AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE
Abinda yagani je ya sakashi ajiye iPad din gefe ya miqawa BB hannu ya dauko masa glass dinsa na qara Gani dakyau ya miqa masa ya karba ya goge da tissue da kyau kafin ya Saka ya sake daukan iPad din ya sake dubawa dakyau.
Numfashi ya sauke ahankali tareda rintse idanuwansa ya Bude fes akan iPad din hannunsa zufa na tsatsafowa daga goshinsa Wanda Hakan ya Saka Lameenu daga Kai sama ya shaqi iska me zafi sbd ganin abinda ya Saka Mam zufa daga gashi to ba qaramin balbalin balai bane Dan haka hannuwansa suka jiqewa da zufa Yana zuba dukkanin idanuwansa da Kunnuwansa akan Mam din Yana jiran Jin Abinda zai fada.
Mam dago jajayen idanuwansa dasukai jajir din a take ya Kalli BB yace bani copies na takardun file din Chris Jeremy.
Da sauri BB ya juya ya nufi locker dinsu ta takardun sirri ya Saka pin ya Budeta cikin sauri ya Nemo takardun Daman sune a sama Dan shine ya ajiyesu bayan yayi scanning da photocopy dinsu.
Yana kawowa Mam da sauri ya karba hannuwansa na rawa ya budesu zufansa na karuwa ya jefa idanuwansa a inda signature din Jamaal take wadda tabbas tabbas da gangan Daman Jamaal yake Saka signature dinsa a duka aiyukan masu mahimmanci sbd signature din Haroon daban tasa daban Dan haka aiki bazai taba yiyuwaba Saida Wanda Saka hannunsa yake ciki shikuma Baya Nan Dan haka sunaji suna Gani zasu ringa rugejewa Daya bayan Daya.
Sakin file din Mam yayi da sauri Yana miqewa ya nufi locker din da kansa ya fizgo dukkanin files dinsu dake ciki na aikin miliyoyin da biliyoyin kudin da zaayi bayan auren dansa
Hannuwansa na wata irin rawa da jijjiga ya ringa budesu Daya bayan Daya Yana duba signing din dayake cikinsu duk na Jamaal Seelah ne ba Haroon seelah ba……..
Kasa tsayuwa yayi ya zube a kujeran datake gurin zufansa na tsiyaya kaman ya hadiye kunama da ranta.
Lameenu dayake tsaye Yana kallan Mam zufansa Tama Fi ta Mam din Dan kaman ana gobara a cikin jikinsa haka yakeji dakyar ya iya tattara yawu ya hadiyewa makoshinsa Daya Bushe yace
“Jamaal ne ko??
Jamaal ne ba Haroon ba,
Signatures din duka na JAMAAL ne ko??
Shine yake tareda mu duk tsawon lokacin Nan?
Shine yake tsaye a gabanmu da bakinmu mum sanar dashi har abinda Haroon Bai saniba ayau din sbd Haroon baisan dukkanin wainnan da na lissafo ayau mune da hannuwanmu muka kashesu ba…….
JAMAAL me mukai Maka??
Wane balai da masifa ne wannan?
Wace masifa Haroon ya sakamu bayan tarin wadda take gabanmu…
BB ma da tini zufan ta katse masa cikin fargaba da shakkar abinda zai iya biyowa Baya kallan Mam yai Wanda zuciyarsa ke Neman bugawa sbd zufa yakeyi sosai hakama zuciyarsa Bata bugawa daidai.,
Lameenu kujeran datake kusa dashi yayi saurin zaunawa Yana cewa
“BB yi sauri kirawo likita ya dawo bana Gani zuciyata Bugawa zatai jinina ya mummunan hawan da baa so yi sauri kirawosa”
Daga Mam din har Lameenu jininsu mummunan Hawa yayi dole Akai gaggawan Kiran Dr Koda yazo Lameenu yafi Dad shiga Mummunan hali Dan haka shi aka fara dubawa kafin Dad Wanda shi zuciyarsa bugawa take Neman yi kawai.
Dr na fita Haroon da BB ya sanar da Dad na Nemansa Yana shigowa BB ya rufe kofar.
Haroon dayake kallan Dad Lameenu dayake numfashi ahankali ahankali alaman ba cikakkiyar lafiya mayar da kallansa yayi gurin Dad dinsa Wanda ya dago jajayen idanuwansa yayi masa kallo Daya na tsaftan gaske ya tabbatarda Haroon ne a gabansa take ya daga hannu ya sauke masa wani mahaukacin Marin Daya Saka gefen bakin Haroon din fashewa da jini.
Dagowa yayi bakinsa na jinin ya Kalli Dad din sedai wani Marin Dad ya sake saukar masa Mai zafin dayafi na farko.
#MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al’ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
51
Radadin Marin Kai tsaye a zuciyarsa yake sauka wadda take tarwatsewa aduk lokacinda mahaifinsa ya Saka masa hannu duk shekarun dayake dasu Wanda da yayi auren wuri da tini ya Tara Yara biyu ko uku.
Jajir idanuwansa sukai a karo na farkon dayaji zuciyansa na tabbatar masa da shidin ba komai bane a Gurin Dad Kuma har abada bazai taba zama komai ba a gurinsu,
A zero yake gabansu Kuma a haka zaici gaba da zama..
Yanda zuciyarsa ke radadi da qunan dayake tafasa jininsa haka ta Dad dinsa ke tafasa ya kallesa da jajayen idanuwansa yace
“Ayau nayi baqin kasancewa Wanda ya haifeka,
Nayi baqin ciki da Dana sanin barinka a qarqashin inuwata sbd har abada bazaka taba zama me amfani ba,
A yanda Aleena ta haifeka ba komai cikin kanka haka ka girma Babu komai a cikin kan naka dayekeda amfani ko buga Maka lissafi Mai amfani……..
Tsananin ‘dacin maganganun ya Saka Haroon rintse idanuwansa dasuke tsananin radadi sbd Jan da suke qarawa hannuwansa na rawa kansa na sarawa ahankali ahankali Yana qara qarfi.
Dad Lameenu da ayau tsaban shock baida karfi ko kadan a zaune yake Yana Jan numfashin wahala da ‘dacin zuciya Bude Baki yayi yace
“Ban taba daukan karshenmu a hannunka zai faro ba Haroon sai ayau din,
Ban taba sanin jinin kafiran dayake yawo a jininku na mahaifiyarku zai taba aiki a kanku ba wataran sai yau,
Haroon Ashe bakada Imani bakada ha nkali???
Tin yaushe ne Jamaal yake acikinmu batareda mun saniba???
Tin tsawon yaushe muke kirari muna dabawa kanmu wuqa a gabansa batareda mun saniba??
Jamaal da yayi alkawarin saiya mayar damu mabarata kafin ya San sirrinmu kenan yanzu Daya San hatta yanda muke kalan numfashinmu kana tinanin a mabaratan zai barmu yanzu???
Wlh Jamaal Saiya tabbatarda ko Baran idan munyi bazaa bamu sadakar ba….. innalillahi wainna ilaihirrajiun,. innalillahi wainna ilaihirrajiun,
Kallan Mam yayi jininsa na sake hayewa a rikice yace
“Wlh mamman Jamaal bazai rasa hada kwararan shedu akanmuba,
Bazai rasa recording na wasu maganganunmu ba……
Kirjinsa ne ke Neman rikewa Dan haka BB Dake tsaye Yana jiquwa da zufan Shima yowa kan Lameenu Yana masa fifita duk da sanyin AC Daya cike office din tsaf Amma dukkaninsu a jiqe suke da zufa.
Mam dayakeji zuciyarsa na tinkudo masa baqin cikin duniya da bacin Rai kallan Haroon yayi Wanda jikinsa keta tsananin rawan Dayake nuna da ciwonsa yafara tasowa Daman gashi tinda ya dawo mum Atee ta Dora daga inda ta tsaya.
“Haroon kaman yanda ka ha’ince ni kabi shawaran Dan uwanka da mahaifiyarsa kuka sakani wannan baqin cikin wlh saina nin ka masa Wanda yafisa Dan bazaka auri wannan yarinyarba wallahi indai nine na haifeka,
Bazaka samu farin cikin dakake tinanin zaka samu ba idan ma ka gujeni ka komawa mahaifuyarka,
Kaman yanda kuka rusamu wlh dakai zamu dawwama acikin wannan baqin cikin da rashin Dan kuwa idan baka sani ba ka sani wannan ciwon haukan Daya kwakwalwanka Babu inda zan zaka Daya wuce na tattara ka na aikaka asibitin mahaukata Koda kanka zai Bude,
Idan har lissafina ya buga daidai Dan uwanka yanda yake kwararren likita na tabbata ya karanci yanayinka Kuma bazai rasa bincike akan abinda ya fahimta tareda Kai ba Dan haka zuwa yanzu yasan mummunan Nisan da qwaqwalwanka yayiba a Juyewa Dan haka ka Saka aranka Babu maganar aurenka gobe wlh….