Hausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 87

*_Arewabooks@Mamuhgee_*
87
Kansa kasa yarda yayi da Abinda yaji Dan haka ko ganin gabansa bayayi ya juyo yabar dakin ya fito jiri na juya Kansa sosai ya sauko qasa kaman Wanda yake cikin maye haka ya Isa motarsa ya shiga ya zauna zufa na feso masa Tako ina yanajinsa a wata duniyar ta daban,

Kansa ba zafi yakeyi ba wuta yakeci sosai da sosai,
Bena dinsa ce ake fadan ta taso a wannan rayuwar dayakejinta kaman duniyar wasu dabbobin ce ake fada?

Bena dince ta taso tana wankin wasu qattin Maza?
Bena dinsa ce ake maganar da yanzu tana hannun yan drugs?
Bena dinsa ce ake maganar ta taso cikin yunwa da wahala irin wannan da ko karensa bazai iya bari ya Rabi irin wannan wahalar ba bare ace Macen datayi nasarar da Saar shiga inda babu wata mace a duniya data shigar masa wannan gurbin,
Bena dinsa ce ake fadan ba ita bace asalin macen da ‘dan uwansa ya so ba,ya muaamalantu da ita suka samu ciki ya haifi Amnah ba….

Bilal da sumayyah ana nufin tare suka  Kone a motan Bilal?
Idan haka ne meyasa gawa Daya aka Gani?
Hakan na nufin dayansu na Raye?
Waye cikinsu a Raye?

Innalillahi wainna ilaihi rajiun”

Wannan mutumin daya haifi su Bena mutum ne kuwa kokuwa wani dabban ne Allah yayi da suffan mutane?

Antaba Kaisa Asibiti antabbatar da lafiyansa kuwa?sbd wasu mutanen ana zaune dasu ne kawai batareda ansan mahaukata bane masu asalin Abinda ake kira hauka.

Wata rawa jikinsa keyi sosai zufansa na qaruwa sbd Wani mummunan zazzabin tashin hankalin Abinda Bai taba ji ba ko tsammata a rayuwar ba Daya rufar masa a take.

Hannuwansa na rawa ta tayarda motar Yaja Yana fitowa daga parking lot din gurin Yana daukan iPad din Naseer dake hannunsa ya nema Naseer din Kai tsaye ya sanar dashi ya Siya masa ticket din komawa Nigeria yau din Nan komai tsakan dare.

Naseer na samun sakon ya miqe daga kwancen Dayake cikin mamaki da tsoro da fargaban ko DD din yaji maganar Bena ne.

Fitowa yayi yaje har bedroom dinsa ya dubo yaga baya gidan ya fita yaje ya duba motarsa ma Bata gidan take yasan yasan komai na maganar rashin sanin inda Bena din take Dan haka baida zabi bayan cika umarnin DD din.

Take yayi contacting Wanda zai Siya musu ticket da komai take sukai sa’a akawai jirgin dazai tashi zuwa Nigeria cikin Daren Dan haka dole ya hau hada musu kayansu ba tareda ko Zeenah ta saniba sbd tayi bacci na gajiya da rashin nutsuwar zuciya dasuke ciki musamman ita da kullum Kuka takeyi sbd shakuwa da kaunar dake tsakaninta da Bena ga tsananin tausayinta da kaunarta data qaru a ransu me tsananin gaske bayan da dd babba ya fada musu komai gameda raywarsu Bena din wadda hatta Umme data ji sai data kwana tana Kuka itada Zeenah,dad kaante kuwa Jin yakeyi da shine yasan da Hakan tini da bazai iya bin komai a hankali dinba kama Ababan zaayi a batar dashi gabaki Daya Annen Kuka ai insha Allah aikin zai karye ko baya Nan.

Koda DD ya iso gidan Yana shigowa bedroom dinsa kawai ya nufa ya a sauya kayansa daga na bacci Daya fita dasu baa cikin nutsuwa ba zuwa Riga da wando marasa tsayi ya saka facemask da Fcap ya fito Kai tsaye ya fito
tini Naseer ya saka kayansu a mota Dazata kaisu airport suka wuce.

Har lokacin cikin Wani irin mummunan hali yake sbd zazzabin dabai taba shiga bane a jikinsa hakama zuciyarsa Wani irin wuta take ci dashi tana qarawa jikinsa zafi da zufa.

Maganar ma rashin ganin Bena ganganci ne ake fada bayan ansan yanda tayi rayuwa hannun mutumin dayake amsa sunan ya haifesu Dan haka shine na farkon zargi ma akan batanta,
Fatansa dai yanzu yafara zuwa ya tsaya gabansa suyi magana ta billions tinda itace yarin dayafi Ganewa akan komai.

Idan kudine matsalansa to zai nuna masa kudinsa ko uwarsa ce calculator saiyayi batan lissafin da zai Basa shikuma Abinda yakeso daga garesa na Ina Bena take.

Hakama zai ninka masa ninkin su ya siyar masa da yancin Annen Bena ko nawa ne ya fada zai Basa daganan zai aikasa inda yakamata ace tini an Dade da aikasa sbd Bai yarda shi din me hankali bane.

Suna Isa airport ko awa Daya Basu rufa ba jirginsu ya daga zuwa Nigeria.

Dagawansu baifi da awa Daya ba Zeenah ta ankara da cewan ita kadaice a gidan take tahau Neman wayar Naseer Bata samu sai ga sakonsa Daya tura mata tin kafin su tashi ya shigo a lokacin na cewan D ya sakasu komawa Nigeria a Daren.

Tana ganin sakon hankalinta yayi mummunan tashi gigice ta kira dad dinsu ta fada masa.

Shima tashi hankalins yayi sbd yasan zafin kan DD bazai bari a tsaya ana komai a nuku nuku a boye ba sbd kada sunan family ya lalace akan Benan Nan ya fahimci yafison kowama ya sani sunan Kaantes ya dade Bai Baci ba.

Da Kansa ya fito dakinsa zuwa dakin dd babba ya sanar dashi halinda ake ciki.

Shiru dd babba yayi Shima baiso Hakan ba dan haka yace suma ba amfanin zamansu a nema musu jirgi gobe su koma.

Dad kaante na ficewa wayarsa ya daga ya kira Abbakar ya sanar dashi a sake budewa Ababa wuta harma dasu Safnah din asake Bude musu wuta ta yanda Wanda yakeda hannu acikin batan Bena zai iya yin Abinda zaa ganesa da wuri kafin DD ya iso zafin abin zai iya baci sosai.

Yana gama waya da Abbakar baccin dake idanuwansa ya kaurace gabaki Daya sbd baisan me Dame DD ya saniba a cikin Daren dazai iya barin qasar a take.

Umme ma hankalinsu tashi yayi data samu labarin abinda yake faruwa na tahowar DD Dan haka ta kasa samun nutsuwa kwata kwata.

************
Ababa a Karo na biyu Abbakar ya sake kawo masa kudi tareda buqatan son gaisawa da Anne wai Bena zatayi magana da ita a waya.

Shiru yayi wannan Karan qin karban kudin yayi ya Dan dake ya koma cikin gida ya jima kadan ya fito ya Kalli Abbakar yace batajin dadi bazata iya fitowa ba ta kira ni zuwa anjima zan hadata da Annen.

Hakan Daya fada ya saka Abbakar cewa shikenan sukai sallama ya miqa masa kudin dayazo dasu baiyi Niya ba Amma sbd kada a Gane komai saiya amsa kudin kawai Yana washe bakin qarfin hali sbd lamarin yafara isarsa.

Abbakar na wucewa yakoma cikin gida Yana hada zufan tashin hankali da tsoro sbd ya tabbatarda akwai abinda yake faruwa,

Wai shi wace qaddarar ce ma ta Kaisa hadewa dasu Safnah?

A baya duk barnarsa dayake abarsa cikin rufin asiri da lumana,
Tafiyar Bena zir na Neman janyo masa masifu kala kala Dan haka wlh bazai yarda su jefasa masifar datafi wadda yake ciki ba ta sanin gaskiyarsa da kaantes sukai akane haihuwar Amnah.

Hande data ga Yana hada zufa ransa bace Yana Neman recorder dinsa da yayiwa mummunan boye wadda duk Abinda su haj Nuratu bulama da Safnah suka tattauna dashi akan abubuwan dasuke buqata.

Hakama abinda Basu saniba a ranar da suka Basa kudin Nan Bai baro gidan ba Saida ya qyalla Ido akan me aikinsu Rabi Daya ga yanda suke maganar komai a gabanta bayan takawo masa kayan Sha
Hakan ya tabbatarda masa da tasan dukkanin sirrinsu.

Ranar Daya tabbatarda Basa gida saidaya koma ya samu ganin Rabin Kallo Daya yayi mata maganin Dayake mata dashi ya kamata take ya bayyanar mata da buqatansa ta zai raba duk Abinda ya samu da ita Amma ta sanar dashi duka motsinsu sbd ya tabbatarda zasu iya munafurtansa.

Rabi data San halinsu ciki da waje Kuma taga yanda suke tsoran shedancin Ababa dayafi nasu take ta amince da buqatansa sbd ganin Suma sun yarfada da nasa balain yafi nasu Dan haka Rabi tasan sai tafi zama safe idan tana tareda Ababa Dan haka cikin qanqanin lokaci yagama sanin sirrinsu a gurin Rabi hatta video din yanda suka kashe hajiyar Alh basheer bulama tana dashi duka suna hannunsa.

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Check Also
Close
Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected