Diddigar Kaya Complete Hausa Novel
Tana kai nan ta cire hijab ɗinta ta ninke, da gudu tayi cikinsu suka fara dambatuwa, dukda kwana biyu rabon da tayi faɗa tana acting classy yau seda ta zage tayi musu duk abunda tace don bata taɓa faɗan magana ta kauce akai ba.
Tana yi tana cewa
“Da kun tambaya tun farko waye Fauxa da baku shiga sabgata ba”
Duk saida ta cika alkawarinta kan da kyar aka dagata kan su.
Taje ta ɗauki hijab ɗinta tana haki ta saka ta ɗauki sweet ɗinta ta cigaba da tsotso tare da rataya jakanta tayi mota, ko da suka dawo gida ita har ta mance ma da abunda tayin.
Chan dare tana cin Samosar da tayi bayan dawowarta da tea kawai Ya Farhan yayi sallama
“Fauziyya zo mana”
Dukda be saba mata irin kiran ba haka dae ta miƙe ta bishi ɗakin su taga yayi, a zuciyarta take masifan Allah ya sa ba aiki ze saka ta ba, tana sanya kafafunta a ɗakin ya maida kofan ya rufe, Faraj dake zaune da dorina yace
“na lura barin ki da ake shi ya sa ko yaushe kika tashi ɗauko mana magana se ki ɗauko kalar wadda ba’a taɓa yi ba, bana Tunanin ko hanyar police station baba ya sani amma wai yau a ta sanadiyarki aka zo har wurin karantarwar shi za’a daukeshi..”
Takaici ya hana farzan din cigaba da magana, Farhan yace
“Fauziyya yau zan tabbatar da na huce duk takaicin da nake kwasa akanki, yau ɗaya zan saɓawa umarnin Baba na be amince kowa ya taɓa ki ba in yi miki dukan sauke takaici, wawuya wacce bata san me ke mata ciwo ba..”
Dukda yadda zuciyarta yake bugawa, bata nuna a fuska ba, ta san sun fi karfinta kuma ihun duniya tayi anan babu me jiyo ta bare a zo cetonta gwara ta sallamar kawai su kashe ta in sun so.
“In de akan yaran da na daka ne wallahi ko gobe suka sake maimaita abunda suka yi haka zan musu, ba police ba su kawo rundunar sojoji….”
Bulalar da Farhan ya fara sauke mata cikin takaici ne ya katse mata maganar, dukan kawo wuƙa suka mata tun tana ihu har ta dena tana jiran kawai su kashe ta, har hijab ɗinta seda bulala ya yayyaga fatanta har jini yake yi..
“Tashi ki fice ko in kasheki kowa ya huta”
Farhan yayi mata ihu hawaye na zuba a idanunshi, iyayenshi yake ji wa takaici, be taɓa ganin baba prof a yanayin da ya ganshi yau ba, wai har wannan yarinya ta ja ake gayamishi maganan da ya saka shi zub da hawaye dukda be yarda kowa ya gani ba amma sun san ba karamin zafi ya mishi ba.
Da sauri ta fito tana layi, dishi dishi take ganin mammi tsaye tana kwala kiran sunanta, Sam bata san ma da wani a gefen mammin ba ta de ji tana cewa
“kama min ita… Yi sauri kama min ita, innalillahi me zan gani haka?”
Yanke jiki tayi sbd yadda duk garkuwar jikinta suka karaya suka gaza ɗaukar gangar jikinta a hannun mutum ta ji ta kan ta karasa ficewa hayyacinta.
DIDDIGAR ƘAYA…(Mai wuyar tsincewa) wannan littafi littafin kuɗi ne..
Ze zo muku a Naira ɗari uku kachal #N300.
Acc no. 0545475847
Acc name. Fatima Muhammad Gurin
Bank name. Gt bank
Se ki tura shedar biya ta wannan layin
09039206763.
Yi maza ki biya naki ki sha karatu cikin kwanciyar hankali, ina me tabbatar miki bazaki taɓa nadama ba
Karku sake a baku labari.
Gureenjoh
DƘ
15
Yana durkushe kan kafan shi ɗaya, ɗayar kuma kanta ne a kai hannunshi na patting kumatunta yana cewa
“ke! Ke!!”
Sede ina bata ma san yana yi ba.
Mammi tace
“yi sauri ɗauko ta mu tafi asibiti Faizan Farhan na da hannu a wannan abun kuma wallahi se sun ga bacin rai da basu taɓa gani ba, wani irin shashanci ne wannan?”
Da sauri ya ɗauke ta yadda yaga ran mammi ya ɓaci be so ta bi su asibitin ba don yanzu suka dawo sbd kafar ta da ya matsanta mata se kuma suka tarar da wannan, haka ta ƙi shiga gida suka juya asibitin tana kiran Baba Prof a waya.
Ba irin faɗan da likitoci basu yi ba, aka samu aka shawo kanta aka yi mata dressing ciwukanta, lokacin baba prof da Baba Alhj da jadda suka iso.
Tana kwance kaman wata innocent, sossai Jaddah ta zub da hawaye tana zagin su Farhan inda take shiga ba ta nan take fita ba, Baba Alhj bazaka ce ya wani damu ba haka nan oga kwata kwata Faizan tunda nurses suka karɓeta ya samu wuri yayi zaman shi ba don mammi da tayi magana ba ma wayanshi yake ta operating, Baba prof ne yace
Duk su koma a kawo ko zaliha ne ta kwana da ita tunda allurar da aka mata ze jima be saketa ba.
Tun suna kan hanya ya kira Farhan da Faraj akan su same shi parlornshi, suna isowa duka nan suka yi, tun kan su zauna babu zato ba tsammani ya saukewa kowannensu zazzafan mari, duk a razane suke Kallonshi ranshi sossai ya ɓaci yace
“baku da hankali ne? Kuna Tunanin duk rashin hankalin Fauza ya kai wadda kuka yi? Irin wannan duka ko a hannun hukuma iyaka tana mace in kuka yi mata illa fa? Ina ce seda na ce muku kar kowa ya taɓa ta sbd abunda ya faru? Kun tambayi dalilinta? Ko don tana da yawan neman tsokana se aka ce a komai ma ita ke da laifi?”
Babu wadda ya taɓa ganinshi yana faɗa haka, yayi sossai da sossai sbd yadda ya ga Fauxa, jadda ma ta karɓa harda Allah ya isa tayi musu, mammi ma Seda tayi nata sossai ta kuma ɗauki fushi da dukkansu, Faizan dae da Baba Alhj en kallo suka zama se daga baya baba Alhj yayi ta ba jadda hakuri.
Tace
“me ya faru ɗazu ɗin?”
Baba prof da ya zauna ya ɗan yi shiru yana Samarwa kanshi natsuwa kan yace a tausashe
“Duk abunda ya farun laifin Fauziyya kaɗan ne Dukda dae ni shi ya fi daga min hankali ba wani faɗar da suka yi ba, da farko dae ni na janyo don na san halin Fauxa na Haɗata da wata yarinyar makota a nan farkon layin ganin kullum tana wahalan samun abun hawa, to wai Fauziyyar sau biyu bata rubuta paper ba tana fita wani ke rubuta mata a madadinta, to ranan sai bata dawo da wuri ba shine yarinyar ta fara zagin ta har ta kai kaina se fauziyyar ta fasa mata baki a mota kaman yadda driver ya bada nashi bayanin, to bayan nan ne suka haɗu da ƙawayen ta wai zasu dake ta shine tayi musu dukan kawo wuƙa iyayensu kuma suka kawo min hukuma sun kuma aibata ni sun yi min kazafi wadda na Barsu da Allah zasu bada shedar shi ranar gobe”
Shiru parlorn ya ɗauka kan Jaddah da ta zabga tagumi tace
“yau na shiga uku da yarinyar nan, to ina take zuwa? Da wa take fita kuma?”
Baba prof ya kalli babanta da yayi shiru hawaye na shirin zuba mishi yace
“kar ka yi mata kuka Sulaiman, da ni da kai duk ɗaya ne haka yaranmu don an zo kamani a madadin mahaifin Fauziyya ba’a yi kuskure ba, a yinin yau na yanke hukunci akan Fauziyya wadda nake so duk ku sheda, bana bukatar shawarar kowa bayan na mahaifiyata, na yanke nan da watanni biyu zan ɗaurawa Fauziyya Aure da Faizan…”
Ɗib haka parlorn ya ɗau shiru, Faizan dae yi yayi kaman be ji ba don ya san kila karan jirgi ya fara taɓa mishi kunnen shiyasa ba ya ji da kyau, ko a imagination baze taɓa kawo wannan hadi ba bare a zahirin gaskiya.
Mammi tace
“Allah ya sanya Alkhairi, wannan haɗi shine daidai”
Baba Alhj yace
“A’a yaya, ya zaka fara wannan kwamachalar? Taya zaka fara Haɗa nitsaste kaman Faizan da fits….”
“Akul Sulaiman, in dae ba kana so ka nuna min bani na haifi Fauziyya bane babu ruwanka naka idanu, Faizan na ba Fauziyya kuma ya riga ya zauna..”
Ba don kar ace yayi rashin kunya ba da se ya tambayi baba wai wani Faizan ne yake referring to, kanshi gabaɗaya ya dau hayaƙi in kuwa baba yayi hakan ba karamin cutar shi yayi ba, me ze yi da sauran wasu? Me ze yi da ƴar giya?