Hausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 52

52
Kasa bacci tayi sbd zafin jikin Amnah datakejin Yana shigarta ahankali Yana dumama nata jikin,

Umme ce tashigo jinta shiru ta tadda cikin wannan halin itama cikin damuwa tace ko Akira likita cikin dare.

Cikin nutsuwa da sanyin jiki Bena tace

“Kodai a bari zuwa da safe Umme sbd dare yayi Kuma ta samu bacci may b kafin da safen ta warware inshallah.”

Ok Allah yasa Hakan Amma dazu fa Rana tana tareda daddynta har yamma har fita sukai suka dawo
Shima inaga Bai San zazzabin ya shigeta ba harya wuce.

Numfashi kawai Bena ta sauke sbd gwara da Bai sani din ba Dan dole dayansu zai kasance da Amnah din ita Kuma idan Amnah na ciwo Bata iya barinta sbd damuwa da susucewan datakeyi.

Bayan fitan Ummen Zeenah tashigo ta hawo gadon Tana shafa Amnah din daga Nan bacci ya daukesu su duka anan Zeenah ta kwana dasu.

Washe gari da safe jikin nata da Dan sauki ba laifi,.
Kaman bazata iya fita tabarta haka ta ringa tarairayarta har kusan 10 kafin ta shirya ta fice zuwa office bayan taje gurin dd babba suyi magana.

A office yau hankalinta ya Dan rabu biyu so Bata Wani jimaba taba gama aikinta ta juyo gida tareda fahat Daya baro motarsa office suka dawo tare.

Ta gate din gaba suka shigo sbd yace zai duba Amnah din da babu lafiya.

Tare suka fito motar Yana kallan yanda duk batada kuzari ya saki Dan murmushi me sanyi Yana mamakin soyayyar datakewa Amnah duk kawaicinta akan komai Banda Amnah.

Itace a gaba gurin shigowa palon kafin shi a kan Amnah dake jikin daddynta idanuwanta suka sauka Shima Kallo Daya yayi musu ya dauke Kai Yana cigaba da wayar Dayake Yi da likitan dazaizo ya duba Amnah jikinta ya sake rikicewa da yamman.

Tana ganin mummynta ta miqa mata hannu Daya tana fara hawaye da Kiran sunanta ahankali.

Qarasowa Bena tayi ta kama hannun Amnah din wadda ta janyota ta zauna ba shiri tana kokarin matsawa ba dama sbd riqetan da Amnah din tayi tana hawaye cikin zafin ciwo.

Jikinta dake gugan nasa sbd kusancin da yayi yawa yasa ta Dan kallan gefen Umme dake gaisawa da fahat
Shi kuwa har lokacin Bai motsaba barema ya nuna yasan da Wani ya zauna gefensa.

Ahankali daqyar ta iya Bude baki murya a sanye tace

“Amnah muje daki naji Yaya jikin naki,
Na sake baki magani.

Lafewa tayi jikin daddynta tana Dan girgiza Kai ahankali Bata iya magana.

Fahat Daya gama gaisawa da Umme dawo da kallansa kan DD yayi ya masa magana suka Dan gaisa sama sama sbd Dawood din da hankalinsa ke kan Amnah.

Miqewa yayi ya tafi bayan duba Amnah itama Bena data kasa nutsuwa da zaman nasu ahakan ta zame hannunta daga na Amnah ta miqe ta bar palon.

Daki ta Isa tana sauke ajiyan zuciya a boye kafin ta wuce tayo alwalan sallar laasar data wuceta ta fito tayi.

Tana idarwa ta fito sbd takasa samun nutsuwan jikin Amnah.

Ko da ta fito likita yazo yana duba Amnah din.

Gefen Umme ta silalo ta zauna a hankali tana sauraran Abinda likita ke fadawa DD.

“Sanyi ne kawai yake son Dan shigarta sai a kiyaye barinta wasa da ruwa gaskia”

Juyawa yayi ya Kalli Bena dake bayan Umme likitan yace

“Madam ai last time na fada Miki Hakan please a sake lura sosai a kiyaye.”

Ajiyan zuciya ta sauke tana gyada masa Kai ahankali.

Magani yace zai Aikowa Amnah din yayi musu sallama ya wuce.

Bayan fitansa bacci ne ya dauke Amnah din har lokacin tana jikinsa.

Shima zazzabin yakejin Yana Neman kamasa sbd zafin jikinta da tin dazu yake shiga jikinsa Kuma shi fatansa batada Wani karfi da wuri wasu abubun ke saurin shigesa.

Abincin dole Bena ta miqe taje dining taci tana gamawa tayi dakin Zeenah Datake ta fama da nata aikin kwana biyu sbd itama zatai joining kamfanin Amma Kuma tana buqatan attending wasu online classes na sati uku ga service dasuke Shirin zuwa wannan Karan inshallah itada Bena din.

A dakin suka zauna itace ta ringa fahimtar da Zeenah din wasu abubuwan na course nata datai attending Wanda ya banbanta dana online da Zeenah keyi Kuma gashi Wanda Bena tayi dama ce da sai Dace ake samunta yanzu bazaa sake course din ha sai after like 3 years.

Har kusan 9:40 tana dakin kafin ta fito Takoma dakinta tana mamakin Ina Amnah ko tana dakin Umme.

Bedroom dinta ta Bude ta shiga Kai tsaye..
Ac din Dayake kashe ya saka mahaukacin qamshinsa yiwa dakin Wani irin gaurayar data sakata kallan gado Kai tsaye.

Zaune yake bakin gadon har lokacin Amnah na maqale dashi taqi yarda ya tafi yabarta.

Idanuwansa Wani laushi sukai da suka sakata rikicewa tana rudewa da kallansu tafara kokarin juyawa a hankali cikin Wani lazy sauti yace

“Kinsan meye time kuwa?”like kinsan ana duba time kuwa??

Dakatawa tayi tareda kasa fita tana daidaita numfashinta dake Dan fita da qarfi ta juyo ahankali batareda ta kallesa ba ta Kalli Amnah wadda da alama tana Jin zazzabin sosai har lokacin sai taji jikinta ya mutu ahankali ta Dan dago tanasan kallansa Amma ta kasa iya sake kallan idanuwansa ta Bude baki ahankali ta furta “sorry na bari kayi having time naka da ita ne”

Bai iya cewa komai ba sai kallan da yayi mata na minti Daya kafin ya Dan sauke numfashi Mai dumi da zazzabin dake cinsa Shima yakai hannu zai Zame Amnah ta sake qanqamesa cikin bacci da radadin ciwo tareda ambatan sunansa cikin bacci da qaraman muryanta me taushi.

Shiru sukai dukkaninsu suna kallanta shi Kuma zuwa lokacin zazzabin yakeji sosai Yana buqatan zuwa gida sosai.

Lumshe idanuwansa dasuka sake saka Bena Neman rudewa ga ciwon Amnah da riqesan da Amnah tayi ga idanuwansa da duk ya motsa su saita ji tana Neman rudewa.

Ahankali ya dago ya Kalli Bena din jinta shiru takasa qarasowa ta karbi Amnah din daga jikinsa.

Ganin kallan da yayi mata ya sakata takowa ahankali ta iso gurin hannuwanta na Dan rawa ta ranqwafo takai hannuwanta cikin sanyi ta Dora akan na Amnah dake qanqame da jikinsa.

Dumin numfashinsa Mai zafi ne ya sauka wuyanta zuwa cikin rigarta ahankali take rawar hannunta ya qaru ahankali ta Dan rintse idanuwanta tana Kai hannunta Daya zata Ciro Amnah numfashin nasa Mai dumi ya sake saukar mata a fatan wuya ta Bude idanuwanta dake rintse ta kallesa daidai Shima ita din ya kalla ganin hannuwanta na rawa ahankali.

Kallansa tamkar wata fitina ce ga duk Wanda yayiwa irin wannan kallan na cikin tsakiyan Ido Dan haka haduwan idanuwansu ya sakata miqewa ahankali daga raqwafan da tai tana cika masa hanci da qamshinta Daya sake tsananta zazzabinsa.

Hannunsa Daya taji akan nata daidai lokacinda taso matsawa baya zata bar gurin sbd saukan dumin numfashinsa fatan jikinta zazzabin itama zai saukan mata.

Tinda take rayuwanta yau ne ranar farko da namiji yayi mata irin wannan rikon Dan haka Saida bugun zuciyarta ya tsaya cak ta rufe idanuwanta ahankali kafin tayi Wani motsi ya Dora hannunta kan Amnah ya Zame a hankali ya miqe ya fice daga dakin yabar dakin da fitinanniyar qamshinsa.

Kasa motsawa tayi tsawon seconds tukuna ta iya motsawa ta silale ta zauna bakin gadon inda ya tashi har lokacin tana sake Jin saukan dumin numfashinsa akan fatarta.

Gyarawa Amnah kwanciya tayi kafin ta miqe ta shiga toilet Bata Wani jima ba ta fito ta saka pyjamas masu tsantsi ta hau gadon ta kwanta tareda hade kanta dana Amnah pillow Daya tana Jin qamshinsa na shiga hancinta a duk numfashin da zata ja.

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Check Also
Close
Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected