KALBIM BOOK 1 PAGE 5
5
*ZUZEAMVENTURES*
08144015291
Aslm barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah
Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500
Garin bata gaban kishiya 500
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500
Za a bakisu akan 3800
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
️️️️️️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki
************
Abdul kuwa yana fita gidan tafiya me dan tsayi yayi kafin ya durkushe a gurin yana fasa wani irin kuka me tsananin gaske sanyin gaske na ratsatsa.
Saida aka fito masallaci kafin ya daure ya qarasa gida,
Koda ya isa zanin dayake rufe da umman me sanyi kawai ya yaye mata ya rufa mata daya daga cikin wanda mama sakina ta basa,
Leqa babyn datake kwance gefen umman yayi yaga bacci takeyi lafiya kalau dan haka ya fice.
Alwala yayi ya dawo daga kofar dakin ya samu inda yayi sallah.
Yana idarwa ya dawo cikin dakin ya taba ummansa yaga tana numfashi.
Ajiyar zuciya me tsananin sanyi ya sauke kafin ya fita sbd gari ya waye sosai.
Gurin me siyarda koko ya tafi
Sai alokacin ma take hada wutar hada kokon dan haka yabar kudinsa ya koma ya nufi daji ya samo abinda zai hura wutan ruwan zafin da mama sakina tace.
Duka sun jiqe abubuwan daya tsinto amma hakanan yaje ya siyo ashana ya karbo kokon daga nan ya kawo mata.
Daqyar ya iya taimakawa umman ta tashi zaune ya dora mata robar kokon wadda ta bude bakinta daqyar kokon na shiga wanda zafinsa ya sakata jin hanjinta da suka nade suka dunqule fara warwarewa harma cikin na dan mata ciwo.
Tana gama shanye kokon amai ya taso mata gabaki daya ta amayar dashi.
Wutar ya hau hurawa wadda ta cinye gaba daya ashanar daya siyo sai daya koma ya qaro wata itama saida ta kusa qarew kafin wutar ta kama jikinsa na rawa ya dora ruwan.
Hura wutar ya zauna yanayi sosai batareda ya hutaba har saida ruwan sikai zafi sosai.
Umman daqyar ta iya tasowa ta nufi bandaki yakai mata ruwan shima ya fito ya dauko babyn ya fito daga daki sai a lokacin ya zuba mata idanuwansa yafara yi mata wani irin kallan tsafta me hade da wata irin kauna me tsananin gasken da batada sirki.
Wanka sosai umman tayi ta gyaro kanta ta fito har lokacin bata iya ko tsayuwar kirki.
Uwar haihuwar data bari a dakin ta shiga ta dauko ta goma gefen gidansu daya zube ta binneta daqyar jikin yana kakkarwa sosai sbd jirin gaske ma take gani.
Yana ganin hakan ya shiga dakin da sauri ya dan gyarosa ya share ya goge duk sanyin dakin tas ya sake shimfida mata wani zanin akan qaramar katifarsu umman ta kwanta.
Fita yayi ya sake siyo mata koko da saura Canjin daya rage ya kawo mata sedai koda ya dawo gabaki daya ta fice hayyacinta bama zata iya ko motsawa ba bare sanin meyake fada.
Ajiye robar hannunsa yayi yana kokarin dagota amma gaba daya jikinta ya sake.
Ambatar sunanta yafara yana shafa fuskanta zuwa wuyanta kuka na zuwar masa sosai.
Kuka me qarfin gaske babyn datake gefensu ta fasa wanda ya sakasa saurin juyowa yana rasa ya zaiyi.
Kuka sosai baby tafara wanda ya sakasa sakin umman ya zauna tsakiyarsu yana sunkuyar da kai shima ya fara kuka yana wani sheshekan da har jikinsa rawa yakeyi.
Ya jima a hakan batareda yasan me zaiyiba har babyn ta gaji tayi shiru ta koma bacci.
Ummansa kuwa wata firgita ta fara tana jijjiga.
Qanqameta yayi yana ambatar sunanta amma batasan ma yanayi ba.
Kusan awa daya a hakan kafin jikinta ya sake sakewa tayi baccin wahala.
Shima a gurin cikin jikinta baccin walaha da yunwa ya daukesa.
Sai azahar ya farka ya fita gidan ya nufi gurin aikin lakar dayake zuwa yana dan tayasu suna basa nera dari.
Acan yayi sallah yayita musu aiki har wanda yafi karfin shekarunsa.
Daga can wani kokon ya sake siyowa ya kawo yasha shida umman wadda sedai ya bata daga kwancen dan bata iya tashi hakama gabaki daya ta koma kamar ba umman tasa ba sbd wasu abubuwa takeyi da fizge fizge da zabura.
Yamma nayi yasan baba ila baya gida dan haka ya dauke babyn ya rufeta da zani kusan uku ya nufi gidan mama sakina da ita sbd tanada kuka.
Harya isa gidan babu wanda ya taresa ya tambayesa sbd gudunsu ma akeyi a kauyen sbd camfa ummansa da akai da baqar mace.
Mama sakin wuni tayi cikin damuwa da tinaninsu dan haka tana zaune tana hada saka da warwara tagansa ya shigo da zani
kallo daya tai masa ta gane jaririyarce ya dauko.
Cikeda mamaki da tsoro ta kallesa tana miqewa ta karbi ‘yar tana cewa
“Abdul meyasa ka fito da ita??
Yaya ummanku?
Ya jikinta?
Kasancewarsa mara hayaniya da rashin sabo da magana sosai sbd baida abokan wasa ko wasu yan uwan daya taso cikin gata yasa ita kadaice ma wacce yake magana da ita sosaima
Ya dan dago kansa batareda ya kalleta ba yace
“Tanata kuka ne tin dasafe,
Umma kuma batada lafiya tanata firgita”
Kasa cewa sakina tayi ta nufi daki takai yar da sauri tana fitowa ruwan zafi tafara dorawa kafin ta dauko abincinta na rana da bata samu ci ba sbd damuwa ta miqa masa tace
“Maza zauna ka cinye yanzu”
Zaunawa yayi yaci abincin ita kuma tana sauke ruwan dauko babyn tayi tahau yi mata wanka sbd batason baba ila ya dawo ya taddasu hakama batason yayi dare a hanya da ‘yar.
Wanka sosai me kyau tayi mata duk da bata taba haihuwaba batasan yaya akeyiba amma dayake anata haihuwa a gidan tana gani kuka tana dan saka hannu sai ta iya.
Tana gama mata wanka kayan data siya guda daya na jiran haihuwar matar Gali ‘dan mijinta ta dauko ta sakawa yar ta dauko madarar shanun datake da ita me kyau ta bata kuma cikin ikon Allah yarinyar tasha take ta koma bacci abinta.
Sake nade masa ita tayi sosai ta basa tace maza ya koma.
Karbanta yayi ya juya ya fice daga gidan.
Koda ya isa gida ummansu ta tashi tana zaune ta zubawa kofa idanuwanta da sukai fari fes hakama bakinta ya bushe sosai.
Cikeda mamaki da dan farin cikin ganin ta tashi ya qaraso yana cewa
