TABARMAR KASHI 2 Book 2 Complete Hausa Novel
Sajjad ne gefansa kuma toufeeq, nadeeya na biye dasu. Sanye yake cikin wasu lafiyayyun suit da aka saqa da asalin zare me daraja na vicuna giviut fabric.
Kalar suit din data dace da kwantacciyar fatarsa da hutu da kulawa suka ratsata. Idanunta ta sauke kan fuskarsa,abinda ta hanga wani irin shimfidadden bacin rai tare da cushewar fuska,ainihin kamanninsa na cikakken miskili kuma fusataccen MT JARMA take gani muraran, hakanan cikin sassarfa yake takowa fiye da sajjad da nadeeya. Kamar ya sani ko yaji a jikinsa tana kallonsa. Nasa idanun va zube a kanta sanda idanunsu suka sarqe cikin na juna sai taji gafafunta sun fara rawa, bugun zuciyarta ya garu ainun, mararta ta daure tamau yana sake kusantota tana jin kamar ana juyata daga hagu zuwa dama, daga gaba zuwa baya. Sai ta fara gani dishi dishi lokacin da mararta tayi wani mugun murdawa dai dai lokacin kuma da likitan ke magana da harshen jamusanci
“Wo sind Fadeelas Verwandte? Folgen Sie mir ins Büro, es gibt etwas sehr Wichtiges, das ich Ihnen sagen mochte (ina ‘yan uwan fadeela?,akwai bayani me matuqar muhimmanci da zanyi muku”. Idanunta ta dauke daga kansa tana mayarwa kan likitan dake nufar office dinsa da sauri sauri. Ganinta yana sake zama dishi dishi toufeed na kusantota idanunsa a kanta,lokaci guda kuma taji wani abu me dumi yana ratsa jikinta sannan ya zarto zuwa qafafunta ta cikin lafayar jikinta,sannan ya taba takalminta ya kuma fara sauka a farin marbles din dake shinfide a gurin.
Idanunta takai kai,wani irin abu ya daki
kwanyarta,jini ne, irin jinin da ta taba gani kenan sau biyu a rayuwarta,zamanin rayuwarta a gidan adam,zamanin da take mararin haihuwa da samun iri, yau ga na uku na fita daga jikinta wanda shi kuma wanna bata da tabbacin jinin meye?. Ruf idanunta suka gama fullubewa, tayi baya gaba daya zata zube a wajen,saidai tsananin zafin naman da toufeeq yayi ya hana hakan faruwa.
Cikin zallar tashin hankali ya tarota ta fada a jikinsa. Tuni afifa ta taso kanta, itama nadeeya ta garaso da sassarfa, shi da su kowa na kiran sunanta da garfi hankali tashe, toufeeq din yana jijiga kafadunta,saidai ko alamar motsi batayi ba. Hankalinsa a matugar tashe yake duban jinin dake zuba daga jikinta,sai ya dauketa cak kawai ya wuce office din likitan da gaggawa.
Suna shiga likitan dake rataye lab coat dinsa ya waiwayo,zuwa lokacin tuni ya shimfideta saman gadon dake dakin,cikin rudani ya juye harshen jamusancin shima yana cewa
“‘Der Arzt hat ihr schnell das Leben gerettet, ich weiß nicht, was mit ihr passiert ist (Dr ka ceto rayuwarta da hanzari bansan me ya sameta ba)” da gaggawa ya danna wani abu sai ga nurses har biyu sun shigo, ya kalli toufeeq
“Sir, geben Sie uns einen Arbeitsplatz?(sir ko zaka bamu guri muyi aiki?)” Kai toufeeq ya girgiza,yana tsaye qyam a gabanta hannunsa cikin nata,yana jin wani tashin hankali na ratsashi
“Ich kann nicht rausgehen und ihr vor meinen Augen irgendetwas antun(bazan iya fita ba,kuyi mata komai a gabana)”. Yadda suka karanceshin sunsan ba zaya fita din ba,abu daya yayi dole ya sake mata hannu don ya basu damar gabatar da aikinsu,ya koma baya kadan hannunsa zube a aljihun suit dinsa, idanunsa da suka sauya launi saboda tsananin tashin hankali qur a kanta tamkar an gaya masa yana janye idanun zai rasata.
Cikin lokaci gangani suka farfado xa ita daga suman da tayi sukayi goqarin tsaida jinin. Bai tsaya ba amma ya ragu,ganin hakan ya sanya likitan ya kunna na’urar scanning ya fahimci ne yakeson yi,sai ya matso gabansa
“Fass es nicht an, lass die Frau es ihrer Tochter antun, ich kann es nicht ertragen, das zu sehen(kada ka tabata,ka bari mace ‘yaruwarta tayi mata,bazan jure ganin haka ba)” likitan nada fahimta sosai da kuma saugin kai ya saki murmushi kawai ya matsa baya yana-sakarwa daya nurse din na’urar,har yanzu murmushi yakeyi sannan yace
“Du liebst sie anscheinend sehr, deshalb bist du so eifersuchtig auf sie(kana son ta da yawa da alama, shi yasa kake wannan kishin)” Kansa ya jijiga da qarfi don ya tabbatar masa da girman hakan cikin zuciyarsa
“extreme Liebe(matsanancin so)” ya amsa masa a taqaice.
Idanun likitan nakan allon computer din sanda take scanning din yana kuma yiwa toufeeq din bayani
“Kaine mahaifin fadeela?” Kai ya sake jinjina masa,sal ya waiwayo a nutse ya kalleshi, sannan ya saki murmushi, haka kawai yaji toufeeq yayi masa,ya miga masa hannu yana murmushin
“‘Ina tayaka murna,munyi aiki successful irin wanda bamu taba yin kamarsa ba,munyi nasarar cire sashen dake sakata jijiga in sha Allah daga yau zata rayu kamar kowanne mutum, amma zaku kula sosai da qa’idoji da kuma zuwa dubata har ta kammala warkewa duk da dai mun fahimci kamar any amfani da wasu magunguna a kanta da sukaso fadada ciwon ya taba wani sashen daban na qwaqwalwarta,wanda inda hakan ta faru ba zata taba warkewa ba, saidai taci gaba da rayuwa akan magani har qarshen rayuwarta,to sai kukayi dabarar tsaida maganin, abinda yayi nasarar hana afkuwar hakan,kuka kuma yi dabarar kawota akan lokaci akayi mata aikin,Glückwunsch(congratulations)”. Wani irin abu me sanyi ne ya sauka saman zuciyarsa tamkar ana sanya sassanyan ruwa ana wanke masa zuciyarsa. Cikin sanyin da mutuwar jiki ya migawa likitan hannu shima
“danke Doktor(na gode dr)”. Maida dubansa yayi ga saahar dake numfashi a hankali saboda allurar baccin da yayi mata bayan farfadowarta
“Wanne irin nau’in so zai gwadawa rayuwarta ne?” Ya
tambayi kansa da kansa,shi kansa baisan iya adadin sonda yake mata ba,ga wasu dalilai da suka qara rura wutar qaunarta me tsanani a ransa,shi kam bai sani ba baisanta yadda zai sarrafa wannan soyayya da qaunar da yakej) cikin qirjinsa ba.
“Setzen Sie sich, Herr (zauna yallabai)” likitan ya fada
yana dubansa, koda suka bashi seat din gaban gadontaya maidashi hannunsa cikin nata vana sake kula da dukwani motsinta
“‘Zamu bata daki itama,zuwa nan da awa sha biyu zamu tattara bavananta zamu sanar maka” likitan va fadi yana sake nazarin scanning din.
Zafafabiyar