TABARMAR KASHI 2 Book 2 Complete Hausa Novel
“Ba zata taba dawowa ba,ta tafi kenan,so ku koya mata haquri,tunda tun farko dama ba da ita ta saba rayuwa ba,dole zata ci gaba da rayuwa ko bayan babu ita” tunda baaba ramatu taji ya fadi hakan ta tabbatarwa kanta saahar ta tafi kenan. Kaifi daya ne shi,wanda tsanani baya sakashi sauya zancansa ko
dawowa da baya. Migewa tayi sali alin ta fice a gurin,cikin ranta tana jin matugar kewa da takaicin subuce musu da yarinya kamar sãahar tayi,ta tabbatar ba za’a maida kamarta
ba.
Sai yamma sosai sajjad suka dawo da fadeela,ko bayan sun dawo din bata ma shigo sashen toufeeq din ba. Tana lafe jikin nadeeya,wanda kafin kace meye wannan wani mugun zazzabi yayi ram da yarinyarnar wani irin rawan sanyi takeyi. Sosao hankalin nadeeya ya tashi,ta dauki waya ta sanarwa toufeeq. Daga masallaci ya dawo, kwanakin tunda suka fara wannan rigimar saboda tafiyar sãahar din shima baya fita ko ina,a gida yake wuni,duk wani aiki ta system dinsa yake gudanarwa.
Hankalinsa yafi na kowa tashi,saidai zuciyar ‘yan maza wadda bata bari aga rauni a tattare da ita. Mota ya kaita,ya sanya baaba ramatu ta shirya tazo su kaita asibiti.
Nadeeya na zaune tana sharar qwalla har suka fice,zuciyarta a mugun karye,ta tabbatar wannan zazzabin na fadeela yana da nasaba da yadda tayi mugun sanya sãahar a ranta,da qulafucinta da takeyi. Gaza jurewa tayi ta mige ta isa daki,ta cire wayarta dake saman dressing table ta budeta,ta zauna bakin gado tana lalubar number sãahar.
Dai dai lokacin da suke zaune a falo ita da afifa suna hada fruit salad din abincin dare,cikin kwanakin gaba daya itama ta sake zama so silent,babu wani karsashi ko kadan a tattare da ita. Duk da yadda fadeela ke tsaye a ranta,amma taqi bawa zuciyarta damar da zata karaya. Har a ranta tana jin hukuncin data yanke shine dai dai,babu gudu babu ja da baya,ta yadda sabo turken wawa ne,amma idan tayi haquri wataran zuciyarta zata rusuna,taji tamkar ma bata taba rayuwa da fadeelan dama duk wani ahalin gidan ba. Gefe guda kuma dukka kunnuwanta na kan motsi da kai kawon gidan,duk da ta tattara lamarinta ta miqashi ga Allah,saboda ta tabbatar tunda har ta bawa Dr girema wuga da nama akan lamarin mahmud,to tasan fa babu fashi aure ne zai zama tabbatacce a tsakaninsu. Abu mafi razani dake jijiga zuciyarta,kaddarar auren adam me daci ce da hallaka dukkan buri da gusar da fata ko sha’awar ci gaba da rayuwa ta aure dama ta duniya gaba daya..
…ita kuma qaddarar auren mahmud fa? yaya zata zo mata?. Tambayar kenan dake barazanar fasa mata zuciya a duk sanda tazo kanta. Ta sani cewa saidai suyi zaman haquri ita da mahmud kawai,amma babu ta yadda za’ayi ya samu yadda yakeso daga gurinta,ta gaya masa wannan ta sake nanata masa,ya shaida masa yes……a shirye yake yayi haquri da ita ya kuna zauna da ita koma a yaya ne.
Wani sashe a zuciyarta kowacce rana nana ya mata cewa JINSIN MAOARYATA
NE,JINSIN MAHA’NTA NE,duk abinda suka gaya maka bashi kake tararwa ba bayan aure,yaudara da cin amana da karya alqawari sun lullube zukata da harsunansu, bata tunanin akwai wata kalma ta soyayya da jan hankali, nuna zallar kulawa da rayuwa yare har bayan mutuwa wadda adam bai furta mata ba,amma yaya sakamakon hakan ya kasance?. To auren me zatayi? ‚AUREN BIYAYYA kenan ko me? tunda dai ita din batakai lokacin da za’a ce tayi auren kai buta da ruwan wanka bandaki ba.
Tsakiyar wanann tunanin wayarta tayi burari,ta waiwaya a nutse tana duban me kiran,zuciyarta na gaya mata mahmud ne, wanda zuwa yanzu ta fara tsanarsa tare da tsanar komai daya shafeshi, yana yaiwata kiranta da sunan caring,caring din da ita kuma bata sonshi, don duk abinda yayi sai taga kamar yana bin footprint na adam ne.
Mamaki yadan kamata gain sunan nadeeya.
Bawai bata kiranta ba,a’ah,tun daga randa ta baro gidan,har tayi kwanaki bakwai babu ranar da bzata fito ta fadi bata kirata ba tana roqonta akan ya dawo. Randa tayi alqawarin ba zata sake kiranta ba tayi fushi ne saboda ta tabbatar mata ba zata dawo ba,suyi haquri ta kula da fadeela,tun daga ranar bata sake kiranta din ba,saidai kullum zata bar mata good morning massage through watsapp dinta.
Wugar hannunta ta ajjiye ta miga hannu ta dauki wayar,ta daga kiran ta karashi a kunnenta. Gabanta yayi mummunar faduwa jin sautin kukan nadeeya,tayi saurin kama sunan
Allah sannan ta samu qwari gwiwar tambaya
“Sister nadeeya,me ya faru?”
“Fadeela ce.
” Sai kuma maganar tata ta
tsaya,abinda ya haddasawa sãahar wani irin muguwar faduwar gaba,ta sake kiran sunayen
Allah
“Karki cemin wani mummunan abu ya faru da ita”
[11/09, 3:42 pm] Mimah Yusuf: *HUGUMA*
* TABARMAR KASHI_*6
Book 02 Page 02
“Ke da mahaifinta dama ba burinku kenan ba? vanzu haka tana asibiti, kuma ko meye ya faru da ita kune ke da alhakin hakan” daga haka ta katse wayar,tabar sãahar da waya a hannu.
“Gaskiya ta fada,meye laifin yarinya da zaku shiga rayuwarta ku gigita mata ita?,rana daya saboda baki shiri da mahaifinta ya birkitaki ke kuma ki tattaro ki bar yarinya kwatsam?”
“Bai isa ya birkitani ba,baida wannan qarfin ikon,abinda na sani kawai bazan taba iya rayuwa dashi a muhalli daya ba muna shagar iska daya”
“‘I dan kukayi kisan kai ai ku kuka sani” afifa ta fada cikin jin haushi tana migewa a wajen.
Maganar Allah itama zuwa yanzun haushinsu takeji,kamar masu ganin hanjin juna? babu dama su hadi guri guda sai kowa ya hau tashi kamar kububuwa?.
Tun daga lokacin da nadeeya ta kirata har zuwa wayewar gari ta gaza moruwa gaba daya, lokaci lokaci sai ta samu kanta da duba wayarta,tanason kiran nadeeyan amma kuma batason tayi abinda zai sanya zuciyarta karyewa. Ko a daren jiya baccinta rabi da rabi ne,iya baccin data samu yi din cike yake da mafarkan fadeela na koke koke,abinda ya hadu kenan yayi mata rubdugu ya kassara duk wani walwala da karsashinta. Don ko da safe kwance tayi a daki,ta kasa fita ko ina. Ba abinda takeson gani a wannan lokacin irin fuskar fadeela,ta rungume yarinyar a jikinta kamar yadda suka saba,to amma kuma ta yaya?,batason cin fuska da cin zarafi don haka ya zama dole komai wuya komai daci ta nisanci dukan abinda yake da jibi da MT JARMA.
Zuwa la’asar juriyarta da dukka
haqurinta ya qare,wunin daki tayi ita kadai afifa yau tana asibiti gaba daya,ta kalli agogo,biyar saura,lokaci irin wannan lokaci ne nayin karatunsu ita da fadeela,ko ya halin karatunta ya shiga ciki?,duk yadda taso ta jure sai da qwalla ta cika idanunta,saboda ta tuna algawarin da tayi mata na har ta gama exam tare zasuyi karatun,to saura guda biyu ta kammala ta baro gidan,batasan waye ya tallafeta sukayi karatun biyun da sukayi saura ba. Batasan ya akayi ba sai kawai ta samu kanta da laluben number nadeeya cikin jerin calls dinta na yau,ta danna number tayi dialing.
Hannunsa zube a aljihun silky trouser dinsa daya dace da short sleeve shirt din dake jikinsa,yana takawa a nutse tamkar saboda shi daya akayi hanyar da zata sadaka da dakunan AMENITY na asibitin. Manyan dakuna dake dauke da dukkan wasu kayan buqata tamkar kana gidanka. Ko baka sanshi ba kalli fuskarsa kasan wani kwantaccen fushi ne zalla a samanta,saidai tarin nutsuwar da yake da ita data cakude da miskilancinsa ya sanya ba lallai ka lura da hakan ba kai tsaye.
Babu abinda ke amsa kuwwa a kunnensa sai bayanan Dr anwar,wanda yake jaddada masa dole ya kiyaye yasan meye asalin abinda ya sanya fadeela a wanann mummunar damuwar,dole ne yayi qoqarin sama mata abinda zai sanya hankalinta kwanciya ya dawo da ita walwalarta,ko don lalurar da take da ita, wadda ta ragu sosai fiye da baya. Shi kansa dr anwar mantawa yakeyi wani lokaci da lalurar tata,saboda komawa baya da takeyi tana raguwa da kadan da kadan a yan watannin da sãahar din ta kasance da ita. Idan yayi zuzzurfan tunani hakan yana nufin babu makawa sai ta dawo cikin rayuwarsu?,kenan tayi galaba dukka shirinta yayi tasiri kenan?,sai ya furzar da iska me zafi daga bakinsa,ransa yana gonewa,yana jin wani irin zafin yarinyar a ransa. Daga ranar da ya shata layi tsakaninsa da kowacce diya mace,babu macen data sake shigowa rayuwarsa tayi masa wannan karan tsayen sai ita. Dai dai sanda ya isa gofar dakin,ya sanya hannu ya murda handle din ya bude,saidai kafin yakai ga shiga yaji sautin siririyar muryar fadeela da ko yaushe bata rabuwa da kuka tana kiran sunan