Diddigar Kaya Complete Hausa Novel

Diddigar Kaya Complete Hausa Novel

Hannu ta sa ta karɓa ta buɗe, kasa ɓoye excitment ɗinta tayi tace
“isn’t it that necklace..?”

Wadda take kallo jiya har yake cewa ze mata kyau.

Murmushi ya saki ganin ta saki ranta, ta mishi godiya.

Zama yayi a gefenta suna hira jefi jefi, duk yadda suka so su hanata tafiya a washegarin tace ita sam gida zata koma.

Duk abunda take chan Kasar zuciyarta bakin ciki ne fal na kayan maye da ta sha, ga sallar asuba gari ya gama wayewa, se istigrafi take yi haka dae Zubair yayi ta lallaɓata yana yaudararta bata yi wani fushi mai nisa da shi ba..

Washegari da safe da kanshi ya kaisu har Airport ya mata sayayya mai yawa ya hada da kuɗi, duk da ya burgeta, sai de fa bata nuna ba.

Sauri sauri ya shigo Airport ɗin don shi ze tuƙa Max Air ɗin zuwa birnin Yola daga Abuja, gashi ya so yayi letti, a cikin jirgin ya haɗu da sauran crew ɗin da kuma wadda ze taimaka mishi suka gaisa, he supposed to be a mazauninshi tunda har an soma shiga amma se ya tsaya daga bakin kofan, waya yake amsawa lokaci lokaci ya kan ɗaga idanunshin nan ya kalli masu shigowa ɗaya bayan ɗaya.

Gudu gudu suka karaso don ana final announcement ne, Sakina ce a gaba sai Rahama kan ita, loggage ɗinsu bai da nauyi so kowacce na riƙe da nata ne a hannu, Sakina ce ta fara wucewa ta mika ticket ɗinta, aka bata na seat number ɗinta ta shige, rahama ma ta shigo tayi hakan sai Fauza ta sanyo kafafunta cikin jirgin….

*Toh Alhamdulillah! Free pages sun kare saura ni daku da kuka biya paid, na san kaunar da kuke yiwa labarin ne ya saka ku nuna wannan soyayya sai dai har yanzu ina kara jaddadawa ba zan san kuna kaunar littafin ba idan har baku comment, ni karan kaina ba zan ji kwarin gwiwar yi muku typing ɗin ba due to squeezing time kawai nake nake yi don ina aiki, bani da enough time na kaina, sannan typing in kun ga kun samu da rana to shikenan amma ka’ida sai dare in shaa Allah zan din ga yi don nafi samun time between magrib, isha. Looking forward for ur comments and love

 

DIDDIGAR ƘAYA…(Mai wuyar tsincewa) wannan littafi littafin kuɗi ne..
Ze zo muku a Naira ɗari uku kachal #N300.
Acc no. 0545475847
Acc name. Fatima Muhammad Gurin
Bank name. Gt bank
Se ki tura shedar biya ta wannan layin
09039206763.
Yi maza ki biya naki ki sha karatu cikin kwanciyar hankali, ina me tabbatar miki bazaki taɓa nadama ba

Karku sake a baku labari.

Gureenjoh

12

Daidai tana sanyo kafa shi kuma yana Juyawa, an tambayeshi wani code da se ya duba paper ɗin don be riƙe ba, har ta gama ta wuce seat ɗinta chan karshe be dawo ba.

“Ke kinga wani haɗaɗɗen captain da ya tafi da ni? Wlh ya haɗu karshen haduwa ina ma zan samu ko phone number ɗinshi ne”
Rahama dake kusa da ita ne ke maganan cikin koɗa kyaun wadda take magana a kai da ita bata sani ba.

Tace
“ni ban ga wani captaina ba, kuna da matsala ai ku kam”
Ta faɗa jin sakina ma ta karɓa tana taya rahama gulman wadda bata gani ba ita kam.

Har suka sauƙa yola basu daina maganan captain ɗin nan ba, Sakina Dan Tsoho hotel tayi don chan zata karasa satin da tace zatayi a gida, yayinda rahama tayi gida don duk iyayenta basa ƙasar, cab ne ya sauke ta kofar gida ta sauka tare da miƙa mishi kudinshi ta Janyo loggage ɗinta tayi ciki.

Harabar gidan nasu tsabtsab ba kowa ta tabbatar yanzun haka suna school tunda kwata kwata karfe goma ne na safe, sashen jadda tayi direct a parlor ta taddata kan sallaya ta idar da walaha tana tasbihi, da gudu ta zo ta faɗa jikinta tayi shiru tana sauke numfashi.

Ɗago fuskanta Jaddah tayi cikin farin cikin ganinta tace
“oyoyo oyoyo! Maraba da mutanen Gombe kune da safen nan?”

Kai kawai ta gyaɗa ta sake mayarwa tayi lamo, Jaddah ta ɗago ta gabaɗaya tana kallonta
“lafiyan ki kuwa? Ko baki da lafiya ne kike hawaye?”

Hannu ta sa ta share kwallar tare da karya wuya tace a shagwabe
“kewarki nayi Jaddah na”

Dariya Jaddah tayi tace
“to ba gashi kin dawo ba? Ba shikenan ba? Oya tashi je kiyi wanka ki sauya kaya bari na sa zaliha ta sama miki abunda zaki ci”

Mikewa tayi ta nufi ɗakinta tana cewa
“ya yi yaji pls”
Tana shiga ta jefar da Akwatin tare da dogon hijab da daga Airport ta sanyo shi zuwa gidan, ta shige toilet ta sakarwa kanta ruwa tana lumshe idanu, se yanzu take jin wani sukuni na rufe ta, lallai ta zalunci ahalinta tayi fatali da tarbiyar gidansu, tunda ta dawo daidai take jin rashin daaɗi a zuciyarta na abunda ta aikata amma fa wani zuciyar na kwaɗaita mata daaɗin shi.

Bayan ta fito tayi shafe shafenta ta janyo tsarabar da Zubair ya Haɗa ta dashi, chocolates ne daban daban se wasu designers perfume guda biyu se, hoodie ash na kamfanin Fendi.

Boyesu tayi a wardrobe ɗinta kan ta zaro riga ƙarami fari da wando navy blue ta saka, wandon a kaurinta ya tsaya ya kuma matse ta ya fitar da duk wani shape ɗinta, gashinta ta taje ta sake shi, tana shirin kwanciya Call na Zubair na shigowa wayanta, da sauri taje kofa ta rufe da key kan ta dawo ta haye gado tare da shigewa bargo ta amsa.

A hankali suke waya tun bata saki jiki ba har ta sake saboda ya iya hira da sanya dariya ga kalamai, ta shagala sossai se jin bugun kofa tayi da sauri ta ce mai tana zuwa ta kashe wayar tare da boyeta cikin Rigan pillow ta dirka taje ta buɗe kofan.

“Jadda tace ki fito ki ci abinci kar kiyi bacci baki ci ba”
Cewar zaliha.

Bayan zaliha ta bi suka fito tare, kan kujera ta zauna bayan ta ɗauki abincin daga cikin tray da zaliha ta shirya ta fara ci, Jaddah na bata labarin irin kewar ta da suka yi gidan yayi shiru sossai a kwana biyu da bata nan.

“Ashe ana kewata amma in ina nan kowa ya buɗe baki Fauxa kaza Fauxa kaza!”

Jadda zata yi magana wayanta ya fara ruri ta duba tace
“oh kai kuma se yau ka tuna dani”
Ko bata faɗa ba Fauxa ta san waye don haka ta maida kanta kan TV Dukda wa’azi ne gwara ta ji da ta ji zancen da zasu yi.

Bata san ma jaddar ta kashe ba saida taji tana cewa
“Fauziyya yi sauri gama ki je ki sharewa Yayanku ɗaki ki wanke mai toilet yadda kwana biyu be zon nan ba na tabbatar yayi kura kuma kin san shi da rashin son datti, yace min ya shigo garin gida ne dae ze ɗauki mintuna masu yawa kan ya karaso akwai abunda ze yi”

Haɗe gabas da yamma tayi kaman zata yi kuka tace
“Jaddah ina Fatima da ni zan mishi aikin ɗaki yau? Allah ya kyauta wlh kin dae san kap rayuwata ban taɓa taka kafa ɗakin shi ba haka kawai ba zan fara yau ba…”

“Fitsararriya ajiye abincin nan ki wuce kan in Haɗaki da abincin in take”
Cewar baba Alhj da yake shirin shigowa sallamar da ze yi ma be yi ba sbd abunda yaji Fauzar na faɗawa Jaddah.

Da sauri ta miƙe tsaye
“ban hanaki saka waennan kayan ba?”

Da sauri ta wuce ɗaki tana tura baki seda ta shiga ta fara kunkuni, kaman zatayi kuka haka ta sanya hijab kato har ƙasa ta fito, ta samu baba Alhj na cewa Jaddah

“Mama ni fa ba tsanar ta nayi ba, halayen ta ne bana so, a yadda Fauziyya ta ɗauko rayuwarta wlh bata so gamawa da duniya lafiya ba, tun da ta sanya kafa ta bar sashena bata sake zuwa ko da gaisheni bane wai dani uban ta zatayi gaba? Har Fauziyya ta bar garin nan bata iya zuwa ta min sallama ba se a bakin mamanta nake ji?”

Kanta ƙasa tace
“key!”

Jadda tace
“Kin san inda nake ajiyewa ai”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected