Hausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 72

72
Shiru motan yayi tsit dukkaninsu kowa na jiran amsan Annen zuciyoyinsu na tsalle da harbawa da karfi,
Ita kanta Anne shiru tayi kanta na juyawa tambayoyin na jiya hankalinta da haukanta tareda dawo mata da abubuwa da dama cikin Kai da zuciya na radadi ko acikin hali na hauka.
Rawa hannuwanta suka fara kafin dukkanin jikinta ya dauki rawar Wani irin tsoro da wuta na cin tikinta gidan Ababa kawai takeson komai sbd balain datakeji Yana tafarasa cikin namanta da jininta.
Ganin haka Safnah ta fahimci kafin Ababa ne da baya barin Annen nesa da gidansa ko kadan Dan haka ta jijiga Annen da Dan qarfi tana cewa “Anne baki fadamun meya sameta ba?
Ya Akai aka haifi Amnah a gidan Ababa?.
Murya na rawa baa cikin hayyaci ba Anne tafara cewa
“Sumayyah ne ta samu cikin Amnah
Ta mutu ta barni gurin haihuwa,
Ta tafi tabar mana Amnah
Ababa ya siyar da Amnah da Bena gurin dangin Bilal,
Ya hanamu fada yace zan mutu idan na fada, Yace Kasheni ya kashe Bena idan na fada,
Yace Bena zata ringa kawo masa kudin dangin
Bilal,
Nikuma naje na fadawa kakan Bilal gskia ba
Bena bace ta haihu sumayyah ne,
Yace zai kula da Bena da Amnah bazasu bawa
Ababa komai ba,
Ababa Bai saniba Benata ta tafi kenan bazata dawo ba, bazan bari ta dawoba, banason ta dawo,inason ta zauna acan ta mutu acan
Amma idan zata musu acan tazo mu tafi tafi karta barni yanda sumayyah da sameerah suka barni, Safnah guduwa tayi ta barni Amma Bena tace indena fadan haka wai itama mutuwa tayi kawai ba guduwa ba,Amma
Amma Amma…
Karyewa harshenta ke Neman Yi sbd yanda jikinta ke rawa da jijiga Dan haka da sauri
Safnah tace momy ta juya da motan su koma su ajeta sbd idan tana cigaba da nesa da gidan Ababa zata iya rasa ranta.
Cikin tashin hankali ma masifa momy tace
Idan muka mayar da ita bayan ta ganki fa ta fadawa Ababan.
Bazata iya fada ba bakiga yanda take ba batada lafiyan hankali fa,
Juya muje mu ajeta Dan Allah momy.

Juya motan momy tayi tana ajiye wayarta datai recording din duk Abinda Anne ta fada tana dagawa Safnah wayar tace
Wannan maganar bansaniba Amma dai zata mana amfani gurin ankarar da Ababa ya dawo bangarenmu sbd kaantes kenan sunsan komai babu Abinda zai samu tarko sukai masa.
Kasa magana Safnah tayi sbd a lokacin Bata
Gane komai har suka Isa nesa da gidan Ababa kadan suka aie Anne Safnah na Kallo ta shige gidan batareda an nuna mata inda zata shiga ba.
Tana shigewa suka bar gurin da mugun gudu suka koma gida kaman babu inda sukaje suna jiran labarin mutuwan Bena.

*****cikin gaggawa Akai Asibitin Kaantes da
Bena kafin a Isa da ita tini labarin ya Isa ga dd babba da sauran family cikin qanganin lokaci kusan kaantes suka cika Asibitin sbd kusan a yanzu Bena itace bugun kirjinsu musamman dd babbanta da shine uwarta,ubanta,kakanta
Kuma abokin shawaranta sbd komai nata shine yake Bata shawara.
Umme da Zeenah kuwa harda Kuka sukeyi sosai sbd Jin motar datai hadarin da ita ta
Kone duk tinaninsu itama ta Kone dinne.
Hana media taji zancen ko kadan akanta sbd kada DD yaji baa son ya sani zaa boye masa hakama Amnah Dake gida an gargadi masu aikin da kada su bari ta sani ance mata
Mummy dinta tayo tafiyan kwana biyo zata dawo inshallah.
Kwana Bena tayi batasan inda kanta yake ba bayan Angama dubata cikin babbar saa aka ga babu inda ta samu matsala buguwan
Kai ne ta samu sosoi Daya fasa hancinta sai goshinta Daya fashe sai Kuma hannunta daya
Dan juji ciwo ya yanke sbd glass na mota.
Hankalinsu kaf sai alokacin ya kwanta Dan haka ake fatan farkawarta koina data ji ciwo anyi dressing nasa an sauya mata kava zuwa
Riga da wando masu laushi da kauri.
Su Safnah kwana sukai jiran mugun labarin daga kaantes Amma Sam babu hakama media dasuke ta jiran suji ana yada masifar data samu kaantes shiru ba komai Dan haka
Suka Dan shiga wasi wasi da tashin hankali
Amma dai sun lafe suna Jira basu motsaba
Dan kila Bena din ta Kone kurmus da motarta baa samu sani ba.

Zeenah ce me jinyarta a Wani muhaukacin luxury Amenity room dake can sama Asibitin
Wanda sai iya kaantes dinne masu Asibitin ake kwantarwa acan sai Kuma manyan masu qasa.
Umme kullum itama sai tazo da daddare ta dubata hakama dad kaante duk yabar office saiya biya ya dubata kafin ya wuce gida.
Dd babba kuwa Shima da daddare kullum sai
Abbakar ya kawosa sun dubata.
Ta farfado tin washegarin ranar data samu mummunan hadarin Amma Kuma tinda ta farfado takasa komawa kanta,
Kanta ya juye gabaki Daya
Tinani da radadi zuciyarta keyi sbd Abinda ya faru da ita bayan hadarin Dayake dawo mata,
Shin da gaske ne Safnah din data Gani kokuwa gizon mummunan hadarin data samu ne?

Meyasa zataga Safnah idanma gizo ne?
Sumayyahnta ya kamata tayi gizo idan har buguwan datai matacci takeson nuna mata,
Safnah ce tabbas ta Gani kuma tai magana da ita Amma shin wa zata tambaya taji gaskiyar,
Ta tambayi Zeenah baa samu kowa tareda itaba inda aka sameta an Bata tabbacin babu
Wanda aka Gani.
Wainnan tinanin ne ke cin ranta da dagula zuciyarta Amma idan ta Tina ansanar mata
Annenta na Nan lafiya Kalau sai taji zuciyarta ta samu kwanciyar hankali da nutsuwa.
Sedai ta Wani bangaren Kuma a yanzu mahaifiyarta take buqata a tareda ita fiyeda komai, Annenta takeso idan Kuma bazata sametaba to Ina zata iya zabar Annenta Takoma inda take komai zata iya hakura dasni.
Data kasa Kwantar da hankalinta Umme da kanta ta aika driver har gida aka dauko Anne bayan Ababa ya saka hande tayi mata wanka da a shiryata da kanta sun rufe iikinta da yayiwa mummunan duka bayan ta dawo da kanta din.
Dukan dayayi mata yasakata kwanciya cIwo itama Wanda ya Dan dawo da ita hankalinta
Dan haka tana zuwa Asibiti tayi Ido biyu da
Bena sai kawai ta fashe da Wani irin kukan
Daya saka Bena kasa dagowa ta kalleta
Daman su biyu ne a dakin da zata shigo aka fita aka Basu guri.
Kuka Anne keyi zuciyarta cikeda Wani irin qunci da bagin rayuwarta.
Bena hawayen ta gangaro dasu masu zafin gaske ta riqo hannuwan Annenta tana yaye mata hijabinta taga yanda gabaki Daya jikinta suke a fashe da shatin bulalan igiyar daure shanunsa. Bata iya cewa komaiba ta rungume Annen tana cewa
“Insha Allah Anne komai yakusa zuwa karshe,zan daukeki na tafi Dake inda zakiyi rayuwa kaman mutane da yardar Allah.”
Girgiza mata Kai Annen tayi tana cewa
“Ko ahakan bana cikin bagin ciki Bena tinda kina cikin walwala da kwanciyar hankali ke.”
Batadai iya cewa komaiba sbd idan tace maganar zatayi Kuka zasu taru suyita Yi gasu
Umme na palon dakin suna jinsu
Cikin nutsuwa tace
“Anne meya faru bayan barinki gida?

Ya Akai kika koma gida bayan nagani da idona mota ta Kade ki??
Bakiga kowa ba a ranar????
Shiru Annen tayi tana Dan shiga nazari kafin ta girgiza Kai tana cewa Bata ga kowaba Bata
Tina komaiba.
Ajiyan zuciya a boye Bena ta sake tareda barin zancen sbd kada ta juyar da kan Annen.
Gida aka Maida Annen daga Nan ita Kuma ta
Dan samu sakewa sbd taga mahaifiyarta.
****** Jinyar sati Daya tayi ta warware sosai aka sallameta ta dawo gida saida tayi kusan kwana uku da dawowa harta fara zuwa office alokacin Amnah tasan accident Mummynta tayi tsoro ya kama yarinyar sosai da daddare Ya Akai kika koma gida bayan nagani da idona mota ta Kade ki??
Bakiga kowa ba a ranar????
Shiru Annen tayi tana Dan shiga nazari kafin ta girgiza Kai tana cewa Bata ga kowaba Bata
Tina komaiba.
Ajiyan zuciya a boye Bena ta sake tareda barin zancen sbd kada ta juyar da kan Annen.
Gida aka Maida Annen daga Nan ita Kuma ta
Dan samu sakewa sbd taga mahaifiyarta.
****** Jinyar sati Daya tayi ta warware sosai aka sallameta ta dawo gida saida tayi kusan kwana uku da dawowa harta fara zuwa office alokacin Amnah tasan accident Mummynta tayi tsoro ya kama yarinyar sosai da daddare kuwa tana kiran daddynta video call ta fada
masa yayi shiru tsawon mintina bayan Jin
Abinda Amnah din ta fada Bai ce komaiba
sai daga baya ya Dan sauke numfashi kadan
yayi mata Saida safe yace ta kwanta ya kashe wayar.
Safnah da mommy a cikin satin kiris ya rage
likitan qwaqwalwa Bai dubasu ba su dukan
sbd samun tabbacin Bena dai ta rayu Kuma ta warke fes,
Abinda ya Hana Safnah zaucewa shine sanin
koda Bena ta Tina cewan ta ganta to batasan
a Ina take ba Kuma waye miiinta Dan haka a
yanzu zabi Daya ya rage musu ko a mutu ko
ayi Rai D yafara kwanciyar aure da ita aurensa
da Bena ya haramtu.
****Yau very late tagama Shirin office ta
fito sanyeda Riga da slim skirt na Wani
tsadaddivar lace milk and coffee brown Da
tsadansa take a bayyane sai qaramin veil mara nauyi ta shiga mota ta ajiye handbag dinta a gefenta ta tayar da motan ta bar kaantes.
Tana Isa office ko zaman awa Daya bataiba ta fita ta shiga meeting acan suka Dan Dade tana fitowa Kai tsaye office dinta ta nufa ta tura kofan kafanta Daya ta Sako ta dakata sbd zuciyarta data tsaya cak da qamshin da hancinta ya shaqar mata cikin office din.
Wayarta dake hannunta ta Dan riqe da garfi sbd subucewan data so Yi.
Sai Data sauke numfashi Mai sanyi ahankali kafin ta qarasa shigo ta tura kofar tana rufewa kafin ta juyo taji anrungumota ta bayanta tareda saka Kansa wuyanta ahankali yana lumshe fararen idanuwansa dasuka gama jigata kafin isowansa daga jiya zuwa yau din.
Ita kanta boyayyan numfashi ta sauke ahankali tareda lumshe idanuwanta idanuwanta na
Dan cikowa da hawayen radadin da zuciyarta
ta shiga duk tsawon wannan lokacin da baya
Nan.
Jin jima a Hakan shiru kafin ya saketa a
hankali ya juyo da ita suka fuskanci juna Yana
mata Wani irin Kallo bakinsa baisan me zai
furta ba sbd baisan Yava zai iero zancen ya
fadesu ba
Itama Jin shiru ya sakata dagowa ta kallesa
cikin nutsuwa da da sanyi ta Bude baki zatai
masa barka da dawowa ya kasa hakuri ya
dagaya sama tareda Dora bakinsa kan nata
Yana shigar da harshensa cikin bakinta.
Lokaci Daya suka tsotsa bakin juna suka
Kalli juna a tare ta shige jikinsa kawai tareda
zagyesa da hannuwanta Hakan ya sakasa iya
Bude baki ya jero kalman “Kina lafiya kuwa?
“Since when kuka fara boyemin Abinda yake faruwa?
Yaushe ne kika samu accident din?
And how did it happen??
Tambayoyinsa a jere idanuwansa na cika da
Abinda Bata taba tsammata ba wato kaman ruwan hawaye yasata kasa riqe kanta ta jefar da wayarta da documents din hannunta masu mahimmanci ta Kai hannuwanta masu taushi ta kama fuskarsa ta Dora bakinta kan nasa tayi masa Wani irin kiss Daya saka hawayen cikin idonsa zubowa Bai tabbatarda hawayen bane sai Daya shafasu yaji sune ya kalleta Dan tabbatarwa da Kansa ta gama da rayuwansa shi kenan.
Matseta yayi jikinta tareda karban kissing din Yana zuge duk was albarkatun bakinta dasuke sake kashesa.

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected