Diddigar Kaya Complete Hausa Novel
“Jaddah yau wurin Mammi zan kwana”
Jaddah tace
“yau kuma ni aka yiwa Hijira kenan, to se da safe”
Tana murmushi tace
“Allah ya bamu alkhairi”
Sashen Mammi tayi ta gaisheta, tace
“Mammi bari na tofa miki Adu’ar nan”
Kasancewar kullum kaman ka’ida duk dare ta kan je ta tofa mata adu’o’in hakanan kan su wuce school kuma Alhamdulillah sossai Mammi take jin daaɗin kafan kaunar Fauxa sbd Allah na ninkuwa a zuciyarta, kuma duk wadda ya san Mammi se ya ji zancen Fauxa a bakinta sbd irin gudumawar da Fauxa ke bayarwa idan Mammi ɗin ba lafiya.
Seda ta shafa mata adu’ar kan ta mike ta nufo hanyar gate, Allah ya taimake ta daidai lokacin baba prof yake baiwa Lawal kuɗi ya amso mishi credit, a jikin flowers ta buya har Seda ya wuce ciki daga masallacin da shi se lokacin yake fitowa, Lawal kuwa yayi waje ta fito da sauri ta fice gabanta na dukan uku uku.
Wayanta ta fidda ta kira su Rahama suka zo da driver ɗinsu da shine yake yawo dasu dama suka wuce suna ihun ganinta at this time around.
Shiri suka yi suka wuce birthday party ɗin wani saurayin Rahama, wuri ne na manyan yara waenda iyayensu suke da kumbar susa, ado ne kala kala zaka gani da kalar dinkunan rashin kamun kai, kuɗi kuwa ba’a maganan adadin da aka zube don wannan party din musamman.
Fauxa ta ja hankalin matasa masu daloli dayawa a wurin kuma kowa so yake ta kula shi, sede fa in tana cikin ji da izzarta ko su Rahama shakkar mata magana suke, Fauxa ta riga ta zama hatsabibiya Dukda bata rabin abunda suke, su suna ɗan taɓa kayan maye hakanan su kan yi soyayyar shan minti sede ko ɗaya Fauxa bata yarda da wannan ba.
A nan wurin suka yi till down, gab asuba ta sa wani ya ɗauke ta suka nufi gida, Seda ta bari an shiga sallah kan ta shige da sauri, alwala ta ɗaura kawai ta nufi masallaci dayake ta chanza dressing ɗinta zuwa yadda ta fita, Jaddah dauka tayi ta makara a wurin Mammi tunda Mammi ba koyaushe take samun zuwa masallaci ba.
Ba se Fauxa ta samu abun yi ba, se ta kwana waje sau biyu ko sau uku a sati wadda hakan ya kara mata buɗewar idanu ba na wasa ba.
****
“Malam kwana biyar ne kawai Don Allah ka yarje mana ka taimaka ka Haɗa wannan plan din, in ba Fauxa ba zamu taɓa jin daaɗin wannan party ɗin ba”
Kallon Fauxa da tunda suka shigo bata ce komai ba yayi, yarinyar tana burgeshi tashen balaga ke dibar ta gashi Allah ya zuba mata sanyin kyau, ya jima yana bibiyarta tana wulakanta shi…
“Albashinka na wata nawa kake so?”
Ta watso mishi tambayar, wani fitinanniyar kallo ya watsa mata kasa kasa yace
“just one night stand please Fauxa na jima da ƙishirwanki”
Wani banzan kallo da ya kara kunna shi kanta ta mishi tace
“am not that kind in baka sani ba ma ya kamata ka sani just say your price!”
Rahama tace
“Sir please just say your price Fauxa ba irin waennan cheap matayen bane….”
“Before the count of three say your price or you loose the opportunity! And I must leave to Abuja”
Dukkansu uku kallonta suke da tsantsar mamaki, barin ma malamin wata iriyar yarinyace wannan? Me take nufi? Ba de hatsabibancin nata take shirin sauke mishi ba!
Be hankara ba ya ji ta ce “3”
Tana murmushi ta danna play a wayanta se ga muryarshi yana faɗin just one night stand please Fauxa wlh na jima da ƙishirwanki…
A razane yake kallonta zufa na yanko masa rahama da sakina suka saki murmushi lallai Fauxa ta ci lakabin da ake mata na
“Hadari malafar duniya, punkasau babban girki, biri da gatari ajalin mai gona, jan ƙasa na bayan ɗaki kowa ya ganki ya tuna Allah. Kadangaren bakin tulu; a barki ki ɓata ruwa a taɓa ki kuma a fasa tulu. Ba a banza ba, biri ke shan duka a rani, kowacce ze hadiye gatari zamu riƙe masa Kota…..”
Wannan kirari ne da babu wadda be san Fauxa dashi ba kuma har yanzu idan ana son ganin fara’arta cikakke to ka yi mata wannan kirarin shiyasa yawancin ƴan korensu da hakan suke cin kuɗin ta.
Cikin dage gira tace
“zaka rubuta mana takarda da sunan zuwa excursion na kwana biyar kuma mu uku kaɗai aka zaɓa daga makaranta. Sannan ka sani ka yi wa kanka don ko biyar ba zaka samu ba! Ka yi abinda na ce kan a tashi or else…”
Daga haka ta miƙe ta kaɗa mishi idanu ta juya ta fice suka bi bayanta suna murmushin irin zufan da yake Haɗawa….
DIDDIGAR ƘAYA…(Mai wuyar tsincewa) wannan littafi littafin kuɗi ne..
Ze zo muku a Naira ɗari uku kachal #N300.
Acc no. 0545475847
Acc name. Fatima Muhammad Gurin
Bank name. Gt bank
09039206763
Yi maza ki biya naki ki sha karatu cikin kwanciyar hankali, ina me tabbatar miki bazaki taɓa nadama ba
Karku sake a baku labari.
Gureenjoh
DIDDIGAR ƘAYA
(Mai Wuyar Tsincewa)
بسم لله الرحمن الرحيم
FATIMA MUHAMMAD GURIN.
(Gureenjo)
ADABI WRITERS ASSOCIATION
Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
*Kowa Ya ga zabuwa..*
And Now..
*Diddigar ƙaya… Paid*
*Shafi Na Goma*
*PAID BOOK*
*LAST FREE PAGES*
Babu yadda wannan malami da ya shiga tasku ya iya haka ya rubuta don tabbas ya san ƙaramin aikinta ne playing wannan audio wa school authorities daga nan kuma ya san aikinshi gabaɗaya ya rasa, time da ta bashi na cika ta zo ta karɓa tana yi mishi murmushin wulakanci irin nata.
Aiko tana isa gida Momma ta kaiwa don ta san daga momma ta amince to Baba Prof ma ya amince ta ci sa’a kuwa babu wadda ya hanata tafiyan suka shirya suka wuce akan ma Gombe ne bayan flight aka biya musu zuwa Abuja.
Karfe biyar na yamma suka sauka a birnin tarayya Abuja Motoci har biyu suka zo ɗaukar su Dukda duka duka su ukun ne kuma mota ɗaya suka shiga ɗaya na take musu baya, babban masaukin baƙin da har gomnoni da kusoshin gomnati ke sauƙa matukin motar tasu ya taka birki, masaukin baƙin ba baƙon su bane hakan yasa suka fito kowacce janye da karamar akwati mai taya suka yi ciki.
A reception suka haɗe da samarin sakina da rahama suka tarbe su har zuwa masaukin su me ɗauke da parlor da kuma ɗaki daga gani ka san na manya ne, a kujera ta yada zango tana bin su sakina dake lafe jikin samarin su da sunan oyoyo da idanu kan ta taɓe baki ta maida kanta ga wayanta tana cigaba da dannawa.
“Ƙawarmu kiyi ordering duk abunda kike so za’a kawo bari mu je mu zo”
Najeeb yaron ɗan majalisar tarayya kuma consultant saurayin sakina ya faɗa, kai kawai ta ɗaga musu su sakina suna daga mata hannu kan suka fice.
“Wallahi rahama kawarkun nan ta cika ji da kai kamar ƴar sarki”
Sakina ta taɓe baki tace
“kuma ba ƴar kowa ba ba”
Saurayin ta suhail wadda ɗa ne ga ministan lantarki kuma engineer yace
“ya zaki ce ba ƴar kowa ba ina gidan Prof kaka ne gidansu? Waye be san su ba a Nijeriya?”
Rahama tace
“sani daban wayewa daban, gidan kaman rijiya haka yake don ta samu mun fito da ita shine fa ta fimu feleke, ka ga kuwa manyan guys da take Juyawa? Iskancinta na da girma wallahi”
Anan suka bar maganan suka cigaba da harkokinsu na baɗala tsantsan rashin ilimin addini da rashin tarbiya suke nunawa a Filin Allah, ba kuma su damu da su su huɗu ne ɗakin ba.
Basu dawo masaukin su ba se dare lokacin fita partyn, sun sameta kwance ɗaure da towel tana bacci, tashin ta suka yi kan suka fara shiri suna hiran irin ɗauke hankali da suke son yi barin ma suhail da yace Zubair din jiji da kanshi na dayawa kuma en matan da zasu je wurin are high class hakan yasa suka ƙara zakewa kowacce ta fita fesss kaman ka sure ka gudu.