Dabi'ar Zuciya Hausa NovelHausa Novels

Dabi'ar Zuciya 55

55
Dz

A hankali cikin kasala da mutuwar jiki take takowa zuwa kitchen din gidan,kitchen din data jima rabonta dashi,saiko yau,tun bayan wayar da samir din yayi,ya umarci hajiya qarama ta baro gidanta su tattaro su dawo cikin gidan professor rashid din,bayan nan dinma ya sanya an qara securiy,wanda gaba dayansu babu wanda yasan abinda hakan yake nufi,don babu wanda ya yiwa bayani a cikinsu.

Baccin daya yanke mata tun cikin dare ne cike a idanuwanta,tun daga sanda tayi mafarkin matar bata sake rintsawa ba,don haka ta yanke shawarar fitowa zuwa kitchen din ta kama wani aikin ko hakan xai debe mata kewa,ya kuma qwarara jikinta.

Tun daga nesa ta hangi biba tsaye cikin kitchen din tana feraye dankali,sai tayi sallama,biban ta waiwayo fuskarta dauke da fara’a tana amsa mata.

“Ina kwana” kaltum ta gaidata tana zaro wuqa a ma’ajiyarsu,ta fara tayata firar dankalin,amsa mata tayi kamar kullum cikin sakewa,sai suka fara taba hira sama sama,duka hirar tasu akan ciwon daddy ne da makamantansu,saidai can qasan ran kaltum maganar da takeson yi mata tana tsunkulinta,bata samu damar yi mata ba har sai sanda suka gama gyara komai suka dora kan wuta.

“Ashe hotonki maman yaya saraki ce a jiki?,kuna da alaqa daman?” A birkice ta dago kanta ta dubi kaltum,razana da firgici suka bayyana baro baro saman fuskar biba,ta soma waige waige da hanzari,ta tabbatar babu kowa sai kawai ta wafci hannun kaltum ta tura qofar baya ta kitchen din ta jata ciki.

Idanuwa ta tsare kaltum dasu,kafin hawaye ya soma wanke mata fuska,cikin muryar kuka,kans murya can qasa ta fara magana

“Duk yadda nayi dake karki tona wannan maganar kaltume saida kika tono ta?,shin bakyason lafiyarki ne?,ko bakison ranki dana iyayenki?,to bari na buda miki komai ko hakan xaisa ki janye kika ki kuma yiwa kanki da yan uwanki gata…….tabbas mamar samir ce a jikin hoton,raihana……wadda ni ba kowa bace face ‘yar aikinta shekaru masu dama,yar aikin data dauketa kamar ‘ya uwa,ta yimin dukkan wani gata,ta bani kulawa da dan uwa zai baiwa dan uwansa,hakan yasa nima na dauketa kamar yar uwata,na kuma riqi samir kamar d’ana…..mutum ce iya mutum,wadda duk yadda za’a kwatanta miki kirkinta ba zaki fahimta ba sai zama ya hadaku da ita…..kwatsam dare daya hajiya jidda ta shigo rayuwar professor rashid…..ta zama matarsa,abinda babu wanda ya taba zato ko tsammanin zai faru,duk da cewa kusan auren cin amana ne jidda tayi da professor amma haka hajiya raihana ta karbi qaddararta…..” Dubanta kaltum tayi tana mamakin kalmar auren cin amana,kamar biba zuwaira tasan me take rayawa saita gyada kai

“Eh…..auren cin amana,domin kuwa jidda ‘yar aikin hajiya raihana ce” idanuwa kaltum tadan bude kadan alamun mamaki,wannan wanne irin labarine haka a birkice?

“Karki dauka gama garin me aiki” biba ta fada tana sake matsawa kusa da kaltum muryata a kwance

“A’ah,irin masu aikin da basu da kowa,suke da matuqar buqatar taimako,ta daukota ta kawota cikin gidanta,ta nuna mata dukkan gata da rufin asiri,ta sanyata taci gaba da karatun jami’a,bayan ta kammala,tasa Daddy ya bata aiki a wani kamfani nasa da alokacin yake gudanar dashi,duk da hankalinsa a sannan ya fara karkata ga siyasa…..amma jidda ta aure mata miji,ta kuma janye hankalinsa gareta ita daya qwallin qwal,munyi imani bata asiri bata kuma aiki dashi,bamusan da wanne siddabaru take amfani ba,amma ta juya tunanin professor gaba daya,bashi da cewa sai tata,kullum kwanan duniya akwai fada ko tashin hankalin da zai saukewa hajiya raihana,tun bata damuwa harta shiga damuwa,kwata kwata ta zama kamar ‘yar kallo cikin gidan,qalilanne cikin ‘yan uwan professor suka koma suna ta tata,kamar irinsu hajiya qarama,jidda ta janye komai ta kuma janye kowa……,lokaci mai tsaho ana a haka,har zuwa sanda jidda haihu yara mata guda biyu,tazararsu shekara biyu kacal,ba jimawa hajiya raihana ta samu ciki itama,wanda tunda ta sameshi babu zaman lpy,cikin da ta fita dashi kenan,rana daya muka tashi cikin gidan nan da maganar bacewarta,qaura wambai babu ita babu dalilinta,sai samir data bar mana,duba na duniya ba’a samu hajiya raihana ba,a sannan jikina ya bani ba mutuwa tayi ba kamar yadda mutane keta fada,saboda ganin girman cigiyar da akayi amma babu labari ko motsinta.

Zuciyata ta sake yarda da abinda take raya min ne na cewa ba bata tayi ba,akwai abinda ya faru da ita,saboda wasiqa dana samu saman gadonta,kuma bisa dukkan alamu tana tsaka da rubutata ne abinda ya sameta ya faru da itan,sirrine tsakanina da ita,bazan iya gaya miki ba…..a lokacin jidda ta shigo dakin kawomin samir daketa rigima akan na lallasheshi,taga wasiqar,ta karanta,a gabana ta duqunqune wasiqar ta kuma sakata a toilet tayi fuloshing dinta

“Dukkan abinda ta rubuta ki daukeshi ki watsar dashi gefe…..bari na gaya miki,yau ba watan raihana uku ba bata nan?,to ki sanya a ranki watanta uku cikin kabarinta…..domin ba zaku sake ji ko ganinta ba,wannan maganar ina gaya miki itane tamkar kana tona sirrinka ga wanda yake kan gargarar mutuwa,kinga ba wanda zaiji saidai ko qasar kabarinsa…….fitar wannan maganar dai da take rasa ranki,hakanan dukkan wanda kika shaidawa shima kin sakashi cikin babban hadari,babbar soyayyar da zaki nunawa dukkan wanda ke tare dake shine,ki kiyaye kunnuwansa daga sauraren wannan batun” maganar data gaya min kenan cikin kakkausar murya da yanayi me ban tsoro.

.

“Na tsorata sosai,don haka a sannan na roqeta kan zan ajjiye aiki,zan koma gida”

“Bismillah,kina iyawa indai kin shirya mutuwa keda duk wanda yake rayuwa tare dake” wannan maganar tasa nayi shuru ina tsuma saboda tsabar tsorata,ta jefeni da wani kallo,sannan ta matso gabana

“Bari na gaya miki wani abu….keda duk wanda yasan qamshi qamshin abinda ya faru bashi ba fita daga gidan nan,aiki kuma yanzu kuka fara har zuwa .lokacin mutuwarku,bance ba zaku dinga zuwa gida ba,amma babu tabbaci har sai abinda na gani” da wannan maganar ta fita ta bani waje……haka na rayu dukka shekarun nan ina kuka a boye na rashin raihana,ina addu’ar Allah ya bayyanata idan tana raye,idan kuma da gasken ta rasu…..to ina mata fatan samun rahamar Allah da dacewarsa,ina kallo take nunawa samir soyayyar da nasan bata gaskiya bace amma bani da abinda zan iya aikatawa…..sai taso sangartashi da lalatashi amma haqarta bai cimma ruwa ba,ban sani ba ko qarfin addu’ar mahaifiyarsa ke bibiyarsa,da kuma alkharin da tayi a rayuwarta ne yayi masa tasiri?……da wannan bata yiwu ba saita canza salo,ta sanya samir yana sabawa dukkan muradi ko buri da abinda mahaifinsa keso,ta wannan hanyar ta kauda dukkan wata jituwa da qauna da yakewa samir din,ya koma kallonsa a matsayin bijirarren da mara biyayya,a fakaice takeson ture samir daga zuciyarsa ta cusa najwa ta qarfi da yaji,taso hadawa da jawahir….amma yarinyar sai Allah ya halicceta daban,kusan ta debo dabi’un samir din,wannan yasa sukafi jituwa qwarai da gaske……abu daya ne yasa naqi shiga wannan yaqin kan rayuwar samir….” Shuru ta danyi,murmushi kuma ya subuce daga fuskarta ta tsakiyar hawayenta

1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected