VENNETE
AMATULMALEEK Complete Hausa Novel

AMATULMALEEK Complete Hausa Novel

Abdulhameed duk da Yana cikin kulaficin son komawa gida a take harma da tsoron inda yaga sunzo din Amma sosai ya saki cikinsa ya ringa cin cimar da Bai taba cinta arayuwarsa ba Dan kuwa baitaba ganin ko dankalin turawa da idanuwansa ba bare ci hakama doya har gwara kifi suna Gani a masu siyarwa na kauyensu da masu zuwa ruwa su kamo.

Dadin dahuwar wadda take ta musamman Dan kuwa duka masu aikin gidan wainda suke da karatu akan aikinsu ake dauka Dan haka masu girkinsu komai nasu kamar a 5star restaurants kake,
Hakama masu aikin tsafatace gidan Suma kusan sai wainda suka samu training me kyau ake dauka sbd kusan gaba Daya rayuwar taurawan datake cikin ASH TALBA tagama kama iyalinsa da kusan gidan komai a daki daki akeyinsa kan tsari da rashin tarkacen da zai damesa.

Ita kanta maamah taci abincin sosai ba laifi suka sha Wani homemade drink da ko zaa kulla musu bomb ya watse dasu basusan dame dame acikinsa duk da fruits ne zalla Amma dai Sam basusan meye shi din ba sudai sunci Kuma sun koshi.

Suna gamawa ta rabe kayan gefe sbd na Amatu da suka rage Mata.

Toilet dayake dakin suka shiga
Dayake ta iya amfani duk da irin wainnan abubuwan sbd tasowa gidan masu arziki Dan haka Bata manta yanda ake amfani da wasu abubuwan ba da yawa.
Wanke musu hannuwansu tayi nata Dana Abdulhameed daketa lashe hannun.

Sabulun tasaka ta wanke masa hannu da kyau itama ta wanke nata kafin ta goge musu bakinsu suka fito tana ce masa ya koma yayi bacci kafin azahar ta qarasa yi ya sake warwarewa.

Hayewa yayi gadon Yana cewa

“To Amma bazaki fita koina ki barmu anan ba ko?

“Babu inda zani Ina Nan zaune harku tashi Nima Dan rintsawa zanyi kafin lokacin yayi.”

Yana Jin Hakan ya sauko daga gadon Yana cewa
“To zan kwanta a gurinki”
#MAMUH#
#ASH TALBA
#LA HOT
#FRIENDSHIP
#LIFE
#AMATULMALEEK
#NAUFAL TALBA

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
YANCI DA RAYUWA
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070
Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest #

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

6
A qasa kan tiles Maamah tayi kwanciyarta kan daddumar sallah tareda Abdulhameed Daya shige jikinta tin tana jiran farkowan AmatulMaleek har bacci ya Dan fixgeta itada Abdulhameed din.

So biyu ana Aiko khaltume dubasu ko sun tashi Amma Basu tashi ba Kuma Madame tace kada a tashesu Dan haka aka barsu sukai bacci sosai batareda Maamah din ta san ta dauki lokaci sosai haka tan baccin ba.

Sanyin tiles ya dayayi musu yawa ya farkar da ita dole lokacin karfe biyun Rana harda minti talatin da takwas Dan haka cikin sauri ta tashi tana janye Abdulhameed Daya cukuikuyeta sbd sanyi ta miqe tsaye tana kallan gadon Taga AmatulMaleek din itama tana motsawa alamar tashi zatayi Dan haka toilet kawai ta wuce Tayo alwala ta fito tayi sallah tana idarwa Amatu na farkawa Dan haka itace ta kamata da kanta takaita toilet tabarota.

Ita kanta Amatu ta Dan iya aiki da wasu abubuwan bandakin sbd zuwan da suka taba yi tafara Dan wayo lokacin.
Fitsari tayi Tayo alwala itama ta fito ta tsaya gefen Maamah tayi sallah tana idarwa Abdulhameed na na tashi daga baccin Shima.

Da sauri Maamah ta miqe ta rakasa toilet sbd fitsarin dayake cewa ya matsesa.

Bayan fitsari harda zawo yayi sbd abincin Daya Dan fara tabashi kasancewar ciki Bai Saba da wannan dadin ba,
Fitowa yayi bayan Maamah ta wanko masa hannuwansa da kyau da sabulu
Gefen AmatulMaleek ya zauna Yana kallan kayan abincin Dake gefen ajiye yafada mata nata ne sunci sun rage Mata tin dazu.

Kallansa Amatun tayi bayan ta Kalli kayan abincin Amma Bata motsaba sbd ba Maamah ce ta Bata ba.

Maamah kuwa toilet din tahau wankewa sosai sbd kada su lalata musu guri Dan tasan tsananin karfin tsaftan masu gidan sbd duk Wanda ko kalilan sani yayiwa ASH TALBA yasan inda qazanta take da inda yake akwai Nisa me yawa da zurfi.

Sosai ta Saka karfinta ta wanke toilet din tayi masa fes ta fito tana kallan Amatu Dake zuru tana kallan Abdulhameed Dake ta fada mata dadin abinda suka ci din tana bacci.

Wani sanyayyan murmushi maamah tasaki tana qarasowa fuskarta a sake ta kallesa tana cewa

“Gashi Kuma bazaka sake ci ba yanzu sbd yafara lalata Maka ciki.”

Dariya yayi Yana maqale kafadarsa Yana cewa

“Zan sake ci mana ai idan munkoma bazan sake ci ba shikenan.”

Daga Maamah har Amatu da batada karfin jikinta qaramar dariya suka saki sbd yanda yake matse da a dauko abincin.

Maamah ce ta janyo abincin bayan ta zauna itama a tareda su qasan.

Bude abincin tayi da kanta ta zubawa AmatulMaleek komai kaman yanda suka hade tana cewa

“Ki cinye tas sbd Kinga ba karfi jikinki ta yanda zaku samu kuzari sai muje akaimu ku gaida mommynku Abeeda harma da sauran mutanen gidan.”

Gyada Kai kawai AmatulMaleek tayi tana Saka hannu a abincin sbd itama ya shiga ranta sosai duk da batada kwadayi Amma shi abinci irin wannan basama ganinsa bare.

Abdulhameed ma dole tareda Amatun ya sake cin abincin itama Maamah hannu ta Saka sukaci abincin tare su uku Abdul naci Yana tambayar AmatulMaleek idan tanajin dadin dayake ji a abinda sukeci din.

Dariya Amatun ta Dan ringa yi masa tana cewa

“Maamah wlh ‘dan Nan naki duk ya haukace sbd cin abinda be taba ci ba.”

Itama Maamah din yar dariya tayi tana cewa

“Kyalesa yaci ai na kwana biyu ne muna komawa kaman yanda ya fada shikenan.”

Cikin kulawa da tsananin so da kaunar juna sukaci abincin su uku suna Dan magana Sam sama,Maamah kusan duk Rabin cin abincin nata su take gyarawa kidin tana ja ye musu qashinsa abubuwan data San bazasu iya ci ba tana musu fira cikin kulawa da kaunarsu.

Suna gamawa wannan Karan su ukun suka shiga toilet suka wanko hannuwansu Maamah na fitowa ta tattara gurin tareda kayan ta fito dasu ta nufi hanyar kitchen tana isowa khaltume da Masu aikin abincin Dake girkin dare kallanta sukai tareda karban kayan hannunta.

Kallan khaltume tayi tana cewa Ina zata wanke kayan saita wankesu da kanta.

Karban kayan khaltume tayi tana cewa ta barshi kawai.

Kasa tafiya maamah din tayi sai data taimakawa khaltume gurin wanke kayan kafin ta koma.

Zama sukai a dakin shiru daga ita Se su Amatu suna Dan firarsu sama sama sbd daga Amatun har Abdulhameed sun warware kamar ba’a nade aka shigo dasu ba ba lafiya sosai Daman yunwa ce da wahalar hanya Se iska da sanyin kwanan Tasha.

Har yamma Babu Wanda ya shigo inda suke aka nemesu Suma haka sukai zamansu.

Koda Akai sallan magrib Wani abincin aka sake kawo musu Basu ci ba sai da sukai sallah tukuna suka zauna sukaci a plate Daya su dukansu dayake wannan Karan farar Basmati rice ce da brown chicken stew wadda Babu Mai sosai acikinta sbd lafiyansu da suke kulawa da ita sosai a gidan.

Kazar Dake cikin miyan zata Kai guda harma da Rabi Kila Dan kuwa duk yanda sukaci ta Basu cinyeba hakanan suka tattara kayan Maamah dince ta sake fita dasu takai kitchen ta dawo.

Har Akai ishai baazo antafi dasu can gurin masu gidan ba sbd umarnin da Abeeda ta bayar na a barsu suyi kwana biyu suci su huta yanda ya kamata kafin su fara Dan zagayawa sbd sam Bata kaunar ganinsu a yanda suke din.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected