AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

Mam ma a cikin ransa kusan tinanin ne a ransa Dan kuwa idan ba bazama sukai suka haukace gurin Neman magajin Omar ba faduwansu zai Sakasa yiwa dansa abinda baitaba tsammata yi din ba Dan kuwa ya tabbatarda Haroon yafi kowanne ‘da rashin amfani,
Ya rasa wane irin Kai ne dashi gashi tsaban rashin basira ya kasa roko ko rarrashin Jamaal ya dawo musu,

Ba komai ya sakashi sakar masa pressure da nuna masa hantara da rashin kauna ba sai Dan ya rufe ido ya dage ya Saka Jamaal dawowa garesu ba Dan yasan duk duniya Haroon ne kadai zai iya Saka Haroon dawo musu Dan kuwa duk Wanda yasansa yasan Haroon ne abinda yafi komai so da kauna fiyeda komai bayan mahaifiyarsa Dan haka suke zafafawa Haroon komai Dan Jamaal ya dawo musu Amma Haroon din kaman kansa Babu komai a ciki Se iska,

Duk maganin da suka Saka masa a drink suna susuta kwakwalwansa Dan ya zama abin tausayin da zai Saka Jamaal ya dawo garesa abin ya gagara sbd yasan duk abinda Haroon zai koma bazai taba zabar barinsaba Koda Jamaal da mum dinsa sunso daukesa bazai taba binsu ba Dan haka yakeda tabbacin Jamaal zai dawo sbd Dan uwansa.

Suna Isa gida kowa mansion dinsa ya shige batareda tsayawa office nasu Dan tattaunawa ba Dan kowannensu Yana buqatan kadaicewa Dan dawowa daidai.

Mum Atee na ganinsa da yanayinsa bayan shigowansa tasan akwai damuwa me girma Dan haka tabarwa Ayesha zaban kayan datakeyi a waya ta bisa zuwa sama tana fatan ba matsalar Haroon bane da itama zuwa yanzu lamarinsa yafara isarta Dan itace kullum me zuba maganin da suke basa a drink dinsa na cin abinci sai kuma ta tabbatarda yasha cikin kulawa da dadin Baki Wanda ahankali ahankali yake yiwa kwakwalwansa illa harma da kuzarinsa batareda sanin Dad dinba Dan abinda yasaka ta ringa basa daban da abinda take basa din.

******Barr Haroon seelah a yanzu ba zaman Nasarawa ne ke basa nutsuwa da farin ciki ba ganin Ameenatou ne da rayuwar ahalinta da yanzu ya zamar musu tamkar Dan uwa,

Ayanzu Daya sabu da zamanta a cikin zuciyarsa Babu ranar da Baya zuwa gidan duk yanda zai gaji da ayyuka kuwa saiyaje gidan da daddare acan yake fira cikinsu sai dare sosai yake komawa masauki.

Babbah da dukkaninsu har zuciyarsu sun basa matsayi me kyau da kauna me sanyi kallansa sukeyi a Dan uwa duk da tsananin tazarar datake tsakaninsu Dan kuwa idan ya zauna cikinsu kaman saika wanke hannu zaka tabasa Dan yanda yake fita daban kaman wata acikin taurari.

Ameenatou sosai suka shaku cikin qanqanin lokaci Kuma a bayyane yake yanzu tsananin son dayake mata duk da itama tana sonsa sosai sedai hakanan wasu lokutan sai takejin kaman irin son datakewa su Yaya Hafiz take masa Amma Kuma tace bazata auri kowa ba sai shi Dan Hakan ne ma yakejin samunta a rayuwarsa zai samu nutsuwa da Kwanciyar hankalin Daya rasa tareda kadaicin rayuwar dayake ciki.

Bai taba sanin wannan son dayake a cikin kirjinsa yanzu ba shine abinda Dan uwansa Jamaal yake ji a lokacinda fadilansa tana raye ba,
Baitaba dauka zaiso mace irin son da Jamaal yayiwa fadila ba sai yanzu dayake Jin Ameenatou har cikin jininsa da ruhinsa Dan kuwa akanta ne yafara Jin Koda Dad dinsa zai yafesa idan har zata zama cikin rayuwarsa zai iya fuskantar Hakan.

Dukkaninsu Babbah sun San so me tsanani yakewa Ameenatoun Dan haka yake sake matsayi sosai a zuciyoyinsu musamman Hafiz dayake Jin farin cikin Ameenatoun zata samu rayuwar da zata zufafa iliminta Dan sunada burin tayi karatu me zurfin da zata dogara da kanta tinda bazata zauna karkashinsuba har abada.

Aikin Daya kawosa fara lalacewa yayi matsaloli suka fara bayyana sbd gabaki Daya hankalinsa da nutsuwan dayake samu a gurin Ameenatou suna can,
Idan ciwonsa yafara tasowa na damuwa Baya gane komai Baya ganin komai idan ba gidansu Ameenatou ya taho ba ya zauna ya zuba mata idanuwansa tana magana yana sauraronta Kokuma Idan tana tareda su Babbah tana zuba sangartanta son ranta batareda damuwa da Yana gurinba Dan matiqar tana taredasu Bata duba kowa duk abinda takeso zatayi Abinta shi Kuma Hakan yake sake kashesa akanta musamman idan tana fadan shi kadai ne zai zama mijinta Babbah zai aura masa ita.

Wannan kalman itace kalman da ayanzu take fin komai Sakasa farin cikin Da bayada shi kwata kwata a rayuwarsa.

Siddeeq hankalinsa yafara tashi sosai da irin son da Haroon yakewa Ameenatou Dan karfinsa yafara Sakasa shakkar lafiyansa ga Kuma bangare Daya aikin dayake gabansu fa Babu haske ko kadan kullum sabuwar matsala ake samu Dan haka yake cikin tashin hankalin.

Ranar dasu Dad suka zauna da turawan da suke cikin aikin suka fara samun barazanar janyewa daga hadin gwiwan kwata kwata jinin Mam Hawa yayi sosai Saida aka kira likitoci gida suka dubasa aka basa magani hadda su ruwa.

Mum Atee hankalinta tashi yayi Dan haka ta dagawa Haroon hankali da kuka Saida ya dawo Lagos a ranar cikin mummunan tashin hankalin abinda ya samu Dad dinsa.

Dad Lameenu kuwa kusan zaucewa yafara kokarin yi Dan ganin Mam a halinda yake ciki yasan balain Da yakai Mam kwance ba qaramin balain da zai kawo karshensu ba kwata kwata ne ba Dan haka ya kira BB ya Bude musu wuta akan tsananta bincikensu ko Wanda ya taba sanin dangin Aminatu ne aka samu a kamosa a kawosa.
#MAMUH

*_ZAFAFA BIYAR_*

1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_

2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_

3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_

4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_

Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200

*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*

*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*

*_MTN/VTU 09134848107_*

_*Al’ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
35
Tinda Haroon ya dawo Dad dinsa ya Hanasa ganinsa Dan Baya buqatan ganin ko fuskan Haroon din.

Mum Atee ce ta ringa lallaba Haroon din da duk inda hankalinsa yake ya tashi da wannan hukuncin na Dad dinsa.

Kusan Shima kwantawa yayi ciwon sbd hukuncin Dad dinsa na qin barin ya gansa.

Da wannan damar mum Atee tayi amfani ta ringa shayar dashi kwayar da suke Banka masa Dan haka sai yafara rikicewa ahankali ahankali sbd fushin Dad din da Kuma kansa da suke Neman juyar masa.

Siddeeq Daya fahimci yanayin Haroon din ya sauya sosai ya fara tsananta sosai daukesa yayi suka koma Nasarawa Koda lamarin zaiyi sauki idan Yana ganin Ameenatou wadda itama kullum take cikeda kewansa da damun su Babbah akan kada fa yaje ya auri wata acan Lagos yabarta anan ita tana jiransa.

Dawowansu Nasarawa ciwonsa tsananta yayi gashi basa ganin likita a bayyane a boye suke Gani sbd kada Yan jarida su ji Barr Haroon seelah magajin SEELAHs yana fama da matsalar data shafi damuwa da kwakwalwa.

Su Babbah Jin baida lafiya sosai suka shiga damuwa da tausaya masa sbd kaunar da suke masa ta wuce ta ogan Hafiz da Kuma Mai son Ameenatou.

Babbah da Yaya Abdul da kansu suka takurawa Haroon din da siddeeq suka Kaisa asibiti da kansu suna zuwa aka basa gado a dakin da Babu Wanda zaisan waye a asibitin.

Kwanciyarsa asibiti ya Sakasa sake tabbatarda bazai iya rayuwa Babu Ameenatou ba Dan kuwa kauna da kulawan da Bai taba tinanin ana samu daga ahali ba sune ya samu Dan kuwa Hafiz ne ma kusan yake kwana ya tashi dashi a asibitin babbah da Abdul ma kullum anan suke kusan wuni dadah da Heartbeat dinsa kuwa kullum sai sunzo da daddare su koma tareda su Babbah gaba dayansu.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected