KALBIM BOOK 1 PAGE 13
13
*ZUZEAM VENTURES*
Best APHRODISIAC
08144015291
Aslm barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah
Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500
Garin bata gaban kishiya 500
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500
Za a bakisu akan 3800
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
️️️️️️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki
**************
Kwana biyu daga mama har Ummitah da inna babu me walwala cikin tsananin damuwa suke wanda ya saka inna fara ciwo ahankali dama ga tsufa sosai ya cimmata komai yi mata akeyi ko mama ko Ummitah.
Maigari baba Alhassan ma duk yanda zai samu mafita ya nema babu dan haka ya kira Mama sukai shawara akan kudin dayake ganin shi kadaine mafita garesu dan hanawa su kawu shehu Ummitah.
Shiru mama tayi sbd nauyi da girman zancen amma kuma basuda zabin daya wuce hakan sbd shi kansa ABDULAZIZ zaifi jin sassaucin hakan akan su bari a tafi da Ummitah dan haka ta sauke numfashi ta dago ta kallesa shima shiru yayi sbd SAYYID shine ‘dansa tal namiji wanda yake so fiyeda duka yayansa dasuke mata kuma dika dika su hudu ne uku mata sai sayyid din wanda yake qaraminsu hakama duka duka baifi shekara goma sha takwas ba zuwa da sha tara so yake shima yayi karatu ya zama kamar ABDULAZIZ da suke kallo kaman wani taurari dayakeda haske mara dishewa,Amma ayau ya yadda ya dirqushe masa rayuwa ta hanyar daura masa aure da Ummitah dan hanawa dangin ubanta tafiya da ita.
Mama ma ganin kaunar Baba alhassan din dayakewa ABDULAZIZ ya sakata amincewa take gashi Sayyid din ma yanada son koyan karatu shiyasa kullum yake yawo makarantar yan boko yana kallansu yanda suke karatu.
Koda mama ta isa gida da maganar inna jikinta ya rikice wanda ciwon ajali kawai yazo mata ba bata lokaci ta zama wani iri haka suka kwana akanta anata abu daya asubar fari tace ga duniyar nan.
Sabon damuwa da tashin hankalin rashin inna suka shiga itada Ummitah dan haka suka ringa kukansu su kadai.
Rasuwar inna ta saka su kawu daga auren dan haka a kwana biyu Ummitah ta fita hayyacinta ‘dan uwanta kawai take tsananin so da buqatan gani.
Mama kuwa rashin inna dana ABDULAZIZ dinne ya ringa zuciyarta itama amma basu janye uzurinsu na aurenba dan haka inna na kwana bakwai da rasuwa aka saka Ummitah a lalle ba sanarwa sedai kawai aka ringa tayasu murnan dole.
Kafin labari yakaiwa su kawu su taho tini baba alhassan yaje gurinsu ya nema aure da dan arzikin daya rage masa duka ya basu sbd zalama suka amince atake ma suka daura auren kafin yan neman auren su tafi.
Mama kuwa duk abinda ya rage musu ta tattara ta siyar tai bikin Ummitan ta siya mata kayan daki da abubuwan buqata aka kaita.
Acan gidan baba alhassan ma gyara musu daki daya yayi lafiyayye da bandaki aka gyarawa amarya ta tare.
Ummitah tayi kuka kaman zata zarewa mamanta hakama maman tayi kuka hadda ciwo amma haka suka rabu.
*****komai ya lafa ankwana biyu kuma Ummitah bata dena zuwa makaranta ba wadda karshe ma itada sayyadin din mijinta sika koma suna zuwa tare daga karshe ma aji daya aka yan dubaru aka sakasu sbd ta dan ringa koya masa abinda bai ganeba tinda ta dade a karatun ita.
Bayan auren shakuwa da kusanci sosai ya shiga tsakanin Ummitah da sayyid suka fara son junansu sosai,
Soyayya me karfin gaske sayyid yake mata kaman yanda itama take masa dan haka hankalin mama dana baba alhassan ya kwanta sukasake duqufa adduar dawowan ABDULAZIZ.
Suna shiga ss3 Ummitah ta samu ciki wanda bayyanar rashin lafiya a tattare da ita ne ya saka aka san da cikin dan haka kulawan da ake bata ya qaru sosai.
Sayyid kuwa dadi ya ringa ji dan baima damu da rashin tsayuwarsa a rayuwa ba sbd tsananin son dayakewa Ummitah da duk abinda ya shafeta.
Bai taba ganin ABDULAZIZ ba amma kaunarsa yake mai tsafta da karfin gaske sbd irin tsananin son da Ummitah ke masa dan haka shima yake shirye daya bisa yayi masa biyayya har inda karfinsa ya qare.
Ahankali ahankali ciwon laulayi ya koma ciwo a jikin Ummitah,
Ga karatu wanda dole ta dena zuwa ga sanyi daya shigeta sosai kwata kwata cikin baizo da saukiba ko kadan dan haka mama taxo ta dawo da ita hannunta tana kulawa da ita.
*******Rashin jinsu kwata kwata tsawon lokaci me tsayin gaske ya saka ya shiga damuwar data taba aikinsa wanda ya saka masa dawowa da abinda yake yi baya dan kuwa lalacewa komai yayi sbd damuwa dan haka dole komai aka dawo farko kuma ba damar tafiya sbd aikine da zai sauya rayuwarsa gaba daya idan yayi nasara dan haka dole ya dage ya tsaya wanda hakan ne ya haddasa masa daukan tswon lokaci meyawa na shekaru bai dawo ba.
A cikin nasara da yardar Allah ya kammala tareda samun zuwa na daya wanda ya janyo masa wata irin suna da daukaka.
Murna da farin cikin mutanensa dasu alh saad suka shiga anata celebrating tareda tayasa murna hakama kamfaninsa take ya samu shiga jerin kamfanin da aka dan san dasu.
A lokacin ne babu bata lokaci ya tattara ya koma Italy daga can ko sati biyu baiyiba ya sauka Nigeria.
Bai kwana a abuja ba ya isa garinsu sbd daukosu kawai yakeda niyar yi su dawo abuja.
Lafiyayyan gida me kyau da tsari dan girma ya mallaka a abujan wanda babu abunda baa sakaba na jin dadin rayuwa wanda tin bai dawoba qasar aka gama komai na gidan da tsarinsa.
Da rana kwatsam ya sauka a garin wanda motarsa ta saka jamaa taruwa a kofar gidansu mama.
Ummitah dake zaune mama da sayyid na gefen suna kokarin ganin taci abinci da lemu da abarban data saka sayyid siyo mata sbd shima gaba daya ya haukace da nema sbd kulawa da ita da Buqatunta gashi kusan ya tare gidan maman shima sbd ita.
Mama na dagowa ta kallesa saida gabanta yayi mummunan faduwa sbd gabaki daya baiyi kama da ABDULAZIZ dintaba
Hawayene suka fara gangarowa daga idanuwanta masu tsananin zafi da batasan ma na menene ba.
