Diddigar Kaya Complete Hausa Novel

Diddigar Kaya Complete Hausa Novel

Suna daga ɗakin Fatima ta shigo a wurin Aunty Amarya da Ammi dake bisa taburma a tsakar gidan suna cin Tuwon dare ta zauna, tace
“waii wallahi Aunty mammi na jin jiki, ciwon kafan nan baya mata ta daaɗi ɗan zaman da na yi na awanni a wurintan nan baki ga ba, komai se an yi mata”

Ammi tace
“Allah sarki, Allah dae ya bata lafiya ai kafa shine komai a jikin mutum, Allah dae ya sa kaffara ne”

Aunty Amarya tace
“Ameen Ammi, Fatima se ki dinga zuwa kina taya Asiya (ɗiyar Yayar mammi ɗin) kula da ita”

Fatima tace
“In shaa Allahu Aunty ai Mammi kaman uwa take a wurina, bari na shiga na dubo su Fa’iza mu ci abinci”

Mikewa tayi ta nufo ɗakin nasu, tana shiga suka Haɗa idanu da Faozia dake kallon kofan, ɗauke kai Fatima tayi yayinda Faozia tayi tsaki me karfi tace
“Fa’iza kin san Allah ko?”

Fa’iza tace
“me aka yi kike tambayana na san shi mana”

Faozia tace
“Daaɗina dake baki iya cin riban zance ba, ko da shike manta ma… Dama Tambayarki zan yi da munafukin ɓoye da na bayyane don Allah wanne ya fi?”

Fa’iza da bata fahimci zancen ta ba tace
“ai munafunci ko ya yake sunan shi munafunci kawai dae gwara wadda ze nuna maka a bayyane ka san dashi da wadda ze nuna maka Musa a fuska fir’auna a zuciya”

“sannan in zaka yi abu kayi don Allah da nufi ɗaya ni fa shiyasa bana son hulda da duk munafuki a duniya..” Fauza ta karasa

Fatima da ta tsaya kikam tana Kallonsu se hawaye ya fara kwaranya a fuskanta, Aunty ce ta fara shigowa ta buge Bakin Fa’iza tana cewa
“yanzu ƴar uwarki zaki Haɗa kai ana cusguna mata a gidan nan Fa’iza? Tana gayamin ina karyatata ashe da gaske ne? Fa’iza..!”

Ammi da ita ma ta shigo tayi kan Fauxa zata make tana cewa
“Ai ba ita zaki daka ba Auntynsu ita uwar iyayin nan zaki mara har se taga wuta..”

Dira Faozia tayi ta Ɗayan gefen kan Ammi ta zagayo ta fice da gudu harda bangaje Aunty goshinta ya ƙume da kofa salati duk suka saki ita kam ko waiwaye babu tayi sashen Mammi da gudu.

DIDDIGAR ƘAYA…(Mai wuyar tsincewa) wannan littafi littafin kuɗi ne..
Ze zo muku a Naira ɗari uku kachal #N300.
Acc no. 0545475847
Acc name. Fatima Muhammad Gurin
Bank name. Gt bank
Se ki tura shedar biya zuwa wannan layin
09039206763
Ko ki tura katin waya ta layin na sama tare da shedar biya ta what’sapp.
Yi maza ki biya naki ki sha karatu cikin kwanciyar hankali, ina me tabbatar miki bazaki taɓa nadama ba

Karku sake a baku labari.

Gureenjoh
DIDDIGAR ƘAYA
(Mai Wuyar Tsincewa)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.
(Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
*Kowa Ya ga zabuwa..*
And Now..
*Diddigar ƙaya… Paid*

*Shafi Na Takwas*

*PAID BOOK*

ƊANƊANO

**WANNAN SHAFI SADAUKARWA CE GAREKI AUNTY HALILLOS GWANATA KUMA MALAMATA❤️**

Karshe dae Aunty bata iya bacci ba seda Baba Alhj ya danne mata goshin aka shafa man zafi, takaici ya hana shi cewa komai, ya aika a kira mishi Faozia ɗin aka tarar bata nan sede Jaddah bata ce bata nan ba kawai cewa tayi a ce tayi bacci Dukda bata san wani laifin ta sake aikatawa ba.

Ita kuwa Faozia tana zuwa wurin Mammi ta shagwaɓe tana faɗamata abunda ya faru, Mammi tace
“Gaskiya Farhan da Faraj basu kyauta ba ai da lafiyata ƙalau babu wadda zan bari ya taɓa ki su da suke gantalinsu akwai wadda ya hana su ne?”

Cikin jin daaɗin goyon bayan da aka bata tace
“ai shine”
Mammi tace
“Faozia am ki rage nemarwa kanki magana kin ji? Bana son yadda kowa ya buɗe baki yace Faozia, Faozia ɗin nan wallahi har raina bana jin daaɗi”

Fauziyya tace
“In shaa Allahu Mammi bazan sake ba”
Mammi tayi murmushi Dukda ta san labarin kanzon kurege ne kullum haka take cewa baze hana gobe tana fita ta jajiɓo wani tashin hankalin ba.

Ƙin zuwa wurin jadda tayi wai tana fushi a lokacin da su Farhan ke bugunta jadda bata zo ta karɓeta ba kuma ta tabbatar sarai tana ji.

Asiya mammi ta kira akan ta zo ta dubo wa Fauzan abunda zata ci.
Faozia tayi Charab tace
“Mammi bari na shiga kitchen ɗin da kaina”

Har ta fita ta dawo tace
“ke fa Mammi kin ci abinci?”

Tace
“Ina ga Tea zan sha Faozia kubewa suka girka a gidan ni kuma ba so nake ba, je kiyi abunda zaki yi ke kam”

Kitchen ta wuce, Asiya dake zaune a parlorn ta bita da harara ko Kulata Faozia bata yi ba don ta jima da sanin Asiya irin mutanen nan ne da suke bari hassadar wani ya gurɓata musu rayuwa, ba tun yau ba ta fahimci Asiya bata ƙaunar ta shiyasa itama bata shiga harkarta.

Hijab ɗinta ta ajiye ta fara dube dube a kitchen ɗin Seda ta fidda duk abunda zata bukata na aikin da take son yi kan ta fara aikin, Yawan bin kawaye da take har ana dukanta duk akan girki ne tana matukar kaunar girki babu abunda yake bata nishaɗi a rayuwa irin ta ganta a katon kitchen tana girke girke, idan kaga Faozia a school ta natsu to kallon recipes take a wayan kawaye don gidansu kam ba’a abubuwan zamanin nan.

Shawarma da suka yi ɗazu har sanadiyar shi aka Chasa ta tayi guda biyu na beef, banda kamshi babu abunda ke tashi a kitchen ɗin tana yin Shawarmanta kuwa tana biski ba me yawa tayi ba ɗan kaɗan ne sosai da kidney sauce, fancy plate ta ɗauka ta zuba biskin daga gefe in a stylish way kan ta zuba kidney sauce ɗin shima a gefe ta watsa parsley a kai kaɗan yadda ya bada wani garnish na burgewa.

Shawarmanta guda biyu ta ɗauko suma ta saka su a plate ta ɗaura Duka a tray ta ɗauko ruwa masu rangwamen sanyi tare da daukawa kanta wani mango drinks ta nufi ɗakin Mammi, tana zuwa ta ajiye tray ɗin tace

“Mammi guess what I made?”

Mammi tana murmushi tace
“Ina zan sani ina zaune a nan na dae ji kamshi na tashi kuma duk hasashe na na rasa gane menene..”

Buɗe plate ɗin biski da kidney sauce tayi tana dariya cike da jin daaɗi tace
“Tadaaa..!”
Tana dariya sossai wadda ya saka Mammi murmushi tace
“Masha Allah, Kice daughter na na shirin zama Chef eyee a ina kika koyi irin wannan delicious ɗin?”

Shagwaɓe fuska tayi tace
“ba irin su bane na bi Zee koyo a gidansu kuma da nisa shine ban dawo da wuri ba su ya Farhan suka bugeni ba..!”

Mammi tace
“masha Allah, am impressed gaskiya karki damu in shaa Allah na miki Alkawari da kaina zan saka ki a catering school ƴata ta zama Chef Faoza..”

Murna Faozia ta fara harda tsalle, Mammi na ta dariya Faozia is such a wonderful child da zama da ita kaɗai ka iya saka ka farin ciki she’s so lively in har ka san yadda zaka tafi da ita, Mammi ta matsarwa plate ɗin tace
“bismillah Mammi”

“thank you bitty”
Spoon ta sa ta fara ci tana yabon hannun na Fauza a girki, itama Shawarmanta taci tas ta cinye ta sha mango juice ɗin kan ta tattare wurin ta fitar, da taimakonta Mammi taje toilet tayi duk wani abunda zata yi ta dawo da alwala, ita ta taimaka mata har ta kwanta…

Tana shirin shiga wanka se taji sallaman Baba Prof hijab ta saka, Seda ya shigo ta gaishe shi ya amsa da kulawa kan ta fice ta bar su da Mammi, ɗakin yaya farida da babu abunda Mammi ta taɓa ciki ta shiga, akan gyara akai akai hakan yasa ta nufi toilet ɗinta tayi wanka, bayan ta fito ta duba wardrobe ɗinta ta kuwa samu kayan bacci sabo dal a Leda Dukda ya ɗan yi mata yawa haka ta saka.

Seda ta ɓata lokaci mai yawa kan ta fito ta koma ɗakin Mammi ta samu Baba prof ya tafi, Har zata juya Mammi tace
“Fauza”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected