Diddigar Kaya Complete Hausa Novel

Diddigar Kaya Complete Hausa Novel

Jaddah sossai ta nuna amincewarta da shawaran a haka suka tsayar kan su Faraj suka yi ta ba baba hakuri yace ba shi zasu ba wa ba Fauza zasu ba kuma biyar da Faizan ya kashe a asibiti su tabbatar sun biya shi, a haka aka watse aka bar Faizan a zaune a wurin.

Seda baba ya kula da Sam kaman baya hayyacinshi ne ya tashi yaje ya ɗibo ruwa masu sanyi ya kawo mishi
“karɓi ka sha!”

Ya kalli kofin kan ya ɗaga ya kalli baba da rinannun idanunshi yace
“na koshi”

Baba yace
“karɓi mana ai ruwa rayuwa ne”

Karɓa yayi ya kafa kai ya shanye tas kan ya ɗago ya sake kallon baban, murmushi shimfiɗe a fuskanshi yace
“karka ɗaga hankalinka Faizan, a yadda na sanka da natsuwa, kawaici da hangen nesa kaman mahaifiyarka ina so ka cigaba a haka, na zaɓa ma Fauziyya Kaine sbd Kai ne Allah ya sha nuna min a duk istikhara na, da kai hankalina ya fi kwanciya, na san bazaka taɓa tozarta abinda na baka ba”

Faizan yayi shiru kaman ruwa ya cinye shi
“baba fa watana kwata kwata uku ne da aure”

Yace
“na sani, Fatima da mahaifiyarta masu fahimta ne na san zasu fahimta”

“baba mahaifiyarta bata taɓa ƙaunata ba, ko gaisuwata bata taɓa buɗe baki ta amsa ba”

Yace
“na sani wannan duk ba wani abu bane ba lallai kowa ya so ka a duniya ba, daga kan Annabawa har Sahabai zuwa malamai babu wadda bashi da maƙiya”

Yace
“Baba Fauziyya da Fatima basu taɓa shiri ba taya zan iya haɗe kansu su zamar min tsintsiya madaurinki daya kaman yadda ka zamarwa iyalan ka?”

Yace
“kai ɗin jarumin namiji ne wannan me sauƙi ne a gareka, ina me tabbatar maka zaka yi alfahari da wannan haɗi watarana, ka je ka kwanta karka yawaita tunani instead ka raya daren idan ba zaɓin Allah ba ce se ka ga Allah ya musanya mata da alkhairi in kuma ka ga an ɗaura to kaddarar ku a sarƙe take da juna tun fil azaal”

Mikewa yayi yace
“Na gode, se da safe”
A ladabce kan ya juya ya fice.

Wannan dare haka ya zamarwa Faizan daren tashin hankali don ya kwana yana rokon Allah akan wannan abunda baba ke shirin tinkarar rayuwarshi dashi, duk mazan gidan a rasa wadda za’a lakabawa wannan fitananniyar yarinyar se shi? Yayi nadamar zuwa yola a ranar ya fi sau dubu kila da be zo ba baba be ganshi ba da wani ya zaɓa ya baiwa ba shi ba.

Jadda da mammi dae sun kwana cikin farin ciki yayinda baba Alhj ya kwana yiwa wan shi Adu’a ya tabbatar ba don shi ba da lamarin Fauza yanzu ya kaishi ƙasa, Ammi ya kira ya mata bayani tashi ɗaya ta nuna Allah ya kasheta wallahi baza ta kara Haɗa zuri’a da Mammi ba an yi mata fin karfi a lokacin fadyaa yanzu kam babu wadda ya isa, har gwara faahim sau dubu da Faizan a gareta.

Baba be kula ta ba ya yi kwanciyar shi don in yace ze biye mata se Amarya ta ji kuma yana so ya sanar da ita ta yadda zata fahimta babu cin fuska ko son kai a wannan tafiyar.

Washegari zaliha ta tashi daga baccin da ta koma bayan sallar asuba bata samu Fauza ba, neman duniya da nurses suka mata bata cikin asibitin ko da Baba prof da jadda da kuma Aunty Amarya suka iso ana kan nemanta ne.

Alamu dae sun nuna fita tayi sede ina zata da rauni a jiki?

Ita kuwa tana tashi ta mike zaune tana kallon inda suka bare mata a fatarta da take matukar tattali, ranta yayi baƙi kirin da irin wannan tozarci da yayyun nata suka mata, ta tabbata duk gidan maƙiyanta ne banda mammi da jadda da Amminta, lallai abunda suke gudu se ta sake yi in basu kasheta ba ba su cika mugaye ba.

Dira tayi daga kan gadon ko hijab ɗin da ta dauka ganin yadda ya fashe yasa ta cillar, takalmin zaliha ta saka ta fice, abun hawa ta tare se gidansu sakina, ta sa me gadi yaje ya karbi kudin ya kawo mai, sossai hankalin sakina ya tashi da ganinta haka.

Anan tayi wanka ta sauya kaya tayi kwanciyar ta bayan ta ci abinci, duk yadda sakina ta so tayi magana kasawa tayi da ta matsa se ta kawo kuka ta sa, hakan yasa zaliha bare wasu tabs tace
“sa wannan a ƙasan harshen ki duka biyu ki barshi ya narke da kin yi bacci kin tashi bacin ranki ze kau”

Sawa kuwa tayi ta kwanta, a haka tayi bacci har sha biyun rana kan ta farka abu kam ya fi karfin jininta ga shi ta bata overdose ne, tana tashi ta gayawa sakina duk abunda ya faru ta kuma ce tana so ta kunsa musu bakin cikin da zasu saka wuyan ta gabas su yanka, wayan sakina tayi anfani dashi ta kira Zubair luckily ya koma da yau abunda yake so da ta bashi.

Haka ta diro ko mayafi taƙi sakawa kaman ba ɗiyar musulmi ba ta nufi fita, Sakina da kyar ta shawo kanta akan driver ya maida ta.

A farkon layinsu tace ya ajiye ta don tana so kowa ya kalleta yadda su Farhan zasu kara jin haushi, aikuwa kaman ta kimta daidai.

Farhan, Faizan, Faraj, Baba Alhj baba prof da polisawa ne tsaye ana batun yadda za’a samo ta shi Faizan kaman dole ce kawai aka mai na shiga case ɗin zuciyarshi na bashi wurin watsewarta tayi don mashayi daga ranshi ya ɓaci abun shaye shayenshi yake nema ya rage zafi.

Yana cikin wannan tunani ya ɗan kalli hanya har ya ɗauke idanu yayi saurin sake mayarwa ya zuba mata su yana kallo, tun daga nesa zaka san a make take mankas, so yake ya janye hankalin baba Alhj sede yana juyowa yaga duk suma sun zuba mata idanu, ga bandage a jikinta ta sa wani riga da da kadan ya sauka kaurinta, hannunta duk a bayyane gashin kanta a Parke cikin loose bon, Baba Alhj ne ya tafi ze fadi, Baba prof yayi saurin tare shi yace

“Menene haka Sulaiman? A kanka aka fara jarrabawa? Kana so se ka ɗaurawa yarinyar nan abunda ya fi wannan?”

Su Farhan yayiwa kallon duk wa ya janyo? Ba ku ba? Kan ya saki baba Alhj ya fara tattaki zuwa gareta.

Maganganu take maras kan gado tana faɗin laifin babanta ne da yayi mata baki kullum yake kiranta fitsararriya gashi fitsara ta bita, ba su Farhan sun ce zasu mata abunda bazata kara marmarin rayuwar banza ba? To gashi ta kara su sakata gabas su yanke yanzu yanzu zuwa tayi don su gani, Kaman Faizan ze yi kuka don tausayin kanshi yanzu da abunda Babanshi ze Haɗa shi kenan?

Har ɗakinta ya kaita a sashen Jaddah tare da taimakon ta ta shimfiɗar da ita se bacci, duk idanu suka zuba mata.

Jaddah tace cikin karfafa mishi gwiwa
“Adu’ar mu baze taɓa faɗi ba professor, ka kwantar da hankalinka abunda kake shirin yi in shaa Allah shi ze zama silar warakar komai, Allah maji roko ne me jin ƙai ka fini sanin cewa baya taɓa juyar da Adu’a sai de in ya musanya da abunda ya fi alkhairi, ya kuma amsa ta hanyar da tafi kowacce daidai, sadaqa maganin masifa ne, haka kuma Qur’ani waraka ce, Adu’a kuma takobin mumini ne duk bamu daina akan Fauza ba kaga kenan muna da yakinin Allah ze karɓa ko ba daɗe ko ba jima”

Yace
“hakane mama, bana kokonto akan Hukuncin Allah sede a duk sadda zan ɗaga idanu na kalli yarinyar nan jikina yana bani wani abu na daban mama, gani nake ana zaluntarta amma ban san ta ya ba, tausayinta ke ratsa zuciyana har na kan zubar mata da hawayen tausayawa in na kalleta, ba ni kaɗai ba sau ba Adadi Aisha ta min magana makamancin haka akan yarinyar nan”

“komai ze tafi daidai professor in shaa Allah auren da ka Haɗa ze zama sanadiyar warwarewar duk wasu al’amuran ɓoye”

Mikewa yayi ya fita bayan ya tofe ta da wasu Adu’o’i, ko da ya dawo ya nemi Faizan ya rasa don barin garin yayi.

Satin shi uku da komawa Fatima ta sake ɓarin cikin wata guda.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected