Zafin Kai 84
84
Rawa jikin Anne ke kokarin dauka sbd Idan akwai abinda duka yake gigitasu to kukan Bena ne,
Bena Bata Kuka sai Abinda yafi karfin zuciyarta ta riqesa,
Rungumeta tayi tana son tambayar ta Abinda yake faruwa Amma tana kasa magana itama sbd itama bugawa zuciyar Tata keyi.
Kuka Bena keyi sosai Amma babu Wani sauki ko sasssuci Datake ji a zuciyarta na Abinda ke cinta.
Shiru Anne tayi tana Bata Daman yin kukan yanda takeso ko ta samu sassauci.
Suna cikin wannan yanayin aka Bude kofan Dakin aka turo ahankali Anne ce kawai ta dago taga momyn Abdul ce ta kawo musu abincinsu anan na dare ta ajiye ta juya ta fice.
Babu Wanda ya Kalli abincin suna zaune cikin sanyi da mutuwar jiki har dare yayi sosai kafin Anne ta saka Bena taci abincin dole tayi sallan ishai ta kwanta.
Kasa barinta Anne tayi itama tayi sallah taci abincin kafin ta kwanta bayan Bena din tana dafata da hannu Daya sbd tayi tsananin kewan kwana guri Daya da Bena dinta.
Sanin sumayyah nada Bilal a me kulawa da ita fiyema dasu ya saka Anne Maida kulawanta akan Bena data fahimci tana cikin Wani mummunan quncin Datake boye mata.
Washe gari cikin iKon ubangiji da falalarsa sumayyah na tashi ta tashi da ‘yar lafiyan hankalinta kaman baya yanda suke rayuwa gidan Ababa lafiyar tana zuwa idan sabon depression ya shigo ta koma sama sama.
Bilal Daya rasa inda zai saka Kansa rungumeta yayi cikin tsananin farin ciki da Bai taba shigaba ya fara hawaye Yana qanqameta jikinsa.
Ita kanta Wani sanyin farin ciki ne a zuciyarta Daya sakata hawaye tana sake shigewa jikinsa tana Jin zuciyarta kaman zata faso da tsananin sonsa Dana Annenta da Bena dinsu.
Rungume da ita ya fito Yana Kiran momyn Abdul wadda itama rungume sumayyahn tayi tana fashewa da kuka sbd itama taci baqar wuya a jinya da kulawa da sumayyahn na shekarun Nan.
Bena da tin datai sallan Asuba take zaune shiru nade a cikin hijab din datai sallah tayi Nisa sosai a tinani idanuwanta sunyi jajir sun kumbura sosai sbd kukan data kwana Yi tsakar dare wadda Anne tana jinta itama hawayen ta ringa yi sbd batasan quncin Dayake cin Bena dinta ba gashi ita ba cikakkiyar lafiyayyar datasan Yaya iyaye keyiwa yayansu acikin damuwa ba bare tayi tasan damuwan yarta,.Abinda kawai ta sani damuwan Bena damuwarta ce tin farko basai ta saniba tana ganinta a qunci itama take shiga qunci,hakama tana ganinta a walwala itama take shiga walwala da farin ciki.
Shiru suke zaune dakin Anne tayi shiru cikin tsananin damuwa tana rasa abin Yi ko fada ko tambaya,
Ita Kuma Bena datai Nisa a tinani idanuwanta a rufe batamasan me Annen keyiba.
Bude dakin sumayyah tayi cikin sanyi da mutuwar jiki da zuciyarta dake sanyaya tana sanyi ta zubawa mahaifiyarta idanuwanta tana kallanta komai na rayuwarsu dasuka sha fama Yana dawo mata tsaf cikin Kai da zuci.
Takowa tayi ahankali idanuwanta na tsiyayan hawaye ta nufi Annen wadda sai alokacin ta lura da shigowarta sbd hankalinta dake kan Bena cikeda damuwa da mutuwar jiki.
Ganin sumayyah ya saka Wani bangare na zuciyarta sanyaya ta zubawa sumayyahn idanuwanta itama sumayyah ta qaraso da sauri ta fada jikinta ta rungumeta tana Kiran sunanta a Karo na farko bayan shekaru.
“Anne, Anne” take furtawa dukkanin jikinta na mutuwa da Wani irin dacin zuciya ja rabuwarsu.
Ita kanta Anne hawayen takeyi tana Jin dumin ‘yarta data Dade da yarda da ta tafi lahira ta barsu.
Sun jima a Hakan Bena bata motsa daga yanda take ba sbd Bata hayyacinta Sam.
Sumayyah ce ta sake Anne tayi kan Bena din itama ta rungumeta tana kiran sunata tsananin son ‘yar uwarta na motsa mata gaba Daya.
Ahankali Bena ta Bude idanuwanta jikinta ba qwari kaman yanda zuciyarta take ba qwari ta kasa ko motsawa a yanda take sai hawaye sirara da suka gangaro mata,
A Karo na biyu na Wani matakin raywarsu zata sake danne qunci tabarwa zuciyarta ita kadai taci azabarta ita kadai batareda ta sanar musu ba Dan hanasu shiga damuwa da baqin cikin rayuwar dasuka samu me nutsuwa da kwanciyar hankali.
Babu magana dake tashi a dakin nasu bayan ajiyar zuciya da hawaye dake sauka a tsakaninsu.
Ahaka suka dauki tsawon lokaci su kadai har azahar sai alokacin suka ci abinci sukai wanka kowannensu yafito fes zuciyoyinsu cikeda nutsuwa da kwanciyar hankali Banda Bena da dauriya kawai takeyi Amma duk dauriyarta Basu Dade da gama cin abincin da sukaci ba zazzabi me qarfin gaske ya rufeta musamman kanta dake tsananin ciwonda takejin kaman zai tarwatse.
Rikicewan jikinta ya saka hankalinsu tashi Basu tsaya Kiran Wani likita ba dole Akai asibiti da ita sbd har Amai takeyi jikinta ya sake gabaki Daya.
Suna Isa asibiti aka Bata gado dukkaninsu kin komawa gida sukai suka zauna Asibitin zaman Jira zuciyoyinsu ba Dadi.
**********
AUis special care Zurich.
Kwanansu biyi da Isa Saida suka gama samun nutsuwa da ganin komai ya shiga daidai inda ya kamata ya shiga na Neman lafiyan DD din tukuna suka samu Daman kunna wayoyinsu Dan samun Daman magana da Wainda suka baro Nigeria.
Dd babba ne ya fara samun labarin batan Bena daga bakin Abbakar Dan haka yayi shiru cikin matsanancin mamaki da tashin hankalin Daya sake tabbatar masa da tabbas akwai abinda yake faruwa wanda suke zargi tin farko.
Wani Dan zufa ya share da tissue me laushi Yana jefarwa sbd tinanin Abinda zai biyo bayan batan Nan nata idan DD ya farka,
Ta bangare Daya ga familynsa Dama suna cikin rudanin Bena data kasance ba mahaifiyar data haifi Amnah ba, lafiyar DD kawai kowa ke Jira ayi magana dole kowa yasan menene asalin Abinda yake faruwa.
Labarin batan Bena kaante shi zai bawa duk Wanda yakeda hannu a batan nata Daman yin koma menene manufarsa na Hakan Dan haka take dd babba ya sanar da Abbakar kada kowa yasan Bena kaante ta Bata baa ganta ba,
Ayi duk bincike da zaayi me tsananin gaske daga boye kada abari kowa ya San Bata Nan,Abar kowa da sanin ta biyosu Nan Zurich gurin jinyar mijinta.
Wanna umarnin na dd babba ya saka hankalin Umme sake tashi Amma Kuma hakanan ta daure take danne tashin hankalinta cikin mutane tana nuna Bena din na can tareda su DD a Zurich.
Amnah ma Hakan Umme ta fada mata Dan haka yarinyar ta Maida hankali akan yiwa iyayenta adduar Allah yabawa daddynta lafiya ya dawo shi da mummy dinta su koma highbridge tare tinda tasan aranar da kafin ciwon daddynta mummy dinta a highbridge ta kwana.
Nafisat ma sosai ta dage gurin cigaba da kulawa da Amnah cikin so da kauna tana sake debe mata kewan iyayenta.
Ahakan cikin tashin hankali da matsanancin tsoro da tsaka me wuya familyn kaantes suke,
Zargi da bincikensu ya qarfafa musamman Daya kasance ace lokaci Daya ansamu D a wannan halin hakama kawai a wayi gari babu Bena babu labarinta.
Abbakar da Kansa yaje gidan Ababa suka gaisa kaman yanda ya Saba ya Ciro kudi me yawa ya miqa masa.
Wani murmushi Ababa yasaki Yana kallan kudin yace
“Sakon dd babba ne ko na Benazir?”
Shima Abbakar murmushin yayi Yana cewa
“Sakon Bena ne sbd tafiyan gaggawa ya kamata zuwa can Zurich gu……
Bai qarasaba Ababa ya Dan sake wata dariyar takaici kafin yace
“Ita Bena din?akace batada lafiya Kuma shine harta warke zata iya tafiya.”



