TABARMAR KASHI 2 Book 2 Complete Hausa Novel
Sake turo gofar dakin akayi,aka dan tsaya kadan a kanta na was mintuna kafin daga bisani ta magantu
“Maji nata kiranki amma tace no answer”
“Maji”?Ta maimaita sunan cikin ranta,a guri daya tasan me wannan sunan,kakar fadeela,ta kuma san afifa bawai sanin maji din tayi ba.
Mamakinta ya gaza bayyanuwa,ta yaye duvet din tana kallon afifa daie tsaye tanata gyalli hadi da baza qamshi
“Wacce maji din?”
“Uwar mijinki” ta fada gatsal kai tsaye. Duk duniya afifa ce kadai zata yi mata haka ta ayaleta,sai taja siririn tsaki ta ja duvet din da nufin komawa ciki, dai dai lokacin kira ha shigo wayar afifa dake hannunta
“‘Yauwa gashi ta sake kira” afifan ta fada tana matso da wayar kusa da sãahar din.
Koda ta tsani toufeeq tana qaunar fadeela,hakanan tanason maji tana kuma qaunar nadeeya. Mutanene masu wani irin karamci tare da maida dan kowa nasu,suna da wani irin saugin kai tamkar ba daga jininsu toufeeq ya fito ba,ba maji ba,duk wata dake da shekaru irin nata ma ba zata iya wofantar da ita ba,do ta samu cikakkiyar tarbiyyar wannan daga gida,tilas ta miqe ta zauna sosai,ta miga hannu tana amsar wayar tare da jefawa afifa harara sannan ta daga kiran tana
karawa a kunnenta,dai dai sanda afifa ta watsa
hannunta alamun ko a jikinta ta fita tabar mata dakin.
[15/09, 5:29 pm] Laila Abdulqadir: *HUGUMA*
*_TABARMAR KASHI_*
Book 02 Page 12
Gyaran murya ta danyi,idanunta akan
sãahar tana sake takowa kusa da da ita,daga
gefan lallausar sofa bed ta zauna tana
dubanta da kyau
“Maraba da shigowa mahmud JARMA
family,na tayaki murna qwarai bisa samun
wannan nasara da kikayi,sannan kuma ina
miki alhinin cewa….nasararki zata kasance
ta gajeran zango ce,sakamakon toufeeq ba mallakinki bane,dukka tsahon rainon
da nayi masa,na raineshi ne don ya zama
mallakina,wato mallakin ‘vata meenal haseena”
wani dan banzan haushi maganar hajiya
qarama ta saukar a zuciyarta,tayi qoqarin
tsaida hawayenta tana son fahimtar abinda
matar take fadi, idanunta na kallon tafukan
hannayenta ba tare data yaye rufin kanta ba
“Na jinjina miki yadda kika shirya komai ya
kuma tabbata lokaci kadan bayan tafiyata,to
amma ki sani,sauyawarki daga sunan nanny
boyi boyi zuwa ga matar auren toufeeq
babu abinda zai canza daga dokoki da
tsare tsaren gidan nan,fatan da nake miki
ki iya kiyayewa,sannan ki jirayi sakamakon
da zai biyo baya nan da kwanaki bakwai
masu zuwa,batun jikata fadeela,banason
ki fiya zaqewa cikin lamuranta saboda
shine samun lafiyarki,kiji kigi ji ki gani kigi
gani,na barki lafiya,asha amarci lafiya” tana
kaiwa nan ta mige,saidai taku uku kacal
tayi sãahar da zuciyarta ke a dugunzume
ta gaza daurewa kalaman hajiya qaramar,ta
tunzura qwarai,itama irinsa ce kenan? me tarin
Izza taqama da izgili,ashe ga inda ya debo dabi’arsa,lallai akwai wani boyayyen abu cikin taku da rayuwar matar cikin gidan,jikinta da zuciyarta sun gama aminta da hakan,adam ya yiwa rayuwa ruhi zuciya da gangar jikinta mugun horon da yasa nan da nan take iya fahimtar wani abu daga wasu mutane da dama.
“Inda kinsan abinda ke qasan zuciyata da baki bata bakinki kina wannan b’ab’atun ba.don haka na roqeki ki kama girmanki,zan nanata miki tun a daren farko na cikin gidan nan saboda daga ke har shi ba zamanku nazo yi ba” zallar madarar mamaki ya saukar mata.wani abu yayi mata tsawa a kanta,ta waiwayo tana son tabbatar da abinda kunnuwanta suke jiye mata,sai sukayi idanu hudu da saahar data dage hular kanta,wanda hakan ya bawa kyakkyawar fuskarta data sake wani sassanyan kyau saboda gyara data ci kamar babu gobe,da kuma haske da annurin
AMARCI dake sauka a fuska da jikin kowacce diya mace data amsa wannan sunan. Kamar ko yaushe yanzun ma kwarjini tayi mata,amma hakan bai hana hajiya qarama ritsata da ido ba,tana mamakin qarfin halin yarinyar.
Tabbas dole ta shiga cikin mutanen da take
targeting,ta yiwa kanta wannan alqawarin,sai ta gyada kanta ta juya ta fice a hankali daga dakin.
Qaramin tsaki säahar ta sauke bataii
zata zauna matar ta sanya mata wata
damuwa,ita sam bata cikin damuwarta bare
tace zata takura mata,ba ita ba,koda shi kansa
toufeeg din ba zata yarda ya zamar mata
damuwa ba bare wata ganwar mahaifi data
fuskanci zuciyarta akwai ayar tambaya.
Ta jima zaune a gurin tana saga da
warwarar yadda zata tafi da rayuwarta cikin
gidan,zata bawa kowa girma,amma sam ba zata dauki raini cin zarafi ko cin fuska ba. A
yadda taji gidan ya fara shuru ya tabbatar
mata dare ya fara yi,sai ta dubi agogon
dake jikin bangon dakin nata,fitsari takeji
sosai hakanan ta tabbatar wadan nan kayan
jikin nata ba zasu barta sakewa ba,don haka
ta miqe ta zare rigar saman,tanar doguwar
rigar wadda ta fidda shape dinta qwarai da
gaske,tun daga girji zuwa qugunta,ta tattareta ta nufi qofar da take tunani bandaki ce da zummar idan ta fito tasan yadda zatayi ta raba kanta da rigar itama yadda zatafi jin dadin kwanciya.
Ya kusa mintuna talatin zaune
cikin motar tasa bayan fitowarsa daga gurin maji,a yau addu’o’in da yasha a bakinta zai iya cewa bai taba jin makamantasu ba daga bakinta.farincikin da ya gani kwance a fuskarta ya taba zuciyarsa,duk yadda yake zaton ta dauki auren ya wuce nan,ta mashi wani babban matsayi da yayi imanin ba nan kusa ta ajiyeshi ba. Motar na a kunne ac naci gaba da aikinta,hakanan fitilun cikin motar. Sanye yake da wani baqin yadi da aka yiwa dinki tamkar na buzaven qasar nijer,dinkin ya zauna matuqa da gaske a jikinsa, kamar yadda baqin yadda ya kwantawa farar fatarsa ya sake fidda ainihin haske da kyanta tare da bayyana zallar hutu da in dadi hadi da kulawar da take samu,bagar sumarsa ta ainihin halfcast na nannade saman kansa tana bada wani sheqi me kyau da sassanyan gamshi kamar ko yaushe.
Waiwayawa yayi a nutse ya kalli tarin ledojin alfarma dake gefansa,wanda duka maji ce ta bashi tace ya shiga gurin iyalinsa dashi,don shi babu abinda ya riqo a hannunsa,duk da yanajin sanda abokansu ke hadawa sajjad,sunyi la’akari da cewa shi din tsohon aure ne,sunsan zai tanadi abinda ya kamata ba sai an gaya masa ba. Su kansu kayan qarin nauyi ne a wajensa,don ya tabbatar tilas ya sadasu da wadda aka siya saboda ita kodon cika kima da martabar maji.
Sashen nasa ya sake saukewa
idanunsa a karo na barkatai,sam baya gaunar shiga sai don babu yadda zaiyi,a duk sanda ya tuna cewa akwai wata mace a ciki me amsa sunan matarsa duk sai yaji kamar dai an takureshi ne kawai. A karo na gaba da qarfi yaja tsakin hadi da balle murfin motar a zafafe ya fito,jibril dake jingine jikin motar ya qaraso da sauri,kafin yace komai toufeeq din ya rigashi magantuwa
“Ka gayawa Jacob ya shigomin da kayan cikin falo, ka kashe motar na sallameka,sai kuma da safe”
“Sir,da safe kuma? na dauka zakaje hutu ko?, ko don madam” jibril din ya fada zuciya daya yana murmushi,saidai kallon da toufeeq din yayi masa ya tabbatar ya tafka baranbarama,sai yayi saurin jan bakinsa ya tsuke yana yunqurin bude daya side din ya fiddo kayan kamar yadda ya umarta.
Hannayensa zube a aljihun wandonsa yake qarewa falon kallo,ya sake jan qaramin tsaki, komai nashi sajjad ya canza masa,duk da kyawun da sassan ya qara ya kuma zuna favourite colours dinsa,to amma shikam bai shiryawa dukka wadan nan abubuwan ba. Da kansa ya gaji da tsaiwa,ya sunkuya ya kwashe kayan da jacob ya shigo masa da su,ya nufi hallway din da zai sadashi da dakunan baccinsu,ransa yana sake baci,komai a yanzun sai yayi sharing da wani,gurin mallakinsa ne a baya,shi daya yake shiga yayi rayuwarsa,idan zao shekara bai fito ba motsin kowa bazai dameshi ba,amma a yanxun bashi da wannan tabbacin.