AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE
Daman ba wani zama zasuyi a Poland dinba Nigeria zasu taho sbd bikin auren Da Haroon din kwata kwata yaji Baya son a dauko lokaci ayi kawai ya tahowansa kusada mahaifiyansa Dan haka sauki kawai sukeson ya Dan samu su taho saiga Kiran siddeeq Wanda ya sakashi shiga fargaba da tsoron abinda Jamaal yaji Dan haka shine ya dagawa mum hankalin komawansa baima jirata ba washe garin ranar ya Siya ticket dinsa ya tahowansa Dan bayason abinda zai janyo fushin Jamaal ya lalata masa komai adaidai lokacinda ake gap da samun abinda yakeso.
Jamaal kuwa a ranar Bai kwana a Lagos ba ya wuce Abuja tareda siddeeq ko su Dad din Basu saniba Dan idan Yana ganinsu zuciyarsa kasa riqe koshi waye din takeyi gwara ya tafi ya Jira zuwan Haroon Daya San duk inda yake idan har baida gaskia Yana hanyar dawowa.
Kwana Daya saiga Haroon din ya diro Amma Bai yadda ya Hadu da Jamaal din ba Kai tsaye Nasarawa ya wuce sbd bayason suyi hayaniya Kuma baisan Menene yaji bama tukuna bare yasan ta inda zai fara.
Da yamma sosai ya iso Dan haka wanka da sallah kawai yayi Bai tsaye komaiba ya wuce gidan Babbah.
Zaune suke a tsakar gidan sai lallabata dadah keyi sbd taqi Shan magani daga ciwon Kai zazzabi ya maqale kwana biyu anata fama da ita.
Zuwansa ya Saka Abdul sakin ajiyan zuciya hakama Hafiz Babbah Baya Nan
cikin sakewan fuska da nutsuwa ya qaraso Hafiz na janyo masa kujeran zama Yana masa barka da zuwa.
Yaya Abdul ya fara bawa hannu suka gaisa cikin tsananin kulawa Yana tambayarsa kwana biyu ko numbernta Baya shiga.
Murmushi ya sake Yana cewa aikin dayake gabansa ne ya sakashi kashe dukkanin wayoyinsa sbd aikin ya koma babba fiyeda yanda suke tsammani.
Gurin dadah ya Maida kallansa Yana gaidata cikeda girmamawa da kulawa kafin idanuwansa suka koma kan Ameenatoun Dake zaune sanye da Riga da wando na bacci ko hula Babu a kanta ko inda yake Bata juyo ta kalla ba maganinta take kokarin Sha tana kasawa sbd batason magani ko kadan.
Hafiz Dayafi kowa shiga damuwan bayan Ameenatou tambayarsa siddeeq yayi suna sake shiga wata firar Amma gaba Daya hankalinsa na kan Ameenatou da yayi magana tayi masa shiru kaman Bata ji ba Kuma kowa yasan ta jisa Daman sun San sai anyi Hakan.
Dadah ce ta Dan rarrasheta tana cewa
“Budurwa bakiji ana Miki ya jiki bane?
Duka fushin bana rashin kiransa da zuwan bane gashinan ai ya taho saiki sauko,
Yi masa hakuri kinji¿
Maganin ta daga duka ta Saka a bakinta tareda binsa da ruwa ta shanye batareda ma tasan tayi Hakan ba sbd fushin Daya taso mata.
Tinda ta fara zazzabin ko ruwa Se ta Saka anbata ko hulan kanta Bata iya sakawa sai an Saka mata sai gashi ta miqe tsaye da kanta ta wuce dakinta tana cewa bacci zatayi.
Hafiz ne ya Bude Baki yace
“Ke meye haka wai?
Inace Wanda ake fushi da ciwon akansa gashinan yazo,Kuma Ashe Zaki iya tashi da kanki kika ringa wahalar Dani da Dadah tin jiya ko bacci na fara saita kirani na kawo mata ruwa Ashe tsaban rashin tausayi ne to Zaki San dawa kikai.”
Tana jinsa Bata ce komaiba saima hararan kofar datai tana Jin zafin abinda yayi mata ranar Yana dawo mata.
Dadah murmushi ta sake tana sake tambayarsa nasa jikin ya amsa mata sbd yasan halin mutuniyar sarai basai an tsaya basa hakurin abinda tayin ba,
Abdul ma sake tambayar jikin da aikinsa yayi kafin suka fada firar tafiyansa Lagos gobe zuwa nxt week Kuma su dadah ma zasu taho duk da ba zuwan kenan ba zadai suje suga inda Allah ya Kaisa dasu.
Duk firar dayaketa yi hankalinsa na kan kofan dakinta Amma Sam taqi yadda ko motsi tayi yaji dadi Bare fitowa.
Sallan magrib suka fita sukayo suka dawo gidan tareda Babbah daya masa ya jikin da fadan rashin Kiran tinda koyayane Daya samu ko mintina bibbiyu a wuni ya ware ya kira din zasuji dadi itama me fushin da bataiba.
Gashi tanata fushi da maimaita shariyan dayayi mata.
Hakuri ya bawa Babbah har suka shiga wata firar inda Babbah din ya sanar masa su Alh Lameenu sun kira akan maganar auren sukeson ta taso ayita kusa tinda dai ba amfanin jiran ko tsaiko.
Har cikin ransa yaji farin ciki Yana mamayesa sedai Kuma fushin da Ameenatou keyi me zafi akansa Yana cin zuciyarsa sbd yasan Jamaal ne yayi mata koma Menene Dan haka Shima take yaji Yana buqatan ganinsa Dan haka anan yayi sallar ishai yaci abinci suna gamawa harya fito Bata fito a dakinba Kuma babbah ya Hana kowa takurata fitowa saita huce da kanta taji ta hakura tukuna.
Yana fitowa da wayar hannunsa ya kira layinsa dayake hannun jamaal Amma Jamaal din yaqi dauka sbd Shima Yana sane da Haroon din ya dawo guje masa yayi.
Kiran dayake yi Jamaal yaqi dagawa ya Sakasa dawowa hayyacinsa akan abinda yake jiransa Dan haka dole ya shirya tinda safe ya nufi Abuja.
Koda ya Isa Jamaal din Yana bacci Dan haka siddeeq na ganinsa ya saki murmushi Mai hade da sakewa Yana masa barka da dawowa.
Kallan hanyar stairs na Hawa sama yayi kafin ya dawo da kallansa kan siddeeq din fuskansa a sake Shima Yana amsawa ya ajiye keys din hannunsa da wayarsa Daya ya nufi dining da aka cikesa tsaf da breakfast din Jamaal din ko zama baiyiba Yana Isa dining din Jamaal ya sauko daga saman sanyeda silk pyjamas farare Kal sai slippers dinsa masu shegen tsada da taushi a qafa kallo Daya yayiwa Haroon ya matse fuskansa datake sheqi kaman ba bacci ya taso ba Yana qarasowa ko zama beyiba Haroon ma ya Dan matse tasa sbd kada Jamaal din yayi masa fada a gaban siddeeq yace
“Meyasa nake Kiran wayanka baka dagawa tin jiya fa da daddare bayan isowana?”
Sai alokacin Jamaal ya juyo ya kallesa da idanuwansa da suka Sakasa Jin kunyar Dan uwan nasa na Abinda ya boye masa duk da haryanxu Yana shakkar idan gaskiyar abinda su Dad keyi ne yaji sbd da bazai zauna haka calm ba.
Ciki muryan dayake kokarin danne bacin ransa yace
“Ka taho ne sbd ban dauka Kiran ba kokuwa sbd kana son sanin abinda na sani gameda ainihin abinda kuke aikatawa a boye?”
Maganar tasa ta Saka Haroon kallansa Yana cewa
“A boye Kuma?
Me kenan??
Me kaji?
Kuma daga bakin wa?
“Daga bakin manyanka,Amma koma Menene baka buqatan sani
kaman yanda ka iya boye sirrinsu bana son sanin komai daga bakinka Amma dai ka fada musu taba Dad jeden shine babban Barna da kuskuren da zasu tafka sbd jinin wani karfi ne dashi baa zubar dashi a sake zama lafiya,
Wannan shawara ce da zaka sanar da daddies Dinka.”
Yana fadar Hakan ya taba sa ya wuce zuwa dining din sbd yin breakfast.
Kasa motsawa Haroon yayi sbd Baisan me zai fada ba.
Yana gurin tsaye Jamaal ya gama breakfast dinsa ya koma sama yayi wanka ya shirya ya fito a shirye qamshinsa na cika iskar gidan ya fice shida siddeeq sbd sosai yake aikin dayake gabansa Dan kasar gaba Daya Jin yayi fita ransa tafiyansa yakeson yi batareda yabar Haroon din ba Koda me zaayi kuwa,
Aikin kawai yake son gamawa ayi auren su tafi Babu ranar dawowa.
A gidan suka bar Haroon yanata sakawa da kuncewa har sai dare suka shigowa gidan ya fice Dan a matse yake dayake ya duba Ameenatou tinda yanzu Kam baida aikin yi bayan zama guri Daya harsai jamaal ya dawo.
Yauma kwata kwata Bata saukoba duk rarrashinta da duka gidan suka taru sunai mata haka ya gama ya koma Amma dai gwara yau din ta zauna Bata shige dakinta ba.
********Jamaal gaba Daya Jin yakeyi kaman ana konasa aqasar Dan haka ya toshe dukkanin hanyar da zata Bata lokacinsa akan abinda ya kawosa ya dukufa sosai akan aikin Wanda tini ya dauki hanyar kammaluwa sbd sosai ake Aiko na masu zallan ilimi gadan gadan ba wasa ba shirme.