Diddigar Kaya Complete Hausa Novel

Diddigar Kaya Complete Hausa Novel

DIDDIGAR ƘAYA…(Mai wuyar tsincewa) wannan littafi littafin kuɗi ne..
Ze zo muku a Naira ɗari uku kachal #N300.
Acc no. 0545475847
Acc name. Fatima Muhammad Gurin
Bank name. Gt bank
Se ki tura shedar biya ta wannan layin
09039206763.
Yi maza ki biya naki ki sha karatu cikin kwanciyar hankali, ina me tabbatar miki bazaki taɓa nadama ba

Karku sake a baku labari.

Gureenjoh

https://chat.whatsapp.com/BjpWJdHnjtpKNK4iCeqNwh

34

Washegari

Kaman yadda ya faɗa da safe ya fito a shirye, sashen Ammi ya fara zuwa suka gaisa sbd weekend ne su baba ma suna gida, ya jima sossai anan kan ya musu sallama ya nufi sashen iyayenshi suma duk ya musu sallama akan zasu wuce yau, duk Kallonshi suke da mamaki saide basu ce komai ba se farin ciki dake shimfide bisa fuskokinsu aka ce tsakanin mata da miji se Allah to shine suke kallo.

Daga nan sashen Jaddah ya wuce, a parlor ya sameta suka gaisa tace
“Ba dae tafiya ba? Na ganka shirye tsab kaman sabon ango”

Tsadaddiyar Murmushi yayi yana kallon jikinshi don be ga wani sabon shiga da ba sabonshi bane, sanye yake da wani ɗanyen bowel sky blue an mishi dinkin boda ya zauna mishi sossai, hula zanna a kanshi ya murza ta da kyau se agogo da wayoyinshi dake a hannunshi banda kamshinshi dake baza parlorn babu abunda kake ji.

“Kika sani ko zan mai dake ɗakinki a yau ɗin?”
Ya bata amsa cike da tsokana, haɓa ta rike tace
“zancen kake nema ai ni na jima da raba gari da kai bana auren nan, ina ni ina zama da miskilin miji ka fi mahaukaci ban haushi? Barni in lallaɓa da su Fahad yauwa…!”

Yana murmushi yace
“ni fito mun da matata mu wuce”

“wai ina Zaku wuce?”

“Dama daga ina muka fito Jaddah? Na kula na zauna jiran ki se mun yi missing flight”
Tsam ya mike ya nufi ɗakin Fauza da kallo baki sake Jaddah ta bishi kan ta fara gyaɗa kai tana jiran ganin ikon Allah.

Tsaye take a gaban madubi sanye da zani da riga na wata Tsadaddiyar super, kanta ba dankwali tayi loose parking wadda ya fitar da wasu daga jikin gashinta ya sassakesu bisa wuyanta da fuskanta, tsayawa yayi Chak hannayenshi zube a aljihu yana kallonta cike da so da ƙauna, ji yake kaman ya tsaga kirjinshi ya sakata ya huta da azababbiyar kaunarta.

Takawa yayi a hankali ya nufe ta ganin yadda take kokawa da zip, bata ji zuwanshi ba se jin hannayenshi masu taushi tayi cikin nata, lumshe idanu tayi sbd yadda sanyinsu suka ratsa har ɓargonta ta shaki kamshi me cike da natsuwa wadda ba tantama daga gareshi ne sbd ita bata taɓa jin irin turarenshi wurin kowa ba, haka suke ne ko combination da yake na musamman ne suka bada wannan sassanyar kamshin bata sani ba.

A hankali ta buɗe idanun ta sauke su tarrr bisa kamilalliyar fuskar shi ta mirror ɗin..

“May I?”
Yayi tambayar yana nuna zip ɗin da idanu, kai ta gyaɗa tare da ɗan murmushi.

Zip ɗin yake ja mata idanunshi kafe a fatar bayantan, bayan ya gama se ya kara taku ɗaya ya haɗe gab ɗin dake tsakaninsu ya sanya hannu ya zagaye ta tare da ɗaura haɓarshi bisa kafadar ta ajiyar zuciya duk su biyun suka sauke.

“Good morning yaya”

Seda ya ɗan juya idanu kan yace
“morning but the Yaya is not accepted, bana so a bani wani sunan precious”

Murmushi kawai tayi, yace
“an gama da zip, then what?”

Ba tare da ta ce komai ba ta nuna mishi sarka dama ta saka dankunne, hannunshi kawai ya miƙa ya ɗauko gashin da suka zazzame yake ɗan tattarewa da hannunshi yana mai dasu sama kan ya fara saka mata sarkar idanunshi kan wani baƙin tawadar Allah dake ɗige daga ƙasan kunnenta, Sam bata ankara ba taji saukar peck a daidai wurin, bugun zuciyarta seda ya so tsayawa.

Sake komawa jikinta yayi yace chan ƙasan maƙoshi da idanunshi da suka fara sauyawa
“am done baby, sai me?”

Tace a hankali itama
“sauran ba lallai ka iya ba, let me finish”

Be saketa ba ta dauki wani silk black rowsleeke ta mishi ɗaurin Zahra buhari, yana ta kallonta, da idanu ta nuna mishi blue and black embroid lafayarta dake ajiye bisa gado, da kanshi yaje ya ɗauko zata karɓa yace

“let me do it for you sweetheart”

Ta ɗan wara idanu tace
“in ba kana so in je in faɗi bane Yaya bani kayana in ɗaura”

Ɗan dariyar maganar yayi yace
“Haba yarinya tsawon rayuwata tun fa da na tashi nake ganin Jaddah da mammi na ɗaurawa in har ban ɗauka yadda ake ba kenan kwakwalwar kifi gareni”

Dariya sossai ya bata wadda seda ta dara, gyara tsayuwar ta tayi tana jiran ganin ikon Allah, tsab kuwa ya ɗaura mata lafayar ya zagayeta dashi, ba karamin kyau tayi ba.

Kallon madubi tayi tana murmushi kan ta ɗaga mishi hannu alamar jinjinawa ya taɓe baki irin ba na faɗa mikin nan ba, bangles ta saka ta ɗauko black handbag da black shoe ta saka, hannunta ya riƙe yana kare mata kallo.

“Kin yi kyau kaman Fure precious pearl”

Tayi murmushi tace
“thank you yaya, and kaima ka yi kyau”

Murmushi suka sakarwa juna kan suka fito, Jaddah baki sake take Kallonsu, Fauza ta kasa ce mata komai se shine ya sallameta, har suka fice bata ce komai ba seda suka fita ta saki murmushi, lallai a gaida yaran zamani.

Daga mota ya jirata ta shiga wurin Ammi sama sama, tayi ta saka mata albarka kan ta wuce wurin mammi itama albarka ta sha, ta shiga wurin sauran matan a tsai tsaye daga nan ta yada zango wurin iyayenta a parlorn baba prof, nasiha suka mata kan suka sallameta.

Fitowa yayi musamman ya buɗe mata gidan baya ta shiga ta zauna, kan ya zagaye ya shiga shima bayan ya zauna tare da sanya hannunshi cikin nata, kan kafadar shi ta kwantar da kanta tana kallon gidan tana tuna irin rayuwar da tayi cikinshi zuwa yanzu, Farhan ne ke tuka su har zuwa Airport kan suka yi sallama.

Ko da suka isa ma be barta ta gyara gidan da yayi kura ita kaɗai ba, a tare suka yi aikin tsab suka kamalla suka yi girki marar nauyi kan kowa ya wuce yaje yayi wanka, kusan a tare suka fito ta shirya musu abincin a ƙasa suka zauna suka ci, bayan ta tattare wurin ta nufi komawa ɗaki ya sanya hannu ya dawo da ita jikinshi yana gyara kwanciyarshi yadda itama tayi lub bisa kirjinshi yace

“Babe zan yi tafiya gobe it’s been a while da na ba aikina hankali hakan kuma yana so ya samar min matsala”
Ya karasa yana shafa gashin kanta.

Da sauri ta ɗago kai tana Kallonshi Rau rau tayi da idanu, ya san me take tunani ko bata furta ba, shafa kumatunta yake a hankali kan yace
“da haka kowacce mace ta saba, nan ɗin gidanki ne babu abunda ze kama ki kinji? Sannan u have to catch up with ur studies, zan samar miki driver kan na koya miki driving ɗin”

Ajiyar zuciya ta sauke tana me komawa ta kwantar da kanta, a hankali tace
“is it outside country?”

Yace
“yeah…”
Ganin zata sa mishi kuka ya saka shi kara bakinshi bisa kunnenta ya fara zuba mata kalamai da suka kusa sakata sakin murmushi ba tare da ta shiryawa hakan ba.

Da yamma likis suka fita tare yayi mata sayayya har da sabuwar waya ya saya mata me dankaren tsada tayi ta murna kuwa.

Washegari da sassafe ta tashi ta Haɗa mishi breakfast bayan ta gama taje ta watsa ruwa tana mamakin yadda be takura ta ba da ta tuna mishi da alkawarin da ya ɗauka na baze nemeta ba se in ita ta amince.

Sanye da doguwar riga orange nd black na kanti ta fito, tayi kyau sossai tana shirin knocking mai kofa ya fito sanye cikin uniform ɗinshi da yayi mugun amsarshi, kan ta motsa yayi hanzarin rungumarta yana me bata peck a kumatu yace
“Good morning my moonlight”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected