Diddigar Kaya Complete Hausa Novel
“Ammi! Baba Alhj basa ƙaunata Ammi, Ammi don Allah kiyi wani abu kar su kasheni tun kwanana be ƙare ba! Ammi wallahi na tsane sa Ammi bana sonsa bana ƙaunarsa, ki tausaya min Ammi..!”
Shafa kanta Ammin take cikin baƙin cikin da yake daskare bisa zuciyarta, in akwai wadda ta tsana a rayuwar nan To mahaifiyar Faizan da Mahaifinshi me ze sa komai na rayuwarta da ahalinta se da umarnin su za’a aiwatar?
Allah kaɗai ya san irin zaman da suke yanzu da mai gidanta duk saboda su, me yasa ne ita bata da ƴanci a nata gidan da mijinta? Me suka fi su? Kuɗi ko suna? Me yasa Sulaiman a ko yaushe umarnin Prof shine gaba da na kowa? Ina soyayyar da Jaddah ke ikirarin tana yiwa Fauziyya ɗin?
“Fauziyya kiyi haƙuri, duk yadda zan yi wurin ganin na hana aiwatuwar wannan aure na yi sede babu nasara sakamakon hakan ma aurena rawa yake, ki daure zuciyarki ki bari ayi auren amma ba zan taɓa yi miki dole ki zauna ko kiyi biyayya ba… Wannan karo ma Aisha tayi nasara a kaina”
Sakin Ammi tayi ta sake mikewa ta fice da gudu, idanunta a rufe suke mafita kawai take nema, sashen Jaddah ta shiga a gigice Sam bata lura da mutanen da suke wurin ba, ta fara cewa
“Zan kashe kaina! Wallahi tallahi zan kashe kaina…. Duk ranar da aka yi Adu’ar aurena da Wannan azzalumin ina me rantsuwa zan mutu! Sede a kai gawata ɗakin sa.. Ku gafarceni Jaddah…”
Natsatsiyar muryar da take bayyana fushi da wani irin ciwo ne ta ratsa kunnuwanta, irin muryannan na no nonsense, muryar da ta tsana fiye da na kowa da komai a duniya, sautin da take jinshi kaman saukar aradu a kunnuwanta da ma gangar jikinta…
“Ka ji ba Baba? Ban taɓa yi muku jayayya ba a rayuwata, ban taɓa sauya fari zuwa baƙi ba idan har ku kuka furta Cewar farin ne, sau ɗaya dae ku dubi Allah karku tilastani yin abunda ba zan iya ba, zan iya shiga wuta aka yi min dole wannan aure saboda ba zan iya adalci tsakanin ta da Fatima ba, above all that baba bana fatan Haɗa jini da fasiƙa…! Idan har aka ɗaura wannan aure an cutar da ni da iyalina…”
Sauƙar gigitaccen mari ne ya hana shi ƙarasawa.
Jajayen idanunshi ya ɗago ya zuba mata na mintuna ba tare da ya iya cewa komai ba, karon farko da wayaunshi kenan da mahaifiyarshi ta sa hannu a kanshi duk akan wannan annoban, miƙewa yayi a zuciye ya fice kaman kububuwa…
“Menene hujjar ki na ƙin wannan aure?”
Jaddah ta jefa mata tambayar karon farko tana kallonta.
Shiru tayi tana kuka sossai don Kalmar fasiƙa da ya jefe ta dashi har tsakiyar zuciyarta take jin zafi da raɗaɗin shi.
“Baki da hujja? To fitar min daga ɗaki”
Kallon ban yarda Jaddahta bace a zaune anan take jefa mata kan ta yi baya baya ta fice da sauri tana kuka.
Dafe kai Jaddah tayi cikin jin ciwon wannan abubuwa da suke faruwa a cikin zuri’ar ta, idanunta ta kai kanshi yayi shiru cikin nazari da tunani, chan ya ɗago ya kalli Jaddah cikin girmamawa yace
“kwarai raina a ɓace yake kuma a ƙuntace hajiya! Ban taɓa yin abunda na muzanta ba irin wannan kab tarihina zuwa matsayin da na taka a yanzu, na kan Haɗa auren maƙota ma su karɓa cikin farin ciki bare na ƴaƴan cikina..”
Shiru ya ɗan yi kan ya kalli Mammi yace
“Ki sanar da ɗanki daga yanzu har a ɗaura auren nan idan na saƙe jin muryarsa da sunan mujadala da auren nan na yafesa har Abada!”
A razane duk suke kallon shi, kwarai ranshi ya ɓaci da wannan lamarin tunda har Baba prof ze iya furta kalma irin wannan.
Miƙewa yayi ya fice ba tare da ya sake cewa komai ba, a maimaikon yayi sashensa se ya nufi sashen ƙaninsa Sulaiman, sama sama yake amsa sannu da matan da suke daga farfajiyar har zuwa harabar na gidan Sulaiman suke mishi har ya isa zuwa parlornshi, da sauri Baba Alhaji da yake shirin cin abinci ya miƙe tsaye yana furta
“Yaya! Ai da ko a waya ka ƙirani ba se ka zo da kanka ba!”
Daga tsayen hannayenshi goye a baya yace cikin natsuwarsa na tsantsan ilimin addini
“Ba buƙatar hakan Sulaiman saboda ina so ka san saƙon me muhimmanci ne, ina so ka sanar da Fauziyya idan har kai ka haifeta na sake jin magana makamancin wadda ta zo dashi yanzu sashen hajiya ka yafeta wa duniya har Abada!”
Da sauri ya ɗaga kai ya kalli yayan nashi zuciyarshi na bugawa, dukda maganan yayi mishi tsauri sede zasu iya kaiwa ko wani mataki domin ganin mutuncinsu be zube ba kaman yadda ƴar wajenshi ta so zubarwa, mutuncin da tun kan a auri mahaifiyarta yake wanzuwa a idanun mutane..
“Kayi hakuri yaya in shaa Allah hakan ba ze sake faruwa ba”
“Allah ya sa!”
Baba prof ya faɗa yana Juyawa ya fice a lokaci ɗaya yana amsa saida safen da Baba Alhajin ke yi mai.
Ya jima bayan ya fita harabar gidan yana safa da marwa, kan ya nufi kofarshi bayan ya sauke ajiyar zuciya mai nauyi…!
***Shin ya kuka gani? Menene hasashenku kan wannan sabon littafi? Su waye ne waennan ahali? Me yake faruwa a cikin wannan gida? Menene musababbin tsanar da suke yiwa juna? Meyasa kowa ya buɗe baki da kalmar fasiƙa yake jefan Fauxa? Wani irin zama zasu yi bayan Haɗa Wuta da Auduga inuwa guda? Akwai fa’ida a wannan aure ko babu? Za’a daura ko kuwa?***
Pls waenda suka fara biya should dm me sbd in saka su paid group.
One more thing comment matters pls, ba zan zauna ina wasting energy wurin typing ku ki yin comment in ji daaɗi ba, so show some love with ur wonderful comments
Duk ku biyo ni a cikin wannan littafi nawa me suna DIDDIGAR ƘAYA…(Mai wuyar tsincewa)
Ze zo muku a Naira ɗari uku kachal #N300.
Acc no. 0545475847
Acc name. Fatima Muhammad Gurin
Bank name. Gt bank
Karku sake a baku labari.
Gureenjoh
DIDDIGAR ƘAYA…
(Mai Wuyar Tsincewa)
بسم لله الرحمن الرحيم
FATIMA MUHAMMAD GURIN.
(Gureenjo)
ADABI WRITERS ASSOCIATION
Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
*Kowa Ya ga zabuwa..*
And Now..
*Diddigar ƙaya… Paid*
*Shafi Na Ɗaya*
*PAID BOOK*
ƊANƊANO
**WANNAN KARO COMMENTS ƊINKU NA DA MATUKAR MUHIMMANCI SOSSAI***
Idanunta da gabaɗaya suka jeme suka kumbure suntum har suka sauya mata kamanni ta sake saukewa kan agogon ɗakin karo na ba adadi, hasken dake ratsowa daga window ɗin ya bata damar kallon lokacin, karfe 12:30 na dare yunƙurawa tayi ta miƙe zaune tana jin kanta na mata wani irin nauyi kaman an ɗaura mata dutsen dala.
Idanunta ta kai kan handbag ɗinta cikin tsananin nazari da damuwa kan ta janyoshi ta zaro wani farin gora ta gimtse cikin hannunta, ɗakin su ta bi da Kallo, ɗakin dake ɗauke da rabi da kwata daga cikin tarihin rayuwarta, duk cikin waenda suke kwance babu wacce zata ce sun yi kusa kusa duk en uwan nesa ne waenda suka zo bukin nan da bata taɓa hasashen yiwuwarsa ba seda taga wankin hula na shirin kai ta dare, kai tsaye zata iya cewa biyar daga cikin ahalinta na ɗakin suna wurin mahaifiyarsu da itama tun zancen ya tashi basu da sukuni.
Ƴar uwarta kuma da suke ciki ɗaya ta ƙaura wa sashen sbd rashin son hayaniyarta, cikin dauriya ta miƙe tsaye jiri na shirin yar da ita, a saɗaɗe ta nufi kofa ta buɗe ta fice, babu kowa a tsakar gidan sede tana iya kallon haske daga sashen mahaifinta alamun idanunshi biyu har yanzu, hannunta har rawa yake wurin cire sakatar ƙaramin gate na sashen nasu ta fice tsakar babban gidan nasu dake ɗauke da sashuka masu ɗan dama.