ABU NAKA BOOK 2 BY SODANGI

ABU NAKA BOOK 2 BY SODANGI

ABU NAKA…

2

 

HAFSAT C. SODANGI
Haqqin Mallaka (m) Hafsat C. Sodangi

 

 

Shekarar Bugu:
2005
An sake Bugawa A:
2015

ABU NAKA-2
M
us’ab ya wuni cikin matsanancin maye kasancewar shi kanshi ba zai iya faxin adadin kwalaben barasar da ya kwankwaxa ba.
Sani ya shigo gidan da saurinshi saboda ihun Mus’ab da yake jiwowa tun daga waje da kuma ta’adin da ya hango Mus’ab xin yana yi na jifa da duk wani abin da ke cikin falon wanda hannunshi ke iya xauka, yana tarwatsa gilasan gidan dasu.
Qarfi mai yawa Sani ya saka kafin ya iya riqe hannun Mus’ab, sunyi duru-duru suna kallon juna cikin haki, saboda wahalar da suka yi kafin suka kai ga tsayuwar.
Sani ya yi nufin jan Mus’ab zuwa cikin xakin kwananshi bai yi nasara ba, sakamakon tirjiyar da Mus’ab xin ya yi, don haka suka zube kan kujerar dake bayansu cikin haki.
“Dame wannan abin ya yi kama Mus’ab?’
Sani ne ya yi tambayar.
Mus’ab ya zuba mishi ido a gajiye, da qyar ya buxe baki ya ce mishi, “An rabani da Aisha, kuana kallo baka yi komai ba saboda kai mugu ne ko?”
Yana maganar da qyar yana zaro ido tamkar dai yanda aka san bugagge yana yi, ga kuma hannayenshi da ya damqi wuyan Sani dasu sunyi mishi kyakkyawan kamu.
Sani ya shiga kici-kicin qwatar kanshi daga hannun Mus’ab.
“Ka sato min Aisha ka kawo min ita nan gidan yanzu-yanzu nan ina son ganinta, ina son rungumarta a qirjina, ina son jin xuminta a jikina, ina son ganin no…….”
Da sauri Sani ya xoraa hannunshi a bakin Mus’ab ya toshe don rage qarfin maganar da yake yi gudun kar ma’aikatan gidan dake waje su ji.
“Mus’ab kanka xaya kuwa, duk barasar ce ta mai da kai haka?”
Mus’ab ya tunzura ya qara shaqe shi ya ce, “Nine mashayin?”
Sani ya qara tsorata da lamarin nashi ya shiga neman hanyar qwatar kanshi daga hannun shi.
Ya ce, “Ban ce maka mashayi ba Mus’ab, cewa na yi ka yi haquri ka sake ni don in samu in nemo varayin da za su sato maka Saddiqa su kawo maka ita, tunda ai ka san ni ban iya sata ba ko da ta kaya ce, balle ta mutum xungurungum!”
Mus’ab ya sake shi. Cikin sauri Sani ya miqe ya kama hanyar fita daga gidan, yana jin Mus’ab yana ihun yau xin nan nake so ka sato min ita.
Washe gari da safe Mus’ab yana zaune kan dardumar da ya idar da sallar asuba, jan carbinshi yake yi tunda ya idar da sallarshi bai tashi ba, shi da kanshi ya san rabon da ya sha barasa da ta gusar da hankalinshi irin na jiya ya yi matuqar daxewa.
Har lokacin kanshi bai bar sarawa ba, ga nauyi da yake yi mishi saboda matsanancin ciwon da yake yi, ga tunane-tunane iri-iri da mafarkai barkatai, har bai iyaa tantancewa da adadin mafarkan da ya yi a cikin daren.
Daga ciki wanda ya fi tsaya mishi a rai shine, mafarkin Hamida da ya yi cewar ta shigo gidanshi tana ba shi labari game da bikin Saddiqa da Sadisu, wanda rashin daxin labarin da take ba shi yasa ya yi ta jifanta da abubuwa har ma ya fasa mata kai.
Gabanshi ya yi mummunan faxuwa da ya qara tsunduma cikin tunanin mafarkin. Shin mafarkin ya yi ko kuwa Hamida ce ta zo gidanshi da gaske ya fasa mata kan? Wai wane irin maye ya yi ne jiya?
Ya qara zurfafa cikin tunani yana nazarin irin jifan da ya ga yana yi mata, ya zubawa wuri xaya ido yana qoqarin tunano maganganun da ta zo mishi dasu sai ga Sani ya shigo.
Mus’ab ya zuba mishi ido cikin fargaba da tsoro, cikin qarfin hali ya tambaye shi.
“Daga ina Sani?”
Sani ya kalle shi cikin nutsuwa ya ce, “Daga inda ka aike ni mana”.
Ya sake zubawa Sani ido yana qoqarin tunano aiken da ya yi mishi, bai tuna ba.
“Ina na aike ka Sani?”
“Sato Saddiqa mana, ba ka ce in tura varayi su shiga gida su sato ta a kawo maka ita ba?”
“Ni!”
Da qarfi ya yi tambayar tare da miqewa tsaye cikin kaxuwa. Ya sake tambayar shi “Ni? Sani na turaka ka aiki varayi su shiga cikin gidan ubana da ya haifeni su yiwo sata?”
“Ai ba sata ka ce suyi ba, Saddiqa ka ce a sato maka”.
Mus’ab ya xan yi taku biyu gaba kafin ya sake ja ya tsaya, ya sake juyowa gare shi ya ce, “To yanzu fa me ake ciki?”
Sani ya kalle shi ya ce, “Ai anyi an gama, kai kawai ake sauraro”.
Kan Mus’ab ya kama sarawa da sauri fiye da da, ya xora hannu ya dafe goshinshi cikin matsananciyar damuwa da fargabar al’amarin. Shi kam ya san babu yanda za ayi a shiga gidansu a sato Saddiqa a fito da ita alhalin Innarshi tana lafiya.
Me suka yiwa Inna? A wanne hali suka barta? Waxannan sune tambayoyin da suka tsaya mishi a rai.
Nan da nan ya juyo don Sani ya amsa su, sai dai kuma abin takaicin shine Sani ya fita ba tare da ya sanar da shi ba.
Mus’ab ya laluba kujera a hankali ya zauna, lokaci mai tsawo yana tunanin ta inda zai bi ya gyara al’amarin da ya riga ya lalace, dama an ce ba za a ba shi Aisha ba saboda shi xan iska ne, to yanzu kuma in aka gane shine yasa aka sace ta me za a kira shi?
Anya iyayenshi za su yafe mishi kuwa? Ya ya zai yi ya sake daidaitawa dasu? Shi ba abin ya xauke Aisha ya yi tafiyar shi da ita ya bar qasar yaje wani wuri suyi rayuwarsu ba, aure mai albarka yake nema a tsakaninshi da ita na raya sunnar Manzo, ban da haka ya kai munzalin shekarun da daidaituwar al’amura yake nema tsakaninshi da iyayenshi.
Tausayin kanshi ya kama shi da ya tuna in har aka gane abin da ya faru yana da hannu a ciki, to shi da Aisha sunyi bankwana kenan har abada. Amma duk da haka ya qudiri aniyar mayarwa iyayenshi da Aisha, don ba zai yarda a wannan lokacin wani abu mai tsanani ya sake shiga tsakaninshi da iyayenshi ba, musamman ma mahaifiyarshi.
Yana kwance cikin ruwan zafi da ya gauraya da turare mai matuqar qamshi cikin tunanin mafita, zai je ya ga Aisha a inda su Sani suka voye ta ya xauke ta ya mai da ita gida, maimakon ya bari sai sun bincika zai gaya musu gaskiyar lamari, iyaka dai ya san abin da yake gudu ne zai same shi.
Mus’ab ya kammala kwalliyarshi cikin fararen kaya babbar riga ‘yar ciki da wando na farin yadin boyel ne a jikinshi, hular kanshi da baqaqen takalman dake qafarshi sunyi matuqar dacewa, ga qamshin turaren shi mai sanyaya zuciya, duk da matsanancin vacin ran dake gare shi bai hana shi yin kyau ba, ga kwarjininshi na musamman a tare da shi.
Ya fito daga xakinshi zuwa falonshi ya nufi kujerar da ya hangi makullan motarshi a ajiye a kai, yana mai xaura agogonshi qirar Rolex a hannunshi. Motsin da ya ji a bayanshi ya sanya shi saurin juyawa, Sani ne a tsaye a bayanshi.
Mus’ab ya zuba mishi ido cikin nuna alamar vacin rai.
“Yanzu ina Aishan take?”
Kafin ya ba shi amsa sai Mus’ab ya ce mishi.
“Ban san baka da hankali ba Sani sai yau, wato kai duk umarnin da aka baka sai kawai ka bi Sani? Ba za ka yi la’akari da yanayin da mutum ke ciki ba a lokacin?’
Sani ya galla mishi harara ya ce, “A’a, kar ka sargeni giya hauka ne?”
Ya juya zai sake fita.
“To baka gaya min inda take ba don in san abin yi, kaima ka san yanzu ba lokacin wasa bane tunda dai komai ya riga ya lalace, ka ji tausayina mana Sani”.
Sani ya kalle shi saboda tausayin da ya bashin ya ce, “Tana gidan Innarta”.
Kan Mus’ab ya xaure, ya sake tambayar shi.
“Wacce Innar tata?’
Ya ce, “A’a, gidan Inna mana, ai ban aiki wani sato ta ba”.
Ya kalli Sani ya yi tsaki.
“Wato kai duk halin da mutum yake ciki sai ka zolye shi ka qara mishi damuwa saboda tsabar rashin tausayi, to ka zu muje saboda mu san abin da suke ciki tunda duk wayoyi da na yi ta yi mata ta qi xauka”.
Sani ya kalli agogon hannunshi ya ce, “Gaskiya sai dai ka yi haquri ka je kawai, Ishaq ya yi waya kana wanka ya ce yana bisa hanya, ina ganin in jira shi ya zo ya fi in bika ya zo ya smau gida babu kowa. Ko me ka gani?”
Ya fita ya tafi ba tare da ya amsa ba. Mus’ab yana tafiya cikin motarshi Marsandi qirar 190, zuciyarshi sai faman shirya mishi kalmomi masu daxi take yi da zai yi amfani dasu wajen shawo kan Aisha don ta sassauto daga tsattsauran ra’ayin da ta xauka a kanshi saboda abin da Gwaggonta ta gaya mata game da shi.
Ya yi parking a qofar gidan cikin matsanancin fargaba da tsoro, nan take ya ji zuciyarshi ta shiga dakan uku-uku saboda cincirindon yaran da ya gani a qofar gidan suna wasanninsu alamar akwai taro a cikin gidan.
A saninshi yau saura kwana tara ayi xaurin auren Aishaa, to me ya kawo taron jama’a tun a yau? Yana gama yiwa kanshi tambayar mafarkin Hamida da abin da take gaya mishi ya faxo mishi cikin ranshi.
“Yaya zuwa na yi in shaida maka cewar Baba da Inna sun dawo da xaurin auren Saddiqa da Sadisu wannan Juma’ar, wai za suyi hakan ne don su shammaceka da jama’ar da za su iya cewa wani abu game da hanaka da suka yi, baka ankara ba sai kawai ka ji an kaita gidan mijinta”.
Waxannan sune kalaman da ya tuna Hamida ta gaya mishi a cikin barcin shi. Ya fito daga cikin motarshi cikin sanyin jiki da matsanancin fargaba ya wuce yaran ba tare da ya kula su ba alhalin yin hakan ba xabi’arshi ba ce.
Yana shiga zauren gidan hayaniyar muryoyin jama’a mata da ya jiyo daga cikin gidan ya dakatar da shi daga shiga.
“Ku miqo min kwandon tsaman can wannan ya cika”.
Muryar da ya jiwo kenan wacce ya fahimci mai ita. Cikin sauri ya juya ya fita, ya samu yaro mai hankali cikin yaran dake wasa a qofar gidan ya ce mishi.
“Maza shiga cikin gida ka cewa Bilkisu wai ta samu yayanta a gidan Abu”.
Ya ce, “To”. Ya shiga cikin gida da gudu, shima Mus’ab ya yi maza ya bar qofar gidan.
Mus’ab yana zaune kan tabarma cikin matsananciyar damuwa, ya qosa qwarai ya ga shigowar Bilkisu.
Ita kuwa Abu sai qoqarin qarasa kwalliyarta take yi, atamfar ‘yar Ingila ce a jikinta sabuwa dal, ga ‘yan kunne da sarqar zinare da Mus’ab ya saya mata sun kama wuyanta, su ma ranar ta fara sanyasu. Qafarta ta yi shar gwanin sha’awa da lalle, duk da dai ba ta gama yin baqi ba tana riqe da mashayin kwallinta a hannunta tana zizirawa a idonta.
“Ni kwalliyar me Abu take yi ne haka?”
Cikin qarfin hali Mus’ab ya kawar da shirun dake xakin ta hanyar yi mata tambayar. Ta dakatar da girgiza tandun nata ta shiga qoqarin fito da mashayin nata don ta zizarawa xaya idon nata. Ta zuba mishi ido kafin ta ce mishi.
“Yaushe ne ka tava zuwa gidana baka sameni cikin kwalliya ba?”
Ya xan qara kallon ta kafin ya ce, “A’a, Abu ba dai irin wannan kwalliyar taki ta yau ba, kwalliyarki ta yau ai ta fi kama da so kike ki cinye wata gasa. Ba don na san tsofaffi basa zuwa gasar sarauniyar kyau ba da sai in yi zaton can za ki tafi”.
Abu ta yi murmushi ta ce, “Ko ba za ni cin gasa ba ai na yi kwalliya yau kam ta cinyewa, tunda yau ne saka lallen Saddiqa. Sa’a ma ka ci ka sameni a gida don can gidan nasu za ni yanzu”.
“Yau saka lallen Saddiqa?”
Ya yi tambayar a firgice cikin faxuwar gaba da razana tamkar Abu ba ta gane yanayin da ya samu kanshi a ciki ba. Sai ta ci gaba da magana.
“Iyayen Saddiqa sun matso da xaurin auren zuwa jibi, sun ce ka xaga musu hankalin yarinya kana nema ka sata ta bijire musu bayan ita ba bijirarriyar ba ce, tunda uwarta ta bayyana mata halayenka babu abin da take yi in ban da kuka, ko abinci ta qi ci. Don haka gara suyi maza su kaiwa mijinta ita tun baka yi dalilin da suka kunyata ba, don haka yau ne ake aikin kayan tsarabar biki su cincin, lkaki, nakiya da dubulan. Yanzu haka ma ai ina jin gidan a ciki yake”.
Bilkisu ta yi sallama Abu ta amsa mata, ta shigo ta durqusa ta gai da Abu sannan ta juya wajen Mus’ab, bai saurari gaisuwarta ba ya balbale ta da faxa.
“Har daku Bilki cikin bukin da su Inna ke shirin yi? Na ce har daku? ‘Yan ina da buki? Ko ba a gayyacesu ba sai sun je? Yanzu ashe har daku cikin wannan bukin?”
Abu ta bar abin da take yi ta zuba mishi ido tana kallon shi. Bilkisu kuwa kuka take ta yi, ya yin da shi kuma yake ta faxa.
“In ban da rashin hankali da rashin sanin ciwon kai me ya shigar daku cikin wannan bukin? Na ga hanaku auren aka yi aka bai wa wasu, ko kuwa kuma kuna cikin masu marawa Sadisu ne? Ko har daku aka haxu aka yi min taron dangin da aka yi aka hanani auren ne? Ta hanyar gwada min fin qarfi, kuma kun biyewa Abu ne?
To ita murna take yi da abin da aka yi min tana farin ciki, kin ganta ai gayenta take yi, yaushe rabonki da ganinta riqe da madubi tana qalqale fuska in ban da yau? Murna take yi tana farin ciki an hanani auren Aisha an qwace min ita, bayan kuma tawa ce saboda kawai bani da gata dama kuma tun farko sai da ita Abun ta sarawa neman auren nawa baki”.
Abu ta katse maganganun nashi ta hanyar qyalqyalewa da dariya. Sai da ta yi shiru sai ta kalle shi cikin nutsuwa ta ce mishi.
“Sambatun kayan ne haka ko kuwa har yanzu a buge kake maye ne ya saka waxannan maganganun?”
Ya yi maza ya qara xaure fuska ya ce, “Wane irin maye?”
Ta ce, “To in ban da haka ka ce don an hanaka auren Saddiqa kar su Bilki suje bikin? Kanka xaya? Saddiqa ba qanwarka ba ce? Ko kuwa barasar ce ta mai da kai haka baka san ya kamata ba sai kanka kaxai ka sani?”
“Bana son kina yi min irin waxannan maganganun a gaban qannena”.
Ta ce, “Kai tafi can ka bani wuri, mene ne basu sani ba a halayen naka? Mene ne qannen naka basu sani ba game da kai? Ni abin kunyar da ka yi ma da Bilkin ka yiwa zai xaga min hankali ne har ya dame ni ya tayar min da hankali? Ita Bilki ai ta san komai naka tunda tare kuka taso shekaru uku ne a tsakaninku, tun ba ta isa komai ba kuma take cikin lamarinka, babu wani abu naka da ba ta sani ba.
Amma Hamida fa? ‘Yar qanqanuwa cikin qannenka, yarinyar da in da kai mace ne ka haifeta da girmanka fa aka haifeta, ba ta san komai game da halayenka ba, in dai ba ta ji a labari ba in wani ya gaya mata”.
Mus’ab ya shiga tsoro da fargaba, ya qosa qwarai Abu ta kai qarshen maganar tata ko kuma ta katse dogon bayanin ta gaya mishi me ya yiwa Hamidan? Kar dai fa mafarkinshi ya zama gaskiya? Kar dai fa da gaske ne Hamida ta je gidanshi ya jefe ta ya fasa mata kai? Tambayoyin da suke kai kawo cikin zuciyarshi kenan.
Abu ta shiga kuka sai dai ba ta bar magana ba.
“Haba Mus’ab, sai yaushe ne za ka bar wannan mummunan halin naka? Duk yanda qannenka suka kai da baqin cikin hanaka auren da aka yi ya ya za suyi? Me za suyi wanda ya wuce abin da suka yi? Dole ne su tsaya ayi hidimar auren Saddiqa dasu.
‘Yar’uwarku ce, hanaka aurenta da aka yi ba zai sa ku yanke zumuncin dake tsakaninku ba, tana da haqqin ku yi zumunci da ita. Kune ‘yan’uwanta da ta fi sani ta fi so, ta kuma fi shaquwa dasu, tunda ba ta da abin da take so take kuma girmamawa irin uwarku.
Raina ya yi matuqar vaci sanda Bilki ta zo min da bayanin shirin da ake yi a kan hanaka aure, na kuma yi nufin zuwa gidan naku in samu shi Malam Abdullahi tunda da yardar shi ake yin komai.
To amma da Bilki ta aiki ita Hamida gidanka don ta je ta gaya maka abin da ake ciki, saboda ka hanzarta zuwa ku tattauna ku san abin da za ku yi ta dawo. A yanayin da ta dawo na kuma kalle ta na tabbatar ba kukan fasa mata kan da ka yi take yi ba, tana kukan baqin ciki ne na yanayin da ta same ka a ciki. Sai na gane ba komai yasa iyayenku hanaka auren Saddiqa da suka yi ba illa kawai su xin mutanen kirki ne masu gaskiya da riqon amana, Ubangiji kuma zai yi musu kyakkyawan sakamako a kan zumuncinsu.
Gaskiyarsu ne, Saddiqa ba matarka ba ce, kai daban ita daban, ka fi qarfinta ba za ta iya rayuwarka ba, kowace qwarya ai da abokin burmin ta. Ka girma ne baka san ka girma ba, in an ganka a tsaye cikin sutura abin gwanin sha’awa, amma hali babu. Da girman nan naka da gwarjinin naka giya kake sha, in ka sha kuma ka yi hauka, qannen ka ma basu tsira ba, to wa zai tsira?
A wannan halin naka kuma wane mutumin kirki ne zai xauki ‘yarshi ya baka in dai ba a kan rashin sani ba, ko kuma yana kwaxayin abin hannunka?”
Wasu hawayen masu yawa suka sake zubowa daga idanun nata, dai-dai lokacin da ta xago idanuwanta ta kalli Mus’ab ta ce mishi.
“Iyayenka mutanen kirki ne, nima rashin adalci ne ya sani vacin ran abin da aka yi makan, in ban da haka ai dukanku xaya ne a wurina, kai da Saddiqa xaya kuke, ita gaskiya kuma ai guda xaya ce daga kauce mata kuma sai a shiga vata, bai kuma dace in yi hakan ba”.
Mus’ab yana zaune ya rasa yanda zai yi, ya rasa inda zai sa ranshi ya ji daxi, ga Abu da Bilki sun qi daina kukan da suke yi, ga shi nashi hawayen sun qi yarda su zubo balle su haxu su duka ukun suyi kukan.
Sai dai zuciyarshi ta kai matuqa wajen quntata, zafin da take yi ya wuce duk yanda za a yiwa kwatance, ya rasa me zai yi. A hankali ya miqa hannu ya xauki xan makullin motarshi dake ajiye kan tabarma ya miqe ya fita ba tare da ya san inda zai tafi ba.
Tuqin kawai yake yi bai san inda ya dosa ba, zuciyarshi cike da baqin ciki da nadama, da dai da hali to da ya ce daga yau ba zai sake tava barasa da hannunshi ba, saboda baqin ciki da qasqanci ga abin da kunyar da ta ja mishi, a dalilinta ya rasa yarinyar da yake ganin tamkar don shi aka haife ta Aisha saboda tsananin son da yake yi mata.
Ga kuma qasqanci da kunyar da ta ja mishi wurin ‘yar qanqanuwar qanwar shi ‘yar autan xakinsu Hamida, wacce ya tabbatar kafin zuwan nata gidanshi ta same shi a halin da ta same shi ba za ta gaskata komai game da labarin da take ji a kanshi ba, da wuya ma ta saurari irin waxannan maganganun saboda tsananin girmamawar da take yi mishi.
To wai ya fasa mata goshi da kwalbar giya ya yi mata rotse saboda wai ya bugu, wace irin giya ce wannan? To wai tunda yake shan barasa ma shi wane alheri ta tava haifar mishi ne in ban da sharri. Ya yi nisa cikin tunanin sharrin barasa.
Sai kuma ya ji wata zuciyar tana ce mishi, babu ruwan barasa, ba ma laifinta bane, gata ne kawai ba shi da shi, rashin tsayayye a kan al’amari ne kawai ya ja mishi, da yana da tsayayye da ba a jefa shi ba ma cikin damuwa da vacin ran da zai samu kanshi cikin wannan halin ba. Inna ce ta rasu ba ta nan ne, da tana raye da ban ma samu kaina a irin wannan yanayin ba.
Kalaman da suka rinqa kai kawo a zuciyarshi kenan, bai kuma ankara ba saia ganin shi kawai ya yi yana shiga cikin unguwarsu ta Tudun Alqali dake cikin garin Bauchi.
Ya yi parkinga a qofar gidansu wanda a yanzu ya mai da shi ginin zamani saboda rushe tsohon ginin da ya yi ya yi sabo. Kawu Gixe yana zaune cikin falon shi ya yi sallama ya shiga ya tsuguna.
Da sauri Kawu Gixe ya soma tambayar shi.
“Me ya same ka Mus’abu? Me ya sameka kake wannan baqin cikin?”
Mus’ab ya matse idonshi hawayen da suka taru suka xiga, abin da ya yi dalilin miqewar Kawu Gixe tsaye saboda tashin hankali.
“Me ya sameka?”
Ya sake yi mishi tambayar bayan ya kafa idanuwanshi a kanshi.
“Maraici ne kawai ya dame ni Kawu, tunda Inna ta rasu ta barni na koma watangaririya a tsakanin mutane, bani da wani tsayayye a kan al’amarina, rashinta yasa na samu kaina cikin baqin ciki da vacin rai, da tana raye da ban samu kaina cikin qasqancin da nake ciki ba a yau. Bani da uwa bani da mai tausayina balle ta rufa min asiri, bani da kowa, bani da inda za ni in faxi damuwata.
Shi yasa na zo gabanka in yi kuka don ka qara sanin har abada ba zan daina kukan mutuwar Inna ba, inda tana raye a duniya da babu mai yi min irin tonon asirin da aka yi min a Misau, an taro an nuna min fin qarfi an hanani auren Aisha saboda wai ni xin mashayi ne, da tana nan a raye Kawu da tasa an bani auren duk da ita xin ta fi kowa sanin mugun halayena, da ba za ta hanani auren ba, saboda ta san rabani da ita zai iya haddasa min vacin rai na samu kaina a yau cikin baqin ciki da qunci da ciwon zuciya, amma wai a hakan Abu ta sani a gaba tana yiwa waxanda suka hanani auren addu’ar Ubangiji ya saka musu da alheri, don wai gaskiya da adalcin sune yasa suka hanani auren da suka yi”.
Kawu Gixe ya koma kan kujerar shi ya zauna ya zubuawa Mus’ab ido, cikin nutsuwa ya tambaye shi.
“Dama kai kana son Saddiqa ne baka yi magana ba?”
Ya ce, “Eh, Kawu hanani yin maganar aka yi ta hanyar tsoratar dani wai idan na ce ina sonta za a gaya mata halina, to ga shi ban tsira ba, abin da na guda shine ya sameni. Inna ce jagorar rabani da Aisha, su Baba da su Abu suka mara mata baya. Ni ban ma qara sanin da hannun Abu a ciki ba sai da na jita ta dage tana ta yi musu addu……”
“Kai tafi can ka rufe min baki, kai ka jawa kanka komai, yanzu ka zo kana wannan surutun da in ba sa a ba zai tashi a shirme da surutu, bayani nake so na yanda aka yi hakan”.
Mus’ab ya shiga yi mishi bayani dalla-dalla tun farkon yanda ya faro maganar a gaban Abu, har kawo lokacin da Innarshi ta yiwa Saddiqa bayanin komai, al’amuran da suka biyo bayan hakan da suka yi dalilin bikin gaggawa da suka tayar, har rotsen da ya yiwa Hamida da ya zama hujjar Abu ta fita cikin lamarinshi, da addu’ar da take yiwa iyayenshi bai voye komai ba.
Kawu Gixe ya sunkuyar da kai qasa cikin tunanin mafita. Mus’ab ya yi matuqar razana, don tunanin ko shima zai yi fushi da shi ne. nan da nan ya shiga ba shi haquri yana magiya.
“Ka taimakeni kasa baki cikin lamarin Kawu ka hana su xaurin auren da suke shirin yi jibi, ka tura shi zuwa wani lokaci dan in samu damar da zan ga Aisha in san yanda na yi-na yi mata bayanin da za ta fahimceni, zan gaya mata irin son da nake yi mata, zan yi qoqari in fahimtar da ita al’amura masu yawa da ke tsakanina da ita a baya, ban samu damar gaya mata abin da ya kamata in gaya mata ba saboda ina tsoron kar a tona min asiri a wurinta, to yanzu kuma tsoron ya qare zan nuna mata……”
“Kai rufe min baki mashirmancin banza!”
Kawu Gixe ya yi maganar a yanayi na vacin rai. Ya yi maza ya ja bakinshi ya yi shiru.
“Kira min Malam Hadi”.
Ya tashi cikin nutsuwa ya fita don cika umarnin da Kawun ya ba shi, ya nufi unguwar Railway don isar da saqon.
Malam Hadi shine amini na qut da qut a wurin Kawu Gixe. Bai yi qasa a gwiwa ba ya biyo shi suka taho tare, ya wuce cikin gida ya barsu nan suna tattaunawa.
Mus’ab yana zaune a wani xaki da ya barwa kanshi a cikin gidan, wanda yake ganin tamkar shine a gurbin na Innarshi da ta rayu a ciki, inda tana nan da ita ce za ta bani Aisha, ba tare da ta damu da cewar ni xin mashayi ne ko manemin mata ba, inda tana nan ma wataqila da ban samu kaina a wannan halin da nake ciki ba.
Ya xan yi ajiyar zuciya kafin ya sake ya sake tsunduma cikin tunanin rayuwarshi a gaban Innar tashi, yanda ya zo mata da yanda ta tafi ta barshi.
“Wayyo Inna!”
Ya yi shiru zuwa wani lokaci kafin daga bisani ya shiga gabatar mata da addu’o’i, tsawon lokaci yana cikin wannan yanayin kafin ya koma kan tunanin Aisha da kalamanta na ba ita ba shi, bayan kuma sun yiwa juna alqawarin kasancewa tare, sai da taimekon shi kan maganar neman auren shi, sai ga shi da abin ya bayyana a kana ta bijire mishi, saboda an gaya mata halayenshi.
Sannu a hankali ya sake tambayar kanshi.
“Ko meye alherin barasa? Ko ya ya zai yi ya daina shanta? Anya in har ya rasa auren Aisha zai iya daina shan barasa a rayuwarshi? Ina ma dai a ce duk mutanen duniya irin Innarshi ne masu qoqarin taimakon mutum, gyara halinshi da mugayen xabi’unshi ta hanyar janshi a ciki, taimakon shi ta hanyar qarfafawa, mutunta shi da nuna mishi munin abin da yake yin a nutse, maimakon a qyamace shi ko a guje shi”.
Kawu Gixe suna tare da amininshi Malam Hadi, kusan minti talatin suna tattaunawa kan hanyar da za su bi su fitowa lamarin. Daga qarshe suka yankewa kansu abin da ya dace suyi, wanda ya sanya Kawu Gixe cikin sauri ya shiga cikin gida ya kira babban xanshi Adamu ya aike shi cikin motar Mus’ab ya zo da ita.
Sani da Ishaq suka iso falon Kawu Gixe cikin ladabi suka gaishe shi.
“Kawu mun zo wajenka neman taimako ka sanya baki cikin maganar auren da ake shirin xaurawa Saddiqa a Misau jibi”.
Ya kalle su ya ce, “Yau ne ya kamata ku sanar dani?”
Sani ya gyara zama cikin nutsuwa ya ce, “Kawu ka yi haquri, muma yau ne da muka bi bayan Mus’ab zuwa gidan Abu muka ji cewar jibin za a xaura aure, mun kuma nemi Mus’ab a waya ya rufe, Abu kuma ta gaya mana cewar ta gaya mishi komai, bai kuma ce mata ga inda za shi ba don haka muka ce bari mu zo gabanka mu roqi wannan alfarmar, don mun san duk inda yake in ya samu labarin an xaga xin zai samu sassauci”.
Malam Hadi ya shigo tare da wasu dattawa su uku, don haka su Sani suka ja gefe suka takure suna jiran su gama abin da suke yi kafin su sake matsawa gaban Kawu Gixe su qara roqon shi ya yi wani abu kan al’amarin.
Suna zaman jiran sai ga Adamu ya shigo da manyan qunshin goro guda biyu.
“To ai ma shi kenan mun isa Allah gafarta malam ko kuwa?”
Kawu Gixe ne ya yi tambayar.
Malamin dake zaune a gefenshi cikin rawani ya ce mishi, “Eh, mun isa ai shaidu ma su kan gamsar wajen xuarin aure, balle mu a nan mu shida ne”.
Da sauri Malam Hadi ya ce, “Ai ga su Malam Isa ma sun dawo”.
Ya yi maza ya leqa ya kirasu suka shigo, su ma su uku. Nan take Kawu Gixe yasa aka xaura auren Mus’ab da Aishatu, abin da ya yi matuqar baiwa Sani da Ishaq mamaki.
An gama xaurin aure an raba goro, jama’a suna watse kowa ya nufi gidanshi, Sani da Ishaq suna durqushe gaban Kawu Gixe sun rasa kalmar da za suyi amfani da ita wajen yi mishi godiya. Sai ga Mus’ab xin ya shigo saboda kiran da Kawu Gixe yasa aka yi mishi.
“Ku gama kafin in fito”.
Kalmar da Mus’ab ya riska kenan na maganar Kawu Gixe. Ya kuma kalli Mus’ab xin bayan ya nuna su Sani da hannunshi.
“Ga masu neman ka can”.
Ya wuce ya yi tafiyarshi. Ishaq ya qanqame Mus’ab a yanayi na tsananin farin ciki.
“Na rantse yau ne na tabbatar da kalmar da Hausawa ke furtawa ta ABU NAKA…. Wai maganin a kwaveka. Kawu Gixe ya xaura auren ka Mus’ab”.
Mus’ab yasa hannu biyu ya hankaxe shi.
“Kai bana son irin zolayar da kuke yi min yau? Haka Sani ya ce min wai sun sato Aisha ashe qarya yake yi min, zuciyata a quntace take ina cikin wani al’amari da ban san shi ba……..”
Kan ya qarasa maganar tashi Ishaq ya yi mishi rantsuwa.
“Yanzun nan muka gama xaurin auren ka Mus’ab, Kawu Gixe ya baka auren, ga goro ga minti ga takardunsu kana kallo”.
Sai a lokacin ne hankalinshi ya kai garesu, gabanshi ya yanke ya faxi, cikin fargaba da tsoro kar dai shima Kawu Gixen irin auren da Abu take so ta yi ya yi mishi, auren huce fushi.
Hannu ya xora kan qirjinshi saboda harbawar da takeyi.
“Kawu Gixe ya xaura min aure?”
Da qyar ya iya buxe baki ya sake tambayar su.
“To wa ya bani?”
Sani yana murmushi ya ce, “Saddiqa”.
Mus’ab ya kalle shi haushin zolayar da suke yi mishi ya qara kama shi, me suke nufi dani waxannan? Basa tausayina ne? Ko so suke su mai dani tamkar mahaukaci? Ya juya ya fita wajen Kawu Gixen ya tafi.
“Ka taimakeni Kawu kar ka bani auren da ba shi nake so ba, Aisha kaxai nake so in ba ita ba ce gara a barni haka kar a xora min nauyin kowa a kaina, a barni kawai in yi zamana a haka”.
Kawu Gixe ya zuba mishi ido.
“Me abokan naka suka gaya maka?”
Ya buqaci sani.
“Kawu rabu dasu, su basa tausayina zolayata suke yi. Sun ce min wai da Aisha ka xaura min auren, amma na san qarya suke yi so kawai suke yi wai su ga na samu nutsuwa, bayan kuma baqin ciki ya sameni”.
Cikin nutsuwa Kawu Gixen ya ce mishi, “Ita na baka Mus’abu, da ita na xaura maka aure, ai taka ce. ABU NAKA…. Maganin a kwave ka. Gaskiya ne da ka ce inda uwarku tana raye za ta baka ita ba tare da ta xaga ido ta yi duba kan irin laifuffukanka ba, ba ta nan, to ni ina nan, nima kuma ba zan iya barinsu su rabaka da ita ba. Don haka a zaman da kake yi a yanzu Aisha matarka ce, na baka ita ta hanyar xaura auren sunna a tsakaninku, mallakinka ce tana qarqashin hukuncinka, yanda ka so haka za ka yi da ita a yau”.
Mus’ab ya sunkuyar da kai a gaban Kawu Gixe tsawon lokaci bai ita ce mishi komai ba. Sai Kawu Gixen ne yake magana mafi yawancin nasiha shan giya da neman mata.
“Manyan musibu ne Mus’abu, aiyukan savo ne masu girma, kai ka sani irin waxannan aiyukan kuma xabi’u ne na mutanen banza, mutanen da basa tsoron Ubangiji, kai ba mutumin banza bane, domin mutanen kirki ne suka haifeka, iyayenka mutanen kirki ne, ka fita cikin wannan rayuwar ko kaxan ba ta dace da kai ba, ba kuma ina yi maka wannan maganar bane a yau wai ko saboda Aisha ta zama matarka, a’a, sai dai don a zuciyata ina burin ganin ka zama cikakken mutumin kirki ba mai yawan cuxanya da zunubai ba”.
Cikin ladabi Mus’ab ya ce mishi, “Na sani Kawu, na roqeka ka yafe min rashin kawo maganar da ban yi ba tun farko na rinqa ganin kamar bani da wani tsayayye kan al’amarina, na manta da cewar duk wani wanda ya tsaya min ya taimakeni ko ya soni ya yi hakan ne a dalilin ganin tsayawarka, taimakon ka da kuma soyayyar ka a gareni.
Kai ne ka tsamoni cikin halakar da na samu kaina a ciki, ka kawoni gidan nan kuka haxu kai da Inna kuka yi min gata, kuka mai dani mutum na zama cikakken xa mai cikakken ‘yanci, kuka xorani a bisa hanya ta rayuwa.
Ga shi a yau kuma ka sake yi min wani alherin na rabani da baqin cikin da ya sameni, ka ceci rayuwata daga shiga halin butulci na ganin tamkar bani da kowa, ka bani yarinyar da nake ganin tamkar ita kaxai ke gareni, in ban same ta ba kuma ba zan mallaki kaina ba, duk da kai xin ka fi kowa sanin mugayen aiyukana, ka fi kowa sanin abin da nake yi. Na roqe ka ka taimakeni ka yi min addu’a Ubangiji ya tsare min aurena da Aisha, ya kuma zaunar damu lafiya”.
Kawu Gixe ya ce mishi, “To Mus’abu zan yi maka”.
“To Kawu ka yi min addu’ar”.
Kawu Gixe ya shirya goro da minti gami da sadakin da ya biyawa Mus’ab na kuxi naira dubu uku ya tashi amininshi Malam Hadi tare da matarshi Furera da tashi matar Raliya, suka koma a cikin motar Mus’ab suka nufi Misau Adamu yana tuqa su, don suje su isar da saqon xaurin auren da ya yi tsakanin Mus’ab da Saddiqa.
Suma su Mus’ab suna ganin tafiyarsu suka bar gidan cikin motar Ishaq, su ma Misau xin suka nufa, zukatansu cike da farin ciki da annashuwa, suna tafe suna hirar Kawu Gixe da alherinshi.

1 2 3 4 5Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected