Kanwar Maza Hausa Novel

Kanwar Maza 28

Ayshercool.

Paid book ne, 500 ne via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank, sai a tura shaidar biya ta 08081012143, wanda suke ba a Nigeria ba kuma, za su iya saya a arewabooks*

Gaba ɗaya suka bi ruma da kallo, ita kuma ta ƙare masa kallo ta ce “in biyo ka mu je ina?”.

“Cewa ki ka yi sai dai ayi miki duk abin da za ayi miki, abinda yakamatan zan miki ai”.

Ruma ta ce “Koma mene ka yi mini a nan ba in da zani”

Mutumin da yake ta ƙoƙarin bata kariya ya fara fusata ya ce “Wai ke wace irin yarinya ce?, duk yadda za ayi a kare mutuncinki a rabu lafiya ana yi, amma ke sai ka ce baki san ciwon kanki ba, ke kin san me zai miki ɗin ne ki ka tura baki kina cewa ayi miki koma menene?”.

Cikin kuka ta ce “Ta ina kake kare mutuncin nawa, da kuka haɗamu maza da mata kuka rabo ni da ‘yan uwana, yanzu ka gama cewa a kasheni, wallahi babu in da zani daga nan, koma me zaku yi mini ku yi mini ni na gaji”

Su kansu waɗanda aka kamo su tare da ruma mamaki suke yi, yadda take rashin mutuncinta yadda ta ga dama.

Ƙaton nan ya sanya ƙafarsa iya ƙarfinsa ya taka ƙafar Rumaisa, ta riƙe kanta ta yi wata irin ƙara, ba ta warke daga waccan azabar ba ga wata ana gana mata, ji ta yi kamar ya karyata, saboda azabar da ta ji, dan ƙato ne na gaske.

Mutumin da haryanzu ba ta san sunansa ba ya ce “Ina ga daga yanzu ba zan sake magana ba, su yi miki duk abin da zasu yi miki, akwai dalilan da yasa nake baki kariya, amma tun da ke na fuskanci baki da hali, duk abin da aka yi miki ke ki ka saya, idan baki nutsu ba haka zaki ta shan baƙar wahala, kina raye amma na lahira sai yafi ki jin daɗi, ki cigaba mara kunyar banza”.

Fuska duk hawaye cike da dakiya ta ce “Eh ayi mini ɗin, ku kasheni daga nan sai me?, wallahi ba zan daina magana ba sai kun gaji kun kasheni, kuma ba lambar wanda zan bayar a gidanmu, ku da Allah ba zan yafe muku ba, ba laifin da na yi muku kuke cutar da ni, Allah ya saka mini duniya da lahira”.

Buɗe baki yayi yana kallon rumaisa, ga fuska duk busashen jini, amma sai kwaroroto take ba tare da ta na tsoron ayi mata wani abu ba.

Aikuwa ƙaton nan ya dinga takata da ƙafarsa, yana dukanta tana ihu tana “La’ila ha illa anta, subhanaka inni kuntu mina zalimin” shine kawai abin da take maimaitawa, dan idan ya takata ji take kamar ana buga mata itace, ko wani nannauyan ƙarfe.

Ɗayan kuwa yana kallo bai kuma cewa komai ba, sai da ƙaton nan yayi mai isarsa ya ƙyale ruma, ba dan ta yi shiru da bakinta ba, sai dai ihun ma da ƙyar take iya yin sa saboda ta galabaita. Haka kowa ya zura mata ido yana kallonta, duk wurin ita ce ƙarama sauran duk da girmansu, amma tafi kowa baki da rashin mutunci.

A gigice mama ta dafe ƙirjinta, hawaye na zuba daga idonta, mutane na ta bata haƙuri, amma a zuciyarta take jin kamar wani na faruwa da rumaisa, mussaman da zuciyar ta ta ta tsananta bugawa.
Idan ka ga mama sai ka zata wani ciwon tayi, duk da ba mace ce mai ƙiba dama, amma ba ramammiya bace ba, tana da kumarinta, amma lokaci guda duk ta zube sai tsawo.
Ba ta iya cin abinci sai su Abubakar sun yi da gaske, da rarrashi da ban baki, ake samu ta ɗan sha abu mai ruwa-ruwa. Duk wata walwala da ake a gidan nan suka dainata, bacci kuwa sai dai ɓarawo, babu mai iya yin sa yadda yakamata a gidan.

‘yan uwa da abokan arziki ana ta shige da fice, ana yi wa mama jaje tare da addu’a Allah ya baiyyana ruma.

Habiba ce ta faɗo gidan su rumaisa a gigice, ta din ga kallon yayyen rumaisa da mutanen da suke zazzaune, can ta hango mama, ta ƙarasa wurinta da gudu, ta zube a kan gwiwoyinta “Mama, wai da gaske an sace ruma?”

Mama ta ƙura mata ido, amma ta kasa magana.

Maƙwabciyar su ruman ce ta ce “Eh da gaske ne, yanzu ku je ku yi ta yi mata addu’a, Allah ya bayyanata cikin aminci, ya tsareta a duk in da take”.

Rushewa da kuka habiba ta yi, tana wata irin sheshsheƙar kuka, gaba ɗaya ta gigice tana wani irin kuka.

A fusace mai sunan Baba ya ce. “Dalla ku fitar mana da mai ihun nan, da wane zamu ji?”

Aliyu yayi saurin cewa “A’a ba haka yakamata ayi ba, akwai shaƙuwa a tsakanin su, bai kamata a hantareta ba”

Aliyu ya fita ya je ya samu Habiba, ta haɗa hawaye da majina tana kuka, ya tuna faɗace-faɗacensu na ƙuruciya tsakaninta da rumaisa, kullum cikin sintirin kan ƙara ake, da yadda yake zaneta ita da yayanta a kan ruma, amma yau ta tayar da hankalinta saboda ɓatan ruma.

Hannunta ya kamo ya ja ta gefe yana rarrashinta, amma babu alamar za ta yi shiru, duk jijiyon kanta sun ɗaga idonta yayi jawur saboda kuka.

“Kiyi shiri kar kanki yayi ciwo, sannan addu’a zaki taya mu, Ubangiji Allah ya bayyana mana ita, ki daina kukan, mu je na raka ki gida”

“Allah ya sa kar a kasheta, Allah ya sa ta dawo gobe” ta faɗa tana sake fashewa da kuka.

Ƙwalla ce ta cika idon Aliyu, domin kuwa dauriya kawai suke yi, ya wayance ya ce “Amin ya Allah, dan idan kin yi salla ki din ga sakata a addu’a kin ji”
Habiba ta jinjina kai, tana cigaba da share hawaye. ya saka ta a gaba ya rakata gida, amma yanayin tashin hankalin da take ciki, zai tabbatar maka da ta kaɗu sosai da ɓatan ruma.

Hauwwaliya ma da take a zaune tana jinyar karayar da ta yi kafin tafiyar runa, ita ma haka ta burkice, dan da har tana mitar ruma ta tafi ba ta zo ta dubata ba balle su yi sallama, sai labarin an yi garkuwa da rumaisa suka ji.

Hatta malamansu ruma na makarantar islamiyya da take gallaba, gaba ɗaya suka shiga damuwa, makarantar kanta kamar ana zaman makoki, saboda babu wanda bai santa ba da halinta. Ita kanta tsohuwar da take sayar da kayan yara a makarantar, da suke yawan faɗa da ruma sai da ta yi kuka, dan wataran idan sun yi faɗa wata ran suna shiryawa, dan idan ruma ta zo da abinci wataran tare suke ci, duk rashin jin ta akwai shiga rai.

Takawa yana kwance a ƙaton falonsa a kan doguwar kujera, yayi zurfi sosai a cikin tunanin da yake yi, abubuwa da dama sun yi masa yawa, gaba ɗaya ya rasa wace matsalar yakamata ya fara tsayawa ya nemi mafita a kai, duk matsalar da ya tunkara, sai abubuwa sun ƙara taɓarɓarewa.

Wani irin zazzafan zazzaɓi ne ya kama ruma, saboda wahalar da ta sha, ga azabar cizon sauro da kuma sanyi suka haddass mata zazzaɓin.
Babu wanda yake ta tata, balle ya taimaka mata, tuni wasu aka fara bayar da kuɗin fansarsu, idan sun ga dama su bayar da mutum, idan ba su ga dama ba su karɓi kuɗin sannan su kashe mutum su ja gawar zuwa bayan wani babban dutse da yake nesa kaɗan da in da suke ajiye mutanen su yar gawar ba tare da suturta gawar ba.

Ruma na kwance ta takure tana ta rawar sanyi, ga azabar ciwon jiki, saboda dukan da ta sha, wasu mutane suka zo a kan babur, wanda aka goyo hannunsa ɗauke da ƙatuwar jaka, ta ɗaga ido dan ta ga su waye, wa za ta gani, dattijon bafullacen nan, da ta haɗu da shi har ya rakota gida a garin su Gwaggo.

Kallonsa take, amma ya kawar da kai kamar bai taɓa ganin ruma ba, ya basu jakar, shima suka bashi wata jakar ya hau babur ɗin aka bar wurin da shi. Tunani ta shiga yi a kan abubuwan da ya gaya mata, da kuma tunanin meye alaƙarsa da wannan mutanen? Kenan duk shiri ne?” Idonta ya sauka a kan lambar dake jikin jakar, sak irin lambar jakar da aka nuna mata bullet a ciki lokacin da za su zo katsina!

1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Check Also
Close
Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected