Acikin Gidana 11
⚡️A CIKIN GIDANA ⚡️
(SEX,ROMANCE,RUNS)
FATIMA ZAKARIYYA
EPISODE 1️⃣1️⃣
Kofar gidansu karima y
aje yana tunanin ta inda zai fara ,shi a tunaninsa yanzu ta gama gayawa kowa komai , Amman dukda haka zai daure yaji ko akwai abun da za’ayi kodan sbd mamansa ,ya Kira wayarta Amman ba’a dauka,daga karshe mh yaji kaman anyi blocking dinsa ,Rufa ido yayi ya shiga cikin gidan gabansa na faduwa dan baisan me zai tarar bh ,Baba ya tarar A tsakar gida ya kunna radio yanaji ,da mamakinsa sai yaga baba na masa murmushi har yana saurin gyara zama, simi simi ya karasa har gabansa yaje ya zube ya gaidashi ,ganin yanda Baba yaketa masa sannu da zuwa ne yasan toh ba lallai an gaya masa bh ,Baba dama gurin karima nazo ya fada yana kallon kasa yanata sosa Kai ,Ai kuwa bata dawo bh daga gidan huda ,Kuma ni ai na dauka saida yammah zakazo Bari na kirata ,mama ce ta fito itama ganin mubarak yanzu abun ya bata mamaki ,mubarak ai na dauka saida yammah ,shigo mana ka zauna itama nasan yanzu Zata dawo ,karima ce kwance tana ganin kiran baba ta dauka ,”Baba Ina yini “” lfy kalau kin taho ne ?” “ A’a baba banajin dadi ne Zazzabi nakeyi sosai “,” toh kiyi sauri ki lallaba ki taho ga mijinki nan yazo daukanki “, tana daga kwance saida ta tashi ,da kyar take magana sbd wani zazzafan ciwon Kai da take Amman haka ta daure,” Baba wlh bazan iya dawowa bh kamar zan mutu fah Baba banida lf..y kafin ta karasa ta fashe da kuka”,kashe wayar yayi yana tunanin toh lfy ,daga rashin lfy sai kuka,kallonsa yayi toh kaji wai batajin dadi Amman nasan nan da anjima Zata dawo ,babu komai Baba yace ,Bari naje gidan aunty Huda din na dubata,ya tashi ya musu Sallama ya tafi ,mama tanata murna take gayawa baban karima ,kaga dan nan ko ,yanason matarsa har yazo su tafi ,ita kuma ba wani rashin lfy kuma idan iskanci nema zatamin bayani ,Bari na fara hada mata kayanta kafin ta dawo ,a kofar gidan aunty Huda yayi parking daga gate ya tsaya yanata sake kiran wayarta Ko Zata dauka Amman bata shiga ,yaro ya gani ya kirasa ,Kai shiga gidan nn ka ce Wai Ana sallama da karima ,yaron ne ya shiga gidan yana sallama aunty Huda ce ta leko Lafiya ,Wai Ana sallama da karima inji wani a waje ,wani kuma wane ?? Wanine yazo a mota ,toh kace tana zuwa ,bayan ya fita ne tadan leka sai kuwa taga Mubarak,da sauri ta tafi , Tana shiga daki taga karima tanata kuka ta dafe kanta ta rasa mene yake mata dadi ,da sauri ta karaso ta riketa , Ke mene yake damunki ne ,kukan take har yanzu aunty Huda kaina ne yake min ciwo kaman zai fado,tana taba jikinta kuwa taji zafi sosai ,Subhanallahi tace,sannu Anya kuwa bazamu tafi Asibiti bah ,kinji jikinki kuwa karima ,ga mijinki can a kofa mah yazo ,da sauri ta dago jajayen idonta,yazo kuma ? Eh yazo Wai kije yana sallama dake ,wani kukan ta kuma fashewa dashi wlh aunty bazan je bh ,kaman zan mutu haka nakeji nah ,kaina ciwo jikina ciwo ,aunty Huda mamaki ta tsaya ,dan dagaske karima batada lfy ,kuma very serious ,yanzu toh ni ya zanyi ,Gaskiya karima tashi zakiyi mu tafi asibiti ,bazai yuba ,A’a wlh aunty bazan iya fita bh ,ki fita Kawai ki barni babu inda zanje ,hijab dinta aunty Huda ta saka ta fita ,har yanzu Mubarak yana cikin mota yana danna waya ,ganin aunty Huda ta fito ne yayi saurin Kashe motar ya fita ,har kasa ya tsugunna ya gaida ta,lfy tashi Mubarak matar taka ce wlh batajin dadi sosai ,ka ganta can Zazzabi takeyi jikinta zafi zau Amman taki harda mu tafi Asibiti ,har cikin ransa saida yaji wani Abu ,batajin dadi ? Aunty Huda dan Allah Ko zamu kaita asibiti baima San sanda ya fada bh ,aunty zan iya ganinta ? toh dan tsaya Ina zuwa tace ta wuce ta Shiga ciki, dakin ta koma karima mijinki yanason ya shigo ya ganki saiki gyara ,tashi tayi tsaye wlh tlh aunty Huda bazai ganni bh ,banason ganin kowa nace miki Banda lfy ta fashe da kuka ,aunty Huda dai ta tsaya ganin ikon Allah ,dan ita abun mamaki yake bata ,mene nata na rashin son ganin mubarak ,zama tayi ta fara bata Baki ,yanzu karima na dauka abun nn ya wuce,dare muka raba dake Ina gaya miki abun daya kamata yanzu mene naki na rashin son ganinsa ,koma mene tunda yazo har kofar gidan nn ai saiki hakura Ko ? ,tana kuka tana gyada mata kai wlh A’a aunty kibarni kawai ,kar ya shigo banason ganinsa inba haka bh wlh zan tafi kuma bazaki dake ganina bh ,tunda nace banaso banaso ki gaya masa,fita tayi ta kuma samunsa yanata raba ido yana jira yaji ance ya shigo, mubarak matarka fah batason ganinka yanzu tace ka barta ta dan huta ,kara rokonta yayi amman aunty Wai da in dan ganta ko ,kayi hakuri Mubarak yanzu dai ka tafi idan taji sauki Zata koma gida sai kaje ku tafi Ko ?,har ransa baiji dadi bh haka ya tafi ,Yama rasa gurin zuwa sbd haka gurin abokinsa Farouk ya wuce,Wanda yake haduwa dashi a joint,abun mamaki Yau Baiga Farouk bh and haka wayarsa ya Kira ,shiru shiru ba’a dauka bh ,sai wani ya gani agurin wanda duk Sun San kansu ,sallama Alaikum abokina ina Farouk ne , Wai Wai !! Tsohon zance ,ai Farouk ya dade a kwance bashida Lafiya yana asibiti an rasa mene yake damunsa ,gaskia ka dade Baku hadu bh kenan,ai inajin yafi sati a kwance ,wani asibitin ne ya tambaya aka gaya masa ,asibitin ya tafi direct
Gurin da akayi Admitting farouk ba kowane Ke shiga bh Amman shi yana zuwa ya nuna ID card dinsa aka barsa ya wuce ,yana shiga dakin yaga matar Farouk tanata kuka a gefensa ,ganin sa ne mh yasa ta tashi ta gaida shi ta fita ta basa guri,mubarak yayi mamakin ganin Farouk yanda ya zama ,yaushe muka Rabu dakai a joint,mutumina mene ya sameka haka lfy,bakinsa a karkace yake magana ,mubarak kaga yanda Allah ya maidani Ko ,garin kula kule nane naje na kwanta da wata yarinya Ashe tanada Cututuka a jikinta dayawa ,kuma yarinya saida tayi kusan sati a gurina na Kama mata daki Ina cinta ba dare babu rana , Ashe yar iskar nn bata gayamin tanada cuta bh harda HIV , dasu ciwon hanta da wani infection da maza suke dauka ,abokina kalli gabana ka gani ,wani dan zani ne aka rufe masa dick dinsa dashi ,Mubarak ne ya daga yana dubawa yaga gindin Farouk daga sama duk ya fara cinyewa ,Subhanallahi da sauri ya maida ya rufe ,wannan wani irin infection ne ya tambaya ,Farouk ne ya cigaba da magana yana hawaye ,Wai wani infection ne Wanda ake samunsa a dalilin kwanciya da mutane dayawa ,to inaga ta kwanta da maza dayawa Nima naje na kwanta da ita ,Mubarak tunda nazo asibitin nn naketa magani kudina sun kusa karewa ,ga dangin matata sun sakani a gaba Wai na saketa ,kukan nn da kaga tanayi kukan batason rabuwa Dani ne baiwar Allah ,taje anyi mata gwaji ita batada Ko wace cuta lafiyarta kalau ,dayake mh na dade ban kwanta da ita bh , Mubarak kaga yanda Allah ya maidani Ko ya fada yana share hawaye ,yanzu duk Wanda mh na taimaka a baya guduna suke ita kuma da nake gudu itace takeson zama dani ,itace take kula Dani itace take bani abinci a Baki ya fashe da kuka me cin rai ,abokina is not late for you ,ka kyale matan bariki ka kama Allah ka rike matarka ,kayi hakuri da shawarwarin Dana Baka a baya marasa kyau ,wlh babu me yi sai Allah ,da mutuwa ne ma haka zakaji anci na mutu. Ni yanzu da wnanan wahalar ai gwanda mutuwar, mubarak kwarai dagaske jikinsa yayi mutukar sanyi ,ya dimauta sosai ,sbd haka kudi ya fito dashi dayawa ya ajiye masa ya fita da sauri ,bai tsaya a Ko Ina bh shima sai Asibiti gurin gwaji ,yana zuwa aka gwada sah akace ya dawo ya karba results gobe ,kasa hakuri yayi yace Ko nawane zai bayar aje a fito masa da result dinsa, Haka kuwa akayi aka natsu aka duba ,cikin ikon Allah lafiyarsa kalau,tunda ya karbi result din ya fita bai tsaya a Ko Ina bh sai gida ,wanka yaje yayi ya fito ya hau kan sallaya ,Adduoi ya shigayi yana kuka yana rokon Allah ya yafe masa yana kuma godewa Allah dayasa lafiyarsa kalau yayi kuka sosai Sannan ya koma ya kwanta ,Aliyu ya Kira bai samu bh ,kamal shima ya kiraka bai sameshi bh, Shiru yayi yana kallon wayar sa matarsa ya shiga tunani da tana nn da tuni ta debe masa kewa koda kuwa da rashin kunyar nema ,tuna abubuwan da suka dinga faruwa ya dingayi ,ya SALLAM !!, na tafka babban kuskure ,yanzu ya akayi na Bari matata ta kamani da wnanan mumunann Laifin ??sai kuma ya tuna yanda akace tanacan Tana Zazzabi ,yanzu haka saboda halin Dana sakata ne ya fada yana maijin tausayinta ,kasa hakuri yayi ya kuma daukan key ya fita zai koma gurinta




