamsar da kanki, kisaka mijinki ihu agado yana kururuwa yana sambatu, mukoyar dake yanda zakiyi spicing up sexlife dinki, and yanda zaki dinga rayuwa da mijinki kullum kaman sababbin aure._ _Idan kinason shiga wanan group din zaki turo 2000 to 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 sainai adding naki a group din, wata daya ne group din, idan kinason ki cigaba da zama duk wata dubu dayane 1000 ne subscription, sababbin zuwa kuma new member zakiyi register is 2k ne, don karin bayani zaki iya tuntubata a number ta 07012181461_ M Shakur ❤️Ahankali Mama takama hannunta tarike tana shafawa tana kallon yanda take kuka saikuma ta girgizamata kai cikeda taysayinta tace "I want you to think this through yar albarka, ke kikasan mijinki, banda haka aure is not do or die, any decision dakika daura, we will support you, kece ke zama da mijinki bamu iyayenki ba, dan haka kiyi tunani mai kyau kinji" gyadamata kai tayi ahankali saikuma tadago kanta tarungume Mama sosai tace "nagode Mama" girgizamata kai tayi tace "karki karamin godiya gabaki dayanku yaranane, Allah yamuku albarka, mezakici naje nadafa miki dakaina" ahankali tace "tuwo damiyan kubewa danye" maidata tayi ta kwantar tace "tom shikenan bari naje" ta tashi tafita daga dakin itama. Wuraren 12 Mustapha yadawo yashiga mata treatment sanan aka kawo mata tuwonta taci sosai sai bacci, dukansu tabasu tausayi, koda ta tashi da yamma taji dadin jikinta sosai aka sake kawo mata wani abincin batawani ci dayawa ba amman ciwon yaragu sai kanta dake kwankwasa haka suka cigaba da managing lafiyanta.   Bai dawo gidanba sai da magrib, yana shigowa Saudat tafesamai gulma da already direban shima yafara fadamai komi, dudda yaji wani iri amman ko ajikinshi yace bazai kiraba yacigaba da more amarcin shi dudda bini bini tana fadomai arai amman yaki kira. Bayan kwana uku! Tana zaune afalon Mama taji sauki sosai Mama na mata tsifa Baba ya aiko Hydar yakirata, gabanta saida yafadi amman tadaure tadauki mayafi tayafa sanan takalli Mama tace "Mama zoki rakani please" Mama bata misaba ta tashi sukai falon Baba, wanda daga Baba sai yayyinta aciki, wuri tasamu tazauna akasa sanan tace "gani Baba" gyaran murya yayi yace "Yan biyu dafarko nabaki 24hrs saikuma dan kaina nakara lokaci, nabari kika sami sauki dan kisamu ki kara tunani da kyau, dan haka inaso ki gayamin gaskiyan komi dake ranki dakuma hukuncin dakika yanke" shiru tayi nadan lokaci saikuma ahankali kanta nakasa tace "Baba kowace diya mace da abinda takeso takuma ke bida agidan aurenta, ni awajena kudi ko yawan dukiya bashine dadin aure awajena ba, kwanciyan hankali, farin ciki, kulawa, dakuma lokacin iyali shine aure awajena, wanda dukansu narasa, Baba Baban Khalid baya sona, bantaba ciwon kai yatambayeni ya jikinba, idanma ina ciwo idan inada sa'a shine zai kwana agidan yaraba daki dani, that's ranan da yan mutuncin shi kenan kenan, idan kuma basanan barin gidan yake yaafi hotel shi baison kamshim mai ciwo, bai damu dayanake ba kokuma yaya nakare, Baba idan zan fadi na buge na kurje agabanshi sannu bazaicemin ba balle ya tashi ya taimakamin natashi, baya kirana, bayida lokacina, Baba bai damu daniba, halayen dayake nunamin ire iren haka da gwaleni dayakeyi yasa I grew out of love for him, Baba, Mama ku iyayena ne idan namuku karya bazanma Allah ba, amman wlh harga Allah Allah yana ganin zuciyata banason Baban su Khalid yanzu ko kadan sabida yanda yake wulakantani, bakuma yaune nadena sonshi ba tunda dadewa, amman nacigaba da zama dashi ina kyautatamai sabida murayu tare kobadan komiba sabida yaranmu, amman at this junction bazan iyaba, yara nakowane kulansu da rayuwansu na hannun Allah ne baniba, shida yabanisu yasan yanda zaiyi dasu, kuma bama kananu bane dazan dinga tsoroba, kuma ko babu komi zan iyama Babansu shaida daya! Itace yanason yaranshi bazai taba wulakantamin su ba, Baba inason karaba aurena dashi bazan iya cigaba dazama dashi ba, zuciyata tagaji dakomi, kayakuri Baba wanan itace iyakan gaskiyata" tunda tafara maganan dakin yay shiru harta gama sanan Baba ya gyadakai ya kalli yaranshi maza yace "ina fatan kun dauki darasi daga maganan kanwarku" dukansu gyadamai kai yayi, Baba yace "wani zubin bakudi ne komiba, mace dakuka ganta anan tanada rauni, mace tafison mijin dazai sota damijin dazai bata kudi, kudi ba komi bane awajen wasu matan, kabama mace time, attention da care kaga yanda zata soka sama da komi, kardan kunzo kunyi kudi kufara wulakanta matanku, mata sun kashi gida biyu ne, akwai mai jure komi kome zaka mata taita jurewa tana shanyewa tana hakura, akwai kuma wacce bazata iyaba data tsaya jurewa tana shanyewa gwara tabarka which is kanwarku dinan dakuke gani, and I am so proud of her, I am so proud of you Yan biyu, Allah yamiki albarka, this shows kodayau zan mutu inada yarinyar dat can take care of herself, ta tsayawa kanta, Nothing beat peace of mind, bazan taba advising koyarda batawaba ta tsaya namiji yabata hawan jini yakasheta abanza yakaita lahira ba No" yabuga kujera yace "mace abuce mai rauni, ana bukata asota ne akuma kulada ita ba'a wulakantata ba, take care of your women mata deserve love, care, and attention, Allah yamuku albarka gabaki daya, kotu zata nemi Baban su Khalid, bayan an raba auren zan baki kudi ki kara expanding business naki, settle down mutuwan aure bashine end of the world ba hasalima is Nothing, kawai ki dage da addu'a sanan kizama mai yawan tsoron Allah kinajina" gyadamai kai tayi, yay murmushi yace "tashi kitafi kinji" tashi tayi ahankali saikuma tajuyo ta kalli Baban nata, batasan lokacin dataje da gudu ta tsugunna gaban kujeran dayake kawai tasa kanta aguiwanshi tahau kukaba sosai, tace "Baba u are the best father in this world, thank you Baba" dagokanta yayi yakai hannunshi yasharenata hawayen kaman wata karaman yarinya yace "I don't take my children for granted, babu wanda ya isa yabanzantar min da my girls, oya dena kukan ya isa haka, kome kikeso ki gayawa mamanki gatanan, ranan visiting din su Khalid kuma zaki kiga yaranki ki musu shopping okay" gyadamai kai tayi yace "to tashi kitafi" tashi tayi ahankali tawuce tatafi duk suka bitada kallo cikeda tausayi dakuma so, Baba ya kalli Hydar yace "start with the procedures, akaimai sallama yau yau dinnan" gyadamaikai yayi yatashi yafita feeling so proud of his Dad, Mahaifinsu wani irin kalan mutumne, tun suna yara yake koyamusu always respect women, mata abin tausayine, abin atausayamusu ne, sanan akuladasu alallashesu, idan kaduba kagani zakaga nafarko daga hakarkarinmu maza aka yosu, to akanme zaku wulakanta su, Baba kan yawan cemusu Annabin mu yariga ya kwatoma mata yancinsu dan haka dole mu daraja su, mu tausayamusu kodan hayayyafomana dasuke yi, Baba always say never hit a woman, Baba nada wani irin believe inhar ka kulada mace, kasota, kabata attention to wlh zata bika kaman kamata magani bazaka taba samin problem da itaba, murmushi kawai yayi yashiga mota yaja zuwa Shari'a court.     _Bari nai amfani da wanan daman namuku tallan clases din danakeyi na matan aure kadai mai suna EROTIC IDEAS, na wanan October._   _Erotic Ideas group na matan aure zalla ne, group ne damuke program guda HUDU aduk sati, ranakun sune ALHAMIS, JUMMA'A ASABAR da LAHADI._ _Duk ranan Alhamis munayin program mai suna MARRIAGE LIFESTYLE, wato ZAMANTAKEWAN AURE, inda nakema mata lectures kan yanda ake zama da miji dakuma dabarun zama da miji, ranan jumma'a kuma muna program din damuke kirada TALK & HEAL wato yi magana ka warke, inda matan aure zasu gayamana matsalolin dasuke fuskanta agidajen mazajen su, zasu iya turamin ta pc idan basuson asansu nisainai forwarding group mu taimaka musu da shawarwari dakuma dabarun dazasubi su magance wanan matsalolin, sai ranan asabar shine ranan LECTURES, inda zan dauki darasi dake dauke da dombin ilimi abu wanda ya dace mata su iya dangane da aurensu, mu koya musu ayi magana akai sosai, sai ranan Lahadi zamuyi lectures akan ilimin daya danganci yanda zaki gamsar da mijinki sanan ki gamsar da kanki, kisaka mijinki ihu agado yana kururuwa yana sambatu, mukoyar dake yanda zakiyi spicing up sexlife dinki, and yanda zaki dinga rayuwa da mijinki kullum kaman sababbin aure._ _Idan kinason shiga wanan group din zaki turo 2000 to 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 sainai adding naki a group din, wata daya ne group din, idan kinason ki cigaba da zama duk wata dubu dayane 1000 ne subscription, sababbin zuwa kuma new member zakiyi register is 2k ne, don karin bayani zaki iya tuntubata a number ta 07012181461_ M Shakur ❤️_Bari nai amfani da wanan daman namuku tallan clases din danakeyi na matan aure kadai mai suna EROTIC IDEAS, na wanan October._   _Erotic Ideas group na matan aure zalla ne, group ne damuke program guda HUDU aduk sati, ranakun sune ALHAMIS, JUMMA'A ASABAR da LAHADI._ _Duk ranan Alhamis munayin program mai suna MARRIAGE LIFESTYLE, wato ZAMANTAKEWAN AURE, inda nakema mata lectures kan yanda ake zama da miji dakuma dabarun zama da miji, ranan jumma'a kuma muna program din damuke kirada TALK & HEAL wato yi magana ka warke, inda matan aure zasu gayamana matsalolin dasuke fuskanta agidajen mazajen su, zasu iya turamin ta pc idan basuson asansu nisainai forwarding group mu taimaka musu da shawarwari dakuma dabarun dazasubi su magance wanan matsalolin, sai ranan asabar shine ranan LECTURES, inda zan dauki darasi dake dauke da dombin ilimi abu wanda ya dace mata su iya dangane da aurensu, mu koya musu ayi magana akai sosai, sai ranan Lahadi zamuyi lectures akan ilimin daya danganci yanda zaki gamsar da mijinki sanan ki gamsar da kanki, kisaka mijinki ihu agado yana kururuwa yana sambatu, mukoyar dake yanda zakiyi spicing up sexlife dinki, and yanda zaki dinga rayuwa da mijinki kullum kaman sababbin aure._ _Idan kinason shiga wanan group din zaki turo 2000 to 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 sainai adding naki a group din, wata daya ne group din, idan kinason ki cigaba da zama duk wata dubu dayane 1000 ne subscription, sababbin zuwa kuma new member zakiyi register is 2k ne, don karin bayani zaki iya tuntubata a number ta 07012181461_ M Shakur ❤️     Dayake karfe goma ne za'a shiga shari'ar su tun 9:30 duka itada family member ta na court din, tana sanye dawata Oman black Abaya mai bala'in kyau, tana tareda Mama dakuma Hussainanta dasukenan kamanninsu daya da jiya itama ta diro daga Dubai dan she needs to support her sister, saikuma su Baba da Hydar dake wani waje daban har lokacin babu Baban Khalid, karfe goma daidai aka shiga dasu cikin kotu kowa ya zazzauna akai shiru Hussaina takama hannunta tarike ganin duktai wani iri ahankali tace "calm down we are all here with you Hassana" gyadama sister kai tayi tana kakalo murmushi daidai lokacin Alkali ya shigo kotu aka tattashi saida ya zauna sanan aka zazzauna, akai shiru itadai sai tsoron rashin ganinshi take, daya daga cikin ma'aikatan kotune yatashi yabama alkali wani file sanan yajuyo yace "ayau shadaya ga watan Augusta zamuji karane tsakanin Hajiya Hassana dakuma Alhaji Alhassan Bakori, inda Hajiya Hassana ta kawo karan mijinta wanan kotun mai adalcine bisa wayan nan dalilan, bai damu da lafiyanta ba, baya kaunarta, yana wulakantata sanan abinharyakai ga yafara daura hannunshi ajikinta da sunan duka, inda tanaso alkali yaduba wanan lamarin sanan ya sauwake mata yaraba aurenta da Alhaji Alhassan Bakori, yanzudai zamu fara da kiran Hajiya Hassana datazo ta tsaya anan".   Rawa jikinta yafara hakan yasa Hussaina takama hannunta gamgam tace "hey take a deep breath calm down kinji, Allah natare dake" lumshe ido tayi sanan tabude ahankali tareda karanto addu'a sanan taji wani karfi da dakewa yazo mata ahankali ta mike tsaye sanan tafito looking so damn beautiful and matured, tawuce ta tsaya a inda aka nunamata ta tsaya. Mutumin yacigaba yace "saikuma Alhaji Alhassan Bakori shima ina kiranshi dayazo nan ya tsaya" shiru akayi Hydar da Mustapha suka juya suna duba kotun koyazo amman babushi, sake kiranshi mutumin yayi. "Alhaji Alhassan Bakori" daidai lokacin Baban Khalid yawani danno kanshi cikin kotun yana sanye dawata mahaukaciyar gizna fara da saida takashema mutane ido, sai zuba kamshi yake idan kaganshi zaka dauke president ne, bayanshi kuma Attajiri ne shima yaci gayu sosai yasami waje yazauna kusada Baba yana gaidashi shikuma Baban Khalid yawuce gaba inda akace yatsaya, yana tsayawa yawani kalli Hassana dake tsaye awajenta sanan cikin daga murya da rashin mutunci yace "ke har kin kisa ki kawo karan Alhaji Alhassan Bakori kotu" jikake kotun yay tsit, mutumin dake kiran sunansu yace "Alhaji kayi shiru koma menene Alkali yanzu zai fara shari'a sanan zai bama kowa daga cikinku chance yay magana"   Ko takan mutumin baibiba yana kallonta still, yace "bari kiji nafi karfin ki kawoni kotu kitonamin asiri, Hassana kisani cewa ni Alhaji Alhassan Bakori nasakeki saki biyu!" Jikake tsit, wasu irin hot hawaye taji sun zubomata daga idanu data kasa controlling, sanan yawani tura hannu a Aljihu yaciro envelope sanan yafito daga inda yake yazo har gaban Alkali cikeda girmamawa yace "Alkali yanda Hassana bata sona nima bana sonta banama bukatar ta arayuwata, dan haka gasakinta nan" ya ijiye kan table din ma'aikatan dake nan kafin babban table din alkali, sanan yace "nabarku lafiya inada meeting da shugaban kasa" yajuya fuuuuuu yawuce, kaman dagaske Attajiri yatashi yana kiranshi. "Alhasann, Alhassan kai" yar guduman nan Alkali yadauka yabuga table, sanan yakalli Hassana dake hawaye sosai yace "koma ki zauna" kasa tafiya tayi, hakan yasa dasauri Hussaina da idanunta sukaija tazo takamota tafito da ita, sanan alkali yace "rayuwa kenan" bashi takardan akayi ya warware yabude sanan yace "Hassana mijinki yasakeki saki biyu, babu abinda zan iyayi kuma dan saki kona wasa gaskene balle kuma na gasken, ina ganin da wanan anzo karshen case dinku kenan tunda daman kuma abinda kuke bida kenan" yakara bubbuga guduman sanan yatashi yafice, nan aka tattashi banda su Mama sai lallashinta suke, dama sakin sukeso bawai wani abuba, but yanda yamata sakin rashin mutunci shine abinda yabatawa kowa rai, cikeda neman gindin zama Attajiri yazo yace "wlh Baba gabaki daya bansan case dinnan ma nafaruwa ba, Allah Alhassan baida hankali, ta ina zaitaba samun mata kaman Hassana? Shi baisan rayuwan aure hakuri akeba, kasan bai fadamin ba direbanshi ke sanardani fa, shine da sassafen nan daidai yana fitowa natareshi, ninema nasa yay latti sabida tsareshin danayi da fada, bansan abinda zaiyi ba kenan, dan Allah kuyakuri, zan mishi magana, kuyakuri wanan abu sam sam babu dadi cikinshi" Murmushi Baba yayi yace "karka damu wlh babu komi, haka Allah ya rubuta, kai kutashi mutafi" yay maganan yana kallonsu, dagata Mama tayi da Hassana danji tayi tama kasa tafiya hawaye sai fitowa kawai yake, girgizakai Attajiri yayi cikeda kula yace "Hasdana kiyakuri dan Allah kiyakuri kinji" babuma wanda ya kalleshi suka wuce da ita waje aka sakata amota sukai gida, shikuma Attajiri ranshi fess fess. KARSHEN MATAN ASOKORO LITTAFI NA DAYA!!! _Tofah yakuke ganin zata kaya???? Nifa at the point Alhaji Alhassan Bakori nake tausayi bama Hassana ba, dan yamugun tafka uban kuskure, mujedai zuwa_ SAIMUN SAKE HADUWA A LITTAFI NA BIYU DAZAIZO MUKU OCTOBER.   Anan nakawo karshen part 1 din book dinan, nadakatar dashine badan komiba sai final exam dina dazaran fara daga 20th har zuwa 13th of October, M SHAKUR dinku takusan zama graduate kusamin Albarka kumin fatan alkhairi, thank you all so much. And inasonku gabaki daya. _Bari nai amfani da wanan daman namuku tallan clases din danakeyi na matan aure kadai mai suna EROTIC IDEAS, na wanan October._   _Erotic Ideas group na matan aure zalla ne, group ne damuke program guda HUDU aduk sati, ranakun sune ALHAMIS, JUMMA'A ASABAR da LAHADI._ _Duk ranan Alhamis munayin program mai suna MARRIAGE LIFESTYLE, wato ZAMANTAKEWAN AURE, inda nakema mata lectures kan yanda ake zama da miji dakuma dabarun zama da miji, ranan jumma'a kuma muna program din damuke kirada TALK & HEAL wato yi magana ka warke, inda matan aure zasu gayamana matsalolin dasuke fuskanta agidajen mazajen su, zasu iya turamin ta pc idan basuson asansu nisainai forwarding group mu taimaka musu da shawarwari dakuma dabarun dazasubi su magance wanan matsalolin, sai ranan asabar shine ranan LECTURES, inda zan dauki darasi dake dauke da dombin ilimi abu wanda ya dace mata su iya dangane da aurensu, mu koya musu ayi magana akai sosai, sai ranan Lahadi zamuyi lectures akan ilimin daya danganci yanda zaki gamsar da mijinki sanan ki gamsar da kanki, kisaka mijinki ihu agado yana kururuwa yana sambatu, mukoyar dake yanda zakiyi spicing up sexlife dinki, and yanda zaki dinga rayuwa da mijinki kullum kaman sababbin aure._ _Idan kinason shiga wanan group din zaki turo 2000 to 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 sainai adding naki a group din, wata daya ne group din, idan kinason ki cigaba da zama duk wata dubu dayane 1000 ne subscription, sababbin zuwa kuma new member zakiyi register is 2k ne, don karin bayani zaki iya tuntubata a number ta 07012181461_ M Shakur ❤️ ************     Saida yazo daidai ta gefenta sanan tawani irin kallai eye to eye sanan tace "Baban Khalid wai mekamayar danine"? Kaman abinda yake jira kenan yasaki Saudat yace "wuce dakinki" sanan yajuyo ya kalleta kaman irin daman an shiryen nan yake yace "mekike tunani nake nufi? Cewa nayi clean this room ga kayan munan ko'ina harda breziya da pant din Saudat, sanan kicire zanin gadon damuka bata ki wanke ki shimfida sabo" yanda idanunta sukai ja saida yaji kaman yahadiya ruwan sanyi at that moment tsabagen dadi, shan gabanshi tayi tace "Baban Khalid wlh wlh kokai wayene baka isaba kasani na gyara dakin dakai da Matan ka kuka kwana ba, kayi kadan ne!" Tafadi cikeda zuciya dan tasoma kaiwa wuya, tace "mena maka dakake min all this humiliation? What have I done to you? Nabaka hakuri harna gaji kaki sauka akan bakanka aisai kacigaba, and barina kafa maka warning" tai maganan tana zaro idanu tace "koda wasa I mean it koda wasa karka sake sakani a harkanka da matanka inba hakaba komenai maka kaik......." bata karasa maganan ba taji saukan mari akan kuncin ta pau!!!! Da sauri tadafe kuncin ta ta kalli fuskan Baban Khalid daya batarai sosai sanan yanunata yace "wacece ke dahar kike ganin zaki iya koramin warning? Ubanwaye ke? Mena gayamiki? Banace miki I will shatter ur ego ba? Saina kaskantar dake nai breaking girman kan nan dakike ji kike takama dashi? Wlh saina wulakantaki Hassana, saina wulakantar dake, jaka kawai" yaja tsaki tareda daukan key mota yabita gefenta yawuce fuuuuu.   Baima jira Direbanshi yadaukeshi ba yaja motan yafice fuuu bai tsaya ko inaba sai office din Attajiri, baima tsaya knocking ba shiga kawai yayi kai tsaye, Attajiri na ganinshi yace "Kai Ango, kafadomin office haka kaman ana yaki meyafaru ne"? Wani dogon tsaki yaja saikuma yashiga zagaye a office din yana sakin tsaki akai akai, hakan yasa Attajiri yatashi da sauri yazagayo yazauna kan table yace "talk to me now nace meyafaru?" Cikin wani irin masifa da kunan rai yace "mema bai faruba" dasauri Attajiri yace "kaida waye"? "Hassana mana" yay dan shiru saikuma yacigaba da masifa, yace "I thought by now yanda nai auren nan kullum zanganta tana kuka ta rame, tana ciwo, tai sanyi sosai tana rokona nayafemata nayakuri da sauransu, but I was strong, shegiyar halitta ce Hassana, ga bakin rai, ga taurin kai da bakin zuciya, yau wai har nine take koroma warning........" nan yashiga bama Attajiri labarin abinda yafaru, saida yagama tsaf Attajiri yace "karka karaya, koma wani kalan wulakanci ne kai doubling dinshi kana mata, sannu sannu zata fara kuka tana rokonka yafiya, yanzu dai mubar zancen Hassana, Yaya Saudat kaji dadinta kuwa" dan shiru yayi saikuma ya yatsine fuska yace "ba laifi amman ba kaman Hassana ba, Hassana daban ce wlh, ni inda zata kwantar dakanta tazo tana kuka tana rokona da wlh na sadu da ita, nai kewan kasanta sosai, wajen dabanne kawai bazaka gane abinda nake fadiba" dariya duk sukayi, Attajiri yace "bari kaji xancen Hassana yadena damunka, mata fa biyu gareka yanzu kana gamawa da Saudat zakaje dakin budurwa dazaka bare dakanka daga leda kaci kai nak, koda ta tafi gidansu karka kuskura kabita zata dawo da kanta kaman yanda tadawo dafarko, sanan kama manta da ita, duk randa kasami chance kana gasamata wulakanci dazaisa tadinga hawaye zata baka hakuri, ai wlh kayafemata ahaka batare daka ciremata wanan girman kanba kaci baya nagayamaka, kaci baya" nan yacigaba da bashi shawarwari na banza.......   Da kyar ta lallaba takoma dakinta tai salla sanan ta tashi taja key motarta da wayanta, ko kadan bamata gani da kyau kanta wani irin bugawa yake kaman mutuwa ma zatayi, lallabawa tayi tana dafa bango tafito tasauko kasa sanan tafito compound, direban Alhaji kadai tagani a compound yana wanke sauran motocin Alhaji, yanayin yanda yaganta yasa dasauri yazo wajenta yace "Hajiya bakida lafiya ne"? Kasamagana tayi tabashi key dinta kawai tace "gidan.....mu" dasauri yakarbi key yana kallonta saikuma yadan kama gefen hannunta yace "sannu muje ki shiga mota" har mota yakaita yasata sanan yashiga gaba yaja, yasan gidansu hakan yasa yadauki hanya yakaita harchan gidansu.   Horn yayi agaban gidansu saida gateman yafito yaduba sanan yakoma da sauri yabude musu gate din, suka shiga ciki yay parking sanan yace "Hajiya mun iso" shirun dayaji yasa da sauri yawaiga baya, kaman ma sandarewa tayi tana zaune inda take a sume bata numfashi wani irin bude kofa yayi yafito saikuma yay ihu sosai yace "help, Hajiya ba lafiya" dasauri mai gadin yazo wajen dayaga yanda Hajiya take saiyawani irin famfala damugun gudu yay flat dinsu, ko one minute ba'a yiba saiga Mahaifinta wani black beauty magidanci kakkyawa yana sanye da suit kaman yashirya zai fita aiki ne, gefenshi kuma mazane manya guda biyu saiga Maman su (step Mum) tafito dasauri itama, suna zuwa wajen motan babanta yafara kai hannu yatabata saikuma yajuyo yakalli yaron dake bayanshi direct yace "Mustapha zoka dubata" matsama yaron yayi yazo yadubata, sanan yakalli dan uwanshi Hydar yace "mukaita ciki" daukanta sukayi Mama tafara salati tace "maiya sami Hassana, kai direba maiya sameta? Nan yafada musu yanda yaganta daharma yadauko ta. Afalon Mama yakaita suka kwantar da ita tareda ciremata hijab, dukansu sai kallon yanda tarame suke sanan yayan nata yafita da sauri yadauko medical kit dinshi yazo bp ta yafara dubawa kawai saiya saki salati, Baba da Mama dake kanshi sukace "meya faru Mustapha"? Baice musu komiba yashiga hada wata allura sanan yakama hannunta yamata a vein saikuma yamata daya a bumbum sanan yasauke ijiyan zuciya yakalli Baba yace "Baba kaga yanda jininta yahau kuwa wlh tana gab da samin paralyze, meke damunta hakane?" Fashewa da kuka Mama tayi tace "tunda naga yarnan kwanakin baya nasan bata hayyacinta, Hassana menene meke damunki? Har Hussaina nakira nacemata takirata taji ko kalau take" duk tsayawa sukai akanta suna kallo sai gashi chan tadanyi motsi dasauri Baba yazauna agefenta dan yanason yaranshi ba kadanba, kanta yashafa yace "Yan Biyu" dan haka yake kiransu tun suna yara, bude idanunta tayi ahankali ta kalleshi saikuma tafashe musu dakuka sosai dayasa jikin kowa yay sanyi. "Kinci abinci"? Baba yatambayeta ahankali, girgizamai kai tayi hakan yasa ya kalli Hydar yace "kawomata shayi da chips" dasauri yafice baiwani jimaba yadawo da shayi mai kauri da chips da egg, Da Mama da Baba ne suka dagota atare sanan yadauki tea yabata takarba kai tea bakinta tayi takurbi kadan saikuma tasake fashewa da kuka ahankali tace "Baba kaima kasan tun ina yarinya am a strong girl, Baba alot are happening agidana, I thought I can handle it alone, maybe matsalan daga nine, nafara zuwa ganin therapist, I did everything cus I want the marriage to work sabida su Khalil da Khalid, but I've heard enough........." tana kuka tasanar dasu daga farko har karshen abinda yake faruwa batare data musu karya ko dayaba, nan fa Baba yafara, Baba wani irin mutum ne dako kadan baiso yaji wani d'a namiji ya wulakantamai yarshi, shifa kafin ma yabaka auren yarshi zai gayamaka idan kagaji da y'ata kadawomin da abata gida batare daka cutarmin da itaba yarana sune rayuwana sune komi nawa, dakaci zalunsu gwara kaci nawa. Shi Baba yamafi iyaye mata supporting yaranshi, cikin fushi sosai yafara masifa yana kallon su Mustapha yace "angaya mishi banson y'ata ne dazai wulakantamin ita haka harda maran min ya? Koyazaci nagaji da itane eh Mustapha? Shi waye waye ubanshi waye kuma yadaure mishi gindi anan Nigeria dazai daga hannunshi yabugi y'ata" yanda Baba yahau zazzaga bala'i bil hakki yasa sai suka shiga bashi hakuri da kyar yay shiru sanan yajuyo ya kalli Hassana dake kuka sosai, yace "stop crying, karki kara kuka sabida shi" share hawayenta tayi tass tana haki, sanan yatashi yace "nabaki 24hrs ki yanke decision din dakikeso kinason cigaba da zamadashi ko bakiso" sanan yajuya yakalli Mustapha yace "zaka tafi da ita asibiti ne ko zaka mata treatment anan"? Ahankali yace "zanje nasayo magunguna anan zan mata" gyadakai Baba yayi yace "tom" saikuma yacigaba da masifa yace "koku su Mustapha ban yarda ku wulakanta matan kuba, ba'a rayuwa haka, yaza ayai ku dauko yara daga gatan iyayensu ku auro saiku kawosu kuna wulakanta su kun zaci iyayensu basa sonsu ne eh? Koko basuda gatane? Idan kaji bakason mace ta gundureka ka tsaneta karabu da ita baka wulakantata kana azabtar da ita ba, inna dinna yusrun, shi addininmu fa mai sauki ne, wlh bazan lamunta ba, zaisan yatabamin y'a" yasakai yafice daga dakin fuuuu yaran suka bishi.   _Bari nai amfani da wanan daman namuku tallan clases din danakeyi na matan aure kadai mai suna EROTIC IDEAS, na wanan October._   _Erotic Ideas group na matan aure zalla ne, group ne damuke program guda HUDU aduk sati, ranakun sune ALHAMIS, JUMMA'A ASABAR da LAHADI._ _Duk ranan Alhamis munayin program mai suna MARRIAGE LIFESTYLE, wato ZAMANTAKEWAN AURE, inda nakema mata lectures kan yanda ake zama da miji dakuma dabarun zama da miji, ranan jumma'a kuma muna program din damuke kirada TALK & HEAL wato yi magana ka warke, inda matan aure zasu gayamana matsalolin dasuke fuskanta agidajen mazajen su, zasu iya turamin ta pc idan basuson asansu nisainai forwarding group mu taimaka musu da shawarwari dakuma dabarun dazasubi su magance wanan matsalolin, sai ranan asabar shine ranan LECTURES, inda zan dauki darasi dake dauke da dombin ilimi abu wanda ya dace mata su iya dangane da aurensu, mu koya musu ayi magana akai sosai, sai ranan Lahadi zamuyi lectures akan ilimin daya danganci yanda zaki gamsar da mijinki sanan ki gamsar da kanki, kisaka mijinki ihu agado yana kururuwa yana sambatu, mukoyar dake yanda zakiyi spicing up sexlife dinki, and yanda zaki dinga rayuwa da mijinki kullum kaman sababbin aure._ _Idan kinason shiga wanan group din zaki turo 2000 to 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 sainai adding naki a group din, wata daya ne group din, idan kinason ki cigaba da zama duk wata dubu dayane 1000 ne subscription, sababbin zuwa kuma new member zakiyi register is 2k ne, don karin bayani zaki iya tuntubata a number ta 07012181461_ M Shakur ❤️     Dayake karfe goma ne za'a shiga shari'ar su tun 9:30 duka itada family member ta na court din, tana sanye dawata Oman black Abaya mai bala'in kyau, tana tareda Mama dakuma Hussainanta dasukenan kamanninsu daya da jiya itama ta diro daga Dubai dan she needs to support her sister, saikuma su Baba da Hydar dake wani waje daban har lokacin babu Baban Khalid, karfe goma daidai aka shiga dasu cikin kotu kowa ya zazzauna akai shiru Hussaina takama hannunta tarike ganin duktai wani iri ahankali tace "calm down we are all here with you Hassana" gyadama sister kai tayi tana kakalo murmushi daidai lokacin Alkali ya shigo kotu aka tattashi saida ya zauna sanan aka zazzauna, akai shiru itadai sai tsoron rashin ganinshi take, daya daga cikin ma'aikatan kotune yatashi yabama alkali wani file sanan yajuyo yace "ayau shadaya ga watan Augusta zamuji karane tsakanin Hajiya Hassana dakuma Alhaji Alhassan Bakori, inda Hajiya Hassana ta kawo karan mijinta wanan kotun mai adalcine bisa wayan nan dalilan, bai damu da lafiyanta ba, baya kaunarta, yana wulakantata sanan abinharyakai ga yafara daura hannunshi ajikinta da sunan duka, inda tanaso alkali yaduba wanan lamarin sanan ya sauwake mata yaraba aurenta da Alhaji Alhassan Bakori, yanzudai zamu fara da kiran Hajiya Hassana datazo ta tsaya anan".   Rawa jikinta yafara hakan yasa Hussaina takama hannunta gamgam tace "hey take a deep breath calm down kinji, Allah natare dake" lumshe ido tayi sanan tabude ahankali tareda karanto addu'a sanan taji wani karfi da dakewa yazo mata ahankali ta mike tsaye sanan tafito looking so damn beautiful and matured, tawuce ta tsaya a inda aka nunamata ta tsaya. Mutumin yacigaba yace "saikuma Alhaji Alhassan Bakori shima ina kiranshi dayazo nan ya tsaya" shiru akayi Hydar da Mustapha suka juya suna duba kotun koyazo amman babushi, sake kiranshi mutumin yayi. "Alhaji Alhassan Bakori" daidai lokacin Baban Khalid yawani danno kanshi cikin kotun yana sanye dawata mahaukaciyar gizna fara da saida takashema mutane ido, sai zuba kamshi yake idan kaganshi zaka dauke president ne, bayanshi kuma Attajiri ne shima yaci gayu sosai yasami waje yazauna kusada Baba yana gaidashi shikuma Baban Khalid yawuce gaba inda akace yatsaya, yana tsayawa yawani kalli Hassana dake tsaye awajenta sanan cikin daga murya da rashin mutunci yace "ke har kin kisa ki kawo karan Alhaji Alhassan Bakori kotu" jikake kotun yay tsit, mutumin dake kiran sunansu yace "Alhaji kayi shiru koma menene Alkali yanzu zai fara shari'a sanan zai bama kowa daga cikinku chance yay magana"   Ko takan mutumin baibiba yana kallonta still, yace "bari kiji nafi karfin ki kawoni kotu kitonamin asiri, Hassana kisani cewa ni Alhaji Alhassan Bakori nasakeki saki biyu!" Jikake tsit, wasu irin hot hawaye taji sun zubomata daga idanu data kasa controlling, sanan yawani tura hannu a Aljihu yaciro envelope sanan yafito daga inda yake yazo har gaban Alkali cikeda girmamawa yace "Alkali yanda Hassana bata sona nima bana sonta banama bukatar ta arayuwata, dan haka gasakinta nan" ya ijiye kan table din ma'aikatan dake nan kafin babban table din alkali, sanan yace "nabarku lafiya inada meeting da shugaban kasa" yajuya fuuuuuu yawuce, kaman dagaske Attajiri yatashi yana kiranshi. "Alhasann, Alhassan kai" yar guduman nan Alkali yadauka yabuga table, sanan yakalli Hassana dake hawaye sosai yace "koma ki zauna" kasa tafiya tayi, hakan yasa dasauri Hussaina da idanunta sukaija tazo takamota tafito da ita, sanan alkali yace "rayuwa kenan" bashi takardan akayi ya warware yabude sanan yace "Hassana mijinki yasakeki saki biyu, babu abinda zan iyayi kuma dan saki kona wasa gaskene balle kuma na gasken, ina ganin da wanan anzo karshen case dinku kenan tunda daman kuma abinda kuke bida kenan" yakara bubbuga guduman sanan yatashi yafice, nan aka tattashi banda su Mama sai lallashinta suke, dama sakin sukeso bawai wani abuba, but yanda yamata sakin rashin mutunci shine abinda yabatawa kowa rai, cikeda neman gindin zama Attajiri yazo yace "wlh Baba gabaki daya bansan case dinnan ma nafaruwa ba, Allah Alhassan baida hankali, ta ina zaitaba samun mata kaman Hassana? Shi baisan rayuwan aure hakuri akeba, kasan bai fadamin ba direbanshi ke sanardani fa, shine da sassafen nan daidai yana fitowa natareshi, ninema nasa yay latti sabida tsareshin danayi da fada, bansan abinda zaiyi ba kenan, dan Allah kuyakuri, zan mishi magana, kuyakuri wanan abu sam sam babu dadi cikinshi" Murmushi Baba yayi yace "karka damu wlh babu komi, haka Allah ya rubuta, kai kutashi mutafi" yay maganan yana kallonsu, dagata Mama tayi da Hassana danji tayi tama kasa tafiya hawaye sai fitowa kawai yake, girgizakai Attajiri yayi cikeda kula yace "Hasdana kiyakuri dan Allah kiyakuri kinji" babuma wanda ya kalleshi suka wuce da ita waje aka sakata amota sukai gida, shikuma Attajiri ranshi fess fess. KARSHEN MATAN ASOKORO LITTAFI NA DAYA!!! _Tofah yakuke ganin zata kaya???? Nifa at the point Alhaji Alhassan Bakori nake tausayi bama Hassana ba, dan yamugun tafka uban kuskure, mujedai zuwa_ SAIMUN SAKE HADUWA A LITTAFI NA BIYU DAZAIZO MUKU OCTOBER.   Anan nakawo karshen part 1 din book dinan, nadakatar dashine badan komiba sai final exam dina dazaran fara daga 20th har zuwa 13th of October, M SHAKUR dinku takusan zama graduate kusamin Albarka kumin fatan alkhairi, thank you all so much. And inasonku gabaki daya. _Bari nai amfani da wanan daman namuku tallan clases din danakeyi na matan aure kadai mai suna EROTIC IDEAS, na wanan October._   _Erotic Ideas group na matan aure zalla ne, group ne damuke program guda HUDU aduk sati, ranakun sune ALHAMIS, JUMMA'A ASABAR da LAHADI._ _Duk ranan Alhamis munayin program mai suna MARRIAGE LIFESTYLE, wato ZAMANTAKEWAN AURE, inda nakema mata lectures kan yanda ake zama da miji dakuma dabarun zama da miji, ranan jumma'a kuma muna program din damuke kirada TALK & HEAL wato yi magana ka warke, inda matan aure zasu gayamana matsalolin dasuke fuskanta agidajen mazajen su, zasu iya turamin ta pc idan basuson asansu nisainai forwarding group mu taimaka musu da shawarwari dakuma dabarun dazasubi su magance wanan matsalolin, sai ranan asabar shine ranan LECTURES, inda zan dauki darasi dake dauke da dombin ilimi abu wanda ya dace mata su iya dangane da aurensu, mu koya musu ayi magana akai sosai, sai ranan Lahadi zamuyi lectures akan ilimin daya danganci yanda zaki gamsar da mijinki sanan ki gamsar da kanki, kisaka mijinki ihu agado yana kururuwa yana sambatu, mukoyar dake yanda zakiyi spicing up sexlife dinki, and yanda zaki dinga rayuwa da mijinki kullum kaman sababbin aure._ _Idan kinason shiga wanan group din zaki turo 2000 to 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 sainai adding naki a group din, wata daya ne group din, idan kinason ki cigaba da zama duk wata dubu dayane 1000 ne subscription, sababbin zuwa kuma new member zakiyi register is 2k ne, don karin bayani zaki iya tuntubata a number ta 07012181461_ M Shakur ❤️         Ahankali Mama takama hannunta tarike tana shafawa tana kallon yanda take kuka saikuma ta girgizamata kai cikeda taysayinta tace "I want you to think this through yar albarka, ke kikasan mijinki, banda haka aure is not do or die, any decision dakika daura, we will support you, kece ke zama da mijinki bamu iyayenki ba, dan haka kiyi tunani mai kyau kinji" gyadamata kai tayi ahankali saikuma tadago kanta tarungume Mama sosai tace "nagode Mama" girgizamata kai tayi tace "karki karamin godiya gabaki dayanku yaranane, Allah yamuku albarka, mezakici naje nadafa miki dakaina" ahankali tace "tuwo damiyan kubewa danye" maidata tayi ta kwantar tace "tom shikenan bari naje" ta tashi tafita daga dakin itama. Wuraren 12 Mustapha yadawo yashiga mata treatment sanan aka kawo mata tuwonta taci sosai sai bacci, dukansu tabasu tausayi, koda ta tashi da yamma taji dadin jikinta sosai aka sake kawo mata wani abincin batawani ci dayawa ba amman ciwon yaragu sai kanta dake kwankwasa haka suka cigaba da managing lafiyanta.   Bai dawo gidanba sai da magrib, yana shigowa Saudat tafesamai gulma da already direban shima yafara fadamai komi, dudda yaji wani iri amman ko ajikinshi yace bazai kiraba yacigaba da more amarcin shi dudda bini bini tana fadomai arai amman yaki kira. Bayan kwana uku! Tana zaune afalon Mama taji sauki sosai Mama na mata tsifa Baba ya aiko Hydar yakirata, gabanta saida yafadi amman tadaure tadauki mayafi tayafa sanan takalli Mama tace "Mama zoki rakani please" Mama bata misaba ta tashi sukai falon Baba, wanda daga Baba sai yayyinta aciki, wuri tasamu tazauna akasa sanan tace "gani Baba" gyaran murya yayi yace "Yan biyu dafarko nabaki 24hrs saikuma dan kaina nakara lokaci, nabari kika sami sauki dan kisamu ki kara tunani da kyau, dan haka inaso ki gayamin gaskiyan komi dake ranki dakuma hukuncin dakika yanke" shiru tayi nadan lokaci saikuma ahankali kanta nakasa tace "Baba kowace diya mace da abinda takeso takuma ke bida agidan aurenta, ni awajena kudi ko yawan dukiya bashine dadin aure awajena ba, kwanciyan hankali, farin ciki, kulawa, dakuma lokacin iyali shine aure awajena, wanda dukansu narasa, Baba Baban Khalid baya sona, bantaba ciwon kai yatambayeni ya jikinba, idanma ina ciwo idan inada sa'a shine zai kwana agidan yaraba daki dani, that's ranan da yan mutuncin shi kenan kenan, idan kuma basanan barin gidan yake yaafi hotel shi baison kamshim mai ciwo, bai damu dayanake ba kokuma yaya nakare, Baba idan zan fadi na buge na kurje agabanshi sannu bazaicemin ba balle ya tashi ya taimakamin natashi, baya kirana, bayida lokacina, Baba bai damu daniba, halayen dayake nunamin ire iren haka da gwaleni dayakeyi yasa I grew out of love for him, Baba, Mama ku iyayena ne idan namuku karya bazanma Allah ba, amman wlh harga Allah Allah yana ganin zuciyata banason Baban su Khalid yanzu ko kadan sabida yanda yake wulakantani, bakuma yaune nadena sonshi ba tunda dadewa, amman nacigaba da zama dashi ina kyautatamai sabida murayu tare kobadan komiba sabida yaranmu, amman at this junction bazan iyaba, yara nakowane kulansu da rayuwansu na hannun Allah ne baniba, shida yabanisu yasan yanda zaiyi dasu, kuma bama kananu bane dazan dinga tsoroba, kuma ko babu komi zan iyama Babansu shaida daya! Itace yanason yaranshi bazai taba wulakantamin su ba, Baba inason karaba aurena dashi bazan iya cigaba dazama dashi ba, zuciyata tagaji dakomi, kayakuri Baba wanan itace iyakan gaskiyata" tunda tafara maganan dakin yay shiru harta gama sanan Baba ya gyadakai ya kalli yaranshi maza yace "ina fatan kun dauki darasi daga maganan kanwarku" dukansu gyadamai kai yayi, Baba yace "wani zubin bakudi ne komiba, mace dakuka ganta anan tanada rauni, mace tafison mijin dazai sota damijin dazai bata kudi, kudi ba komi bane awajen wasu matan, kabama mace time, attention da care kaga yanda zata soka sama da komi, kardan kunzo kunyi kudi kufara wulakanta matanku, mata sun kashi gida biyu ne, akwai mai jure komi kome zaka mata taita jurewa tana shanyewa tana hakura, akwai kuma wacce bazata iyaba data tsaya jurewa tana shanyewa gwara tabarka which is kanwarku dinan dakuke gani, and I am so proud of her, I am so proud of you Yan biyu, Allah yamiki albarka, this shows kodayau zan mutu inada yarinyar dat can take care of herself, ta tsayawa kanta, Nothing beat peace of mind, bazan taba advising koyarda batawaba ta tsaya namiji yabata hawan jini yakasheta abanza yakaita lahira ba No" yabuga kujera yace "mace abuce mai rauni, ana bukata asota ne akuma kulada ita ba'a wulakantata ba, take care of your women mata deserve love, care, and attention, Allah yamuku albarka gabaki daya, kotu zata nemi Baban su Khalid, bayan an raba auren zan baki kudi ki kara expanding business naki, settle down mutuwan aure bashine end of the world ba hasalima is Nothing, kawai ki dage da addu'a sanan kizama mai yawan tsoron Allah kinajina" gyadamai kai tayi, yay murmushi yace "tashi kitafi kinji" tashi tayi ahankali saikuma tajuyo ta kalli Baban nata, batasan lokacin dataje da gudu ta tsugunna gaban kujeran dayake kawai tasa kanta aguiwanshi tahau kukaba sosai, tace "Baba u are the best father in this world, thank you Baba" dagokanta yayi yakai hannunshi yasharenata hawayen kaman wata karaman yarinya yace "I don't take my children for granted, babu wanda ya isa yabanzantar min da my girls, oya dena kukan ya isa haka, kome kikeso ki gayawa mamanki gatanan, ranan visiting din su Khalid kuma zaki kiga yaranki ki musu shopping okay" gyadamai kai tayi yace "to tashi kitafi" tashi tayi ahankali tawuce tatafi duk suka bitada kallo cikeda tausayi dakuma so, Baba ya kalli Hydar yace "start with the procedures, akaimai sallama yau yau dinnan" gyadamaikai yayi yatashi yafita feeling so proud of his Dad, Mahaifinsu wani irin kalan mutumne, tun suna yara yake koyamusu always respect women, mata abin tausayine, abin atausayamusu ne, sanan akuladasu alallashesu, idan kaduba kagani zakaga nafarko daga hakarkarinmu maza aka yosu, to akanme zaku wulakanta su, Baba kan yawan cemusu Annabin mu yariga ya kwatoma mata yancinsu dan haka dole mu daraja su, mu tausayamusu kodan hayayyafomana dasuke yi, Baba always say never hit a woman, Baba nada wani irin believe inhar ka kulada mace, kasota, kabata attention to wlh zata bika kaman kamata magani bazaka taba samin problem da itaba, murmushi kawai yayi yashiga mota yaja zuwa Shari'a court.

Post a Comment for "MATAN ASOKORO COMPLETE HAUSA NOVEL"