KALBIM BOOK 1 PAGE 8
8
*ZUZEAM VENTURES*
Best APHRODISIAC
08144015291
Aslm barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah
Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500
Garin bata gaban kishiya 500
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500
Za a bakisu akan 3800
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
️️️️️️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki
*************
Koda cikin Fatima ya isa haihuwa karfin da zatai naqudar arziki batada shi sbd yunwa da ciwo tareda cikin da duk ya janyeta ta koma kana ganin qashin bayanta ya fito dosai da duk qashin kirjinta kana ganinsu idanuwanta sunyi ciki sosai tayani muni dik ya gama sauya kamanninta sbd ciwon da yunwar da bayan Allah da yayita babu abincin da zai dawo da ita yanda take kila.
Abdul yana kokarin daya fi na shekarunsa sbd har local government yake zuwa nema da aiki harma da tallan rage wadda bayayi da yawa sbd baya iya dadewa waje yake komawa gida gurin ummansa dan komai shine yake mata sbd baba ila ya rabasu da Mama sakina wadda take cikin tsananin daci da ciwon rai na hakan amma Abdul dinne ya roketa akan kada ta rabu da baba ila sbd su shiyasa kawai take zaune a gidan amma aurensa gabaki daya ya fita daga zuciyarta ba sauran sonsa ko qwaya daya a ranta gashi daman Allah bai bata haihuwaba tayi neman haihuwar harta gaji ta barwa Allah.
A cikin wannan halin da suke ciki ne Allah ya kawowa Umman naquda cikin ciwo da ukubar rayuwa tareda yunwar data gama kame duk wani kayan cikinta da gangar jikinta ta haihu,
Haihuwar data taho musu da sabuwar kaddarar da babu yanda zasuyi bayan rungumar rayuwa a yanda taxo musu batareda taimkon kowa ko kulawan kowaba bayan ta mama sakina da suke samu jefi jefi Abdul ya reni kanwarsa da mahifiyarsa wadda ta koma masa tamkar UMMITA wadda take yar shekara biyu zuwa uku dan kuwa duk inda zashi dasu yake zuwa sbd fita sukeyi su tafi yawo dan haka duk inda zashi yanzu suna tare dan haka da yawa ake musu kallan almjirai ko yan yawon neman sadaka duk da yana iya kokarinsa akansu gurin ganin ya tsaftace su.
Yanzu sun dena zuwa irin guraren dake kaman kasuwa ko tasha gurin aikin nema ko sanaa sbd bayason ana kallan ummansa da ummitan dan haka Local government yake zuwa dasu har makarantarsa wadda yake gaf da kammalawa yanzu.
Har ciki a ke barinsa shiga dasu saiya kaisu bayan ajinsu yace su zauna karsu tashi saiya gama ya fito.
Haka zasu sauna suyita wasa a gurin harya gama batareda da damuwa da abinda dalibai ke fada akan mahaifiyarsa da rabin ransa dayake jinta kaman shine babanta sbd BAABAH take kiransa dan bata san kowa ba bayanshi da ummanta hakama shi take kallo ubanta tinda umman ta koma kaman ita tare suke wasa duk da umman ta dena magana.
Daga makaranta shagon dayake aiki yake wucewa dasu ya siya musu abinci suci ya ajesu guri daya suyita walwalansu harya gama se yamma su nufo gida sbd baya kaiwa dare sbd su duk da megidansa yana son ya ringa kwana shagon sbd yadda dashi da yayi da kuma kokarinsa tareda amanarsa amma sam baya iya hakan sbd kare mutuncin ummansa da Ummitansa dan haka duk abinda yake samu a aiki ko sanaa yamma nayi yake wutowa gida dasu su wanka suci dan abinda ya samu ya ringa koyawa ummita dan karatun yara har suyi bacci itada umman ya gyara musu gurin kwanciya ya kaisu su kwanta shima ya zauna gadinsu dan baccinsa rabi da rabi ne akansu sam bayada wata irin yadda da kowa gashi basada koda rabin gidan a zube dan haka baya wani bacci akansu.
Ranar wata alhamis ya samu wani aiki a wani sabon kamfani da zaa gina a local government na gyaran shinkafa me kudin dayafi tsaron shagon dan haka ya karba ya hada biyu yana yi sedai aikin gurin akwai hadari dan haka dole yake barin su ummita a gida amma saiya fada musu yafi so ashirin kada su fita koina.
Sunji maganarsa basa fita dik ya tafi harya dawo baya cikin nutsuwa amma yana tarar dasu a gida basa fita koina sedai gidan zai tarar anyi masa kaca kaca hakama sunyi wata irin dauda hakanan zai tsaftacesu ya gyara gidan ya basu abinci suci su koshi suyi sallah wadda tasa ce kawai ta arziki su kam ture ture sukeyi a gurin sallan tsakanin umman da ummita yana jinsu zai kyalesu a gama a hakan.
Akwai wata irin kauna da so me tsananin gaske tareda shaquwar datake basa tsoron da baisan na mene ba a tsakaninsa da Ummansa da Ummitansa haka suke sakasa wasa dasu dole wanda su kadai ne suke ganin dariyarsa da walwalwansa dan Allah ya sako masa wani irin kame kai tin yana yaronsa shiyasa ya taso hakan.
Tin yana fargaban barinsu a gida yaje ya dawo harya dan rage fargaban yana aikinsa cikin dan nutsuwa amma bawai hankalinsa baya gidan bane dan baya kara ko minti daya yana tashi aiki yake komawa gidan dan ya dena zuwa makaranta exam kawai yake jiran ranar yinta yazo ta gamawa tinda suka shiga ss3 ya dena zuwan waec kawai yake jiran yi.
A yau tinda ya kamo hanyar zuwa gida yakejin baida nutsuwa dan haka ya qara sauri yana jin kirjinsa na nauyi ya kuma saba da hakan a duk lokacinda bay taredasu jin yake zuciyarsa ta ringa shiga damuwa da nauyi kenan.
Yamma ne sosai dan haka bai biya gidan mama sakina ba dan bata sabulu da omon daya siyo harda ita ba dan haka ya wuce gida saiya dubosu saika ya fito dasu yaje ya kai mata batareda ya shiga gidan ba san anjima da baba ila yai masa iyaka da shigar masa gida sedai ya tsaya daga waje gefen gidan mama sakinar ta fito ko kawai ya aika mata ummita ta shiga takai ta fito shikuma yana waje yana jiranta su koma.
Yana doso gidan tin bai karasa ba ya hango Ummita tana fitowa daga hanyar bayan gidansu tana kuka hannuwanta da kafafunta qasa da jini.
Wani irin abu ne ya daki kirjinsa da tsakiyar kansa dan haka da sauri ya qaraso ya tarbeta tareda ajiye kayan hannunsa ya jawota gaba daya jikinta yana kallan hannuwanta muryansa dayake da wahalar ji shima dan baya wani magana sosai sbd baida abokin firar yace
