TABARMAR KASHI 2 Book 2 Complete Hausa Novel
Dai dai sanda take isowar farfajiyar gidan,biyu daga cikin security din gidan na qoqarin bude qofar gidan,sai ta tsaya cak tana jiran ganin su waye?
Wasu laflyayyun range rovers ne guda uku,biyu daga ciki ta sansu farin sani,mallakin toufeeq ne. Tunda ya siyesu suke ajjiye bai hau su ba,to amma ya akayi yau aka fiddasu daga gidan?,ina akaje dasu bata da masaniya?.
Waiwayawa tayi tana gogarin kiran daya daga cikin me kula da motocin gidan,saidai kowacce kalma dake bakinta ta qafe tas!,cikin sakannin da basu haura biyar ba yawun bakinta ya dauke,wani abu me nauyi da girma ya daki kanta,abinda ya sanya mata dawo da dubanta zuwa gabanta a hankali kamar me ciwon wuya.
Cikin wata lafiyayyar abayar take blue black. lya adon jiki kadai ya isa ya gaya maka daga wanne gabila da kuma kalar nau’in ahalinta
“alhamdulillah,alhamdulillah,a’uzu bi kalimatillahit taammati minsharri ma khalaqa,Allahumma anzil ni munzalan mubarakan wa’anta khairul munzaleen” addu’o’in data furtasu dukka a bayyane kuma daki daki,cikin nutsuwa ta haqiga,addu’o’i masu qarfi da tsananin tsari.
Wata mummunar faduwa gaban hajiya qarama yayi,ta runtse idanu da kyau tana kuma budesu,suka sauka fes akanta SHIFA
CE,maji,matar yayanta Mahmud,bayan shudewar shekaru talatin da wani abu,sai yau gata a gabanta,sun hade cikin gida daya,sun hade cikin gidan toufeeq,toufeeq din da tace ta sanya a ranta ita ta haifarwa saidai ta haifi wasu a gaba shi da nadeeya,toufeeq din da tace itace dashi har abada…
…kai alwashin
da taci suna da yawa,wasu lokaci yayi mata halacci ya bata damar cikasu,wasu kuwa har yanzu walagigi takeyi sun kasa cika kamar yadda taso.
Murmushin da ta gani saman fuskar shifa bayan isowarta dab da ita,ita da fararen danginta wanda koda baka tambaya ba zakasan cewa yes,larabawan Algeria ne shi ya sake dugunzuma hankalinta,murmushi?, murmushi fa a fuskar shifa,shin ko yawan shekaru da tsahon lokaci yasa ta manta wace ita a wajenta? ‚bata tunanin zata bari taga koda haqorinta muddin ta tuna ita din fauziyya ce
“Assalamualaikum hajja fauziyya” maji ta kawar mata da dukka wata tantama daga ranta. Ko wacce gaba ta jikinta sai data cika saboda tasirin sallama,amma kuma nuna hakan a tattare da ita babbar faduwa ce,don haka itama ta saki nata murmushin,murmushin da ko kadan bai shiga fuskar maji ba bare ya ratsa zuciyarta,tasan wace fauziyya,kuma bata tunanin shekaru zasu canza halinta
“Wa’alaikummus salam,baqi ne haka damu? marhaban bikum” wani murmushin maji ta saki har sai da farare tas din hagoranta da toufeeq ya gado suka bayyana,wanda shekaru bai ragesu da komai ba. Waiwayawa bayanta tayi kadan ta kalli ‘yan uwanta da suka yo gaba,suka bar sauran suna fidda luggage dinsu
“‘Baqi? baqi,nidai nafi gaban baquwa,saboda daukan ciki wata tara,naquda ta kwana biyu cur babu sassauci a gasar da babu uwa ko uba,haihuwa zuwa raino har na tsahon shekara shida….kin tuna,su kuma dukka wadan nan da kika gani,bari nayi miki taqaitaccen bayani duk da idanunki na shaida sun gama gaya miki,wadan nan sun zarta baqi,ahali ne kuma halastattun dangi ga d’ana
Muhammad toufeeq,d’a na halali ga mahmud umar jarma….mun shigo cikin gidan d’ana da
sunan Allah tare da dukkan amincinsa,zamu zauna adadin yadda Allah ya deba mana,amincin Allah a gareki” ta furta tana miga mata hannu. Tamkar an shukata haka hajiya qarama taji,tsahon shekaru yau matar da take kalla a matsayin matsala yau ta sake waiwayarta,ta yarfa mata maganganu a gaban masu aiki da dukka hadiman gidan da sukayi tsaye suna mamakin jin bayanan maji. Tunda suke basu taba ganin gilmawar wata mace da sunan mahaifiya ce ga sir toufeeq ba,kowa yana kallon hajiya qarama ne a matsayin uwar kowa,hatta da Dr jarma. Ganin ta gagara bata hannun sai ita ta kamo nata hannun ta hade guri guda a sukayi musabahar,ta sake sakar mata murmushi tana cewa
“Kada ki manta,har yanzu a mazaunin qanwata kike,saboda haka daga zamana zuwa fitata hukuncina zai iya hawa kan kowa,ciki harda ke a mazaunina na uwa ga dan da ake qarqashinsa yake bada ci da sha da suttura harda mafaka ga kowa,saina tabbatar da wanzuwar matar alkhairi a gareshi wadda zata kula da rayuwarsa sanann na sake barwa Allah shi amana,kamar yadda nayi tsahon rayuwarsa ta baya, alqawarin kuma Allah gaskiya ne,ya kulamin da su fiye da yadda zato yayi tsammani” sai ta zame hannun nata daga na hajiya qaraman,kai tsaye ta cusa kanta zuwa cikin gidan ba tare data nema jagoranci daga kowa ba.
Wata iska me nauyi da zafi ta zuqa ta kuma fesar,me yake shirin faruwa?
“Kada ki damu, kwanaki bakwai kawai zatayi idan ta dade ta koma inda ta fito,ta barki da yaran da take taqamar a kansu,ki kuma sake mantar dasu suna da wata uwa a duniya wai ita shifa har abada” wannan saqar da zuciyarta tayi mata ita ta kawo sassauci cikin ranta,sai ta juya cikin gida tabi bayan su maji din. Dole ne kamar kullum tayi amfani da kissa da kyau
Cikin hararrami ta dinga bada umarnin kwashe kayansu maji zuwa dakunan da sajjad ya shirya musu,tun a ranar hajiya qarama taga wani irin banbanci muraran,wato shi tuwo dai ba’a taba canza masa suna,daga nadeeya har fadeela babu wanda ya yarda ya saki maji koda kuwa na minti daya ne,suna maqale da ita,bayan sun gama koke koken su,don koda wasa basu taba sanya ran zuwanta ba,nadeeyan rabonta da gain majin tun kafin ta tafi makaranta karatu,yanzu haka shekara kusan shida kenan dr jarma saidai ya bata haquri yace ba yanxu ba,shi ko toufeeq sai ya dauki zancan da gaske saiya shashantar dashi har kayanta ta taba hadawa da yace mata gobe ko jibi zai siya mata ticket tabi jirgi
Zuwa Algeria,amma ranar data kirashi yana airport ma zai tashi zuwa dubai haka taci kukanta ta haqura.
A yau din da taga majin sai takejin kamar duk duniya bata da sauran wata bugata,taci kukanta qwarai,amma yadda maji din ke kwantar mata da hankali tare da jaddada mata ta yiwa yaa moha uzuri sai ta samu relief. Duk wani shiga da fita na hajiya qaraman idanun maji na biye da ita,saidai kawai tayi murmushi ta girgiza kai,koda nadeeya ta tambayeta takance
“B komai nadeeya, Allah yayi muku albarka,ya tsaremin ku”
Tun kafin ya iso gidan labarin zuwanta ya riskeshi daga bakin nadeeya da kuma fadeela data rasa inda zata sanya ranta saboda murna,yau gata ga maji. Yana toilet cikin bathtub amma zuciyarsa na wani irin daka,yana jin doki da son haduwa da mahaifiyar da tayi silar kawoshi duniya,wadda rabonsa da ita shekara gome kenan cif,amma wani irin abu me kama da toro da shakkarta yana tasowa hadi da danne wancan dokin da yake ji. A qalla ya kusa kashe awa guda kafin ya garasa wankan ya fito,ya daur towel a qugunsa yasa qarami yana sharce ruwan dake kwance cikin gargasarsa data yiwa murdadden jikinsa ado.
Cikin wani sassauqan yadi mara nauyi ya shirya,duk da ba wani zaman ado yayi ba amma kyansa ya fito ainun,rashin walwalarsa ta qaru a ‘yan kwanakin saboda damuwar da dr da sailad sukeson jafeshi a cewarsa. Kamar yau din,bashi da niyyar fita amma hakanan ya fita bayan sajjad ya gama ce masa dangin amarya zasu zo su sake ajjiye wasu kayayyaki.
Wani takaici yazo masa wuya ya tsaya masa.don me za’a dinga masa shige da fice a sashe?,bayan shi ya fadi cewa bayason dukka wadan nan abubuwan amma anqi sauraronsa.
Hasalima shi sashensa ba gurin shigar kowa bane,wannan ya sanya dai dai da masu aiki kebantattu gareshi, su daya sai sajjad ke shiga masa guri. Baisan me yasa sajjad din be gyara spare part din dake gidan ba suje suyi koma meye a can,key din ya jefa masa ya tattara ya fita ko breakfast dinsa da Jacob ya hada bai tsaya yayi ba.