AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE
Dad Lameenu Bai gama Jin karshen zancen ba wata mummunan zufa ta tsinke masa Yana cewa
“What???
Yaushe wannan babban balain ya samu??
Ina Haroon din yake yanzu??
Mam na Jin Hakan ya ajiye wayar hannunsa Daya karanta wani article da aka rubuta gameda rushewan da SEELAHs keyi a boye batareda sun bari duniya ta saniba.
Ajiye wayar yayi Yana Dan rintse idanuwansa da suka fara sauyawa Dan kuwa Yana fatan ba abinda zuciyarsa ke Saka masa bane zaiji daga Lameenun.
Cikin tashin hankali lameenu ya buqaci ganin BB yanzu yanzu Dan zuciyarsa bugawa zatai idan Yana sauraron wannan mummunan tashin hankalin ta waya.
Kashe wayar yayi Yana kasa kallan Mam da shima ya kasa tambayar Lameenun komai BB din yake Jira yaji komai Dalla dalla daga bakinsa.
Kafin BB ya iso daga Mam har lameenu da jininsa ya Dade da Hawa Dan tini aka kirawo likita Yana cikin auna BP dinsa BB ya iso take ya sallami likitan akan saisun gama magana.
iPad din hannun BB ya fara kamo hotunansu Hafiz da Yan gidan kaf ya ajiye ipad din gabansu bayan ya kamo hoton Ameenatou datake sanye cikin hijab dinta na islamiya tana murmushi asalin kyanta da kuruciyarta a bayyane tana kallan gefe Dan kuwa batasan ana daukanta hoton bama.
Bayani Daya bayan Daya a tsanake BB yafara jerowa Wanda yayi mugun girgiza su musamman Mam Dan kuwa Bai taba tinanin Shima Haroon zai fada irin kaddarar Dan uwansa ba ta yiwa mace son da Bai kamata ba adaidai lokacinda suke buqatan nutsuwansa da hankalinsa tareda sadaukarwansa fiyeda komai a duniya yanzu.
Ameenatou dukkaninsu suka zubawa idanuwansu da sukai jajir,
Tayaya Haroon zai bari zuciyarsa ta mutu akan mace bayan yasan Menene a gabansu,
Tayaya Haroon zai bari mace ta shiga zuciyarsa,
Tayaya zasu iya samun yanda suke so daga zuciyar Daya mutu akan mace.
Kenan shi tasa mummunan kaddarar akan matan da yayansa suke so ne ko me?
Shima Haroon macen ce zata shiga tsakaninsa da ita?
Ta Ina zai fara karban wannan kaddarar ta Haroon bayan haryanxu Bai fito daga baqin ciki da radadin ta Jamaal ba.
Wani nauyi kirjinsa yayi Yana tafasa da wani irin zafi da radadin da baisan mezaiyiba akan Haroon din Daya kashesu da ransu a Rana tsaka.
Lameenu da tini jininsa ya sake hayewa akan babban tashin hankalin da Basu Saka masa Rana ba da sauri aka sake dawo da likita.
Da sauri likita ya dawo Yana cewa a kwantar masa dashi flat.
Mam tsaban tafasa da qunan da zuciyarsa keyi Jin yayi Haroon baida sauran amfani a garesa ko kadan Dan haka take ya Bada umarnin a Siya masa ticket a ranar zashi Nasarawan.
Lameenu na Jin Hakan yaso wartsakewa su tafi Amma Ina hawan jinin ya sharbesa da kyau Dan haka Yana ji Yana Gani Mam din ya tafi.
##MAMUH#
#DR JEEY
#AMEENATOU
#MAM SEELAH
#BABBAH
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al’ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
37
Motoci ne na alfamar guda biyu harda securities suka dauko Alh Mam seelah daga airport.
Wayarsa Dake gefensa ya dauka tareda kasheta gabaki dayanta Dan kuwa Baya buqatan Kiran kowa sbd har lokacin zuciyarsa a cikin wani matsanancin zafi da radadin take Mai tsanani.
Daga Haroon har sauran ma’aikatansu manya da abokan huldan Babu Wanda yasan da zuwansa a ranar Kuma aaukan dare sukai Dan haka Kai tsaye masaukinsa Dake cikin Abuja aka nufa dashi Saida safe zai fuskanci Haroon, Haroon dinma ya fuskacesa.
Bayan samun nutsuwa da komai cikin Daren kasa tintsawa yayi ya shiga tinani masu zurfi da sakawa da warwaran ta Ina zai bullowa wannan masifu haka wani bayan wani,
Idan har Haroon na son wannan yarinyar sosai Yana buqatan sauya ha yar handling na abubuwan ta wata hanyar ba irin hanyar dayayi ta farko ba ta rabasa da Jamaal a daidai lokacin dayafi buqatansa da sonsa a kusa fiyeda komai dayake buqata a duniya Dan ko dukiyar Omar da sukeso idan basuda tasu dukiyar tayaya zasu karbeta?
Dole Yana buqatan sauya takun kammala komai cikin hanya mafi sanyi da karfin gaske Amma kwata kwata Babu maganar yabar Haroon yin auren wannan auren a yanzu Dan baima gama zama me amfanin dasuke buqatan ya zama ba ya moru bare idan yayi auren gaba Daya qarasa zama mara amfanin zeyi Kuma sai yanda mace tayi dashi Wanda baqin cikin haka zai iya sakashi yafesa ko illatasa Dan haka bazai taba barin ayi Hakan ba a yanzu saiyaga sauyin Haroon din.
****Har washe gari Haroon Baya cikin cikakkiyar lafiyan hankalinsa Dan shock da tsoron da zuciyarsa take ciki tareda mummunan firgici da tashin hankali ya Hanasa dawowa daidai duk da maganin Daya kwana Yana Sha a cikinsa Wanda harya wuce kaidarsa.
Ya boye kansa bayan siddeeq Babu Wanda yake iya ganinsa duk da ma’aikatansu da yawa dakeson ganinsa da masu zuwa da masu bugo waya duk ya kasa ganin kowa sbd state din dayake ciki bamai dubuwa bane hakama siddeeq din kansa duk ya dage sosai da kokarin hada mafitar gagurumar matsalar shiyasa Shima kansa Baya guri Daya.
Duk daqiqa Daya Dake wucewa sai Haroon ya Tina mahaifinsa da abinda zai iya biyo bayan wannan mummunan aikin kaddarar Daya samesa Dan haka hankalinsa ke sake tashi.
Tinda safe ya samu labarin Dad dinsa na Abuja daga bakin siddeeq Dan haka cikin sabon rikicewa duk da halin dayake ciki ya shirya ya fita aiki Dan Neman mafita koman kankantarta akan aikin kafin Dad ya iso Nasarawan.
Hafiz da siddeeq ganin Halinda yake ciki yana aiki gaba Daya cikin ficewa hayyacinsa riqesa sukai tareda zaunar dashi sai a lokacin idanuwansa suka ciko da wasu irin hawaye masu radadin gaske.
Kallan Hafiz siddeeq yayi tareda cewa ya tafi aikinsa kawai inshallah zaa samu mafita.
Dayake duk ma’aikatansu manya da wainda sukeda kusanci sosai irin Hafiz sunsan ansamu gagarumar matsala Amma bayansu Babu Wanda ya sani shiyasa Hafiz yake cikin damuwa sosai na ganin Halinda Haroon ya shiga akan Hakan.
Kasa aikin yayi ya taho gida Shima bayan siddeeq ya sauke Haroon din sunbar site gaba Daya Dan ciwonsa Daya tashi gadan gadan a gurin tin kafin kowa ya fahimci wani abu ko a gane musamman Hafiz da bazasu so yagani ko ya san ciwon Haroon din ba.
Yana Isa gida jikinsa duk a mace zuciyarsa ba dadi,
Bai boyewa su Babbah ba ya sanar dashi damuwa me tsananin da Haroon yake ciki take Babbah ya daga wayarsa ya Saka Kiran Haroon din Dan basa kwarin gwiwa da adduar samun mafita da nasara a duk inda take Amma wayar Haroon din a kashe Bata shiga kwata kwata.
Ameenatou ma Kiran nasa ta Saka kaman zatai kuka Jin halinda yake ciki Amma kayinsa Baya shiga kwata kwata.
Yaya Abdul ma ya gwada Kiran da tasa wayar duk dai Bata shiga.
Dadah da tashiga damuwar itama kallan Abdul tayi bayan sunkai har kusan rana Ana kiransa baa samu tace
“Bara na sauke abinci saina hada masa nasa kwando ka Kai masa saika dubo mana lafiyar tasa tinda Kiran ya kasa samuwa”
Ameenatou na Jin Hakan ta marairaice fuska akan zata bisa
Dadah ta girgiza mata Kai tana cewa