Diddigar Kaya Complete Hausa Novel

Diddigar Kaya Complete Hausa Novel

Wannan karon har gida ta zo sbd yadda duk ta ɗaga mai hankali, ta kasa fahimtar komai na Allah ne.

Shi kam ya ma tafi chan wata ƙasa ne hakan yasa dole ba yadda ya iya ya barta ta koma gidan, a gidan bayan mutane shiddan nan har yanzu babu wadda ya san da maganan auren na Fauza da Faizan, a fakaice Jaddah ke mata gyara ba tare da ta sani ba, asalin gyaran shuwa Arab take mata.

Dayake yanzu ko parlorn Jaddah baba be yarda ta wuce ba necon tan ma karasa mata ake yi yasa bata fita rana, skin ɗinta ya kara wani irin kyau da sheki tayi fresh tayi kiba abunta, nasihohi take sha har ta gaji da jinsu amma tayiwa baba alkawarin bazata sake shan kayan Maye ba har abada.

Yanzu wayanta bashi da anfani don tayi ta neman Zubair bata samu se kawai ta jefa shi kasan akwati.

Ko da Fatima ta zo ma sannu be hada su ba har tayi kwana bakwai ranan ne baba ya kirata yayi mata nasihu masu yawa kan ya faɗa mata auren Faizan da Fauziyya da ya hada, ba karamin girgiza tayi da wannan zance ba, tsanar da ta yiwa Fauziyya me yawa ne matuka gashi zata aure mata masoyi ta zama suna shearing komai nashi, abunda ba zata iya amincewa dashi ba kenan.

Ta dawo wurin mamanta hankali tashe cikin matsanancin kuka, Fauza ya sa aka kira mai itama ya faɗa mata, abinka da shiririta irin na fauza dariya kawai tayi ta fito abunta bata taɓa dauka serious bane seda abu ya karato dangi suka fara zuwa nan ne musababbin tashin hankalinta ya fara…
Ko da ta nemi halaka kanta kawai kiran sakina tayi tace ga abunda zata sayo mata ba tare da ita sakinar ta san ita zata sha ba, ta sayo ta bi ribibin en buki ta bata…

DAWOWA LABARI

“FAUZIYYA!!!”
ya fadila ta faɗa tana jijjiga ta da karfi, firgigit tayi tare da ɗago kai se taga babu kowa a jirgin se su uku.

“Me haka? Me yayi zafi da zaki ɓata a tunani haka? Kin san tun yaushe muke tsaye akanki?”.

DIDDIGAR ƘAYA…(Mai wuyar tsincewa) wannan littafi littafin kuɗi ne..
Ze zo muku a Naira ɗari uku kachal #N300.
Acc no. 0545475847
Acc name. Fatima Muhammad Gurin
Bank name. Gt bank
Se ki tura shedar biya ta wannan layin
09039206763.
Yi maza ki biya naki ki sha karatu cikin kwanciyar hankali, ina me tabbatar miki bazaki taɓa nadama ba

Karku sake a baku labari.

Gureenjoh

16

A natse suke saukowa jirgin, Ya fadila na riƙe da hannunta da kallo ɗaya ka mata zaka san cewa wannan ɗin amarya ce, don kwalliyarta na ban mamaki, ba fa na fuska ba lafayarta kaɗai ka kalla ze tabbatar mata da ita ɗin Amaryar babban gida ce.

Hannunta dake riƙe da jakanta ya bayyana lallenta me kyaun gani, chan jikin mota Faizan da Fatima ke tsaye suna jiran su har yanzu mita take mishi

“habeeby ka san halin Fauza, wlh tsoro nake ta tarwatsa mana gida muna zaman lafiyanmu, ba wai ina ja da shawaran Baba bane amma raba mana gida shi ya fi alkhairi”

Ya ɗan kalleta sbd tausayin da take bashi don ya san fitinar Fauza babu wadda ze shaƙa dayawa irin Fatima duk yadda kuwa yayi, yace mata cikin natsuwar shi
“Na sani Fatima, amma ba mun gama maganan gida ba? Baba be lamunce min raba gida ba tunda tun tasowarku a tare kuka taso da Fauza kowaccenku kuma ba baƙuwar ɗaya ba ce, na san baki da fitina kiyi hakuri ku zauna tare har ku samu fahimta”

Ajiyar zuciya ta sauke tare da ɗauke idanunta daga kanshi, se suka sauka kan su Fauza dake tahowa yadda take tafiya kaman ƴar sarki dole ya fusgi hankalin jama’a ga kyau tayi, abunda ta san zata nunawa Fauxa hasken fata ne kaɗai ko tsawo Fauza ta ɗara ta Dukda ta fi ta shekaru, dama kuma Hausawa sun ce tsawo rabin kyau, da sauri ta maida kallonta kan Faizan se taga su yake kallo shima.

A take ranta yayi baƙi kirin, ta tabbatar ba don Fauza bata son Faizan ba da se ta saka mata hawan jini in ta gane tana mutuwar kishin shi, hannunshi ta kama ta rike wadda ya saka shi ɗauke lumsassun idanunshi daga kan su Fauzan ya maida shi kanta.

“Tunda sun taho mu shiga motar habeeby kafafuna sun fara ciwo”

Ya juya cikin kulawa da hakkin shi yace
“so sorry, na barki a tsaye”

Motar ya buɗe mata ta shiga ya rufe, motar bayan wadda na abokin shi ne Faisal shi ya nunawa ya fadila suka shiga, shi kuma ya zagaye suka zauna da Fatima wadda hakan yayi mugun yi mata daaɗi har suka isa gida tana gayamishi abubuwan da likita yace ta dinga yi a kan ɓarin da take yawan yi.

Bayan sun sauƙa a tamfatsetsen gidan nashi dake maitama da kanshi ya musu jagora zuwa ciki Dukda ya fadila da ita aka zo jeren na Fauza, a bakin kofa Fauxa ta ja ta tsaya a hankali tayi ta karanto adu’o’in da Baba prof ya umurceta ta karanta kan ta shiga gidan, bayan ta gama tayi sallama tare da sa kafar dama se ta lumshe idanu, shikenan fa ita kuma wani sabon baabin qaddara ya buɗe mata, Allah kaɗai ya san abubuwan da zasu faru a cikin wannan gida kuma Allah shi kaɗai ya san ko gidan zaman ta ne ko ba gidan zamanta bane, ko a mafarki bata kawo auren mijin Fatima ba, ba ma wannan ba kuma wai Ya Faizan har yanzu kwakwalwanta be gama ɗauka ba bare zuciya da gangar jiki.

Tamfatsetsen parlor ne wadda ya ɗauke set ɗin kujeru har biyu, ya ƙawatu sossai masha Allah, kofofi uku ne a parlorn daga tsakiya wani hadadden staircase ne golden color wadda ya tafi a karkace har zuwa sama, dukkansu shi suka bi zuwa madaidaicin parlorn dake saman wadda na kasa ya fishi girma sede ya fi na kasa haɗuwa, dining section ɗin ma kaɗai abun kallon ne haka TV stand ɗin daga ka ganshi zaka san ba karamin kuɗi ya ci ba, console har biyu ne a parlorn ɗaya a dining section ɗaya daga tsakiyar stairs in kana haurowa, kofofi huɗu ne a saman, na farko daga dama ya fadila ta buɗe suka shige da Fauza da ya kaka.

Yayinda shi kuma ya shiga na biyun yana cewa Fatima ta duba ko me aikinta ta gama abunda su ya fadilan zasu ci, ta amsa da to tana shiga nata ɗakin wadda yake next to nashi, jakanta kawai ta ajiye ta fito, ta san shi. shi mutum ne me matukar son yaga nashi a gidan shi, yana son en uwanshi har bata san yadda aka yi ya rabu dasu yake ketare kasashe da sunan aiki ba, idan yaga nashi a gidan se abunda babu ne baya saya, ya dinga tambaya kuma ko akwai abunda kake bukata ayi maka, hakan ya sa itama dole take yi don bata son ɓata mishi Sam.

Kitchen na ƙasa ta je don ita kaɗai ke shiga na saman, ta samu me aikin nata ta gama duk wasu abunda ta faɗamata tayi a waya don haka a tare suka kwaso suka hauro sama dashi kwankwasa kofar tayi tare da buɗewa da sallama.

Su ba baƙin juna bane don haka tun tuni ma Fauza ta yaye lafayarta tana kwance a kan tamfatsetsen gadonta tana karewa tsaruwar ɗakin nata kallo, Baba prof da jadda sun yi kokari don su suka mata komai, dukda be so jadda ta sa hannu ba amma tace auren Fauxanta guda in bata fasa asusu ba na wa zata fasa kenan.

Mammi kuwa ita ta zubewa ya fadeela kuɗi akan wadda Faizan ya tura mata da umarnin Baba prof ta Haɗa mata lefe na gani na faɗa, kamshi da kyaun ɗakin kaɗai ze tabbatar maka da lallai nan ɗin na Amarya ne, akwai set ɗin kujeru akwai TV akwai kuma fridge a ɗakin, daga dan lungu window kuma akwai coffee table ɗaya da kujerun shi guda biyu masu kyau se karamin kofa da ze sadaka da madaidaicin balcony ɗinta wadda be wuce na tsayuwar mutum ɗaya ba an tare shi da wani black and gold glass.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected