Qamshi Complete Hausa Novel

Qamshi 11-15

*✨QAMSHI  11-15 ✨* 

*✍️RASHOW*

                

tun k’arfe uku na dare na farka nayi istihara kamar yanda na sama raina Zanyi najima Ina sallah har asuba tayi, tashi nayi na gabatar da nafula wato salatul Fajr sannan na zauna a gurin nayi lazumi har aka kira assalatu mikewa nayi na gabatar da sallah asuba. 

na jima Ina kai kuka na ma Allah buyi gagara misali bayan na idar nayi azkar din safiya don bani wasa da azkar domin shine takobin mumini Seda na shafa addu’ar sannan na mike na ninke abun sallan na miyar dashi yanda nake adanawa sannan na durkusa a agaban gado na nadaga bakin katifar da take kan gado,hannu nasa a karkashin katifar na dauko wannan bakin laida da Hajiya Diddy ta karbomin agun alhajin mu. 

mayar da katifar nayi kamar yanda yake sena zauna a bakin gadon na kunce daurin da nayi ma bakin laidar sekuwa ga tulin kudi sun bayyana. 

idona na zaro waje don kuwa tunda nazo duniya bantab’a ganin kud’i masu yawa tsiraran su hakaba,wani irin yawu na hadiye baki bude. 

gyara zama na nayi da kyau sannan na mik’e da sauri naje na kulle kofar d’akina sannan na dawo na zauna na zazzage kud’in akan gado wani irin Kallo na kebin kudin. 

Seda na gama bin kud’in da Kallo sannan na fara rabasu Kashi Kashi,na cire yan dubu dubu da ban, se yan d’ari biyar biyar ma daban,sannan na fara aikin k’irgasu dalla dalla don banison asamu matsala. 

bani nagama kirga kud’in nan ba har saida naga rana ta b’ullo ta jikin labulen window na sannan na sarara musu, a hakan ma da naso nasake tisa k’irgawa kar wani ya mak’ale ajikin d’an uwansa .

cikin hanzari na futo na nufi cikin kitchen dake cikin falon mu,na kunna gas wanda na dan tara riban da nake samu nasiyo mana don amfanin mu duk da d’an karami ne, daura ruwan bak’in tea nayi na mishi hadin komai sanna na futa daga kitchen din na nufi d’akin da kaji na suke don na kwashe Kwan da sukayi karsu fasa su shanye,Se da na basu abinci da ruwa sannan na futo daga d’akin kajin. 

bayan na gama bama kaji ruwa da abinci na dibo kwai din da sukayi naje na a dana shi acikin gurin da na warewa domin adana d’anyar kwai, gurin na mayar dashi kamar store don Yana da kofa harda makulli da nasa akayi min shi. 

kwai (egg) na kulla a cikin laida baka,na nufi cikin gidan mu wato sashin da matan alhaji mu suke.

Sashin Mami Zulay amaryan alhaji mu na fara shiga, a haraban sashin nata na hango ta a duke da amalar wani abun takeyi a tsakar gidan na duk’a na gaishe ta da girmamawa don muna shiri sosai da ita, don ita tafi sauran matan baba na kirki ga hakuri, tana da Yar ta guda daya ta mace.

“Mami na ashe kin   tashi “?

Murmushi Maam Zulai tayi tace. 

“na tashi khubra, yau dai ban bari maganin nan ya rinjaye niba. 

murmushin nima na mayar mata tare da sake gaishe ta. 

“Antashi lafiya Mamin mu yaya karfin jikin?”

“lapiya law khubra jiki yayi sauki sosai ,yaya hajiya ta tashi dafatan komai lpia.

nayi murmushi nace komai lafiya Mami,amma Mami ina Zahra take ta barki kike tsaye anan ke kadai?

Nayi tambayar Ina Kallon aikin da Mami takeyi na Shirya musu abun karyawa da takeyi. 

Dafa kaina tayi tace. 

“karki damu diyar arzik’i zahra suna ciki nima abu nafuto zan dauka kika ganni anan. 

Kaina na daga mata sannan na mike nace. 

“Mami na allah yakara miki lpia. 

” amiin Khubra nagode da gaisuwa. 

Ajiye mata laidar dake hannu na nayi a kasa kusa da ita nace. 

” Mami na ga kwai ba yawa a soyama Zahra, Mami na acigaba da mana addu’a ma wannan sana’ar nawa. 

murmushi Mami Zulai tayi tana me cewa. 

“in banda abunki khubra yaya za’ayi ki debo kayan jauran ki haka,ai semu karya jarin,dakin bari har sekin dad’a bunqasa tukunna seki bamu alakoron.

tayi maganar da sigar zolaya tana dariya. 

dariyan nima nayi nace. 

kai Mami na yanzu kwai guda goma ne dayawa ?  

ai addu’ar ku na cigaba da kuke mana akoda yaushe bazai taba bari kasuwar mu tayi qasa ba, don haka Mami na Kimin addu’a da bakin ki me albarka. 

Murmushi Mami ta sake yi tace. 

“to shikenan khubra mun gode Allah yasa nan gaba abud’e mana k’aton gidan gona Allah kuma ya kauda idon makiya arzik’i yata bunkasa. 

” amiin Mami na, maybe hajjin bad’in bad’ad’a dake za’aje irin wannan addu’a haka. 

nafada Ina dariya. 

“kajimin yarinya. 

wato bama na bad’in nan ba har sekin karamin da bad’ad’a ko.? 

Dariya nayi Ina tafiya nace. 

” to mami banda abunki har yau she na bunkasar da zan miki alkawarin zan biya Miki kujeran makka shekara me zuwa? kinsan ni bani karya don asoni. 

kai Mami ta daga tace. 

” hakane kuma. 

“to muna matukar godiya da wannan kyautar .

Futa nayi a sashin Maam Zulay na nufi sashin Maam Saratu, daga bakin komar falon ta na tsaya nayi sallama yaran ta ne suka amsa min,shiga cikin falon nayi na samu guri daga kan kujerun da suke falon na zauna kamar yanda naga yaran ta guda biyu sunyi,yaa Kamal dana gani a falon na fara gayarwa Rabe kuma ya gaisheni tunda shidin na girme shi duk da ba wani girma na can bane.

duk rashin jituwar da mukeyi da matan Alhajin mu bashi ya hana mu yaran gidan girmama junan mu ba.

Maam Saratu tafito daga cikin dakin ta tana cewa. 

” a’a Yaya nakejin kamar muryan yar gadaran gidan nan a dakin nan? 

tana me k’arasa futowa cikin falon. 

basarwa nayi kamar banji taba,zama tayi a daya daga rub’abb’un kujerun ta da suke falon, duk da bawani Yara ne da Maam Saratu ba amma kayan dakin ta yafi na kowa lalace wa agidan. 

sanda ta yi kusan minti uku da zama sannan na dubeta nace. 

“Maam barka da safi da fatan antashi lafiya. 

” lafiya law alhamdulillah na tashi. 

” ai na d’auka maganar ma bazaki iya bane kin wani hakimce akujera sekace fulanin gidan sarki. 

murmushi nayi wanda ya zamemin jiki in bason magana shi nakeyi ma mutum don hakan ma ya wadatar basai nace komai ba,hakan kuma yakan qular da wanda nayi domin shi, don sukance raini ne hakan. 

ba tare dana ce mata komai ba na mike na isa  kusa da kafarta na ajiye baqar laidar dake hannu na nace. 

“Maam ga kwai a soya masu rabe amma sadaka ne. 

mikewa nayi na nufi kofa domin futa a sashin…… 

” keee dawo ki d’auki Kwan ki, kamar ke har nice zaki kalla don bakida kunya kicemin sadaka kika bamu kwai, da yake ance miki mu mabara tane ko.?

bance mata komai ba na juyo da nufin na d’auki laidar kwai din  caraff Rabe ya d’auke laidar Kwan kamar walqiya yana cewa. 

“dan Allah Adda khubra kiyi hakuri ki barmana wallahi mu muna son kwai din zamu soya mun gode Allah ya qara budi tunda mama tace bata so kinga shikenan semu had’a da nata mu soya sema yafi auki, mun gode my Adda. 

Dafa kafadar shi nayi Ina sake murmushin da Maam ta tsana nace. 

“cewa zakayi allah shikarb’a don sadaka na bayar d’an kanina. 

murmushin na kuma yi na juya nace. 

Byee yaa Kamal. 

Nayi tafiya ta cikin isa da izza kamar yanda suke cewa shiyasa suke kirana da qamshin gadara.

Ina jiyo muryan Rabe yana murna suna tafawa da Yaa Kamal.

1 2 3Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected