AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

“Shine kacemun kana Abuja sbd kada muyi bankwana kafin na wuce ko??”

Siddeeq Daya rasa ta inda zai fara gyaran matsalan Dake kokarin faruwa fitowa yayi da sauri daga motan ya zagayo ya rufe mata kofar Data shigo ya sake dawowa mazaunin driver da sauri ya zauna sai alokacin ya juyo ahankali ya saci kallan JEEY Daya zuba mata fararen idanuwansa Yana kallanta cikeda mamaki da shakkar ko tanada matsala ne Dan baisanta ba baima taba ganinta ba yake ganin.

Hadiye numfashi siddeeq yayi cikin Dan daidaita murya ya riqa JEEY din magana Yana washe Baki da nuna kulawa yace

“AMEENATOU,
barka da fitowa,yau ke kadai kika fita ne??

Hakan daya fada ya fada ne Dan JEEY yasan wacece din shiyasa ya ambaci sunan nata Kai tsaye Yana tada motar yaja ahankali suka bar gurin Yana juyawa Dan maidata gida.

Dauke idanuwansa JEEY yayi akanta tareda rufe iPad dinsa daidai lokacin ta sake motsowa kusa dashi tanason fada masa maganar da batason siddeeq yaji sedai tana motsowa da fuskanta Dan fada mata din Yana juyowa da tasa fuskan kadan ya rage fuskokinsu ya Hadu tayi saurin yin bayan kirjinta na bugawa ta dago ido ta kallesa Shi kuwa Kai tsaye ya Bude Baki yace siddeeq ya ajiyesa site.

Kasa magana tayi sbd kirjinta Dake bugawa har lokacin shiyasa har motan ta tsaya Bata iya cewa komaiba harya Bude motan ya fice yabarta zaune tana kallan inda ya tashi da ido fuskansa da numfashinsa Daya bugu fuskanta na dawo mata.

Gida siddeeq ya wuce ya ajiyeta Yana mata zancen aikin Dake gabansa ne duk suka Saka kansa daukan zafi shiyasa Baya cikin mood kwata kwata yau din.

Bata iya cewa komaiba ta Bude motan ta ficewanta tareda shigewa gida.

Mota ta musamman ce tazo ta daukesu guraren 2 na Rana tayi Abuja dasu daga can suna Isa airport ba Bata lokaci jirginsu ya daga zuwa Lagos.

Suna sauka Lagos Abdul ne da kansa yaje da motan Aliyah ‘yar Alh Lameenu wadda tinda Taga Abdul din taji yayi mata sbd batason namiji me kudin da shine zai juyata tafison Wanda itace me kudin Kuma yar me kudin dazata ringa yanda takeso baya hanata bare ma Saka ido Dan Bata wani zama kasar itama kullum tana yawo karatun ma duk ta kasa tsayawa tayi sai yawon kasashe.

Dayake Dad ne yace yaje da motan ya daukosu shiyasa ya taho da motan ya daukosu.

Gidan Abdul din a kusa da tsadaddiyar anguwan masu shi da mansions din seelah din suke yake Dan haka daga gurin mum Atey driver ya kawo musu abinci bayan isowan nasu.

Gida ne me maana Wanda ya bawa Babbah da Hafiz mamaki sosai sbd ace anbawa sabon ma’aikaci gida irin wannan me Dan yalwa da kyau da tsari Kuma komai akwai a aciki gaskia sedai Dan zasu hada zuria ne Amma tinda a cikin kudin aikin Abdul din akace kamfani zai ringa cire kudin haya sai sukafi Jin nutsuwa da Kwanciyar hankalin sakewa da Hakan.

Daki uku ne a gidan sai Palo biyu da kitchen sai back door da store sai kowanne daki da toilet dinsa.

Kowa daki Daya ya dauka Abdul Daya,Hafiz Daya sai su Babbah Daya sbd Ameenatou tafiyanta zatai gidanta Nan da kwanaki Dan haka baa Raba dakin da ita ba Amma dai na Hafiz itace a ciki da komai nata shikuma yana kwana Palo kafin ayi bikin Amma kayansa suna dakin Yaya Abdul Wanda nasa dakin na daga gefensa daban nasu Babbah ma Yana daga gefe daban na Ameenatou dinne a tsakiya.
#MAMUH#

*_ZAFAFA BIYAR_*

1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_

2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_

3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_

4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_

Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200

*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*

*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*

*_MTN/VTU 09134848107_*

_*Al’ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
46
Haroon yanason dawowa Lagos Amma sbd kada ya zama ana ganinsa a Lagos Kuma ana ganin Jamaal a site yasakashi hakura ya zauna tareda Jamaal din Wanda Shima yafara kokarin Maida hankali ya gyara career dinsa data watse ta matsayinsa na lawyer.

A bangaren su Dad kuwa tsarin katin gayyatar Omar na musamman ne,

Duk tsawon shekarun Nan da basa tare bawai sun yanke muamala ne kwata kwata ba aa Suna waya da sauran gaisuwa a waya batareda kowannensu ya nunawa Dan uwansa komaiba,
Shi Bai taba yi musu wata maganar bare nuna wani abin daban kaman yanda suka Basu taba cewa komaiba bare nuna shakka fargaban yasan wani abin kawai dai kowa na nesa da Dan uwansa duk dubaru da nuna kaunarsu Bai Bata zuwa inda suke ba kaman yanda ya toshe hanyarsu ta zuwa inda yake iya Hulda da zumuntar waya sukeyi tareda nunawa juna kauna da kulawa a iya wayar sai yanzu da wannan kyakkyawar Daman ta taho musu wadda baida kowanne uzuri ko dalilin Badawa na qin zuwa auren Haroon Wanda sune ma ya kamata ace sinje Neman auren nasa batareda anje dashi Mam dinba Dan shine iyayensa.

*****Ta bangarensu Amarya Ameenatou kuwa suna fama da kadaici da bakuntar sabon guri Amma irin rayuwar da suka samu kansu a ciki ta wadata ta Saka bakuntar zuwan musu da sauki ga Kuma hidiman da aketa kokarin farawa gadan gadan.

Su mum Atee dasu mummy Sarat da jamaarsu sun kawo lefen auren Wanda ya amsa sunan lefen gaske na auren masu abun duniya Dan kuwa sosai dadah da umman fadila datazo tarbon lefen sbd Jamaal da siddeeq harma da Haroon din suka girgiza da tarin kayan da aka kawo din tareda wasu mahaukatan sarkokin Dalma(zinari/gwal/gold).

Da dadah da umman fadila sai Jamaar amanar dadah biyu da suka taho bikin Tim daga Nasarawa Dan lasa arzikin Suma da Kuma tabbatarda amanarsu Dan idan Basu taho auren budurwan gidan Babbah ba yar gaban goshin dadah dasu Hafiz ai basuyi komaiba.

Duk da basuda wani karfi Saida Babbah ya fidda kudi masu Dan kauri a Dan abinda suke Tarawa na bikin ya Bada tukuicin da sedai masu aikin da sukai shigo da kayan ne suka karba Amma mum Atee Sam kin karba sukai suna nuna ai ba komai bazasu karba tukuicin ba bayan a cikin ransu dukkaninsu qyanqyamin taba kudin ma sukeyi sbd Yan dari biyar biyar ne a hade dubu hamsin cif.

Su umma anan duka wuni sunata duba kayan har dare suna sake Saka albarka da adduar fatan farin ciki me dorewa a auren.

Washe gari masu gyara na musamman aka turowa Ameenatou wadda za’a fara gyarawa Tin daga satin har satin auren Wanda ya rage saura sati biyu cif.

Ranar farko da aka fara yimata gyaran ta fara sauyawa abinta sbd fatarta irin me santsin Nan ce dake karban komai da wuri,

Farin ciki da dokin datake ciki itada Haroon ya wuce duk inda ake tinani sbd karfi da yaji duk yanda Babbah da Dadah suka Kai basa ganin laifi ko illan komai datakeyi Saida suka ringa Jin kunya da mamakin irin son datake wa Haroon Wanda ya Sakasu shiga tsoro da duqufa da adduar Allah yasa irin girman son dayake mata ya tabbata a rayuwar auren nasu yakuma barsu tare har karshen rayuwarsu.

Haroon a wannan lokacin yana cikin kwanakin farin cikin rayuwarsa me tsananin gaske da Bai taba samun kansa a cikinsu ba Wanda Hakan ya sanyaya zuciyar ‘dan uwansa da mahaifiyarsa akansa wadda Bata isoba har lokacin Amma ta sheda farin cikin Da Haroon dinta yake ciki Wanda takejin a matsayinta na uwa a garesa tayi missing Daman basa wannan farin cikin dasuke Gani tareda shi sedai tana Jin dadi har ranta daya samesa sanadin macen dayakeson.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected