Diddigar Kaya Complete Hausa Novel
Kau da maganan Fauxa tayi don be shafe ta ba, anan ta kwana ma yau..
Washegari Monday ko aiki ɗaya bata yi ba da taje school ma babu abunda ta rubuta se surutu da neman magana, a ranar Ammi ta dawo itama Seda tayi faɗan hannun nata sede baba Alhj be ce komai ba.
Bayan 2days ta ɗan samu sauki ta cigaba da aikinta, zuciyarta kuwa na kiyasta mata yadda zata rama abunda ya mata sbd ta sha wahalan qunan sossai.
Yau tana kwance bisa kujerar Jaddah tana danna ƴar karamar wayar jaddahn sbd ita ba kaunar kallon tashoshin wa’azuzzuka da shi kaɗai suke dashi gabaɗaya gidan take ba, jaddah ta fito rike da tray tana kallonta tace
“Fauziyya don Allah miƙawa Faizan abincin nan kinga yaran duka suna wurin Ibrahim(baba prof)”
Haɗe rai tayi tace
“Jaddah eyyah ki jira su in sun dawo su kai mishi”
Jaddah ma rai ta ɓata tace
“zan saɓa miki wlh Fauziyya, ki wuce ki tashi ki kai in dodonki ne se ya cinye ki, in kuma baza ki je bane ki gayamin”
Hawaye ne ya cika idanunta, ita ba mikewa take son yi ba don ko da yaran suka je wurin baba prof da be ganta ba seda ya aiko fakiha tace mata tace tayi bacci idan kuwa bata ce haka ba se ta kirɓa ta in aka dawo sake kiranta, gashi yanzu Jaddah zata saka ta kaiwa wannan azzalumin abinci.
Mikewa tayi ta ɗauki tray ɗin da Jaddahn ta dangwalar ta fito, shiru tayi tana tunani, in ta taɓa ji da kyau Jaddah ta taɓa maganan rashin son yajinshi sbd muguwar ulcer ɗinshi ko yaya ya ci yaji se ya kwanta, murmushi ta saki taje kan kujerun tayunsu ta ajiye tray ɗin da gudu ta koma gidansu taje ta fara binciken drawer ɗinta akwai wani yaji me zafi da ta daka ranar girkin Amminta sbd an yi mata dole daka yajin shinkafa da waken, kowa da wahala yaci yajin sauran ne ta kulle ta boye a sif ɗinta.
Da gudu ta dawo ta buɗe miyan kubewa danyen ta juye duka, cokalin da ta biya ta ɗauko a kitchen ta saka ta juya kan ta ajiye shi a wurin, ta dauki abincin ta nufi sashensu, a gaban site ɗin ta kalli Haɗaddiyar beymach ɗinshi baƙi siɗik se ɗaukar ido yake da yayi parking a wurin, baki ta taɓe ta isa kan motar da sbd yanayin kyaunta mutum kan iya finshi tsawo ta ɗaura a kai ta juya tayi tafiyar ta.
Tana nan kwance a parlorn na Jaddah har wuraren karfe tara da rabi, wayan Jaddah ne ya fara ringing ta ɗauko ganin Faizan ta taɓe baki ta mayar ta ajiye tare da lumshe idanu kaman tayi bacci, Seda ya kira sau biyu a na ukun ne Jaddah ta fito tana tambayar Fauziyya kam bacci tayi ne ana ta kira bata ji.
Ganin baccin take yasa ta ɗauki wayan tare da amsawa ta kara a kunne, cikin kamillalliyar Muryarsa da se ka saurara zaka ji sbd rashin son hayaniyarsa yace
“Jaddah abincin fa? I’ve been waiting.”
Jaddah ta kalli Fauza tace
“ba’a kawo bane? Tun fa ɗazu na bayar a kai maka, ikon Allah..”
Yace
“wa kika bai wa?”
Ta fara jijjiga Fauziyya sbd nauyin baccin da ta riga ta sani tace
“Fauziyya! Ina abincin da na baki ki kaiwa yayanku ne?”
Juya keya tayi kan tace
“yana kan motanshi mana”
Ba tare da yace komai ba sbd yana jin duk abunda suke yi ya katse wayan, Jaddah na ta mamakin ikon Allah akan Fauxa se kawai sallamanshi taji, juyowa tayi zata yi magana taga ya nufo su hannunshi riƙe da ruwa me sanyi wadda ya fara kankanra na kamfanin Faro babba yana tafiya ne cikin ƙasaitarshi yana me buɗe murfin.
Kan Jaddah ta ankara ya fara tuttulawa fauxiyyan ruwan sanyin, a firgice ta mike zaune tana jan numfashi sbd sanyin ruwan gashi a duniya ta tsani ruwa ya taɓa ta yanzu se tayi mura gashi ya zuba sossai a kanta da fuskanta, hawaye ta fara don sossai ta firgita sanyin ruwan kuma ya ratsa ta, ko a jikinshi cikin muryarshi me taushi yace
“wuce ki ɗauko!”
Mikewa tayi tana share hawayenta ta fito, ko da ta ɗauko abincin don tuna muguntan da ta mishi a ciki bata san sadda murmushi ya subuce mata ba, a gabanshi ta dire ta juya ta fice ya ja tsaki kan ya buɗe ya zuba kaɗan.
Spoon ya ɗauka sbd shi fa irin mutanen nan ne da ko tuwo zasu ci seda spoon, da bismillah ya kai loman abincin bakinshi Sam be kula da bala’in dake ciki ba seda ya haɗiye ya ɗaura na biyu a bakinshi.
A firgice ya dawo da abincin yana sakin tari kaman ze shiɗe, da sauri Jaddah ta dauki ruwa ta mika mishi ya amsa ya sha sede ba sassauci, tari yake kaman ze mutu gabaɗaya ya Haɗa zufa, idanunshi sun rine sun zama jajazir, da kyar ya samu tarin ya lafa se kuma gefen cikinshi ya riƙe.
Salati Jaddah take tayi tace
“na shiga uku! Yaji ne a abincin ko me?”
“Zaliha! Zaliha!!”
Zaliha ta fito da gudu ta zube a ƙasa Jaddah tace
“ke Zaliha kin saka attarugu a markaden kayan miyan nan ne?”
Girgiza kai tayi tace
“ban saka ba Jaddah ai kin ce yallaɓai Faizan baya so, wlh ko kaɗan ban saka ba”
Fauxa dake daga window tana ta dariyar cin nasara, kwanciya yayi a kan kujeran duk dauriyarshi ulcer na azabtar dashi shiyasa yake mugun kiyayewa.
Kaman wasa Seda Faizan yayi ciwo sossai kan ya samu sauƙi, kaman yadda itama saida tayi mura da zazzaɓi, kowa kuma Seda yayiwa Zaliha faɗan saka attarugu a abincinshi baiwar Allah gata da gaskiya sede babu yadda ta iya haka take shiru take bada hakuri.
Zaune yake gaban baba prof kanshi a ƙasa, baban ya tambayeshi jiki, cikin girmamawa ya amsa da da sauki Alhamdulillah, bayan shirun seconds kan yace.
“In Allah ya kaimu Laraba zan koma Abuja sbd akwai tafiyar da zamu yi da shugaban ƙasa”
Murmushi baba ya saki, a ko menene ya kan yi alfahari da wannan yaron nashi, Faizan ba irin normal pilots bane, yana daga cikin manyan pilots da idan ba da su ba shugaban kasa baya tafiya ko ina, bayan nan yana da hannayen jari da kampanunnuka ba daya ba ba biyu ba, Sam be dogara da aiki ɗaya ba, yaro ne shi me tsantsan biyayya ga iyayenshi, babban ɗabi’ar shi kuma kunya yanzu ya san akwai abunda yake son faɗa mishi ne sede yana jin nauyin maganan shine yake ta kwana kwana.
Baba yace
“masha Allah, Toh Allah ya kaimu ya nuna mana”
Yace
“Ameen baba!”
Baba ya kalleshi yace
“akwai wani abu ne kuma? Naga kaman kana son yin magana”
Kanshi ya dukar yana shafa kwantaccen Suman keyanshi yace
“dama akan maganan Fatima ne”
Murmushi baba ya fadada yace
“masha Allah, ka shirya auren kenan.. Toh tunda har ka furta wani satin in shaa Allah zamu je wurin mahaifinta mu tambayar maka ita, ai Fatima yarinyar kirki ce ta samu tarbiya me kyau daga Mahaifiyarta Allah ya tabbatar mana da alkhairi”
Da Ameen Faizan ya amsa, dukda maganan magana ne da ya kamata yayi farin ciki sede ko kaɗan be wani ji daaɗin hakan har chan ba, hira suka taɓa kadan da baban har baba Alhj ya shigo suka kara tattaunawa kan ya musu sallama ya fice.
Bayan ya koma aiki da kwanaki biyar aka tambayar mishi Fatima kuma an bashi sede an ja auren se ta gama secondary school in ya so se ta fara jami’a a gidanshi.
****
Kwance take kan gadonta jikinta yayi tsami da bugun da ya Farhan ya mata da magrib ɗin saboda bin wata ƙawarta da tayi gida bata dawo ba se da ana kiran sallahn magrib tun karfe 1:30, da farko basu so dukanta ba sede Sam ta ƙi faɗan inda taje hakan yasa ya Farhan da Ya Faraj suka zane ta har Seda Baba prof da za shi masallaci ya karɓe ta, Allah ya isa take ta ja tana cin alwashi kala kala a kansu, fa’iza dake ɗakin tun da suka dawo daga sallar isha’in bata ce mata komai ba…