Hausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 91

91
Familyn Kaantes sai alokacin da sukaji Safnah da momy na hannu Daman shi Ababa tini yana hannun hankalinsu ya Dan kwanta suka dawo da sabuwar damuwarsu akan ta inda zaa fara Neman Bena da Anne yanzu.

Ta bangaren Umme kuwa da alh Bulama rasuwar hajiya sabuwa ta dawo musu sbd ganin yanda su Safnah suka kasheta cikin rashin Imani da tausayi.

Kowa ya shiga jimami tashin hankalin Jin wannan masifar,
Umme tayi Kuka fiyeda lokacinda suka rasa hajiyar,
Alh Bulama kuwa bayan ciwo da baqin cikin rayuwar dasuka samu kansu aciki harda baqin ciki da radadin rasa ‘ya dayayi sbd Safnah tashiga cikin tsakiyan zuciyansa fiyeda yanda ake tinani ashe ita din ba tsatsonsa bace.

Umme itace ta ringa tausan Dan uwanta tana Jin radadin sa na rashin ‘ya ko ‘dan Kansa.

Matansa kuwa murna da Jin dadi suka hau Yi sbd har ga Allah sun azabtu da Safnah sbd itace take jiya rayuwar Alh Bulama din da matansa yanda takeso haka akeyi babu wanda ya Hana.

DD kwana daya da wuni Daya yayi a Asibiti kafin ya Dan warware ya dawo gida lokacin labarin rasuwar hande yazo musu babu Wanda yaji komai akan Hakan saidai suka bita da Allah yaji qanta tinda musulma ce Kuma mutuwa na kan kowa hakama kowa Yana fatan idan ya rasu ya sadu da malaikun rahama.

Bayan dawowarsa daga Asibiti Kai tsaye kaantes ya koma sbd highbridge din ana gyara na sauya komai na gidan Daya buqata.

Zuwa wannan lokacin Amnah ta fahimci mummy dinta batanan baa San inda take ba Dan haka ta kwanta rashin lafiya sbd rigima da kukan data ringa yi musu ba kakkautawa.

Shi Kansa Daddyn nata Dake Neman yin kukan Sam qin yadda tayi da rarrashinsa Dan haka Shima kusan Neman komawa kwance jinyar yakeyi sbd Yana gab da rikicewa gaba Daya Shima idan ba gano inda matarsa take akai ba.

Cikin tashin hankalin Rigima da ciwon Amnah sukai kwana biyu Shima a lallabawa kawai yakeyi sbd baida lafiyan,

Bincike kuwa tini aka bazama babu kama hannun yaro dukiya me yawa ake zubarwa Dan tsananta binciken Amma shiru.

 

*******Nafisat dake kwance tareda Amnah tana shafa kanta datai bacci jikinta da zafi sosai sbd rigima data gama kafin baccin.

Wayarta ce tayi haske alaman shigowan kira Dan haka ta Zame Daga jikinta ahankali tareda nufar toilet ta shige ta kunna ruwa ta dauki wayar cikin nutsuwa da sanyi tace

“Hello Ina wuni Yaya sulaiman?”

“Lfy kalau alhmdllh,kina jina ko Nafisat?,Yaya Amnah?ya jikinta?”

Numfashi Nafisat ta sauke ahankali tareda Dan zaunawa gefen bathtub tana cewa

“Lafiya kalau,Amma ta kasa yarda da rashin Anty Bena ko yanzu rashin lafiya ce sosai a jikinta.

Shiru sulaiman yayi kafin ya Dan gyara zamansa cikin napep din da yanzu Janta kawai yakeyi sbd batar da tinanin mutane da kamanni yace

“Inshallah ta kusa kasancewa tareda mahaifiyarta Amma dai yanzu Mummyn tata batada lafiya duk lokacin Nan fama akeyi da ita Dan haka yanzu Abinda mukeso dake passport dinta da id cards dinta duka Zaki tattara guri Daya ki samu yanda zakiyi ki fitomin dasu anjima idan anshiga sallan ishai masallacin kaantes.

Shiru Nafisat tayi tareda Dan Nazari duk da Bata taba musawa duk Abinda yace kaman yanda Shima Bai taba musawa Bilal Abinda yace ba Dan haka tace

“Zanyi kokarin yin Hakan anjima Amma Dan Allah Yaya sulaiman kada ku bari Amnah ta Dade a Hakan babu mamanta wlh zata iya kamuwa da Wani ciwon,yarinyar nada qawa zucin mamanta sosai,
Dan shiru tayi na sakanni kafin ta qara da cewa

“Shima daddynta Yana cikin mummunan halin”

Gyada Kai sulaiman yayi Yana cewa ” wanna duk sai yanda Sir Bilal yafada zaayi”

Sallama sukai ya kashe wayar itama ta kashe tana kashe ruwan tareda fitowa daga toilet din.

