Tantiriya a Gidan Yari Book 2 Page 46-50
PAID GROUP 300
ACCNT NO
0175487861
ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK
YAN NIGER
+22790795939
TANTIRIYA
A GIDAN YARI
BOOK 2
~YARAN JAURO~
46-50
Official
By
AsmaBaffa
SADAUKARWA NE GA
AIDA MAMAN TASNIM
PAGE NAKI NE
Sadiyabala58
UMMIN SADDIQ
ALLAH YASA AYI AIKI A SA’A.
ALLAH YA BAKI LAFIYA ME DOREWA ME AMFANI TARE DAMU GABA DAYA DA YAN GROUP DIN TANTIRIYA A GIDAN YARI GABA DAYA DA MA AL’UMMAR MUSULMAI.
Maryam wata Digital camera ta dakko Yar karama ta Maida video din cikin wayarta,tace nayi nayi ya so ni yaki kawai sai naji zai auri Iman ashe shirme nayi na hada su daki daya da Iman ya mata ciki gashi zai aure ta,ni wacce jaka ce ne? Ya akayi kaina ya kulle,tsaki ta ja wlh sai na tona Masa asiri.
sabon layi taje ta siya ta bude Whatsapp da shi sannan ta Nemo duka numbers din yaran Jauro mata da mazan har su Karima da basa gidan suna gidan miji da Jauro ta hada tayi marking ta tura musu gaba daya har ogan Annoor da Iman din kanta.
Lokacin Annoor Yana Office Yana duba wasu files Dan shi baya ganin marasa lafiya sosai,Wanda suke aiki karkashinsa suke dubawa, ba kowa yake dubawa ba,kula yake da komai na asibitin tunda Yana da likitoci
gasu nan da yawa.
Yana duba file hannunsa rike da biro gefensa lemo ne a kwali,wayarsa ce tayi vibration na shigowar sako har bazai bude ba sai yaga bakuwar number Kuma an turo video,dubawa yayi ya bude video din Yana kallo,idonsa ya Murza da hannu daya,wayar ya ajiye a gefe ya sake Murza idanuwansa sosai da hannu biyu,ya jawo wayar ya sake bude video din yaci gaba da kalla yace Kai kamar fa ni,Baki ya bude ganin Iman,gefen kansa ya daka da hannu tare da girgizawa ko ba kalau yake ba,dawowa farko yayi yaga yanda aka fara hasko su a zaune suna Shan Ice cream,Nan take ya tuna ranar,yaga hotel din tabbas ranar da Iman Bata kwana a gida bane an mata fyade.
Yace Innalillahi wa innailayhirrajun ya akayi to ban sani ba ban San nayi ba? Salati ya dinga yi ya ajiye wayar tare da zuba tagumi,tashi yayi ya mike kawai ya ajiye aikin ya fito cike da tsananin damuwa,gida ya nufa Wanda bangaren Yan gida ma kowa ya gani,Iman tana kwance tana chating sakon ya fado wayarta,tana dubawa ta sake kalla wayar tayi jifa da ita tasa hannu a baki sai kuka.
Jikinta na rawa ta fito Palo kenan Jauro ya shugo Wanda shima ya kalla,yace ta faru ta kare munafukai Allah ya tonu asirinku,Ashe abinda kike yi kenan,kunci amanata ba a Dan iskan namiji sai mace, da ace baki bada kanki ba bazai taba ko gwadawa ba Iman,kanku kuka yiwa ba ruwan Jauro wlh.
Haidar ne ya shugo shima ya gani takaici yasa ya dawo gida ya zaci shi kadai ya gani,Shima Nabeel fitowa yayi Yana dakinsa yau Bai fita ba tunda yaji tarihinsa ya daina sukuni,matan ma duk fitowa suka yi,Rahma da Nabeela,Sajid Yana gani ya goge shi gaba daya a wayarsa,Laila da Karima ma duk gogewa suka yi daga wayarsu suna gidan auren su.
Hashimu ne ya shugo ya tsinci labarin yace mu Gani nima,Jauro yace tsaraici ne babu kyan Gani ni na goge ma,Habiba tace abi a sannu ba lallai ace….Abba ne yace yi mana shuru ai ke dama Sailuba ce ko me aka yi dai dai ne,Abba ya shako Annoor yace Dan ubanka tsaya a nan tsakiya mu saka a tsakiya Kai wanne irin Dan duniya ne Kaine Dan Sunna amma sai aka samu abin kunya a wajenka,ya Kalli Iman yace ba banza ba Ashe kike makale Masa ashe da abinda yake baki a sirri.
Annoor jajayen lips dinsa ya turo yace nifa ba abinda nayi ban San komai ba,yes Ina son Iman amma bazan taba lalata ba wlh, ni da ace ni dan Kwalta ne ko me mata hudu bazai fada min wankan tsarki ba indai akan Iman ne amma ta ya zan mata haka da hankalina,Jauro yace dan ubanka wannan waye idan ba kai ba? Annoor yace gunki nane amma ba ni bane,ka zauna kana tabe yarinya kana shanye mata kirji kace ba Kai bane,Annoor yace ai Kuma Kawu yafi na sha Wiwi,da mutum ya Sha Wiwi gwara ya sha nonon mace,Abba ne yayi sauri ya toshe kunnensa da hannunsa ya juya wajen Jauro,Jauro shi Kuma Gani yayi Annoor Kuma da gaskiyarsa a nan,Abba yayiwa rada yace kaga Kuma da mutum ya Sha Wiwi gwara nonon matarsa ko ya kace,Abba yace na Dade da sanin haka,yaran nan na yanzu da iya magana suke,Jauro yace muci gaba da yi musu fada,radar suka daina Jauro yace koma me kayi Kaine zaka aureta sai ka karasa ragowarka da ka rage,Abba yace shine magana itama Yar banza fitsararriya ai da Gani zata aikata itace ta bashi dama azzaniyatu kawai,Iman tana kuka tace wlh ban San komai ba fyade yayi min bana kaunarsa bana sonsa ko an aura min shi ya hadu da masifa da bala’i,Annoor yace ni ance miki sonki nake ko ni ruwan Sanyi ne zaki Raina min hankali ko nasan na yi wani abu Dake,wlh ka sani Allah ya is….kafin ta karasa Kawu ya sharara mata Mari,yace ya girme ki kice zaki zage shi,wa yace ki bashi hadin Kai kece babbar marar kunya ai,Annoor harda fari da Ido ya Kalli Iman,Abba yace baka kyauta ba Jauro shima a mare shi ai shine Jagora,wlh sai an mare shi ya kamo kunnen Annoor Yana cewa ya lalata yarinya marainiya ga halin da take ciki Kuma ka mare ta,Jauro yace na tsani rashin kunya ni bana son yaro ya raina babba,wlh ni na rike ku ba Wanda ya isa na sa doka ya tsallaka,na Sha fada miki bana son rashin kunya shi zaki zaga,Bai girme ki ba? bana fada muku cewar za a iya wasa da dariya amma banda Raina babba bare ki zage shi,tare kuka yi iskancinku ki dawo Kuma kina shirme,ko bakya so sai kin aure shi,shine ma gatanki ki sani,yasan asalinki kin San asalinsa sannan ga abinda ya faru a tsakaninku wa kike nufi zai rufa miki asiri idan ba shi ba.
Iman tayi tsaye Sororo tace ai shine ya min fyade shi yasa ya min dinki ya bani kwayar Hana daukan ciki sabo da yasan ya cuceniiii….ta karasa da kuka,Habiba tace na yarda dake Iman sabo da Sanda ake duba ki ya zaci ciki ne Dake har da suma Yana gudun abin kunya,Jauro sai lokacin ya tuna da abinda ya faru a baya,yace biri yayi kama da mutum,Abba yace na dawo bayanki Iman Kai Annoor jakar ubanka lalatacce,Jauro ma yace mun gane gaskiya Iman kece da gaskiya.
Annoor yace amma Abba ku tuna fa wlh ban sani ba ta ya akayi idan Ina nemanta ban San tayi ciki ba,ta ya Ina Likita zance a duba ta ai baza kuji labarin ba ma,Abba ya sake daga kai sama Yana tunani yace kafi Iman gaskiya Annoor,Jauro yace ni dai Ina bayan Iman,Abba yace na zabi Annoor,Habiba tace Dan Allah wannan abin nasu fa bincike ya kamata ayi da alama basu San sunyi ba,sannan a duba waye ya turo sakon,a tsaya ayi Duba da bincike,amma ku kanku an kasa gane me gaskiya a ciki,kuce Kuna bayan wannan anjima ku koma bayan wannan ba shine ba,Abba yace to gwana ta gwanaye..
Nabeel yace gaskiya ne Ummi ni na yarda dukkansu baza su aikata ba,kowa yayi hakuri a dauka kaddara ce ayi musu aure a hankali ma gaskiya zata yi halinta,Allah baya bacci.
Rahma headphone dinta ta gyara tace mu akewa kallon Yan iska sai gashi,Yaya Annoor har baya so Iman ta zauna da kayan bacci a gidan nan ana tattalinta,gashi ashe mu namu me sauki ne, Allah ya bayyana gaskiya amma tunda aure zaku yi ai normal ne,Nabeela tace gaskiya wlh da matsala ayi bincike sosai,Rahma tace Yaya Annoor har duka ne yake idan ya ganni da wani Ashe shima Yana dan ehhh ehh…Jauro ya galla mata harara tayi shuru.