TABARMAR KASHI 2 Book 2 Complete Hausa Novel
Yanzun ma key din motarsa ya dauka
ya fice daga gidan shi daya,ransa a bace,shi dinma bai duka duka wannan hidimar zaa yita yiba me hana mutun sakewa,hatta da fadeela yanzun ganinta sai lokaci lokaci,duk sun yamutsa gidan da shirye shiryensu,yau basu nan gobe basu can,cire wancan canza wannan siyo wannan ajjiye wancan,duk Dr girema ya daure musu qarqashin ko nawa sukeso zai dauka ya basu. Ko su jibril da sukayi yunqurin biyoshi hanasu yayi,bai tsaya ko ina ba sai bristol palace,ya kama royal suit da ya saba ya wuce ciki bayan ya kashe dukka wayoyinsa yana fatan samun relief ya kuma daidaita kansa,shi kansa yasan yanata misbehaving ne,yana kuma batawa sajjad wanda dama shi kadai yake iyawa dashi,yasan abinda ya faru dashi a baya yake hunting mind dinsa,yanaso yayi cooling temper dinsa kafin ya dawo cikin gidan.
*******Kayanta taketa hadawa guri
daya,amma fiye da rabin hankalinta ya dilmiya a zuzzurfan tunani. Idan lissafinta yayi dai dai,ranar da zata isa Nigeria ya kama saura kwana biyu rak a fara bikin,kamar yadda kwanan wata ya nuna mata jikin dallelen invitation din me rubutun ruwan gold a jiki, wanda har yanzu hasken katin da tsarinsa basu bacewa idanunta ba,don sam baiyi kama da katin biki ba. Jagwab ta koma ta zauna saman kujera,ba qwarin zuciya ba har gwarin gangar jikinta tana nema ta rasa, komai gani takeyi yana fara zuwar mata a cakude,ko a mafarki bata taba tunanin akwai wani abu da zaizo ya rusa tsarinta ba dai dai da qiftawar idanu, bata taba kawowa wata mace zata shiga rayuwar toufeeq ba baya ga hassenarta wadda aka fi sani da MEENAL YA’AQOUB AJI,saugin abun har yanxu ta tabbatar meenal din bata san da zancan ba,don ko jiya sunyi waya kuma lafiya lau suka gama sukayi sallama.
Sautin qarar wayarta ya tabbatar
mata da shigowar kira wayarta,ko da ta duba taga sunan baby na kamar yadda tayi saving number meenal haseena sai da gabanta ya fadi,ta zauna sosai tana daga wayar da hanzari,don jikinta ya bata ta faru ta qare.
Yadda ta zata din kuwa haka ne,kukan meenal haseena kawai ya tabbatar mata da zarginta,cikin hargagi da daga murya da muryarta da tayi sirantaka da yawa har take bada wani irin amo da ba kowa yakewa dadi ba
“Momy? kina ina akaci amanata?, kina raye kuwa momy?”
“Ina raye baby meenal,ki kwantar da hankalinki,ba wani abu bane babba”
“Ta yaya zakice ba babban abu bane,bayan next week zaiyi aure? zai auri wata bani ba,bayan kinyimin algawarin bazai sake auren kowacce diva mace ba bayan ni?,yanzu duk zaman da nayi shekara da shekaru ina jiransa ya tashi a banza?,duk wani buri na da naci a kansa ya zama mafarki?”
“Haseena!”
“Momy!!! ba abinda zakicemin,na dauka ina da uwar dana wuce nayi kuka na zubda hawaye na? ta isa ta sharemin kowanne kuka nawa ashe kuskure nayi!”
“Meenal ki saurareni mana,kin manta wacece fauziyya?,kin manta waye toufeeq a wajena?,ubansa ma ya yake a gurina barshi?” Maganar ce ta sanya meenal din yin shuru,saidai har yanxu bata fasa kukan da takeyi ba
“Wallahi momy idan har ban auri yaa toufeeq ba mutuwa zanyi”
“Indai kinga baki aureshin ba saidai idan bana raye,ke ko bana raye saikin aureshi,shine mijinki” hajiya qarama ta maimaita da confidence,tana ajjiye wannan alwashin har tsakiyar zuciyarta
“Wani ma yayi rawa bare dan makadi?,bani da qwai a duniyar nan fa sai ke,ke kadai na mallaka kuma duk duniya babu wanda nakeso kwatankwacin yadda nake sonki,idan ban sama miki farinciki da jin dadin rayuwa madawwami ba me nayi kenan?,koda tsiya koda arzigi saikin mallaki muradin ranki,ki rubuta wannan ki ajjiye,alqawari ne dauka”
“Ki tabbatar kin cikashi momy,saboda komai zai iya faruwa,inason na auri yaa toufeeq a watannin da muka riga muka tsara tun farko,bazan iya jurewa rashinsa na tsahon wani lokaci ba,bazan iya jurewa ganinsa da wata mace ba bayan ni”
“Ki kwantar da hankalinki ki kammala exams dinki,sati biyu fa kacal ya rage,a satin bikin ma zan miki booking ticket,ko Dr jarma banason ya sani,saidai kawai suga isowarki”
“Thank you momy”
“Naji,amma haka zamu rabu kina wannan kukan don kawai ki hanani sukuni?”
“Na daina”
“Kin tabbatar?”
“Kinsan idan na fadi abu bana canzawa ai”
“‘Yayi kyau,ki huta da kyau” . Wani qaimi taji yana shigarta tare da karsashin son ganin ta gudanar da komai,don haka ta sake migewa tana qarasa hada kayanta,tare da duba jirgin garfe nawa zata bi.
********Tun daga saukarta farkon layin zuwa shigowarta cikin gidan hankalinta ya soma tashi,ta sake tabbatarwa eh lallai aure MT JARMA zaiyi,irin auren kuma dake nuna cikin wadata da tarin arzigi za’a yishi,ba irin aurensa na baya ba. Abinda ta lura dashi cikin nutsuwa da zurfafa dubanta akan kowa,kamar kowa fuskarsa dauke take da annuri da farincikin auren,komai na gidan an canzashi an sake masa fasali da tsari, hatta da uniform na ma’aikatan gidan kuwa. A ranar kasa zaune tayi ta kuma kasa tsaye,hatta da fadeela da nadeeya bata samu ganinsu ba a ranar,don ba’a basu zama ba,yaa moha zai dawo musu da masoyiyarsu,a wannan karon da a sunan nanny ba,a sunan MATARSA ta sunnah.
Tanason ta fita don fara aiwatar da wasu abubuwa,amma baqin da aka fara yi a gidan da abokan kasuwancinta da suketa zuwa ganin kaya sun hanata motsawa,komai kawai yinsa takeyi ba cikin nutsuwarta ba,tana da bugatar zuwa ta sabunta tsonon aikinta,don dama an jima ana gargadinta akan hakan, bata fuskanci da gaske bane sai da taga kwabarta tana shirin yin ruwa. Komai a quntace take yinsa cikin yage da tsabar duniyanci wajen iya boye damuwa da tashin hankali ta kuma bi sahun ‘yan murna da Allah ya sanya alkhairi.
*_KALLON KALLO *
[14/09, 7:42 pm] Mimah Yusuf: *HUGUMA*
* _TABARMAR KASHI*
Book 02 Page 10
*_KALLON KALLO_*
Hantsi ne wanda yazo mata a birkice,irin birkicewar da bata taba hasasota ba. Tun safiyar data tashi take jinta sukuku,amma ta danganta hakan da fitar da taketa son yi jama’a na tsaidata,saidai ta yanke a ranta gobe komai matsi taje din,don da zafi zafi ake dukan qarfe. A safiyar a daki tasa aka ajjiye mata breakfast dinta ta tsakura ta ajjiye,saboda kullum damuwa ce ke narkewa a zuciyarta,yadda taga dan uwanta Mahmud jarma ya dauki lamarin auren nan sai yake sake sakata cikin tashin hankali. Kamata yayi ace dukka wadan nan shire shiryen da zumudin akan auren toufeeq ne da meenal
‘yaruwarsa,ba wai akan wata nanny ba. Da wannan baqinciki ta kwana ta tashi,da gyar ta samu wajen sha daya da rabi ta shiga wanka,ta fito ta shirya kamar kullum cikin shigar alfahari da fariya na wani dandaqegen lace,ta cika jikinta da turare,ta fito don ganin meye kuma yake gudana cikin gidan gaba daya,wanda kusan wannan din al’adarta ce,komai na gidan idanunta suna kai tana biye dashi saidai idan bata qasar tayi tafiya.
Tana takawa ne cikin jin izza tare da yadda take samun komai yadda takeso,idan ka cire yadda al’amuran a yanzu suketa son yi mata gardama,wanda ta tabbatar sako sako da dauke mata hankali da neman kudi sukayi shine musabbabiyyar faruwar hakan.
Zuciyarta a cike fal da qunar yadda gidan yake kasancewa kullum cikin hada hada da kai kawo jama’a,duka a shirin fara gudanar da bikin da batasan da meye yafi saura ba?,tana tsoron ma a qare dukka shagalin akan wannan auren data sanyawa suna MATACCE,azo bikin shalelenta abubuwa sugi armashi saboda komai an gudanar dashi a wannan.