AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

Cikin girmamawa yace

“Sir Haroon barka da dawowa”

Batareda Jamaal ya amsa ba Dad Lameenu ya Kalli siddeeq Wanda Shima Kai tsaye ya juya daga office din ya fice tareda Turo musu kofar.

iPad din hannunsa ya ajiye gabansu tareda bayanan daya samo akan bincikensu ya fara da cewa

“Ranka ya Dade na samu tabbacin ‘yayan matar sir Omar Daya gudu da abinda ta haifa a daren yanada nasa ‘yayan guda biyu Kuma dukkaninsu Maza ne sedai Kuma matarsa an bani tabbacin kafin barinsu gombe a wancan lokacin ta haihu Wanda nakeda tabbacin ba haihuwa tayi ba babyn sir Omar dinne”

Cikin zaquwa Dad Lameenu yace

“Bayanin inda suke shine babban abinda muke buqatan Jin idan an samo”

Hakama Menene asalin abinda aka haifa din?
Mace ne ko namiji??
Hakurina da bugawan zuciya akan wannan lamarin ya kusa kamani BB a gaggauta samo mana inda suke sbd tashin aikinmu yau da aka samu shi kadai bazai riqe mana matsayinmu da tsagwaran dukiyar da muka rasa ba muna tsananin buqatan dukiyarmu Dake hannun Omar.

Dad da Shima abinda yake ransa kenan ya Kalli Haroon dayake tsaye har lokacin gabansu Yana kallan fuskokinsu da bakinsu yace

“Haroon ya qara muku kudin Daya kamata banason aurensa yazo duk tsanani duk wuya batareda an samo mana inda suke ba,
Idan Kuma bamu samo Hakan ba to tabbas lokacin zuwansa garemu yayi Dan bazai taba yiyuwaba ayi auren ‘dana dayake matsayin dansa batareda yazo ba,

Zuwansa Nigeria kuwa ba abune da zai taba yiyuwaba yazo ya tafi batareda ya kaiwa abinda ya Haifa da cikinsa ziyara ba Wanda shi da kansa zai kaimu ga Magajinsa batareda ya saniba.

Kallan Haroon ya sake yi Yana sake cewa

“Ka Basu duk adadin kudaden da suke buqata kaje ka fara Shirin aurenka Dan daga lokacinda Omar ya sauka a Nigeria dukkanin motsinsa a tafin hannunmu zai zama.”

Gyara Kai Jamaal yayi Yana kallan BB dayakejin bazai iya barinsa ya sake ahakan iskan yanci ko Daya ba Amma Kuma Yana buqatan sanin abinda yake faruwa kafin komai Dan kuwa zantukansu sun Saka kansa daukan zafi.

Gyada Kai BB yayi Yana Jin nutsuwa da farin cikin Suma wahalallen burinsu ze Kai karshe sbd a saukake ma auren Haroon din zai kawo Omar har gida Kuma zuwansa kaman bayyanar abinda yake boye ne.

Maganganun sauran ayyukansu dasu BB din keyi ne suka fara Kai tsaye tareda tambayan huldan datake hannun BB din da yaransa ya tabbatar musu da komai Yana tafiya lafiya kalau duk da an kama wasu yaransa Amma ya tura yaronsa Daya Daya bari aka kamasa aka Saka cikinsu Sbd ya hanasu fadan komai sedai aka wayi gari sun rasu dukansu su biyu sai shi Dayan yaron nasa sun fito dashi Dan haka Babu matsala Tako ina.

Juyawa Jamaal yayi ya fito idanuwansa basa ganin gabansa sosai sbd Ja da tashin hankalin Daya tsinci kunnuwansa daji batareda ya tsaya jin sauran abubuwan da hankalinsa yake Neman kasa dauka duk da ya Dade da sanin ba imani a lamarinsu Dad bare tausayi sbd abinda sukaiwa fadila da har yanzu baida sheda ko tabbacin sune sukai Amma ayau da kunnuwansa Yana Jin abubuwan da baisan tayaya ma zaace sune suke aikatawanba,

Haroon ya San dukkanin wannan abin dayake faruwa kenan ya boye masa tinda gashi suna maganar a gabansa batareda sanin ba Haroon dinne ba.

Yana fitowa Kai tsaye mota ya nufa Yana miqawa siddeeq hannu ya basa key batareda ya Juyaba,
Kirjinsa yake Jin ya toshe masa Babu iska ko kadan Babu abinda yake buqatan so kaman ya fita daga Mansion din.

Siddeeq na ganin Hakan ya miqa masa key din motar Haroon Daya fito dashi Dan fitarsu idan sun gama.

Saida siddeeq ya nuna masa motar ya nufi inda take tin kafin ya Isa ya Budeta Yana Isa shiga kawai yayi ya tayar da reverse ya fice daga Mansion din Yana saukar da duka glasses din motar sbd iska ta shigesa.

Yana ficewa siddeeq ya Ciro wayarsa Yana shakkar abinda ya faru daga cikin office din Amma dai koma Menene Haroon Yana buqatan sani Dan dawowa sbd ansamu matsala ga dukkanin alama.

Su Dad kuwa farin ciki da zaquwan auren ne gaban Daya ya mamayesu sbd ga dukkanin alama sanadiyar auren zasu samu abubuwa da dama dasuke so suke fata,
Haroon ya fara zama abin Alfaharin da zai sake fitar da sunan seelahs da tsayuwarsu hakama dawowan Omar dasuke fata ta sanadin auren da dole zaizo ko Dan Yan jarida dazasu yada maganar auren koina da rashin zuwansa auren ‘dan farko da zaayi a Seelahs din tinda na Jamaal kaman auren boye ne da ba kowa ya saniba Amma wannan da kansu zasu Kai masa gayyata ta musamman da matsayin zamansa wakilin ango da zai karba auren da hannunsa.

******Haroon dayake tareda mahaifiyarsa tana jinyarsa cikin tsananin so da kauna da kulawa tareda tattali Jin yayi zuciyarsa ta karaya Da yanda tin farko ya zabi mahaifinsa akan mahaifiyarsa,

Bata taba nuna masa banbanci tsakaninsa da Jamaal ba sedai shine Karan kansa ya zabi mahaifinsa akanta sbd sonsa dayakeji cikin ransa fiyeda komai.
#MAMUH#

*_ZAFAFA BIYAR_*

1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_

2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_

3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_

4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_

Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200

*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*

*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*

*_MTN/VTU 09134848107_*

_*Al’ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
44
Mum Aleena datake Jin batason sake rabuwa da ‘danta sbd halinda yake ciki na tsananin buqatan kulawansu dan sai sunyi da gaske zasu iya rabasa da depression din Daya kamasa,

Drug kuwa da suka samu a jininsa Basu sanar masa ba itada Jamaal sbd sunason tantance shine yake Sha da kansa kokuwa sbd sun kasa yadda ko sanin tayaya zai zama Yana Shan kwayoyi irin wainnan.

Siddeeq Kuma ya tabbatar musu da Babu kwayoyi mayen ko makamancin Hakan da Haroon yake Sha Amma Kuma duba da depression dayake ciki da tsananin matsi a Hannunsu Dad zai iya samun kansa da Shan kwayoyin Dan samun fita hayyaci ya Dena Jin komai.

Tin daga ranar da Haroon din ya taho aranar ya ringa yiwa mum din kuka kaman karamin yaro cikin ciwo da tsananin buqatan again Dan uwansa akan bayason rasa Ameenatou kaman yanda ya rasa fadila,
Shi a yanzu ba yabon mahaifinsa yake nema ba Ameenatou kawai yakeso a rayuwarsa.

A gaban Mahaifiyarsu Jamaal ya Sakasa sukaiwa juna alkawari.

Idan Haroon yayi masa alkawarin dawowa ga mahaifiyarsa Dan samun lafiyansa da rayuwar nutsuwa da Kwanciyar tare Kuma da cika burin Mum dinsu na ganin yayanta duka biyu a tareda ita to shi Kuma yayi alkawarin zuwa ya gyaro dukkanin abinda Haroon yakeso Dan samun yabo daga Dad dinsa da Kuma zama abin alfaharinsa tareda tabbatar da aurensa da yarinyar Amma ana daura auren zasu taho tare.

A daidai wanna gaban Babu abinda Haroon bazai iya yiba akan samun Ameenatou da samun nutsuwan zuciyansa data Dan uwansa da mum Dan haka ya amince da dawowa cikinsu gaba Daya bayan auren take mum ta rungumesa cikin farin ciki da Jin dadi sosai tana Jin kaman tinda ta haifesa sai yanzu ne zata samu zaman datakeson yi da ‘danta hakama zata kaman yanda ta kaunaci fadila take taji tana kaunan Ameenatou har cikin ranta duk da Bata taba ganinta ba Amma tayi masa alkawarin inshallah da ita zaayi aurensa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected