Dabi'ar Zuciya Hausa NovelHausa Novels

Dabi'ar Zuciya 59

59

Yadda amirun yace zuwa washegarin bai samu ba,saboda ya wuni tare da daddyn,shi da hajiya qarama wadda tun wancan lokacin bata bar gidan ba,da kuma auta jawahir,kusan wuni sukayi kusa da daddyn.

A zahiri jinya daddyn yake,saidai kuma a badani wani idanu da kwanya basira ce tazo masa,dukkan wani motsi na mummy yana ankare dashi.

Daga sanda taji kalaman
“Allah yayi maka albarka” da suka fito daga bakin daddyn bayan sun dawo daga toilet,inda samir ya taimaka masa yayi alwala wani abu ya daki zuciyarta,saida tana ta qoqarin boyeshi da fake murmushi da jin dadi a zahiri,abun da yasoma daga hankalin daddy,daurewa yake,cikin ransa yana maimaita

“Innalillahi wa inna ilaihi raji’un” yana fatan idanunsa ne kadai suka ga hakan,zuciyarsa nata bijiro masa da tarin tunane tunane kala daban daban.

Ba yadda mummy batayi da najwa taje ta zauna ba itama amma fafur taqi,sai kumbure kumbure take,da alama fushi take ko gaba ga dauka akanta saboda maganar takardun kadarorinsu?,abinda takejin ko zata fashe ba zata barwa fawwaz ajiyarsu ba,kaya ne masu tarin tsada da daraja.

Kaltum kuwa daki ta koma,faduwa gaba dama qunci takeji sosai cikin ranta,duk sanda taga wulgawar jauhar da yadda take shigewa samir gaban kowa sai taji ranta ya baci,don haka ta kebe kanta a daki,ta dauki qur’ani dan qaramin,ta fara tilawar haddarta,wanda zuwa dare sai gashi ta kammala izifi ashirin cif.

Zuwa magariba kowa ya watse daga dakin sun tafi sallar magariba,sai samir wanda ya daurawa daddyn Alwala,ya kuma sanya masa abun sallah,sannan ya dawo ya zauna bayan ya dauki wani littafin azkar .

Yana shirin budawa wayarsa ta dauki tsuwwa,gaba daya ya manta da ita,tun daxu kuma yaji ana kiransa,alwalar da yake daurawa daddy ta hanashi dagawa.

Mamaki sosai ya kamashi ganin sunan murtala da umar sai kuma amiru,amirun da tunda ya fita office bai dawo ba,don yanzun shine ke tafiyar da ayyukan office dinsa.

Bai gama wannan nazarin ba kiran amiru ya sake shigowa,ba tare da jinkiri ba ya daga

“Har yanzu bakasan abinda ke faruwa ba?” Amirun ya jefa masa tambayar

“Me ya faru?”
“Ya akayi aka fidda maquden kudade daga asusun company haka?,daga daren jiya kawai?,ko akwai abinda zakayi da kake buqatar kudade masu yawa haka saraki?” Mamaki sosai ya kamashi,gaba daya tunda lalurar daddy ta tashi hankalinsa baya kan company din sosai,koda muhimman takaddu da shi xai sanya hannu wani lokaci saidai a kawo masa su gida,ko shi ya shiga a tsaitsaye ya duba ya saka hannu,sauran ayyukan kuma amiru ya tafiyar dasu

“Bansan abinda kake magana a kai ba, please amiru…..ka yimin bayani”

“Kudade masu matuqar yawa da zasu iya jawo girgizar kamfanin nan aka fitar,kuma abun mamakin dana tsananta bincike…..akwai sanya hannunka dana daddy gaba daya,dukkan wata alama ko shaida suna nuna cewa akwai masaniyarka kai da daddy”

“La’ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin….turomin dukka bayanan ta email”

“Ok” amiru ya amsa,dukka suka kashe wayoyin,cikin hanzari ya jawo computer dinsa dake ajjiyr gefe,wanda dama yau ya wuni duba wasu ayyuka,da contact da suka sassamu masu tsoka,wanda yake sanya ran nan da wasu ‘yan kwanaki zai maida hankali kansu ya karbi aikinsa.

Shuru ne ya ratsa dakin bayan sun gama duba komai shi da daddy,sai system din da suka sanya a gaba suna kalla

“Inaji a raina dama akwai babban qalubalen daya tunkaromu……kabi komai a hankali…….mu qara kaifin addu’ar da mukeyi…..karka nuna maganar ta tada maka hankali,kaci gaba da rayuwarka kamar ko yaushe,bincike kuma ya gudana ta qarqashin qasa” ajiyar zuciya mai nauyi ya saukar,ya samu fiye da rabin nutsuwa cikin ruhinsa,lalllai kudi aka fitar musu maqudai,kusan fiye da rabin jarin kamfanin,amma shi wannan ba shine damuwarsa ba,tunda cikin abinda Allah yayi masa zai iya maida gurbin kudin cikin tashi lalitar,abinda yake tsoro…..irin fahimtar da daddy xaiyi masa,kada wannan ya jawo yarda da amincin da ya fara samu daga gareshi,saiya rufe idonsa kadan,qwaqwalwarsa na lissafa masa mutanen da xasu iya kasancewa suspect.

A rikice mummy ta koma da baya,ta kuma fara laluben hayar dakinta,ba shakka ko tantama babu najwa nada masaniyar wannan al’amari,wacce irin yarinya ce wannan takeson xame mata ‘yar fata?,sai data fara biyawa ta dakinsu,ta tabbatar mata ta sameta yanzu a dakinta sannan ta wuce can uwar dakanta.

Kasa zama tayi,sai kai kawo da take daga can zuwa nan,har zuwa sanda najwa ta turo qofa ta shigo dakin,idanun mummy dake cike da zallar bacin rai da tashin hankali ta xuba mata har ta qaraso

“Me kika sani dangane da fitar kudi daga azare company?” Yanayin reaction na najwan kadai ya isa gaya ma mutum gaskiyar abinda ke faruwa,tun asali najwa irin mutanen nan ne da basa iya boye abinda ke ransu da zuciyarsu,saita sauke headphone din kanta,ta jingina da mudubin mummy bayan ta ajjiye wayarta saman madubin ta goye hannuwanta a qirji

“Ni da fawwaz muka fitar dasu,saboda ni gaskiya it’s high time to get the money nima,na gina kaina na gina rayuwarta,saboda gaba daya ke na fuskanci ki fara sanyi,dukkan wasu plan naki sun daina aiki…..bazan zauna na qare a haka ba, Daddy ya mutu nida jawahir a bamu kason saraki ace mu raba ba,ke kuma a baki one over eight,kinga mu asara ta hau b…….” Wani lafiyayyen mari ra zabgawa najwa,marin da yasa wuta ya dauke mata na wasu sakanni kafin ta dawo dai dai ta zubawa mummy idanu,zuciyarta tana tafarfasa,tunda aka haifeta ba’a taba marinta irin na yau ba,ko duka ba zata iya tuna sanda akayi mata shi ba,sai yau?,kamar ita da girmanta da shekarunta?,tana da matakin karatu mai zurfi,tana jin kamar ta maida hannu ta rama marin ne ko mummyn xataji irin yadda taji……

“Shashashar banza da wofi,wadda bata komai da hankali,fawwaz dai fawwaz dai?,qanin ubanki ne shi din?,da har zaki fara aiwatar da abubuwa bada shawarata ko masaniyata ba?,inda ta haka na tara duk abinda na tara da yanxu nakai warhaka ina al’amurana?,abun ba iya taku bane?,yanzu wannan kinsan matsalar da zata haifar?,kinsan dimbin masifun da xai tono?,to xanyi maganinku daga ke har fawwaz din” qarar wayar najwan dake gefe ya sanyasu maida hankalinsu,gaba daya suka kai hannunsu a tare,mummyn ta riga warcewa saboda ganin sunan fawwaz din,dama nemansa take ido rufe ya dawo da takardun nan,ga kuma wannan ta sake faruwa

“Kana jina da kyau?,ka saurara kaji abinda xan gaya maka,bisa kakkausar murya da kuma gargadi,baka da gadon najwa koda mutuwa tayi…..bare gadon ubanta…..saboda haka…..na baka awa ashirin da hudu,duk wani abu nata data baka da wanda ka karba,ka tattaromin shi ka kawomin cikin girma da arziqi,duk wani abu namu dake hannunku kaida uwarka,don na tabbatar akwai masaniyarta cikin komai,ida ma kun shirya wani zagon qasa ne to haqarku bata cimma ruwa ba,amma na baku awa ashirin da hudu,daga yamzu zuwa gobe,tunda baku san abun arziqi ba” daga haka ta datse kiran,tama kashe wayar gaba daya

1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Check Also
Close
Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected