TABARMAR KASHI 2 Book 2 Complete Hausa Novel

TABARMAR KASHI 2 Book 2 Complete Hausa Novel

Da daren ranar dukka su biyun suna dakinsu,afifa waya take amsawa tsakaninta da anty farheen,duka maganarsu akan yadda shirye shirye zasu guda na ne,sayayyar kayan dakinsu zuwa gyaran jikinsu. Cikin satin takeso yaa muhyi ya samar musu da visa su ukun,china turkey ko Dubai,duk wadda tafi sauri da sauqi,su dora kayan ta sama yadda zayazo da wuri

“Amma ta sama anty akwai kudi fa”

“Karki damu,biyan buqata akeso,indai china ne ma babu matsala,akwai lucky cargo da kayan zasu iso cikin kwanaki galilan har nan kano(me bugatar hulda da amintaccen kamfanin saboda kawo kaya daga china zuwa Nigeria dukka states,sai ya tuntubeni ta wannan number don na hadashi da kamfanin kai tsaye 08187255862)”. Sati guda takeso suyi a can,satin da suka dawo kuma sai a fara gyaran jiki da sauran hidimomin da suka shafi amare.

[14/09, 7:42 pm] Mimah Yusuf: *HUGUMA*

* TABARMAR KASHI_*

Book 02 Page 09

Muryar maji dake dauke da wani allausan sauti me cike da nutsuwa ce ta mamayi kunnenta. Wata nutsuwa ta saukar mata wadda ta sanyata amsa sallamar cikin tsari.

“Ina fatan binty bakiyi fushi da ni ba,inataso na kirayeki amma ban samu damar hakan ba‚nadeeya kamar rowar rak’am(number) dinki takeyi” murmushi säahar ta saki me cike da kunya,ai ita ya dace ace ta nema maji din,don rashin kyautawa tunda tabar gidan bata sake nemanta ba

“‘Masa’al khair” säahar ta gaidata

“Masa’an nur ibnaty kina lafiya ko?,ya iyayi ki?”

“Bikhair walhamdulillah”

“Ma sha Allah, ya kuma shire shiryen aure? muna hanya cikin satin nan in sha
Allah” nauyinta ta sake ji ya kamata,saita kasa magana

“Ina fatan za’a yi haquri da halin moha,ya taso me wani irin zafi da rashin son raininaso qwarai na saisaita wannan dabi ar tasa,saidai ban rayu dashi ba,ya sake zuwa kuma bayan ya girma Allah ya jarabceshi da wata irin jarabawa data sanya dabi’unsa suka sake zafafa,ina rogon alfarma ayi haquri da shi,a kuma yi qogari a saita min shi, kyawawan dabi’u da na san dasu na haifeshi su dawo gangar jikinsa suyi tsiro, zuciyarsa ta zama irin ta kowa”

“In sha Allah” kawai ta fada,don batasan fadin kowacce kalma da zata nuna ta dauki alaqawarin,saidai daga qasan zuciyarta tana mamaki,dama shi din bai rayu da maji ba”?

“Inason diyata tafi kowacce amarya kyau a duniya,don wannan shine karon farko da za’a aurar da moha a gaban idanuna,akwai me gyaran amare da zata iso nan da jibi daga nan gasar tare da ‘yar uwata,ina fatan diyata zata bada hadin kai?” Sosai abun ya yiwa sãahar girma,suma da gaske suka dauki bikin?,sun dauka auren gaske ne kenan?,ba yadda ta iya ta amsa a sanyaye da

“To,mafi mishkila,jazakillah bi khair”

“Nice da godiya da shigowa rayuwarmu da kika yarda zakiyi” maji ta amsa mata cikin qauna da kulawa,har cikin jininta takejin qauna da soyayyar sãaharita din ma’abociyar sallar dare ce,a duk sanda ta roqawa rayuwar toufeeq da nadeeya abokan rayuwa na gari sai taii sãahar ta sake kwantawa qwarai a ranta,tana ta qoqarin ganin yadda zata qulia al amarin tana daga can,sai gashi cikin hikimar
Allah komai yazo cikin sauki darajar istikhara din data dinga yi tana neman zabin Allah.

Ganin kamar saahar din tana kunyarta ya sanya tayi mata sallama,tare da gaya mata tayi serving number dinta a wayarta,koda tana da bugatar wani abu kada taji komai,kai tsaye ta kirata.

Gudun mantuwa da girman majin ya sanya tana ajjiye wayar afifa ta dauki wayar tata ta fara duba tarin miscall din data samu,wasu na cousins dinta ne wasu na yayunta,wasu numbers dinma batasan nasu waye ba.

Tana tsaka da saving kira ya shigo wayar tata,kamar ba zata daga ba,saboda batasan number din ba sai kuma ta dauka din ta kara a kunnenta. Baquwar murya ce a kunnenta,ta amsa sallamar da akayi mata

“Sunana elyas,ina daya daga cikin ma’aikatan
MT JARMA,na kira ne bisa umarninsa,yace na shaida miki,idan akwai wasu kudade da kike bugata na hidindimu ki fada sai a tura miki” wani irin baci ranta yayi qwarai ta mige ta zauna sosai,ma’aikacinsa ne,tasan kuma irin respect din dake tsakaninsu dashi, uwa uba ma shi din dan aike ne gaba daya bashi da laifi sai ta rasa abinda zatace masa,ta lumshe ido takaici yana cin zuciyarta

“Hello madam,kina jina?”

“Ina jinka,elyas ko?” Kai ya gyada

“Yes madam”

“Bari na baka shawara,koda gaba kada ka sake yarda ka shiga irin wadannan abubuwan,saboda bai dace ba,kudi kuma kace masa har yanzun dai bashi da kudin da zai bawa sãahar….” Cikin kunnuwansa ta
qarasa fadin kalaman,yadda yaga elyas yayi shuru yana qifta idanu yasan akwai matsala,ya fahimci tana da tsiwa da rashin barin kota kwana,zata iya fadin wata maganar ma da zata iya zubda masa girmansa a idanun yaransa.

“Da wa kike?” Sautin murvarsa dake da wani irin zurfi da haiba suka sauka mata a kunne a lokacin da bata zata ba,dalilin da yasa batace komai ba kenan har ya sake maimaita tambayarsa. Cikin dakiyarta tare da son fanshe bacin ran da afifa da sauran family ke gasa mata saboda yadda suketa shirin biki tace

“Ni ba wulagantacciya bace, kuma bana neman komai a gurin kowa,ka rige arziqinka na rige mutuncina” wani irin zafi maganarta tayi mata,yaji babu dadi sosai a ransa,saidai takaicinsa ragagge ne tunda umarnin maji ya cika

“Hey!,watch your words.…karki dauka
kiranki yana da alaqa da damuwa da akayi dake..
bazanvi tolerating nonsense ba,don bazan biva sadakinki sannan na dauki wadan nan tsiwar da rashin kunyar ba” daga haka ya kashe wayar yana furzar da iska me zafi daga bakinsa. Lallai idan batayi wasa ba sai ya mata horo me tsanani, ya cire duk wannan jin isar tata da rashin kunya,abinda takeyi masa kaf tarihin rayuwarsa ba wanda ya taba gwada masa irin hakan sai ita. Wani mugun tsaki yaja ya jefar da wayar,maji ce sila,inda ta fahimci maganarsa tun farko da bata sanya yasa ay! kiranta ba. Ya miqe tsaye yana boye hannunsa a aljihun trouser dinsa,yana jin zuciyarsa na sake zafafa,dai dai lokacin da sajjad ya shigo dauke da wasu manya manyan kwalaye shi da jibril. Har suka gama ajjiye kwalayen jibril ya juya ya fita baice musu ta tafas ba. Zama sajjad din yayi ya fara bude kwalayen,wasu irin shegu suit ne da yadiddikan vicuna,qiviut fabric guanaco da baby cashmere wadanda duka aka viwa wani lafiyayyen kwantaccen dinki. Kallo daya zaka yiwa kwalayen zuwa sutturun ciki kasan maqudan kudade kamfanin da yayi kwangilar aikin ya lasa daga hannunsu

“Here’s our wedding attire,ya ka gansu?” KO duban inda yake toufeeq baiyi ba,don dama yana cike da sajjad din. Tafiya yayi ta sati daya,amma kafin ya dawo sajjad din ya sanya an canza komai na sassansa,an canza tsarin komai ma,ya zuba masa dukka wasu kaya da suke favorite dinsa a design da kuma color,sannan ya fidda sashen da aka zuba jeren säahar din. Yayi masifa kamar zai ari baki har sai da girjinsa ya dinga zafi kasancewar bame doguwar magana ba,yana ganin kaf girman gidan da sassan da yake dasu amma ya rasa inda zaiyi mata matsugunni sai cikin sashensa? haka ya haqura ya gaji,don sajjad ya gaya masa yayi din waye zai aureta da za’a ajjiyeta a wani muhalli na daban,sanann muddin yaci gaba to zai sanarwa da Dr girema auren meye zaiyi,da kuma abubuwan da yaketa yi din,wanda sam basu dace ba,don meye bazai sassauta zafin kansa ba?. Haka ya gama qure sajjad da zazzafan kallon nan nasa ya debe fararen idanunsa yabar masa wajen,yasan indai yaci gaba da tsayawa sajjad bazai gaji da gasa masa magana a fakaice ba,shi kuma bazai iya doguwar magana ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected