Diddigar Kaya Complete Hausa Novel

Diddigar Kaya Complete Hausa Novel

“Zubair ka kasheni! Na shiga uku”

Yace
“Babe wanene wannan ɗin? Ya za’ayi ya barki cikin mota window a dage mota a rufe?”

Se a lokacin zazzafar hawaye ya sauko mata tace
“yayana ne! Kuma wallahi baya ƙaunata ko na sulen kwabo ba rufamin asiri zai yi ba, kashina ya bushe..”

“Yaya zamu yi kenan babe? Ko na saka hukuma?”

Ta zaro idanunta gabaɗaya tace
“whattt? Ka rufamin asiri ka barni da abunda ka ja mini Zubair… Na shiga uku! Gashinan zuwa.”
Tana kai nan ta kashe wayar tare da makalewa a cinyoyinta.

A jikin motar ya tsaya ya fara kiran Baba prof.

Bayan ya ɗauka cikin ladabi yace
“Baba akwai wata gagarumar matsala ce da ta tunkaro rayuwarmu wadda dole ce ta sa zan bayyana muku don idan na rufe ma na ha’inceku”

Baba prof yace
“Kowani bawa da kalar tashi kaddarar da jarabawar, ruwanmu ne mu karɓa ruwanmu ne kar mu karɓa amma idan muka karɓar mun cika wani sashe ne na imaninmu kaman yadda in muka saɓa ya zama kaman saɓawa ubangiji…. Menene?”

Yace
“baba ku zauna a parlornka ku jirani don fa idan na faɗa a waya ba lallai na gamsar da ku ba.”

Kashe wayan kawai baba yayi dama yana zaune da Baba Alhj da Jaddah ne, yana sauke wayar ma se ga mammi ta kawo musu tea kasancewar su akwai kaunar sha’i musamman wadda yaji kayan haɗi.

“Kai da waye haka? Allah ya sa dae lafiya”
Jadda tayi tambayar.

Cikin nazarin abunda ze faru yace
“Faizan ne kuma dae kaman ba lafiya ba”

Tea ɗin Mammi ta zuzzuba ta miƙawa kowa, suka fara sha suna ɗan tattauna abunda ze iya kasancewa don duk tsumayin abunda Faizan ke tafe dashi suke.

Parking motar da aka yi dab kofar baba prof ɗin shi ya sa duk suka maida hankali kan kofar gabansu na faɗi, kaman an cillo kayan wanki haka ya watso ta ta faɗi a ƙasa gashinta ya rufe mata fuska, duk tsaye suka miƙe suna kallonta.

“Faizan menene hakan? Wacece wannan ɗin”

Runtse idanu baba Alhj yayi ya sake buɗewa jiri na shirin yarda shi yace
“Fauziyya???”

Duk kallonta suka yi daidai lokacin ta miƙe tsaye tare da janye gashinta tace
“Na’am”

Da gudu Farhan da shigowanshi kenan ya tare Baba Alhj dake shirin faɗuwa amma ya fusge yayi kanta, ya fara dukanta yana cewa
“ni kike amsawa idanu a sama don tsaurin ido? Fauziyya kasheni kike son yi ki huta? A ina ya samo ki? Kalar tarbiyar shigar da muka koya miki kenan? Innalillahi wainna ilahi rajiun..!!”

Misalta irin tashin hankalin da suka shiga a sannan ɓata lokaci ne, barin ma da suka fahimci a buge take, sossai jadda ke kuka abunda ya kara ɗaga hankulansu kenan.

Baba prof ne ya hana a taɓa lafiyanta, yace
“Aisha kamata ku je wurinki, karki bari kowa ya fahimci halin da take ciki zamu yi zama in an watse bukin nan, amma ko kofar parlor ban yarda ta taka ba”

Da kallon takaici da kyama kawai yake bin ta har Mammi ta cire hijab ɗinta ta rufe ta don se layi take yi a haka kuma duk wadda ya ganta se a ajiye alamar tambaya, ita kuma ta yafa mayafin kayan ta da ta ɗaura a kai ta rungumeta suka wuce cikin gida. Allah kaɗai ya san irin mazan da ta bi da irin surartan nan, haka dae babu daaɗin rai aka kira likita ya zo ya duba Baba Alhj da jikinshi ke neman yin tsanani ana gwadawa kuwa jininshi yayi mugun hawa.

Jadda ma jininta se da ya hau bata taɓa zato ko tsammanin hakan daga Fauza ba, yarinyar karama waye yayi influencing nata haka?

Rai babu daaɗi aka watse haka bukin auren ya rage armashi don abunda ya tunkaro su in basu yi da gaske ba akwai babbar matsala.

Haka mammi ta saka ta a gaba bayan ta kwantar da ita tana kallo hawaye na zuba mata, wani irin tausayin rayuwar yarinyar na rufe ta, me ta nema ta rasa? Menene ya tura ta ga wannan halaka haka daga gidan mutunci? Mammi ta hana kowa kusantar ɗakinta yayinda Ko motsi Fauxa bata yi ba se washegari da rana ya gama fita, amai da ciwon kai ya tasheta.

Mammi na zaune kan sallaya ta idar da wahala lokacin sha ɗaya taga tashinta da gudu zuwa bayi, da kallo ta bita har ta ɓace, yadda ta kwana bacci haka duka ahalinta suka kwana kan sallaya suna mata Adu’ar shiriya.

Ko da ta fito zata sake komawa ta kwanta mammi tace
“Fauziyya”
Ta amsa ba tare da ta iya ɗaga idanu ta kalleta ba.

“Koma ki watsa ruwan zafi”
Komawa tayi bayin, bata da wani tunani kuma da zata yi tunda abunda ya faru ya riga ya faru, kafin ta fuskance su ne take jin tsananin tsoro amma yanzu da bayan Kowa ya sani kunya ne ke ɗawainiya da ita.

Mammi da kanta ta aika aka ɗauko mata kaya, ta sa aka hada mata abinci aka kawo har ɗakin, sadda ta fito ta shirya mammi ta mata nuni da tray ɗin, haka ta janyo ta ci sbd yunwa dake dawainiya da ita, rama sallolin kanta tayi duk abubuwan nan bata yarda ta Haɗa idanu da mammi ba sbd kunya.

Bayan ta idar ta gaida mammi tana wasa da kasan hijab ɗin nata.

Mammi ta amsa kan tace
“Fauziyya”

“Na’am mammi”

“Fauziyya kin san irin rayuwar da kika jefa kanki kuwa?”

Kanta na ƙasa hawaye ya fara kwarara bisa fuskanta tace
“mammi Adu’a Zaku yi min, nima ban san me yake damuna ko meyasa nake fadawa halaka bayan na sani ba, wani lokacin kasa fahimtar kaina da rayuwa ta nake, chan kasan zuciyata bana jin daaɗin hanyar da na hau sai de wani zuciyar na tirsasani ƙarbar hakan ta wani fuska…”
Kuka ne ya ci karfinta.

Mammi ma hawayenta na tsananin tausayin Fauzan ta share, tace
“ɗauko Alqur’ani ki karanta Fauziyya”

Mikewa tayi tayi yadda mammi tace, tayi karatu har azahar suka yi salla tare, kan mammi ta sa ta sake kwanciya.

An yi walimar Fatima Dukda sun fahimci armashin auren ya ragu sossai sai de babu wadda ya san dalili washegari aka ɗaura aure aka yi saukar Qur’ani.

Ko kofar ɗaki kaman yadda Baba prof yayi umarni Fauza bata taka ba, ta ci abinci tayi ibada se tayi bacci, duk tunani ya fara cin karfinta ita yanzu ko wayanta bata san hannun da yake ba, taji mammi na maganar Amarya zasu kai wani sati kan su tare don haka daga washegarin ɗaurin auren mutane dayawa suka watse.

A daren Ammi ta zo ta sashen mammi daga bakin kofa ta tsaya tace
“ke Fauziyya! Tunda ba a nan aka binne cibiyarki ba ki tashi ki wuce mu tafi, tun aka fara hidimar nan neman duniya na yi miki babu wadda ya iya buɗe baki ya ce min ga inda kike? Meyasa ne ake nema se an tauye min hakkina a matsayinki na ƴata kaman yadda aka tauye min sauran hakkokin nawa? Me kuma aka ce kinyi wannan karo?”

Kanta ta ɗago tace
“Ammi kiyi hakuri”
Ammi ta aika mata da wani kallo tace
“ban gane ba? Kinga tashi mu tafi mayi maganar kaman kowacce uwa da ƴa a ɗaki”

Mammi tace
“baba prof yayi umarni akan ko kofa be amince ta taka ba har se ya neme ta”

Wani irin kallo Ammi ke mata
“wani ta kashe ko mene?”

“Wannan kuma shi zaki tambaya Ammin su”

Neman tada zaune tsaye take wai baba Alhj ya ki ce mata komai, Jaddah ta ƙi ce mata komai sannan yanzu zata zauna da yarinyar ta ace ba haka ba? Akwai wadda ya haifa mata ne..

Baba prof be so hankalin kowa ya dawo kan abun ba amma saida Ammi ta janyo hakan Dukda yadda Fauza ke hanata maganan.

A take kowa ya san akwai abu a ƙasa, hakan tasa ya kira meeting kawai.

Kowa da kowa har da Amarya ta hallara, babu wani bare duk mutanen gidan ne.

Kai tsaye ya buɗe taro da Adu’a kan ya fara magana akan jarabawar yana misalai da magabata akan dole Allah ze jarrabeka ta hanyar ‘ya’yayenka wani dukiya wani mata babu yadda babu kaman yadda mahaifin Annabi Yusuf annabi yaqub yake annabi amma ‘ya’yanshi suka so halaka ɗan uwansu, kaman yadda annabi nuhu yake annabin Allah amma ɗan shi ya fita yana saɓawa Allah har Allah ya halaka shi tare da sauran masu saɓo, misalai dae kala kala.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected