AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

Tin anan Kunnuwansa sukai masa wani irin dim suna kokarin dauke jinsu,
Idanuwansa kuwa wani dishi dishi suke son fara masa Amma ya rintse su da karfi tareda budewa Yana budewa motarsa da sauri ya fito batareda ya kasheta ba hakama wani parking din tsakiyar Titi yayi Yana qarasowa gurin da gudun gaske ganin motar Dad Omar data Abdul sun hade guri Daya kaman kayan wankin da aka hada aka matse cikin mafi muni da tashin hankalin kallo a kusan karkashin babbar motar wadda da alama itace tayi musu hawan tela.

Daukewa ganinsa yafara yi da gaske hakama kunnuwansa Dan haka take yafara Neman kasa karasawa sbd jiri da rashin Gani,
Daidai lokacin Mam ya iso gurin da drivernsa tareda Lameenu cikin matsanancin tashin hankalin da Bai taba Shiga ba Shima nasa ganin da Jin kusan daukewa yayi can sama sama yakejin maganganun mutane da iska suna kadawa hakama gabansa Baya Gani sosai Yana Sako Kai inda police din gurin janye masa shida Jamaal daidai lokacinda aka shimfide gawar Haroon da aka samu cirowa a gabansu cikin fararen kayansa da suka sauya take Babu ko dogon haskensu koina jininsa ne ya sauya kalar kayan gabaki dayanta.

Daga Jamaal har Dad lokaci Daya kafafuwansu suka sare a gaban gaban gawar suna zubewa Jamaal take ya qarasa zubewa qasa Yana rarrafowa gaban Haroon din Dan cetan ransa sbd Bai yadda da wani abin ya Riga ya faru ba da Haroon dinsa, Dad kuwa zubawa gawar idanuwansa yayi hannuwansa na wata irin rawar tashin hankali bakinsa na rawa yace

“Kuyi sauri ku kawo mota muje asibiti Dan uwansa likita ne kwararre gashinan zai taimaka masa kuyi sauri,
A kawo mota,
Me kuke Jira?
A kawo mota da sauri ‘dana Yana buqatan taimakon gaggawa,
Yaro na Yana buqatan Isa asibiti,
Lameenuuuu a yi gaggawan kawo mota Dan Allah karku bari yarona ya mutu a Haka yanada raunin zuciyaa, HAROON,HAROON,
HAROON my boy,
Yarona ‘dan Albarka Karka tafi ka barni Kai kadai nake dashi a cikin abinda nake tsananin so a duniyar Nan,
Haroon,Haroon…… innalillahi wainna ilaihirrajiun….

Dukkanin maganganun da Dad din keyi Baya hayyacinsa sbd Bai yadda da Babu Rai a jikin Haroon ba sbd jamaal ma kwata kwata ya kasa yadda da Babu Rai a jikin Dan uwansa Dan haka yaketa kokarin dawo da numfashi a jikinsa ya hanyar dubarunsu na likitoci hannuwansa na wani irin tsananin rawa hakama nasa fararen kayan tini sukai kaca kaca da jinin Yana rungumo Haroon din idanuwansa na qanqancewa Yana ihun su kawo ambulance Shima.

Lameenu rudewa yayi Shima yafara cewa a kawo ambulance Maza Maza daga SEELAHs hospital Yana Jin tsananin tashin hankali da tausayin halin da yaga Mam a ciki yau harma da tsoro da fargaba duk ya shiga sbd dukkaninsu Basu taba kawo tinanin Haroon zai shiga motar Omar ba,to mema ya shigar dashi,

Babban tsoro da tashin hankali da mugun firgicin dayake ciki shine bayan wucewansu Omar din tareda Haroon Saida ya Jira Jamaal ya gama wayoyinsa tukuna ya fice kafin ya fidda wayarsa ya kira Lameenu din Kuma daidai wannan lokacin ne siddeeq ya shigo mansion din Bai dauka su Jamaal din sun wuce ba sbd yanata Kiran wayarsa busy yake.

BB ya sanar da Lameenu cewan Haroon fa yabi motar Sir Omar a dakatar da aikin kokuwa a qaddamar dashi yanda aka tsara sbd Haroon na ciki,

Kai tsaye Lameenu Bada umarnin yayi ayi aikin kaman yanda aka tsara sbd Ameenatou bazata taba zama sirikar Mam ba ta yanda zai fisa Iko ko mallakar dukiyar gaba dayanta bayan wuyar da suka shawo akanta Dan haka gwara Bata zama sirikar tasaba tin farko suna gamawa da Omar itama su gama da ita shikenan sune magada tinda sune ake kallan uwa Daya Uba Daya dashi Kuma kada a kuskura duk tsanani bayan aiki a cewa Mam an sani su tsaya akan Basu San Haroon yabi motar ba.

Hakan da siddeeq yaji ne ya sakashi Kiran Jamaal Wanda ya gama wayarsa harya fara Nisa a hanya ya fada masa take shikuma ya sauya hanya yabi zuwa gidansu Ameenatou Dan cimma su Dad din da bawa Ameenatou kariya kafin ya samu a dauro auren a dawo yasan Dan uwansa ya samu mallakar macen zuciyarsa.

Wuto babbar motar ta fara ci dashi Dan haka Akai saurin Bude ambulance din data iso aka fara dauke gawar Haroon aka Saka kafin ta Abdul wadda itama kallo Daya zakai masa ka fashewa gawar da kuka sbd daidai lokacinda su Abdul din suka iso gap da motar su Dad sun musu magana kenan babbar motar data taho da mugun gudun ta haye kansu gaba Daya cikin rashin tausayi kuma Yana hayewa kansu da motar sedai kafin ayi wata wata drivern ya Bude motarsa yana kokarin guduwa a raunane Dan Shima ya raunana sosai

Sedai Yana fitowa motan zai gudu yaran BB Dake gurin a rarrabe suka taso suna rufesa da dukan mutuwa suna cewa ya kashe mutane zai gudu
Take mutane da Jamaar gurin suka tayasu aka rufesa da dukan da take aka kashesa a gurin Shima duk yanda Yan Sanda suka so samunsa da Rai tini Rai yayi halinsa cikeda baqin ciki suka dauki gawarsa Shima aka jefa wata motar daban.

Dad Omar da Babbah sune Basu rasu ba Amma sunfi wainda suka rasu kakkaryewa sosai tareda wahalalliyar azaba hakama gabaki Daya sun sauya daga mutanen da aka Sansu Dan Babu Wanda ake gane ko fuskansa sunyi mummunan raunana Tako ina Dan haka a cikinsu Babu ma Wanda alamun sauran Rai yake a jikinsa amma dai an duba suna raye din Dan haka Akai gaggawan daukansu zuwa asibiti,
Sai Ahmed da Hafiz da Suma sukai Mummunan kariya ta hannuwa da kafa hakama sun raunana sosai sedai su suna hayyacinsu sedai rikitacciyar azaba Da jininsu Dake zuba kaman ba daga jikinsu yake fitowa ba.

Suma kwasansu Akai zuwa asibiti gaba Daya,

Jamaal har acikin ambulance din rungume yake da gawar Dan uwansa ya kasa sakonsa duka jikinsa rawa yakeyi sosai kaman zai jijjige Haroon din Dan haka koda aka Isa asibitinma da qyar aka bambare gawar daga jikinsa Akai ciki da ita.

Dad Koda ya iso Lameenu na biye dashi sbd kada ya Fadi hakama su Mum Atee tini suka qaraso asibitin
Hakama su Aunt Didi matar Ahmed da Fatmah duk sun iso
Mum Nur kuwa Kuka kawai takeyi sbd tsoron dataji duk ya dabaibaiyeta.

Siddeeq Daya kasa hakuri wayoyin kowa kira yakeyi gashi itama Ameenatou din taqi farfadowan sai ruwa ake zuba mata Dan haka ya daukosu tareda dadah cikin sabon tashin hankali sukayo asibitin da ita.

Suna isowa itama aka karbeta sedai samun ahalin seelahs kaf a asibitin ya Saka su dadah cikin masifaffen tashin hankali kafin dukkaninsu su motsa daga inda dukansu suke tsaye Dr zayyan ya fito daga dakin emergency din da suke ciki da duka su Omar da Haroon din bayan fama da taqaddamar da sukasha da Jamaal kafin ya yadda Allah ya karbi ran ‘dan uwansa ya koma garesa Dan haka kallansu Dr zayyan din yayi idanuwansa jajir hakama Shima hannuwansa yar rawa sukeyi idanuwansa na cikowa da kwallan Daya kasa riqewa ya kasa kallan Dad dake tsaye shi yake jiran abinda zai fada,mum Atee da Dad Lameenu na gefensa kowa Dr zayyan din yake kalla,
Su mum Sarat da Dadah ma duk a tsinke suke,
Sai su mum Nur da kukanta ya tsaya cak suna kallo bakin Dr zayyan din ya Bude cikin sauti me tsananin sanyin gaske yace

“Sai hakuri,sai hakuri, Haroon seelah da AbdulRasheed Allah ya Riga ya dauki ransu lokaci yariga yayi Babu abinda zamu iya sai hakuri da rungumar hukuncin ubangiji”
#MAMUH#

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected