AKWAI LOKACI BOOK 2 BY UMMU AFAN
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Story & written
By
The special writer
UMMU AFAN
FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION
(F.C.T.W.A)
HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER’S OF THE NATION
I DEDICATE THIS PAGE TO YOU Hauwa’u idris ( maman daddy )
Allah yabar zumunci inajin dadin comment din ki Allah yabar kauna keep it up
AKWAI lokaci
PAGE 101to105
PROF yashigo direct dakin amaryar ya wuce sai yaji kofa gam
Kuma gashi bashida spire key
Duk guda hudun suna hade da juna
Ya koma dakinsa yayi wanka
Ya koma kan bed dinsa yadauki waya
Yasoma dialing din number husnah yayita ringing
Husnah bata daga wayar ba
Prof yayi mirmushi Wanda shikadai yasan abinda yasashi murmushi
Ya rufe ido Dan bacci amma bacci yace baisan zancenba
Yadauki wayarshi kawai yakira Ahmad
Saida yakira Ahmad sau biyu kafin ya dauka
Ahmad yace kai ango yadai kira da wannan lokacin
Hakeem yace kai dai bari wallahi man
Wallahi yarinyar nan ta kulle min kofa
aikafin yakai karshe Ahmed yafashe da dariya sosai yayi dariyarshi
Kafin yace amma wallahi husnah ta burgeni
Sosai
Hakeem yace Dan iska dariya zaka min ko
Ahmad yace aikaine abokina duk kabi ka tsorata masu yarinya aidole ta kulle kofarta
Dan batasan mezaifaruba idan akabarku Ku biyu
Hakeem yayi murmushi yace duk tagama buyanta badai ta shigo hanu ba
Zanbata mamaki zata shigo hanu ai
Ahmad yace wallahi dai kabi yarinyar mutane a hankali
Bafa babbar mace bace
Dan nasan kasaba da manyan mata
Yayi dariya yakashe wayar shi
Hakeem cikin murmushi yabi wayar da kallo
Yace zanrama ne
Kafin yakoma amma bacci fa yaki Sam
Daya rufe ido zaiga husnah alokacin da yake kissing dinta
Sai yayi murmushi ya rungume pillow kawai bacci yayi awun gaba dashi
Laila duk abinda kefaruwa tana lebe tana gani aikuwa ganin Hakeem ya burda kofa yaji akulle duk ta gani
Har wayan dasukayi da Ahmad taji aikuwa cikin farinciki ta koma part dinta ta sanar da su hajiyarta da kanwarta suby
Dan basu komaba ita suby auran nata ya mutu shiyasa zata zauna gurin Laila
aikuwa cikin farinciki hajiya rukayya tace aikin banza Ashe ma duk abinda suke yarinya bata so
Suby tace a a karku manta dama boka yace zai sa gaba a tsakaninsu
Watakila aikin ne boka ne yafara aikitakanta
Inbahakaba wazaiki yaya Hakeem a matsayin miji
Hajiyarsu tace tabbas maganarki hakatake
Kunga ganiba gwamma da muka sake mishi kudi gashi anfara aganin cigaba
Laila dai da farin ciki ta kwanta abinta zuciyarta fati kal
Karfe hudu dai dai na asuba Husnah tafarka cikin nannauyar baccin da ya dauketa
Tashi tayi tashiga bathroom alwala tayi kafin tayi nafilfilunta kamar yarda tasaba ana kiran sallar asuba tayi sallarta tayi adduointa da karatun alkur’ani
Kafin tacire kayan jikinta Dan jiya bata samu daman cire kayan ba saboda gajiya
Tashiga wanka kafin tafito
Spray kawai da shuwa tashafa sleeping dress tasaka duguwar riga abinta tafada gado abinta
Sosai taji dadin baccinta Hakeem bayan yadawo daga sallar asuba yasake tana dakin husnah shiru bata budeba
Direct dakinshi ya wuce dakinsa
Shima baccin yakoma
Karfe bakwai da rabi dai dai mai aikin mummy ta buga kofa
Suby kanwar Laila ita tabude kofar
Taga me aikin mummyn Hakeem ce
Tace sannu suby ta yatsina baki yadai ina zaki da basket din abinci haka
Tace hajiya ce ta aikeni nakawo ma amarya abin karyawa
Suby ta kebe baki tace to aikuma basu tashiba amma kawo saina na mika mata
Tabata abincin
Suby ta karba tashige dashi part dinsu gurin su Laila da hajiya rukayya
Laila cikin murna tace yauwa suby dauko maganin a side drawer kikawo
Aikuwa haka suka barbade komai da maganin nan
Farfesuf na kayan ciki sai kunun gyada da kosai
Kai kuma farfesun ganda Wanda yasha kayan hadi sosai
Haka suka bikomai suka badeshi tas
Hajiyq rukayya tace maza ke suby tashi kikaimata
Laila tace abarta ta kai Dan tanason ganin amaryar
Hajiya rukayya tace a a idan kika kai dakanki za azargi wani Abu
Zakiganta ai mudai burinmu kawai tabar gidan
Suby tace wallahi nimafa basanin amaryar nayi bama dan haushi
Husnah cikin bacci taji ana buga mata kofa ta tashi tayi hanyar falonta
Tayi kofa tabude sukayi ido hudu da suby
Suby sai tadauka kaman gezo idonta suke mata wannan irin zukekiyar yarinyar kuma daga ina
Husnah ta ce sannu suby tace ina antyntaki
Husnah ta yatsina fuska tace antyna kuma
Suby tace ina nufin amaya
Husnah tayi murmushi tace OK ai tashiga wanka
Tana ganin suby tasauke ajiyar zuciya
Husnah ta kibata hanya kuma
Suby tace ga shi inji hajiyar yaya Hakeem akawo mata
Husnah tace OK angode barin kaimata
Suby ta mika mata basket din husnah tarufe kofarta
Murmushi husnah tayi ta ajiye basket din ta ajiye kan dining kafin ta koma kan bed koma bacci
Sai karfe goma dai dai ta tashi
Ta gyara bedroom dinta da falonta ta badeshi da kamshi
Ko ina yadau kamshi kafin tashiga bathroom tayi wanka tafito ta shirya cikin wani tsadaddar super Holland dark blue sai adon pink ajikinsa
Yadda dinkin yazauna ajikinta shizaifi Baku sha’awa sosai das yamata dinkin ma kawai a in kallone
Matsalarta daya bata son dankwali ta tace gashinta takama da ribbon pink
Kafin ta murza daurin Dan kwalinta abin wuyanta ma pink ne
Gaskiya husnah tayi kyau matuka
Tadauki ta kalminta plate shoe tasaka
Har ta zauna zatafara break fast saikuma taga rashin dacewar hakan
Bata je tagaida mummy ba
Gyalenta tadauka maishegen kyau tayafa
Pink colour
Tafita tayi hanyar kofarta tasaka key ta kulle
Bayan ta fita
Dama dole saitabi ta main falonsu gabadaya tana fitowa kuwa taga mutan gidan gaba dayansu a falo
To itabasaninsu tayi ba
Ganin harda manya yasa husnah ta durkusa tana gaida su hajiya rukayya da kuma Laila
Laila ta watsa mata harara
Wai ita hakimar bata fitowa ne saike
Hajiya rukayya tace inazata fito ansamu duniya
An auri mekudi an asirceshi
Suby ta kalli husnah tace ‘yar buzuwa kotafiya za ayi ne
Husnah ta kalleta tace inje ina ai munsamu gida nida antyna
Dan nadawo kenan gwamma muma muzauna muci arzikin Dan da alama bamu kadai bane ‘yan cin arzikin
Husnah tana gama yada musu magana tayi waje abinta
Har suby zata bita hajiya rukayya tace a a kyaleta kar ajimu tun yanzu mana
Laila race lalle ma Dan talaka be iya samun wuriba
Wannan zakewa haka harda dauko ‘yar riko
To wallahi wannan yarinyar kamar aljana bazata tazauna min agida wallahi
Kalli yadda take tafiya kamar wata ‘yar sarki
Hajiya rukayya tace aibakisan halin talakabakenan idan yasami guri
Kuma ke Laila da kike cewa bazata zauna ba yayar tata ma ba zaman zatayi balle ita ‘yar cin arziki
Nan dai suka muna funcinsu
Husnah tayi sallma a falon mumy shiru ba kowa
Ta nemi guri tazauna a tafkeken falon su mummy
Mummy ta sauko daga sama bata lura ba harzata shige kitchen
Husnah tayi saurin sauka kasa tace mummy ina kwana
Mummy hafsat tajuyo tayi tazali da surukar tata
Tace a a husnah ai ban lura bama meyasa kika zauna nan baki haura saman ba saikace bakuwa
Husnah tace bakomai mummy nan ma yayi
Mummy hafsat tace a a nan gidanku ne ko ina zakishiga
Kina da damar hakan kinjiko
Ya bakunta husnah tayi murmushi kawai batace komai ba
Mummy tace kinci abinci ko husnah tace yanzu zanje nayi
Kafin mummy tayi magana Abdul Hakeem yayi sallama yashigo wata tsadaddiyar shadda milk colour sai wata hadaddiyar hula da ya murza akansa Wanda yasake fito da kyakkawar fuskarshi mai kewaye da kwantacen saje dayakarawa fuskar tashi kyau