Furar Danko Book 1 Complete Hausa Novel
“Dama haka ake jiyyar mara lafiya Madam?”.
Hararsa ta ɗanyi da taɓe baki. “Ka dai san mai jiyyarka ba dai Mawaddat ba”.
“Uhm hakane ashe Ahmad ne kuma fa”.
Ya faɗa yana danne dariyarsa.
Sake taɓe bakin tai taƙi cewa komai. Da ga haka shiru ya ratsa falon, yana tunanin faɗa mata zancen tafiyarsa da ya taso ne, dan abinda ma ya kawo Ahmad kenan, amma sai yaga bari dai ya bari ta sake nutsuwa ko zuwa gobe in sha ALLAHU. Kusan mintuna goma ya sake takalota da faɗin, “Ba abinci gidan ne? Ina kuma yaran nan banji motsinsu ba?”.
Yanzu kam kai tsaye ta bashi amsa da “Sun wuce”.
“Abincin fa?”.
“Na daina girki a gidan nan”.
“Miyasa?”.
“Ba sai da dalili ba, dama can ra’ayi nayi, yanzu kuma na daina sai ka bari sai ka auro matar da zata maka”.
“Kishiya kike sha’awa kenan?”.
Kamar bazata tanka masa ba sai kuma tai murmushi. “Sai dai idan yau zaka aurota ko gobe kafin cikar jibi da zan ƙara gaba maybe wasu su kalleta a matsayin hakan”.
Murmushi kawai ya saki, maimakon cewa wani abu akan batun nata sai cewa yay “Bani furar da Ahmad ya kawo Please dan yunwa nake ji”. Kamar bazata je ɗin ba sai kuma ta miƙe. Babu jimawa ta dawo da furan da kofi ta ajiye masa ta koma inda ta tashi. Television ta kunna shi kuma ya zuba furar ya fara sha.
“K mi kika ci?”.
“Ba buƙata”.
Ta faɗa a takaice.
“Okay amma da kinsha furan da ga gidan Ammah ya amso ta”.
Ɗagowa tai ta kallesa. Sai ya jinjina mata kai alamar tabbatarwa.
“Gama ka bani kofin bana jin sake tashi”. Ta faɗa tana maida kanta ga wayarta. Bai sake magana ba har ya gama ɗin ya zuba mata, sai dai bata da yawa dan haka ya miƙe da kansa yaje kitchen ya sake ɗakko wata ya ƙarasa cika kofin ya miƙa mata. Hankalinta nakan waya take shan furar harta shanye, sake ƙarawa tai. Sai da ta shanye ta biyun yay ƙaramar dariya da faɗin, “Babu wata furar Ammah da kika sha yarinya a titi ya sayota”. Da sauri ta kallesa tana yamutsa fuska, ya sake sakin dariya da nuna mata 8-10. Filo ta ɗauka ta jefa masa da yin ƙwafa tana harararsa, sai kuma ta fara ƙaƙarin amai shiko ya cigaba da dariyarsa. Kofin takai kitchen ta wanke dan bata ƙaunar ƙazanta, duk da kuwa aikin na cimata rai dan ma yana ƙoƙarin taya ta ne, tun tana ƙorafin mai aiki har ma ta bari tunda dai taga kwanakin sun ƙare mata a gidan. Falon ta dawo ta cigaba da ɗan kallon abubuwa a TikTok. Shiko yana kwance shiru ya zuba mata ido ta ƙasa kawai yana kallonta. Kiran sallar magrib ne ya tadasu su duka. Smart ya wuce massalaci ita kuma ta tafi ɗaki. Bai jimaba ya dawo gidan saboda abinda ke damunsa ba wai ya gama sakinsa bane gaba ɗaya, jarumtar da ya saba ce kawai ta dannewa. Bai samu Lulu a ɗakin ba dan itama tana nata ɗakin a cikin makamancin irin nasa yanayin koma ace wanda yafi nasan. Dan wani abu ne ke faman ratsa mata jiki mai ban mamaki. Ga tsigar jikinta sai faman tashi take kamar mai jin sanyi. Al’amarin kamar wasa sai ya fara neman fin ƙarfin Lulu, dan da ƙyar ta iya tashi tai sallar isha’i……..✍️
Lulun mu muya hwaru kuma?
‘…..!!
8️⃣6️⃣
……..Tana idar da salla falo ta koma a daddafe, a ganinta ko zata samu sassaucin abinda takeji ɗin, sai dai kamar ma ana ƙara iza mata wutar masifa ne a cikin jininta. Saman 3sitter ta haye tare da dunƙule jikinta waje ɗaya tana jin hawaye na ciki mata ido. Ta rasa wannan wace irin masifa ce haka mara daɗin kwatance.
Ana idar da salla shima Smart gidan ya nufo, dan har yanzu ba wani ƙarfin jikinsa yake ji ba, tunda ya shigo falon idanunsa suka sauka a kanta, ya ɗan yi jimm yana kallonta kafin ya ƙaraso ciki sosai yana ambatar sunanta. Bata motsa ba, hakan ya sashi fahimtar babu lafiya. Har inda take ya ƙarasa, ya kai zaune a kujerar da take yana mai leƙa fuskarta. Hankalinsa ne ya tashi ganin tana hawaye.
“Ya Salam kuka kuma? Baki da lafiya ne?”. Yay maganar yana riƙo hannunta data dafe cikinta, gaba ɗayanta ya ɗago zuwa jikinsa, sake shige masa tai cikin yanayin kamar mai rawar sanyi. Hakan sai ya bashi mamaki dan ba halinta bane hakan sam kusanta kanta da shi, sannan bai manta da gargaɗinta na ɗazun akan karya sake taɓata ba. Jin yanda tama kanannaɗe masa a jiki tana shashshekar kukan da ke ratsa masa zuciya ya sashi kasa iya cewa komai. Kusan mintina uku suna a haka kafin ya ɗago fuskarta dake kwance saman ƙirjinsa hawayenta na sauka masa, itama ɗagowa tai a hankali suka zubama juna ido cikin wani yanayi mai wahalar fassara. Hannunsa ya ɗaura saman fuskarta cikin ɗan lumshe idanu da buɗewa ya furta, “Mawaddatan’warahmah!”.
“Uhhmyim”.
Ta amsa shi acan ƙasan maƙoshi tana lumshe idanunta hawayen da suka sake cikashi suka zubo. Jiyay gaba ɗaya hankalinsa ya sake tashi, cike da damuwa ya ce, “Har yanzu kina fushi da ni akan abinda ya faru shiyyasa kike kuka ko?”.
Idanunta da sukai mugun canja launi ta sake buɗewa sosai a kansa, fuskarta a ɗan taɓe kamar mai son sakin kukan shagwaɓa ta girgiza masa kai.
“To mike damunki? Ko baki da lafiya?”.
Maimakon bashi amsa sai ta kamo hanunsa ta ɗaura a saman cikinta. Kallon cikin yay da sauri, sai kuma ya dubeta da faɗin, “Yana miki ciwo ne”. Kamar ba Lulun nan da ya sani masifaffiya ba, ta ƙara manna hannunsa akan cikin nata muryarta data koma can ƙasan maƙoshi na ƴar rawa-rawa ta ce, “Hydar yan….” sai kuma ta kasa ƙarasawa kawai ta sakar masa kuka. A karo na farko gabansa ya faɗi, ya kamata zai tayar yana faɗin, “Kinga tashi muje asibiti”. Girgiza masa kai tayi da sake nannaɗewa a jikinsa tare da kai hannunta saman gashin da ke kwance a fuskarsa luf-luf ta zubawa lips ɗinsa idanunta da sukai matuƙar juyewa fiye da yanda idan tasha kayayyakin ta sukeyi. Sororo yake kallonta, dan wannan kam shi shaida ne ba ɗabi’a ce ta ta ba. Yanda ta motsa ƴan yatsunta cikin gashin sajensa ya saka tashi tsigar jikin yamutsawa, tare da harbawar zuciya, abinda ke ƙoƙarin lafawa da ya girgiza ƴan maza a yinin na yau na ƙoƙarin zaburowa. (Anya ba wani abu daya fi ƙarfin kan yarinyar nan ta sha ba?) wani sashe na zuciyarsa ya ayyana masa, sai kuma yaji hakan bai kama hankali ba… (To mike faruwa?) Ya sake ayyanawa, sake ji yay zuciyarsa ta motsa, dan kuwa kalaman Ahmad na daren jiya ne suka shiga maimaita kansu a kwakwalwar sa, sai kuma furar da suka sha, tabbas akwai alamar tambaya… Saukar lips dinta saman nasa a bazata ya katse tunaninsa, sai riƙon da tai masa mai lafiya daya sakashi yin baya gaba ɗayansa ya zube a kujerar…..
Dama mai neman kuka ne aka jefa da kashin awaki, kuma kamar Lulu ta kawo kuka ne gidan mutuwa. Sai ya kasance ita da aka saka a tarko ma ya fita rikicewa. Ganinfa ƙurar yaƙi na neman fara tashi a muhalin da bai kamata ba bai ma san lokacin da ya bar falon da ita ba zuwa bedroom ɗinta ba…..
Sai da ya gama tabbatar da ta shiga hannu fiye da yanda yake buƙata, duk da harga ALLAH bada saninsa ta sha abinda ya kaita ga miƙa wuyar ba cikin sauƙi. Gashinta da ke cikin ribbon ya wargaza tare da duƙo fuskarsa gab da tata suna kallon juna, murya can ƙasa kamar zai saki kuka ya furta, “Kin yarda Aliyu Hydar ya zama Mawaddat? Mawaddat ta zama Aliyu?”.
Shiru kamar bazatace komai ba, sai kuma ta ɗan buɗe idanunta data lumshe a kansa itama, so take tai nazari akan maganar tasa amma ta gagara samun kowace irin dama daga gangar jikinta zuwa ƙwaƙwalwa, sai ma hannunta ta ɗaura akan nasa tana girgiza masa kanta. Itama acan ƙasan maƙoshi ta ce, “Ina jin shakku”.