AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

Ahmed ma Yana cikin farin cikin gaske Jamaal ne kadai yake Jin kirjinsa da zuciyarsa cikin nauyin Daya hanasa ko numfashin daidai.

Karfe goma saura kusan kowa ya gama Shirin daurin auren,

Haroon Wanda Jamaal ne ya tayasa shiryawa cikin kyakkyawar farar shaddar datai masa wani irin kyau haskensa da Bai taba sanin yana dashiba bayyana sosai.

Ayau hatta turare iri Daya sukai amfani dashi sbd komai dayake jikinsu iri dayane babu banbanci abinda Basu taba yiba kenan tin suna kanana har girmansu sai yau din.

Time Haroon ya kalla yaji jikinsa ya mutu da farin cikin wannan ranar Dan haka ya Ciro wayarsa ya Saka Kiran Ameenatou wadda itama kusan ankusa gama shirinta tana dauka ajiyar zuciya kawai ya fara saukewa kafin ya ambaci sunanta Yana ce mata Yana Sonta kawai ya kashe.

Murmushi kawai tayi tana damqe wayar a hannunta tareda cigaba da shiryawa.

Jamaal tsayuwa yayi bakin window ranar aurensa na dawowa sabuwa acikin zuciyarsa Dan haka nauyin kirjinsa yake sake karuwa Yana sakashi shiga yanayin tashin tsikar jikinsa idanuwansa na Neman sauya Amma ya kasa Hana zuciyarsa shiga wani irin tsoro duk jarumtarsa.

Matsowa Haroon yayi Yana kallan time da yayi yace

“Muje ko time yayi”

Juyowa Jamaal yayi ahankali ya zuba masa idanuwansa da suka sauya sedai Bai iya cewa komaiba.

Tsoro yakeji sosai Dan haka ya Dan dauke idanuwansa daga Haroon yanayin gaba Haroon din ya biyosa yana gyara zaman babbar rigar jikinsa.

Motar Mam da securities dinsa ce ta fara barin gidan ya wuce daurin auren zuciyarsa fes,

Fitowan su Jamaal yayi daidai da fitowan Dad Omar tareda Ahmed zasu shiga mota Dan haka Kai tsaye ya kofar harabar Daya hada gidajen suna nufa suka Isa gurinsa idanuwansa na kansu Yana kallansu a tare zuciyarsa na cika da farin ganin auren yarsa Dan haka Kai tsaye rungume Jamaal yayi kafin ya rungume Haroon da yau Shima yake cikawa kowa idanuwa da kwarjini Mai sanyi.

Cikin kulawa da kauna Dad Omar ya kallo Haroon yace su shiga motarsa suje daurin auren tare.

Cikin farin cikin Hakan Haroon ya juyo ya kallo Jamaal zaice da Dan uwansa yake son zuwa daurin aurensa sai Jamaal din Wanda ya kasa samun nutsuwa ya girgiza masa Kai Yana kallan fuskansa Yace yabi Dad din kawai.

Murmushi me sanyi Haroon yayi tareda gyada Kai kaman qaramin yaro yabi dad da Ahmed dukkaninsu suna murmushi suka shige mota.

Jamaal na kallo suka tada motar suka bar harabar gidan Shima ya juya yabar harabar gidan.

Dayake sun Dade da fita kafin ya fita Kai tsaye biyawa sukai suka dauki Babbah sbd Shi Daman da Omar zasu tafi daurin auren sai gashi Kuma sunzo da Haroon sai Hakan yayiwa Babbah dadi sbd zaiso ya sake bawa Haroon amanar Ameenatou
Babbah na shiga suka tada motar suka bar gurin.

Jamaal na kama hanyar zuwa gurin daurin auren siddeeq ya kirasa kaman bazai daukaba Saiya Isa sai kuma ya dauka
Abinda siddeeq din ke sanar masa yaji Yanzu daga bakin Lameenu da BB a Mansion shine ya sakashi juya kan motarsa ya kama hanyar gidansu Ameenatou sbd bazai taba barin wani abu ya samu matar Haroon ba aranar aurensu kaman yanda Shima ranar auren ya rasa tasa matar.

Wayar Dad Omar yake kira cikin gaggawa Amma Sam Bata shiga,
Ta Ahmed ya koma kira kwata kwata Bata shiga itama,
Ta Haroon ya kira ita Kuma Saiya jita a cikin motar dayake din Dan haka yayi wurgi da wayar seat din gefensa tareda qarawa motar tsananin gudu yana nufar gidan.

Yana Isa kofar gidan Hafiz da Abdul sun fito kenan cikin Shirin wucewa ko kashe motar baiyiba ya fito da sauri Yana kallan Abdul yace

“Yi sauri karbi bayansu Dad da Babbah ka sanar musu kada su bi ta Aneyam nzki road,
Ka tabbatarda Basu bi hanyar ba yi sauri, yi sauri…

Abdul na Jin Hakan da Kuma ganin yanda Jamaal din yake a zafafe ya sakashi fadawa motar Hafiz ma ya fada suka bi bayan su Haroon din da mugun gudun gaske.

Shikuwa Kai tsaye harabar gidan ya shiga daidai fitowan Ameenatou din zata bawa Hafiz agogonsa Daya manta gurin sauri cikin mahaukacin navy blue tsadaddiyar lace din Daya fidda kayanta da kuruciyarta akansa idanuwanta akansa suka sauka ta tsaya cak daga inda take tana masa kallan Daya Sakasa qin kallan fuskanta bare gane kamanninta.

Takowa tafara yi ahankali tana nufosa cikin sanyin da duka jikinta kawai taji yayi hakama kirjinta nauyi yayi mata take me tsananin.

Gap take da isowa gurinsa wayar hannunta tayi ringing daidai Nan tasa wayar Shima tayi ringing itace ta fara daukan tata tareda kaiwa kunnenta tareda tsayawa cak daga inda take.

Daga nasa Kiran yayi da siddeeq yayi masa sedai baima gama Jin Abinda yafara fada masa ba Ameenatou ta Yanke jiki ta zube a jikinsa kaman matacciya Shima Neman zubewan yakeyi siddeeq daya iso bakin gate din gidan a haukace sbd mummunan tashin hankalin da baa Saka masa Rana ba ya shigo da mugun gudu.ya taresu gaba dayansu.
##MAMUH#*_AMEENATOUH_*
_Mamuhgee_
#Arewabook@Mamuhgee
#ZafadaBiyar

 

56
A jikin Jamaal gaba Dayanta Ameenatou din ta zube Dan haka baida zabin Daya wuce riqeta da hannuwansa Shima nasa kafafun na gagararsa daukansa.

Siddeeq da idanuwansa ke rikice da wani mugun ja riqesa Shima yayi Yana Kasa kallan fuskarsa data fara gaba Daya.

Umman fadila ce tareda anti zulaihat cikin mutanen dadah da suka taho daga Nasarawa biki ne suka fito daukan kaya a harabar gidan suka tarar da wanna tashin hankalin da sauri siddeeq yace umman tazo ta dauke Ameenatou daga jikin Jamaal din.

Da sauri suka qaraso tare umman ta tattaro Ameenatou din daga jikinsa tana tambayar lafiya a rude Tana raba idanuwa a tsakanin Ameenatou din da Jamaal da Kuma siddeeq din.

Siddeeq Bai iya cewa komai bayan cewan suyi ciki da Ameenatou din shikuma ya kama Jamaal Wanda har lokacin kaman jiri yake Gani suka fito daga harabar gidan Kai tsaye motar da Jamaal din yazo da ita suka nufa shi siddeeq din yabar wadda yazo da ita a gurin.

Saida ya zaunar da Jamaal din a mota kafin ya zagaya da sauri ya shiga motar zai tayar Jamaal ya dago jajayen idanuwansa ya kallesa daqyar ya iya Bude Baki yace

“Bani key ni zanje na dubo Kai ka Jira anan din Sbd A,dole Ina buqatan barin wani anan din incase.

Siddeeq kallansa yayi da nasa jajayen idanuwan Shima Yana girgiza Kai sbd bazai iya barinsa yayi tuqi ba a lokacin da kansa.

Bude motar Jamaal yayi tareda fitowa ya zagayo ko gabansa Baya Gani dakyau wani irin wuta da radadin azabar nauyi yake ji a kirjinsa Babu abinda yakeso kaman ganinsa gurin da ake maganar.

Karban key din yayi Bai tsaya komaiba ya fada motar Yana rufewa ya tayar Kai tsaye yayi mata wani irin mugun ja yabar gurin siddeeq na bin bayan motar da kallo hankalinsa na mummunan sake tashi sbd kaman zata tashi sama tsaban mugun gudun da Jamaal din keyi.

Jamaal na barin gurin yayi cikin harabar gidan Yana fiddo wayarsa aljihu Yana rasa a cikin wainda suka tafin waye zai kira tinda Babu me lafiyan dauka Kila.

Jamaal kuwa tuqin yakeyi idanuwansa na Neman rufewa Amma karfin hali Dana zuciyarsa Basu bar hakanba Saida ya hau titin da zai Kaisa Aneyam nzki road Wanda yake kaman bypass Babu mutune sosai.

Yana Jin Nisa sosai a kan titin
Tin daga nesa yafara hango mutane da Jamaan tsaro sun rufe titin hakama hadda masu daukan hotuna da wata katuwar mota a gurin datake kokarin kamawa da wuta anata ihu da hayaniya.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected