Diddigar Kaya Complete Hausa Novel
Akamun fa’iza ta kawo ta kwaɓa ta saka mata har lokacin kuka take, tayi tayi ta ci wainar da saura kaɗan ma su kammala ta ƙi tace ta koshi, cikin rashin jin daaɗi Mammi ke bin ta da ido har ta fice se ta saka fa’iza juye wainar a flask ta bita dashi su je su ci a gida don ta tabbatar ko sashen Jaddah Fauxa bazata kara zuwa ba se an tabbatar mata da baya gari.
Haka kuwa aka yi da fa’iza ta kawo mata ma ƙin ci tayi, Allah ya isa kuwa ta ja mishi yayi cikin kwando, gashi Ammin ta bata nan ta tafi kauyensu jiya uncle ɗinta ya rasu, da magrib ma da kyar ta samu tayi alwala ta tako zata fito zuwa masallaci kenan ta tsaya Chak jin muryar dake tashi a speaker na masallacin, tsaki ta ja ta koma ɗaki nan tayi sallah har isha bata fita ba, a Cewar ta bazata bi sallar azzalumi ba don Allah ba karba ze yi ba. bayan tayi isha ne ta kunna speaker ɗinta iya daidai jin kunnen ta ta saka waƙa abunta anan mood ɗinta ya fara dawowa daidai.
Tana ji su fai’za na cin abinci bata fita ba, idanunta a lumshe take jin Fatima na fesawa fa’iza ita duk yadda take jin karatu bata taɓa jin me natsuwa da kwantar da hankali irin na Ya Faizan ba, fa’iza na dariya tace mata
“zaki ce haka ne ma tunda kina son shi”
Fatima ta ce
“ban gane ina son shi ba? Ko de muna son juna?”
Fa’iza tace
“ai ko makaho ya shafa ya san ke ce kike mahaukacin son ya Faizan shi ba take yake ba, ba ta yadda za’a yi yana son ki ne ke karan kanki kan ya miki magana ɗaya se kinyi hamsin, sannan ya tafi yayi wata da watanni ko a wayan Jaddah baze ce a baki ku gaisa ba idan ma yana jin kunyar Mammi kenan, ni wlh bana son miki kasancewa da ya Faizan ina so ki samu me son ki inda zaki ji….”
Tsawa ta daka mata
“dakata fa’iza! Don ina maganan soyayyata dake ba shi yake nufin ki gayamin duk wani banzan maganan da ze fito daga bakin ki ba idan ma ba kitsa miki aka yi ba don baki da wannan wayaun, to henceforth as from today kika kara min irin wannan maganan wlh se nayi mummunan saɓa miki ni ba sa’ar ki bace”
Fa’iza tace
“Ya Fati daga faɗar gaskiya?”
“Bana son gaskiyar ki riƙeta”
Daidai lokacin Fakiha ta shigo da gudu tana shelan ya Faizan ya ce a je a karɓi tsaraba yana sashen Jaddah.
Da sauri duk suka tashi suka fice daga tsakar gidan.
Taɓe baki Fauxa tayi, Fatima na neman magananta ta tabbatar harda shagube a zancen nata, amma ba ta ita take ba yanzu ta samu ta warke shine damuwanta kuma wlh akan Fatima zata rama abunda ya mata tunda shi azzalumin ya fi karfinta.
Chan da yunwa ya fara damunta don ko abincin rana bata ci ba ta sa a zuciyarta zata ci wainar fulawa yasa ta mike ta fito a hankali ta nufi kitchen, ja tayi ta tsaya jin kuka na tashi a hankali….
DIDDIGAR ƘAYA…(Mai wuyar tsincewa) wannan littafi littafin kuɗi ne..
Ze zo muku a Naira ɗari uku kachal #N300.
Acc no. 0545475847
Acc name. Fatima Muhammad Gurin
Bank name. Gt bank
Se ki tura shedar biya zuwa wannan layin
09039206763
Ko ki tura katin waya ta layin na sama tare da shedar biya ta what’sapp.
Yi maza ki biya naki ki sha karatu cikin kwanciyar hankali, ina me tabbatar miki bazaki taɓa nadama ba
Karku sake a baku labari.
Gureenjoh
DIDDIGAR ƘAYA
(Mai Wuyar Tsincewa)
بسم لله الرحمن الرحيم
FATIMA MUHAMMAD GURIN.
(Gureenjo)
ADABI WRITERS ASSOCIATION
Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
*Kowa Ya ga zabuwa..*
And Now..
*Diddigar ƙaya… Paid*
*Shafi Na Bakwa*
*PAID BOOK*
ƊANƊANO
**WANNAN SHAFI SADAUKARWA CE GAREKI AUNTY HALILLOS GWANATA KUMA MALAMATA❤️**
“Aunty wallahi son shi ze kasheni! Kin Reneni ne da soyayyar shi hakan ya bani karfin gwiwar kwallafa rai a kan samunshi sede gashi har yanzu shi bana gabanshi, yanzu har fa su fa’iza sun san nice me cusa kai a gareshi shi ba ta ni yake ba! Aunty kinga wulakancin da ya min a gaban su Fa’iza da kannenshi maza?”
Ta karasa tana me kara rushewa da kuka.
Aunty tayi saurin sa mata hannu a baki tace
“Haba Fatima! Me yasa ke kam kullum rashin haƙurinki kara gaba yake? Na faɗa miki na kara jadadda miki idan har Faizan be aureki ba to wallahi ba ze auri wata ba, wannan alqawarin da na daukar wa kaina ne tun kan in shigo gidan nan, tufka nake ana warwarewa amma ba matsala ki kwantar da hankali na miki alqawari Faizan ba ze bar garin nan ba tare da an tsayar da magana tsakanin ku ba!”
Wani wawan tsaki Fauxa ta ja kan ta juya ta fice daga gidan gabaɗaya, a chan gefe da sashensu inda aka yi wasu kujeru haka masu kyau na tayoyi ta zauna, tana me kallon qonannan hannunta, murmushi ta saki na jin daaɗin ba ita ba aikin gida har se ta warke, makaranta ma in ta je ba rubutu ai kuwa za’a sha neman tsokana.
Bata san iya adadin lokutan da ta ɗauka a wurin ba, chan ta hangosa yana tahowa cikin tafiyar nan tasa me cike da natsuwa kaman saraki, sanye da wasu kananun kayan still farin Jean da navy blue shirt a ko yaushe Adonshi da shigar shi masu kyau ne da salo irin na burgewa.
Maganan Fatima ne ya faɗo mata bata san sadda ta kwashe da wani irin dariya ba har da hawaye, wai amma Fatima tayi asara ta taɓe duniya da lahira fisabilillahi ta rasa abun so se wannan? Dariya take tayi tana sakewa wai fa har da kuka Fatima ke yi sbd shi? Ta kara kwashewa da dariya tace
“Taabbb Allah ka rabani da aikin wahala”
Har ya wuce tana babbaka dariyar ta kaman sabon kamu inda Allah ya taimake ta ba Kallonshi take ba don ta san in har ya san dashi take yadda ba kowan nan se na lahira ya fi ta jin daaɗi, ji fa yadda yake tafiya, ita wallahi tafiyar da yake yi ko ita mace bazata yi irin shi ba, dariyarta tasha daidai sashensu na samari ta ga ya ɗan tsaya ya waigo, daidai itama ta ɗago ta kalle shi se suka Haɗa idanu, kallon kanki ya taɓu ya watsa mata.
Ko seconds biyu be yi ba ya juya ya karasa shigewa sashen, mikewa tayi tana share hawayen dariyarta kaman wacce duniya ta yiwa daaɗi ta wuce sashen Jaddah, tana shiga ta narke tana tafiya kaman marar lafiya.
Jaddah tace
“zo ki karbi tsarabar ki na wurin Faizan”
Haɗe rai tayi, Fa’iza tace
“ke kinga rikicin da aka kwasa da ya Faizan kan Jaddah ta kwasar miki chocolates ɗin nan karfi da yaji? wlh ki gode mata ta san yadda kike son chocolates shiyasa, ga su da daaɗi kaman zasu tsige kunne”
Kallon chocolates ɗin tayi masu tsada ne sossai, daga gani ma maybe ba a nan Nijeria ya sayo su ba sede tunda daga hannunshi ya fito basu ba ta sha’awa ba, kau da kai tayi tace
“Jaddah da baki wahalar da kanki ba don ni kam ba sha zan yi ba”
Jaddah ta saki baki zata yi magana kenan Fauxa ta fara kukan hannunta na zugi, da sauri Jaddah ta karɓe hannun tana salati tace
“Faozia garin yaya? Me ya sameki haka?”
Ai jin tambayan Jaddah yasa ta kara narkewa tana fashewa da kuka, she’s so fragile in tana abu kaman little baby, Fai’za tace cikin damuwa.
“Jaddah ita da ya Faizan ne”
Nan ta bata labarin abunda ya faru tsakaninsu, Jaddah tayi ta masifa ta kuwa ci alwashin se ta saɓa mishi wani irin mugunta da bakin hali ne wannan?
A kan cinyar Jaddah ta kwanta tana jin daaɗin yadda Jaddah ke ta zuba mitan abunda ya farun, ta kara da
“mutum ne se baƙin miskilanci yanzun nan yasa yarinyar da yake ikirarin buduruwarshi ce kuka amma ko a kwalan riganshi”