Tana fitowa ganin DD a dakin ya sakata rudewa sbd Bata taba tsammanin shigowarsa ba Dan haka tai saurin qasa da Kai tana gaidasa a girmame.

Kaman bazai kalletaba qafafunta kawai idanuwansa suka kalla zai nufi ‘yarsa dake kwance kan kujeran dakin Bena din zai dauka sai yaga babu alaman ruwa ko kadan a qafafunta bayan daga toilet ta fito.

Mayun idanuwansa da duk suka fada a kwanakin na rashin matarsa ya dago ya zuba mata Yana kallan hannuwanta Suma ya gansu a bushe tsaf babu ruwa ba alamansu bayan yaji qarar ruwa shigowarsa a toilet din.

Fuskarta ya kalla itama ruwa sai ya Dan Kalli wayar hannunta take ya tabbatarda waya tayi ta sirri idan har babu ruwa hannuwanta da qafafunta da fuskarta Kuma ta kunna ruwa to Hakan na nufin tabbas waya tayi.

Bai furta komaiba ko gaisuwanta be amsa ba ya dauki Amnah din ya fice daga dakin.

Kai tsaye dakin Zeenah ya kaita Dan fasa tafiya yayi da ita ya fita Yana fidda wayarsa ya kira Naseer sbd shi yanzu kowa baya yarda dashi akan duk Abinda ya shafi Bena da ‘yarsa Dan haka take yace Naseer ya saka qaqqarfan bincike akan me aikin Bena Kuma Nanny din Amnah.

Naseer na Jin Hakan yafara kokarin bincikar masu aikin gidan ma gabaki Daya.

DD gaba Daya yanzu ko mutane bayason shiga bayason suna nemansa Kuma,
Kadaice Kansa yakeyi sbd baya buqatan kowa atareda shi matiqan ba matarsa ce ya dawo qarqashinsa ba.

Ranar ma haka ya wuni cikin tsananin zafin jiki da ciwon Kai Dana kirji me tsananin gaske Wanda ya saka hankalin dd babba ma nasa hankalin b kwance yakeba da batan Benan,

Wainda dake asibiti kaf acikinsu babu me sauran amfanin da zai iya magana bare yasani ko ma ya fada inda Bena ta tafi.

Safnah ma dai har tsawon kwanakin Bata farfado ba sbd ba qaramar buguwa kanta yayi ba.

Ababa duka qafafunsa biyu babu me Aiki dayan bullet ya lalata dayar itace ta karye tin gidan DD babban baqin rayuwarsa da quncin Daya dabaibaiye rayuwarsa shine yau ko qafafun da zai iya daga Kansa tsaye baida,
Hande ta mutu ta bar duniya,
Ga hukuma na jiran su warke ayi gidan yari dasu ita momy ma da Safnah akwai yiyuwar ratayesu zaayi da ransu suna ji suna Gani su mutu Subar duniyar,shi kalan nasa hukuncin kuwa Kila life in prison ne sbd dumu dumu ansaka sunansa cikin tare suka maumalan qwayoyin da aka kama momy dasu Dan haka shi tasa mummunan qaddarar ta qarew yari ce har mutuwa da qafafu biyu babu ko Daya.
Daya Tina Hakan Wani irin Kuka yake fasawa wanda ke saka jikinsa daukan rawa Yana Rasa ta yanda wannan mummunan kaddarar ta samesa,Jin yake dama shine ya mutu ba hande ba ya huta da wannan biyu babun.

 

*********Koda Akai sallan magrib Saida likita yazo ya duba DD sbd jikinsa dake tsanani,
Bayan tafiyan likita daqyar Anne ta sakasa yaci abinci yasha magani.

Hakanan ya daure ya fita sallan magrib masallaci daga can Bai jiraba kaman yanda dd babba keyi wasu lokutan na tsayawa jiran sai anyi ishai ya baro masallacin gaba Daya.

Bedroom dinsa ya nufa Kai tsaye ya tube tareda sakarwa Kansa ruwan sanyi sbd ciwon Kansa ya rage ya samu Jin sassauci.

Ya jima Yana cikin ruwan kafin ya gama ya fito daure da towel fatar jikinsa tana Wani irin kyallin daukan Ido sbd duk yanda yake cikin tsananin damuwa da quncin zuciya fatarsa da kyansa suna Nan saima daukan Ido Dayake qarawa sbd rashin fita.

Yau jallabiya ya saka da hula ya Kalli time yaga lokacin sallan ishai yayi har na fara ya fito a natse cikin kamewa Yana nufar hanyar fita.

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Check Also
Close
Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected