TABARMAR KASHI 2 Book 2 Complete Hausa Novel

TABARMAR KASHI 2 Book 2 Complete Hausa Novel

“‘Waye ya baki izinin shafa wannan abun?” Kusan daukewa numfashinta vayi, saboda a saman fuskarta yayi maganar muryarsa can gasa kamar me shirin rad’a mata, hucin furucin bakinsa dake cakude da mint scent ya daki fuskarta. Bata gama kokawa da wanna ba ta tsinci lausasan lebunansa masu dan tudu a saman nata siraran labban, ta gama fahimtar abinda yake shirin yi mata, saita tattara dukka qarfinta ta sanya hannunta saman girjinsa ta turashi baya tana gocewa gefe cikin bacin rai.

Idanunsa da wani abu ya sirka a cikinsu ya daga yana dubanta

“Duka wannan baya cikin sharudanmu,koma meye zanyi ko zan sakawa fuskata ba damuwarka bane, na kula kawai da fadeela,i will do my very best, that’s all” ta fada muryarta tana rawa. Kafin yace komai yaji qofar na bada alama na shigowar wani,don haka ya juya da dan hanzari kai tsaye ya wuce cikin office dinsa.

Saima ce rungume da files, gaba daya fuskarta zuwa zuciyarta babu wani sukuni ko annuri, ido suka hada da säahar, sai säahar din ta dauke kai tana gyara rufin lafayarta sannan ta durfafi office din itama kai tsaye,cikin ranta tana jin kamar ta zura da gudu tabar office din, a karo na biyu ta sake dawowa aiki da wannan mutumin da bashi da kirki ko kada,ko yaya zata kasance musu?.

A nutse ta buda ta shiga da murtukakkiyar fuskarta,har hanzu office din yana nan kamar yadda ta sanshi,saima sake qawatashi da akayi da gyare gyare.
Guri ta samu ta tsaya tana harde hannuwanta a girji, bugun zuciyarta har yanzu bai daidaita ba. Bashi a office din,amma taji qarar ruwa daga toilet, sai ta zabi taci gaba da tsaiwa kawai.

A galla mintuna kusan goma sha biyar ya shafe kafin ya fito,kallo daya ta masa ta dauke kanta, gaba daya fuskarsa ta sauya,ya koma real MT JARMA dinsa data sani,kamar ba shine yanzu yanzu yaso matseta yayi mata mugunta ba,ya jade fuskarnan da kyau,abinda ya sake qara masa kwarjini kenan

“Have a seat” ya fada yana jan tashi kujerar baya tare da shirin zama a kai,har yanzu bai kalleta ba.

Batason suia magana da vawa,don haka ta garaso ta zauna din, ya buda wani file dake gabansa ya ciro wata takarda ya ajiye saman file din

“As my new P.A,aikinki zai zama a qarqashina ne, zai kuma zamana kan umarnina,na baki access da duk wani kira mo email da ya shafi office dina, sauran abinda zakiyimin idan ta kama zan sanar miki, koda ya fita daga tsarin aikin PA”

•_HAJIYA QARAMA_*

Ita da masu aikinta biyu suka isa makarantar, kai tsaye har zuwa office din shugabar makarantar.

“Abincin jikata ne FADEELA Muhammad jarma” dubanta headmistress din tayi

“Cute angel,ko ba ita ba?” Ta fadeta da sunan da yawanci ake kiranta dashi a makarantar. Murmushi hajiya garama ta saki tana gyada kai “Eh ita fa”

“‘Amma dazu mamarta ta kawota da kanta,kuma da abincinta tazo kamar yadda aka saba” kai hajiya qarama ta jinjina,tana jin dacin kiran sãahar da sunan mahaifiyar fadeela

“Ba itace mamarta ba,matar ubanta ce,nanny dinta kuma ada” ta qasan glass matar ta dubeta

“Eh amma ita muka sani a yanzu,don ko last week da za’a shiga sabon session itace tazo tayi updating data na fadeela,da sunanta muka cike komai,so ko yanzun ba zamu iya karbar abinci daga hannunki mu bata ba,sannan koda daukarta ma a yanzu ita ke da alhakin hakan,idan fana da uzuri kuma zata kiramu da kanta ta bamu shaida akan wanda ta turo din”.

“Turqashi!” Ta furta tana dukan hannun kujerar da take zaune a kai ba tare da tasan ta aikata hakan ba

“Madam kinsan da waye kike magana kuwa? hajiya fauziyya ce ni fa qanwa ga Dr mahmud JARMA, uwa ga MT JARMA, sannan kaka ga fadeela,kinaso ki gayamin matsayin matar uba ya wuce na kaka?” Ita kanta matar mamaki sai daya darsa mata a rai, saboda bataga meye abun tashin hankali ko bacin rai ga gin karbar abinci ba,amma duk da haka ta basar ta girgiza kai

“Ko kadan kuma wannan ai family issue ne ma hajiya,abinda na sani dai kawai, duk wanda aka sanyashi cikin data na dalibi shine zaici gaba da juyawa da kulawa da komai nashi,dama kusan ita fadeelan ce kadai bata da wannan record da muke dauka a duk shekara,so wannan karon kuma ta samu,haqginmu ne mu kula da lafivar dalibi da tsaronsa, ki koma da abincin hajiya idan kuka sasanta a gida sai kuzo asan sunan wanda za’a cike dashi, ko kiyi kiranta muji hakan daga bakinta”.
Tsantsar bacin ran da take ciki ya hanata sake cewa komai sai kawai ta miqe tana fita dava office din, adama na biye da ita da lunch bag din. Sai data kusa minti ashirin a tsaye jikin motar tana juya abun a ranta, ita yarinyar zata dinga shigewa rayuwa haka? lallai zata nuna mata kurenta,amma kafin sannan bari taje ga mataki na gaba.

“Gida zamu koma hajiya?” Driver dinta ya tambayeta,saita girgiza kai

“Gidan yaaya zaka kaini”

•_DR MAHMUD JARMA RESIDENT_

Yana duge gaban garamar luggage dinsa, daya daga cikinsu wadda duk sanda tafiya ta kamashi yake amfani da ita. Yana tsaka da zugewa hajiya mansura ta shigo dakin dauke sa tray data shiryo masa kayan abinci a ciki.

Idanunta a kansa har ta garaso ta ajiye,ta koma gefan gado ta zauna

“Kwanaki uku kenan inatason yin magana da kai, amma sai nake ga kamar baka da lokacin kanka a ‘yan kwanakin nan” ba tare da ya dago ya dubeta ba va iiniina kansa

“‘Inata shire shiryen yin tafiya ne kuma a galla tafiyar zata dan iya daukana lokaci wala’alla me dan dama kafin na dawo,duk da bana fatan hakan” ya bata amsa yana tsaida luggage din bayan ya gama rufeta. Sosai take kallonsa,cikin kwanakin gaba daya kamar ma cikin nutsuwarsa yake ba,to amma ita abinda yake gabanta a yanzu yafi tasa a damuwar a gunta

“Labiba gaba daya na kasa gane kanta,yini take ta kwana tana kuka,ta daina fita ko ina,ta daina walwala ta daina magana da kowa”

“Duka akan me?” Yayi mata tambayar yana zama saman stool. Mamaki yadan kama hajiya mansura yadda yayi kamar baisan komai a kai ba, duk da haka ta hadiye cikin lanqwasa murya da karyar da kai

“Akan yayanta toufeeq mana, tunda yayi auren nan ita kuma ta koma haka” idanunta yake kalla kai tsaye,yama rasa abinda zaya fada, baisan me yasa daga mansura har fauziyya kowacce idanunta ya rufe akan batun hada auren toufeeq da ‘yarsa ba,duka duka ma yaushe yaron yayi auren da har za’a tsaya rakito masa wani auren?,shi yasan abinda su basu sani ba yadda haseena take zabin fauziyya,labiba take zabin mansura, haka säahar take
ZABINSA, ya riga taoufeeq nema masa auren sãahar ba tare da shi kansa ya sani ba. Bayan ya samu dukkan labarin aurenta da adam daga bakin muhyiddeen,ya tabbatar ya kuma yi imanin SÄAHAR itace macen da tafi dacewa da toufeeq,itace kuma madadin AMEESHA data sanyawa rayuwarsa dafin da yasa yake kallon mata amatsayin ABU GUDA. SAAHAR itace tayi masa kamanceceniya da SHIFA, dabi’unsu suna gogayya da juna,yafi kowa sanin wacece shifa da halaccinta a garesa,wannan ya sanya ya yiwa toufeeq sha awar mallakarta.
[21/09, 9:16 am] Mimah Yusuf: “HUGUMA*

_TABARMAR KASHI*

Book 02Page 25

“Yanzu ba zaka sanya baki ba ko don a samu hankalin yarinyar nan ya dawo jikinta?” Agogon hannunsa da ya manta bai cire ba ya soma zarewa

“Bana shiga lamarin da ban isa na hadashi ba, daga ke har fauziyya na gaya muku, toufeeq yana da ido so ba sai an tursasashi ba,ko ni bani da ikon bashi umarnin ya auri wance,idan ya gani yanaso bazan hanashi ba” maganar tasa ta tabata sosai, kuma dama fauziyya tana can tana nata yaqin kenan? ya tabbata ta shirya cin amanarta da gaske,iska ta furzar a bakinta tana gangance idanu

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected