Diddigar Kaya Complete Hausa Novel

Diddigar Kaya Complete Hausa Novel

Yunkurawa Fauza tayi zata miƙe daidai lokacin da aka turo kofa hakan ya sa Fatima yin baya baya zata faɗi cikin zafin nama yayi hanzarin isowa ya tarota yana aikawa Fauza dake tsaye tsakiyar gadon bata kai ga Sauƙar da tayi niyya ba wani irin dead look.

*Yanzu wasan ya soma*

DIDDIGAR ƘAYA…(Mai wuyar tsincewa) wannan littafi littafin kuɗi ne..
Ze zo muku a Naira ɗari uku kachal #N300.
Acc no. 0545475847
Acc name. Fatima Muhammad Gurin
Bank name. Gt bank
Se ki tura shedar biya ta wannan layin
09039206763.
Yi maza ki biya naki ki sha karatu cikin kwanciyar hankali, ina me tabbatar miki bazaki taɓa nadama ba

Karku sake a baku labari.

Gureenjoh

17

*Assalamu Alaikum warahmatullah barkanmu da warhaka, fatan duk muna cikin ƙoshin lafiya? Alhamdulillah na gode sossai da adu’o’inku gareni Allah ya saka da alkhairi jiki yayi sauƙi se a ɗaura daga inda aka tsaya in shaa Allah.*

A hankali ta samu wuri ta zauna akan kujeran parlorn saman chan nesa da inda suke, dukda zuciyarta a tsinke yake don har Ga Allah Faizan na daga cikin waenda take jin shakkarsu don tana tsorace dashi ne tun tana ƴar ƙaramarta, matarshi kawai ya kama suka fita daga ɗakin nata bayan ya ce ta same su a parlor.

Ya ɗan yi shiru kan yace
“Fauziyya kike ko?”

Kai ta ɗago tana Kallonshi wai ita yake tambaya sunanta? Bata amsa ba seda yace
“wai ba da ke nake magana ba? Kin san Allah ki rufawa kanki asiri ki zauna lafiya da mu tun muna sheda juna, ba zan lamunci rashin kunyarki da fitsaranki ba, ba a kaina kaɗai ba har da matata”

Kallon Fatima yayi yace
“Daga yau ki sallami Baaba ta dinga tsabtace gidan nan tana girka muku abunda Zaku ci da ke da ita, ba zan iya cin jagwagwalonta ba don haka ke zaki kula da nawa abincina da gyaran ɗakina”

Fatima na murmushi tace
“in shaa Allahu habeeby”

Ya sake kallon Fauziyya yace
“Daga ni har Fatima akwai wadda kika fi shekaru?”

Girgiza kai tayi yace a ɗan zafafe
“baki da baki ne?”

A hankali tace
“A’a”

Yace
“madalla! Saboda haka duk safe ke zaki gaisheta, karki kuskura in sake ganin abunda ya faru yau ya faru don bazaki ji da daaɗi ba Fauziyya, matata ta fi karfin wulakantarwanki, Abu na ƙarshe shine babu wani zancen rabon kwana don zaki zauna ne a matsayin ƙanwarmu..”

Kallon Fatima yayi yace
“ko kina da abun cewa?”

Tace
“ya Faizan na ga baka ja kunnenta akan shan kayan maye da kuma bin maza ba!”

Wani irin kallo Fauziyyan tayi mata kan ta maida idanunta kanshi jin mai ze ce, se taga ya kauda kai da alama ita yake kallo ganin zata kalleshi ya kawar da nashi idanun, bazata ce ga expression ɗinshi ba amma da saisaitacciyar murya ya furta..

“Gate ban amince ki taka ba tare da izini na ba Fauziyya”
Abunda ya faɗa kenan ya sallameta, ta mike ta wuce ɗakinta ba tare da ta tanka musu ba.

Fatima tace
“Abunda zaka ce kaɗai kenan?”

Ya ɗan miƙe tsaye kan ya ce
“me zan ce to? Babu wadda ta sani anan garin da ze shigo har gidan nan ya ruɗe ta, hakanan tun da ta sanya kafarta cikin gidan nan na yiwa gateman kasheɗin bayan ni da ke kar ya bar kowa ya fita daga gidan nan ko ya shigo idan har ba da sanina ba”

Ganin ze wuce room nashi tayi saurin mikewa
“amma fa kai da kanka ka ce ka ganta a nan garin kenan ai baka san ko akwai wasu bad friends ɗinta a nan ba…”

Ya dakata tare da juyowa ya kalleta na seconds kan ya juya kawai ya wuce ɗakin shi, zama tayi kan kujeran dabas tana sake sake, ta so ya gayawa Fauziyya maganan da ze hana ta bacci wlh akan shaye shaye da yawace yawace da take yi amma ba komai da ita take zancen.

Itama mikewa tayi ta wuce ɗakinta don shiryawa ta dawo turaka.

Samun wuri tayi kan kujera ta zauna tare da ɗaga throw pillow ta ɗaura kan cinyar ta ta zabga tagumi, wai haka zata yi wannan zaman? In aiki ne be dameta ba don horon da ta sha kwanakin nan a gidansu na aiki ba kaɗan bane har ma ta saba, amma bata da waya ba abokin hira, shiru haka ze yiwu kenan? Chan ƙasan ranta kuma maganan Fatima ba ƙaramin kuna yayi mata ba amma ba komai zata yi lokacinta.

TV ta kunna ta rage daren da kalle kalle daaɗi sossai ta ji da ta ga ba wa’azu zuƙa bane, se karfe sha ɗaya ta kwanta don ma ita ba gwanar ci ba ce da dole se ta fita ta nemi abinda zata ci.

Buga kofan ta da aka yi da karfi shi ya tasheta a ɗan firgice, dalll haka aka kunna mata bulbs ɗin ɗakin duka Fararen waenda suke da matukar haske, da sauri ta sanya hannu ta rufe idanunta, duniya ta tsani a kunna mata wuta daga tashi daga bacci.

“Malama tashi ki sama min abunda zan ci karfe bakwai nake da lectures”

Dukda yadda ranta yayi mugun ɓaci bata tanka ba, haka kuma bata ɗaga idanu ta kalleta ba.

“Da ke fa nake magana malama!”

Har lokacin bata yi magana ba tana calming kanta ne, bayan ta gama Adu’ar tashi daga bacci ta sauka kawai ta shige toilet bata ce komai ba.

Se hakan ya kular da Fatiman, a fili ta furta
“kammm ni zaki mannawa hauka? Wato ga mahaukaciya tana magana?”
Kwafa tayi ta fito ta je ta zauna a parlorn saman ta ɗaura ɗaya kan ɗaya tana girgizawa, time ta dibar mata in bata fito ba kuma wlh se ta kai karata wurinshi.

Ita kuwa Fauziyya watsa ruwa tayi ta fito ta ɗan shafa mai da turare kadan ta saka cotton bubu ta fito, a kan kujera ta wuceta ta nufi hanyar kitchen ba tare da ta ko kalleta bane.

“Ke! Ina zaki je? Ba’a shiga min kitchen kije na ƙasa wannan ɗin abincin mijina kaɗai nake dafawa a ciki gudun barbaɗe”

Juyawa kawai tayi ta nufi ƙasa ba tare da tace komai ba.

Dankali ta fere me yawa ta zuba gishiri tuli guda kan ta soye shi yayi kararau ta juye a warmers ta ɗauka ta je ta ajiye kan dining kan ta wuce ta haura.

Har zata wuce ɗakinta Fatima ta ce
“Fauziyya..!”

Juyawa tayi ta nufi dining ɗin saman, ganinshi a ciki yasa ta ce
“Ina kwana”

Kaman yadda yayi mata umarni
“lfy”
Shine abunda ya amsa da kan ya cigaba da cin abincinshi.

Kallon kiran me kika min kawai take yiwa Fatiman, ita kuma se tayi shiru na seconds kan tace
“tunda ni ba zaki gaisheni ba, ina kwana? Fatan kin tashi lafiya?”

Wani irin kallo Fauza ke mata na kina kure haƙurina, ɗaga idanu yayi ya kalleta se tacewa Fatiman
“Ina kwana”

Fatima tace
“lafiya ƙalau ya kwanan bakunta?”
Bata amsa ba hakan ya sa Fatima cewa
“yauwa kin gama abincin ba?”

Kaɗan ya saura zuciyar Fauza ya zo wuya tace
“uhm”

“yana ina to?”

“Kasa”

“ka ji ki, ai anan ne muke karyawa, je ki ɗauko mana”
Seda ta lumshe idanu ta buɗe kan ta juya ta nufi sauka, shi karan kanshi da kallon mamaki ya bita a sanin halinta bazata bi umarnin Fatima kai tsaye haka shiru ba, ko ta fara sauyawa ne… Kafadan shi yayi shrugging kan ya cigaba da cin abincin shi.

Bata jima ba se gata da food flask ta zo ta ajiye kan dining ɗin ta juya zata tafi
“ke bazaki ci bane Fauza?”

Juyawa tayi ta kalleta kawai kan ta juya ta wuce ciki.

Tana shiga ta faɗa kan kujera tana ji kaman ta fashe da kuka sbd yadda ranta yayi mugun ɓaci gashi bata fitar da abunda ke ciki ba, ita kuma haka take in har bata rama abunda aka mata ba ranta yayi ta zafi kenan da kuna.

Kakari taji me ƙarfi se kuma taji ana kiran
“ke! Ke!!”

Ta san ita kaɗai yake kira da ke hakan be sa ta amsa ba, tana kwance kan three seater taji ya turo kofan ya shigo.

“Ke! Bakya ji ina kiranki ne? Ko yadda kwakwalwanki yake a toshe haka kunnuwanki?”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected